mu mu uku tahaifa??? Muktar yaagyada masa kai alamar ah
Malam yafito yace suzo ciki dadyn su yana kira tare suka mike suka shiga ciki
Sunan muktar kawai yake kira Amman idanuwansa arufe suke"" muktar ne yakarasa inda yake yariko hannunsa daya yace ganinan Abba
Muhammad yatattaba hannunsa batareda yabude idonba sannan yasaukarda ajiyar zuciya yacigaba da barcinsa.
Muktar waje yasamu yazauna batareda yacire hannun nasaba"" sai kallon mahaifinsa yake yasan bashida laifi bekamata yarikajin haushin mahaifinsaba .
.
Anafara kira dakyar yasamu yacire hannunsa daga rikonda yayimasa yawuce masallaci
Muhammad sai goshin Magrib yafarka har lokacin muktar yana kusa dashi yakuramasa ido nantake idanuwansa suka kawo kwalla yabuda bakinsa dayayi masa nauyi yace muktar kayi ha kafin yakarasa muktar yarufe masa Baki yana girgiza masa kai
Abba mekamun dazakabani hakuri wannan nasan ba laifinka bane koma kanada laifi baici kabani hakuriba saboda Kaine kahaifeni nine yadace nabaka hakuri hawaye suka sauko akan fuskar muktar
Muhammad yarike hannunsa gam yace kadaina kukan nan Dana bakayimun komaiba nine mai laifi asanadina gashi kunrasa mahaifiyarku
Ah ah Abba bakaine kayi sanadin rasuwartaba"" kuma dama lokacintane yayi koda hakan baifaruba dayanxun bata duniya danhaka karka dorawa kanka laifi kayi hakuri Abba kaga bakada lafiya kasamu natsuwa tukun
Kai yagyamasa sannan yarufe idonsa ranar dai muktar asiviti yakwana sai washe gari aka sallameshi suka koma gida"
..
Karfe shadaya koda tabuga khadija sun iso Dan tunda dare tadami Usman kamar tayi kuka gabadayan su sukaje "" khadija tasoma shiga tareda labila sukaci karo da muktar xaifito ta witsiyar ido yake kallon tauraruwar tashi'
..yace badai harkunzoba?? Khadija ah mana nidanaso muzo tunjiya
Toyanzun ina kika baro dadyn?? Tace yana waje tayi maganar tanajan hannun labila suka shiga gidan Zahara u tana biye dasu
.
Tsakar gidan tasamu su inna Muhammad yana kwance faruq yana masa fita matarsa tana zaune gefe daya""
Yana ganinta yatashi zaune yana murza ido wannan kamar fateemar sa saidai wannan tafita yarinta bakinsa dauke yake da magana
tagaidashi dajiki da itah da labila da zaharau ya amsa shiduk mamaki yakamashi hatta muryan iri dayane
Khadija takarasa wajen faruq danbasai anfada mataba tasan shine tagaidashi cikin murmushi tamkar damacen sunsan junansu
Ya amsa shima da murmushin afuskarsa"" yace Ina yaran suke?? Taciro masa anwar dayake bayanta tace ga sunan ahannunsu tayi nuni da labila yakarbi anwar
Yace barakalla yasunan wannan??? Tace anwar wannan sapna wannan husna"
Daidai shigowar su muktar da Usman da kaleed suna biye dashi
Suka gaidashi ya amsa sukamai yajiki yace dasauki"" malam ne yafito daki tareda wata tabarmar yashinfida masu suka zauna
Duk suka gaidashi ya amsa shirune yadan biyo bayan gaisuwar sannan malam yayi gyaran murya yace Muhammad ga khadija khadija ga mahaifinki
Dan naSan kece kawai bakisan shiba ko ahoto yakalli Muhammad yace kaima nasan bakasan dacikinta marigayiya tabaro garinkuba
Koda tazo cikin watansa uku tasha wahala batada aiki saikuka duk da taki tasanar damu abunda yake sakataa kuka harcikinta yatsufa ranar da tahaifeta ranar takoma wajen mahaliccinta
Yanisa wannan shine mijinta wadan nan kuma yarantane biyu basa nan"" suna makaranta""
Muhammad yadago idanuwansa dasuka sauya kala yace
Kuyi hakuri banada bakinda zan iyah Baku hakuri naso ace nariski fateema Dan Na nemi gafarar ta wlh malam babu abunda yafaru cikin hankalina
Ranarda abun yafaru nayi tafiya lafiya qalau muka rabu itakuma rukayya batanan tacemun zataraka kawarta garinsu wajen buki
Hardakudi nabata Ashe bansaniba tafiyarda za arusa gida nane akai dataimakona tunda nabata kudi dakudina aka nemo mun magani
Taje wajen bokanta tasanardashi damuwarta akabata mangwaro tabaiwa fateema
Tana dawowa abunka damaiciki anabata tahau ci batayi bisimillaba harda muktar yaci dayace tasammasa
Tunda naduro garin naji zuciyata tayi zafi ko kofar dakinta ban kallaba sanda nashiga
Aisha ✍🏼
☠ *HATSABIBIN BOKA..*☠
PART 2⃣
36
By gentle
Lady💃🏽
Washe garima haka sainadinga wasar buya Dan banason ganinta watarana ina wajen aiki naji kawai raina yabaci kuma babu Wanda yabatan rai.
Sainaji kamar anaturani gida
Nabaro wajen aiki dasauri zuwa gida ina shiga kaitsaye dakinta nashiga tana zaune hartadauka nahucene duk da itah Batasan tayimun laifiba..
Kawai nahauta da duka kamar zan kasheta tunda nake bantaba dukan maceba wandama yake dukan matarsa kallon jahili nakemasa
Saigashi wai dakaina nadaki matata wacce nakeso fiye dakomai aduniya "" sanadin hakan cikinda yake jikinta yabare inaganinta cikin jinie Amman zuciyata tagama bushewa natsallaketa nabarta kwance yaronta sai kuka yake..
Bansan wayakaita asibiti ba danbansake wai wayartaba saidarenda Allah yakaddaro darabon za asamu wannan yarinyar.. Yayi shiru daga bisani yacigaba nayan shudewar watanni tasameni dakina muna zaune da rukayya take sanardani batajin dadi zataje asibiti
Nikuma nace bazataba daga tacemun dame zataji da wulakancinda nake mata koda ciwo kamar jiraye nake da ita nace nasaketa
Tanemi tayi idda dakinta tunda saki biyune"" kawai sainace mata tatafi Na iyar kuma nace tabarmun gida alokacin karfe dayan dare
Haka tafita nadauko muktar naturashi waje narufe gida bansan yanda suka karkareba
Tunda taga wannan aikin yayi saitakoma takarbo na mallaka""
Tamallake gidan tazama miji nikuma nazama mata"" nine dafa abinci nine wanke wanke shara wanki kai hatta gyaran dakinta ninakeyi ""
Haryakai tana karbo kayan kannenta ina wankewa" nakoma injin wanki dakarfi dayaji"" Dan zalunci dagas take girki Amman saitace wai abincin murhu yafi dadi tasani siyo itace nakoma Dan daudu
Cikin wata daya nazabge yan uwana duk wacce tazo gidan saitayi mata fata fata kuma tasa nayimasu iyaka dagidana kuma babu yanda zanyi saina korasu
Gabadaya kowa yadaina zuwa gidan har kana nan yara
Aikina tuni nadaina zuwa"" " natare agida itakuma saiyawo kamar wacce taci kafar zomo
Kai in takaice maku labari sallah zuwa masallaci ya gagareni dankuwa kayan jikina kamar na mahaukaci gefen wandona tattasai gaban rigata bakin tukunya gefen fuskata markaden kayan miya Duk yanda nabata jikina saita hanani yin wanka koma nayi wankan saidai namiyarda wadanda nacire hartakai ina kyankyamin kaina dakaina """
Ahakan aketa tafiya aboka naina dasukaga nadaina fita aiki sukazo hargida danjin ba asi tana barci sukaxo nafita kofar gida muna magana Ashe tafarka
Ta dauko ruwan wanke wanke masu daddagin tuwo damiya bamusan meke faruwaba saidai mukaji saukar ruwan ajikinmu duk Tajika abokaina sannan tazuba masu kwandon rashin mutunci Wanda kokare akaiwa wannan saiyaji badadi ballanata mutum sukuma tundaga ranar suka Dauke kafarsu dagidana.
Alokacin nagammace mutuwa da rayuwa yanda kasan Dan fursuna ni inaganima yafini danshi yanada yanci kuma zaici yakoshi nikumafa
Shekaru sunja abubuwa duk sunfaru alokacin taga haukar banza take duk tsayin shekarun nan tasan kulba Dade muktar zaidawo sannan ga faruq kenan sune zasucinye dukiyar Muhammad" aduk abunda nayi yatashi abanza Kenan
Saitaje wajen kawarta tasake fadamata damuwarta" suka sake rankayawa wajen bokansu tasanar dashi itafa haihuwa take so kota halin kaka
*hatsabibin boka* yace aitunfarko itah tayi garaje aidayanzu tayi biyar yabata maganie yace tasa inhar tasha komai yayi daidai sukayi godiya tadawo gida tanawani kankanba ita gamaiciki
Bayanshudewar watanni uku saitafara rashin lafiya tanata amai takirah kawarta sukaje asiviti akatabbatar mata tanada ciki saimurna tacewa kawarta waidatasani Aida tun shekarun baya tasanardashi matsalarta Dan itah haihuwar tafiye mata komai
Sanda tadawo tasanar dani kokadan banji dadiba banyi murnaba aikuwa tahau bala I waisanda fateema tanada ciki rawar kafa naitayi akanta wato Fateema kawaice ta iyah haihuwa tonima nayi cikin danhaka duk abunda kasan kayiwa fateema nima haka zakayimun danni Yaya biyu zanhaifa kuma duk maza
Nakalleta da murmushi nace cikin watannine dake taya zakisan abunda yake ciki macene ko namiji bakisaniba Dan babu wanda yasan gaibu face Allah
Tace tonidai nafadamaka Yaya biyu zanhaifa kuma maza danhaka komai nakeso kaine zakamun hatta wanka yanisa tundaga ranar nahau bauta tayi amai inkwashe kazanta Kuwa ko mai tsohuwar hauka ya sallama mata
.
Idan mace tanada ciki kunsan babu wanda yakaita son tasauke abunda ke cikin nata tahuta
Amman wlh alokacin nafi rukayya son tahaife cikinta kozan sarara kullum cikin lisafi nakeyi sainaga kamar ana karawa yini tsayi darekuma dazaran Nashinfida kafaduna zakaji takwalamun kira yiwannan yiwannan.
A haka akaita gurgurawa harcikin yadan taso tarage amaye a maye sai shegen kwadayi kamar kura
Indai fannin kayan kwalama kudama zasu sallama mata
Tasha wuya nima nasha wuya cikinta yana wata biyar tasoma zuwa awo saidai an tabbatar mata batada isasshen jinie danhaka tarikacin kayanda suke Karin Jinie kafin lokacin haihuwarta
Haka nayita siyen kayan Karin jinie Amman kullum tsamurewa takeyi ahakadai harcikin ya isah haihuwa ranarda tasoma nakuda da darene narasa yazanyi Dan tayi fada damakota bata shiri dayan uwana
Towaye xankirah ya taimaka mana??? Tasha wahala sosai naje makotanmu kozansamu mai taimakona duk inda nabuga kofa maigida idan yafito nafadamashi taimakonda nake nema saiya mere baki danharsu rukayya bata raga masuba
Mutum dayane nasamu yayarda yaje tado matarsa itakuma tace rukayya tayimata rashin mutunci idan maye yamanta ai uwarda bazata mantaba degiya bikice kowayayi Dan amayarmasa.. To itah batayi abunda za a miyar mataba dama irin wannan ranar suke jirah itama tadandanie abunda kowace uwa take dandana""
Illai kuwa rukayya takusa leka barzahu danko nishin kirki tadai[truncated by WhatsApp]
☠ *HATSABIBIN BOKA!!.*☠
PART 2⃣
37
By gentle
Lady💃🏽
Saida haske yasoma fitowa nafita nasamu Dan adaidaita mukaje dataimakonsa nasakata adaidaitar tashi mukaje hospital aikuwa nasha fadan likitoci
Dancewa sukai bama zasu taba taba sukabarni babu kalar magiyarda banyiba sukace wannan saurace mezasuyi mata
Bayan sunbar wajen dakamar mintuna biyar saiga nurse din tadawo dasauri tanata bani hakuri sannan takaita dakin haihuwa
Nikam nagama fiddarai da rukayya saikusan shabiyu tahaihu yaro namiji Khalkyawa gashi jajir dashi kamar kakwanta jini yafito
Dakin Hutu aka Kaita dantahuta saida aka karamata jinie da ruwa"" Nina dauka rukayya zatayi sanyi tunda tawahala Amman tana tashi tahau masifa waisonayi tamutu to ta Allah batamuba dagani har makotan unguwarmu saitayimana wankin babban bargo
Takumayi dankuwa bargon ma saiya tausaya mana yanda mukai yaushi makotanmu saigashi suna barin unguwar suna komawa wata
Darana zaman gidanka ya gagareka dadarema haka wadanda suka tsira daga tsafinta Kali lanne wato wani Abu danagane talaka idan yana addua sautari zakqsameshi kamili yana yawan azkar
Amman abunda zaibaka haushi dazaran budi yamasa yawa sai hidindimun aiki susha masa kai kullum buxy yake bayasamun damar tsayawa yayi azkar
Shizaisa dazaran anyi masa aiki suduf zaikamashi abokanan kasuwancinsa wadanda sukejin haushi idan Allah ya daukakashi ko matarsa
Yadace lokacinda kasamu budi saikasake dagewa kafidama saikaga Allah yakareka dakai da dukiyarka
Nikaina nasan nayi sakaci da addua danbakoyaushe nakeyiba shiyasa rukayya da bokanta sukasameni aruwan sanyi
Rukayya kam saifariya ake anhaifi kyakkyawa saitacemun dani yabiyo datayi kuka Amman yanxu bakinciki nakeyi da yaronta aikoba komai tafi fateema iyah haihuwa
Dan yaronta yafi Na fateema kyau saidai bakinciki yakasheni Amman yaronta saiyayi arxiki danyanada jarinsa wato kyau
Auren jari zaiyi Dan bazai auri Yar talakawaba komai kyanta "" habaicikam nashashi yafi cikon kando datazauna maganar kenan ranarsuna banda kawarta babu Wanda yazo dagama harcewa tayi gayyar na ayya idan basuzoba sundauka haushi zanji dagadai ankarawa namansu auki
Ai ita karama dabasu zoba itah taradawa yaronta suna qaseem tanakiransa da maifarin jinie" tunsanda tahaihu maimakon tasamu lafiya saiciwo yacigaba dacinta duk sanda taje asiviti magana dayane batada jinie..
Kuma itah tasan tanacin abubuwanda suke karawa mutum jinie
Baxa a wuce sati biyu ba bata reda anyimata Karin jinie ba hakan yasa akayita yimata awo ko akwai ciwonda yake shan jinie ajikinta
Anyi awon kashi fitsari jininta Amman basuga wani ciwon ba alokacin rukayya tasoma sanyi
Abunda bamu saniba yaronda tahaifa aljanine babansa"" lokacin da taje Neman haihuwar hatsabibin boka yaturo mata wani aljanie acikin hadimansa
Shine yatara da itah tasamu ciki "" wannan yaron ba ruwan nononta yake tsotsaba jininta ne yakesha
Tun rukayya tanama iya daukarsa hartakasa karshe yayen karfi dayaji taimasa aikuwa ranar da ta yayeshin ya Aniya kuka
Bayajin rarrashi kwanansa biyu baici komaiba saiya mutu da rukayya tasan abunda tayi dabata aikata hakanba domin aljanin acikin yayansa bayason kowa kamar yanda yakeson wannan yaron
Lokacinda yamutu aljanin bayanan *hatsabibin boka* yaturasu aiki wani gari saibayan kwana uku da mutuwarsa yadawo alokacin har rukayya tasoma miyarda jikinta
Tana barci yafitomata acikin barcinta alokacin yagamasanin sanadin mutuwar dansa idanuwansa sunyi jajir saboda kukan dayayi
Tana ganinsa ta tsorata takata iska yaxama yasauka kusa da itah yashakureta" ta yita kakarin mutuwa Amman baikyaletaba saida tasuma
Yasake watsamata ruwa tafarfado tana nishi dakyar tabude baki tace kaiwaye mekuma naimaka dakakeson kasheni dariya yasheke da itah alokaci daya tareda kuka
Nawani lokaci cikin kakkausar murya yace nine uban danki"" wanda kika kashe saboda zalunci kinsan bazaki iyah bashi abincinda yakesoba meyasa kikaje Neman haihuwa
Kisani nine nasadu dake kikasamu ciki kuma yaronda kika Haifa ina sonsa sosai jinin jikinki shine abincinsa meyasa kika kashemun yaro???
Narantse dakarfin izzata nima sainayi sanadin mutuwarki kafin nakasheki saina ganamaki axaba kala goma shabiyu
Saikin koma tamkar dabba a idon kowa sainarabaki daduk wani abunda kikeso yanda nayi kuka kema saikinyi saikin gwammace dama hakura kikai yanda Allah yayoki dabakije Neman haihuwaba
Yanagama fadar haka yawatsa mata wani Abu ajiki takwamtsa ihu tatashi zunbur tana kallon jikinta gashi tahada zufa sai waige waige takeyi
Ta share zufa dafarko tamaida mafarkin wasa Amman saigaciwo yatasota gaba kuraje suka fitomata ajiki hannunta ya shanye da kafarta
Kai intakaice maku labari komai najikinta yasauya nayita kashe kudina a iska harkasar waje Amman basauki takira kawarta suje wajen *hatsabibin boka* kozai taimaka masu
Aljanin yasakasu demuwa suka kasa gane dajin ranarda suka dawo sukai hatsari kawarta tamutu gaban idonta
Kwanya tafito Amman alokacin itah bata sumaba sanadin ganin abunda yafaru da kawarta takwalla ihu tasuma saidai tafarfado taganta asibiti
Tayita kuka tana kiran sunana akatambayeta wayeni awajenta tace mijinta akanemeni danaje tana kuka tasanar Danie komai duk abunda tayiwa Fateema tace tasan alhakin fateema ne yakamata tana zamanta lafiya da Fateema Kawa tazugeta me akeyi dawani kawancen
Tanagama bani labari nabaro asivitin ko kallonta banyiba gidan Antyna naje nasamu faruq yanagidan da matarsa
Inakuka nashiga tana ganina tamike tana tambayar lafiya nace Anty ta cuceni tarabanie da matata da Yayana
Zaunar danie tayi tana cewa wacece kuma Muhammad cikin kuka nacemata rukayya nan nafadamata komai
Nace yauyau zanje kano naga matata tace nayi hakuri xuwa safe faruq ma yace zaizo yaga Dan uwansa da mahaifiyarsa
Saidai kafin safe ciwo yarikeni dakyar naga safiya tsaye aka kwana a kaina
Aisha ✍🏼
☠ *HATSABIBIN BOKA!!!*☠
PART 2⃣
38
By gentle
Lady💃🏽
Sanadin haka nasamu hawan jinie saida nayi sati uku anajinya sannan nasamu sauki likita yatabbatar mun zuciyata ta kunbura aguji yimun abunda zaibatamun rai sannan inrage Yawan tunani
Yanisa shekaran jiya ana sallamoni nace bazan sake kwana dayaba sainazo kano ganin natashi hankalina karciwona yatashi """
Suka yarda muka taso fatana daya naga fateema hawaye suka zubo masa yace Ashe banada rabon sake ganinki fateema Nina San nayi bankwana da jindadi da farinciki ""
Nasan shikenan babu wani sauran jindadi agareni"" kiyafemun nasan nacutarda rayuwarki gabadaya wajen yayi shiru bakajin komai saitashin kuka daga shi har su muktar
Labila ma kuka takeyi hartanajan ajiyar zuciya" " yanzun duk wannan abun da mamanta takeyi Ashe akwai mata masu irin wannan rayuwar
Sundade suna kuka sannan malam garba yayi gyaran murya yace Muhammad kadaina kukan nan kasan bakada lafiya yanisa koda mahaiifiyarsu takoma ga mahaliccinta batakoma dakai araiba
Dantasan komai nikaina bata sanardani abunda yafaru da itah acen ba saida tarihi yasake maimaita kansa yarka gatanan yanuna khadija itama tatsilge rijiya dabaya
Rashin sakaci da addua dakuma riko da Ibada shine yakareta dayanzu itama sai labari
Muhammad yadago yakalleshi yace itama haka akaimata??? Yagyada kai sosai kuma bokanda yayiwa mamanta shine yayimata
Anan yasake basu labarin komai"" faruq yajinjina kai yace waime yasaka irin wadan nan bokayen baza arika kashe suba
Aiwadan nan barinsu cikin al umma bala ine saboda annobane"" Usman yanisa yace taya kake ganin mai aiki da aljanu irin wannan za a iyah farautar ransa cikin sauki
Aganinka akwai Wanda zaishiga dajin yatsirah daransa??? Mutuminda ya gagari aljanu ballatana Kuma mu mutane
Baxance bazai farautuba Dan baifi karfin Allah ba Amman kafin mutum yaziyar ceshi saiya nemi addu oin tsarin jiki sannan kuma yakasance mai takawa
Gabadaya wajen shiru yayi kowa da abunda yake sakawa aransa bayan shudewar wasu lokuta Usman yamike yace shizai shiga wajen hajiya labila ma tamike tabishi
Bayan fitarsune Muhammad yagabatar masu da matar faruq sadiya"" anan yake tambayar muktar shibaiyi aureba???
Malam yayi murmushi yace baiyiba kuma gashi" yagirma baisan meyake jiraba muktar murmushi kawai yakeyi yana Sosa kai
Khadija ce tafadamasu ai kuwa malam yayi murna sukacigaba da tattaunawa"" ""
Tunda sukabar gidan labila batadaina kukaba sunashiga gidan hajiya ta ruga dakinta
Hajiyar tana zaune falo tabita dakallo sannan tamaida kallonta wajensu kaleed dasuka shigo bayanta tareda sallama ta amsa masu bakinta sake
Saman kujerah suka zauna suna gaida itah" ta amsa tana tambayarsu me akaiwa waccen kuma???
Usman yace mefa daga gidansu khadija muke kinsan mahaifinta yazo shine damukaje yake bamu labarin abunda akaiwa mahaifiyar ta shine tayita kuka nasan tatuna da mahaiifiyar tane.
Hajiya tanisa tace sai hakuri kunsan dole taji wani iri uwafa akace aibabu wani Dan kwarai dazaiso ace ga mahaifiyarsa ta aikata hakan
Allah yakyauta sukace Ameen" tayi shiru daga bisanie tace wainikuwa babangida yanzun tana ina???
.yanisa alamun rashin jindadi yace abun yayi tsamari Dan hauka takeyi bata wasaba
Amman nasa ankaita asivitin mahaukata dalilin labila kawai nake jin tausayin lubabatu Amman tayimun abunda " harna mutu bazantaba mantawa da abunba saidai inkauda idona kawai
Hajiya tace hakane Amman aikomai yawuce saimu kalli abunda yake gabanmu"" yace hakane hajiya ina hafiz??
Tagyara zamanta tace yanxun kuwa yabar gidan nan kasan anmiyarda matarsa gida haihuwa
Usman yakishingida akujera yace Niger zamuje jibi nasan bazai sameniba kifadamasa yashirya dawuri yasameni gobe kaduna dagacen zamuwuce
Hajiya tace ikon Allah zakuje gaida kakannin khadija ne??? Yana kallon kaleed yace ah ah maigidanki zamuje tsaida maganar auren sa
Inaso idan muktar yashirya ahade harna labila kozatasamu Dan kwanciyar hankali kar damuwa tayimata yawa kafin muga yanda ciwon mamanta zai kasance
Hajiya tace ikon Allah kace kishiya za ayimun ina zaman zamana tokai maigida haka akeyi ??. Kaleed murmushi kawai yayi
.
Hajiya tace dole kayi dariya Amman bakoai Nina San bayan daurin dankwali da shafe shafe baza agwadamun komaiba
Dariya suka sa gabadaya Usman yace ina dayan maigidan nakie??
Tace wai Abdul yana islamiyya"kasan yanzun harda sukeyi baicika zama gidaba
Yace aikuwaa ya dace yadage kafin yagama secondary yasauke dannasan dayaje Kasar waje zaiwatsarda karatun
Yasamu abunda yasamu Allah yataimaka """basuwani dadeba Usman yace shizaiwuce tare suka wuce akabar labila
Gidansu khadija suka koma yayimasu sallama sukafito nan yabar khadija suka koma kaleed dadi duk yakumeshi
Yamatsu suje yaga zainab dinsa yau kusan kwaana uku basuyi wayaba kuma bazai kirataba soyake kawai taganshi
Washe gari Hafiz yaje kaduna yakwana dasafe Usman yakira Abdul yasanar dashi sukahade airport din sukabi jirgi zuwa Niger dama kaleed yasanarda hassan zuwansu
Jirginsu yana sauka akazo daukarsu kaleed saida yasake kwankwantawa hassan karfa afadawa zainab
Suna isa Gida fadar mai martaba sukaje bayan sungaisa kaleed yawuce gida anan yabar su Usman
Da sallama yashiga gidan mamansu tana wajen hutawarta yaran gidan suna ganinsa sukahau ihun murna Suna ga ya sultan gayaya sultan zainab tana daki kwance tayo bururut tafito
Haleema yadaga sama yanayiwa wasa yashafa Kansu kaitsaya wajen mom yawuce saibayanshi zainab taganie
Waifa fushi takeyi kwana biyun dabai nemetaba Amman yanzun data gansa Sam tamanta wani dadine taji duk yakumeta
Aisha✍🏼
☠ *HATSABIBIN BOKA!!!*☠
PART 2⃣
39
By gentle
Lady💃🏽
Tana ganinsa tatashi daga kishingiden datake tace sultan saukar yaushe ?? Yana murmushi yakarasa saman shinfidar yacire takalmansa yatankwashe kafarsa sannan yazauna yagaida itah ta amsa cikin fara a
Yace jiya nakirah dad nafadamasa yau zamuzo baisanar dake bane??? Tace kaima kasan halin baban naku mantuwa kamar maici dagari.
Kaleed yayi dariya yace kusan hakane mom bataliyar gidan nan aimunkai Karamin wani kauye
Tayi murmushi yakabaro su khadija dasu anwar?? Qalau suke tacema agaidake shekaranjiya mukaje kano acen dad yabarota saboda mahaifinta yaxo
Tace Allah mai iko shikuma saiyanzu Allah yaganar dashi gaskiya """ kaleed yanisa yace hakane wlh mom danaji labarin abunda akaiwa mahaifiyarta dakuma wanda akaimata sainaga ninawa mai saukine inhar akwai Wanda akafi cutà khadijace
Yabata fuska babban takaicin mahaifiyarta tarasu naso ace tana raye taga sakayyarda Allah yayimata
Tace kenan reshe yajuye damujiya
Kaleed yace har wacce maman anwar tafadamana wacce tayi sanadin mutuwar mahaifiyata itama tasoma ganin sakayya
Nan yabata labarin komai tajinjina kai lallai mata suna barna aduniya waishin anyama wadan nan suna tunawa damutuwa kuwa??.
Bashakka sun manta da ita idan ma basumantaba tosun manta kwanciyar kabari innalillahi wa inna ilaihir rajiun"" kasacefa za atona ciki da falo asaka akasa akawo itace ashinfida akawo kasa azuba sai ankulle ko ina baza abar wata Kafa kome kankantartaba
Ko sauro baxaisamu hanyar shigaba kayi la akarida zafinda muke ciki ayanxuma dakake wajenta iska yana kadawa
Amman duk dahaka zakaji kamar ana gashinka kalu innalillahi wa inna ilaihir rajiun shedan yarigada ya shagaltar damu munmanta komai mun manta kwanciyar kabari
Munmanta tsayin da za ayi ranar alkiyama Rana za asassauto da itah tsakaninta da kwakwalenmu kamu dayane
Zufan jikinmu harsaiya kawowa mutun gawuya wasu ga kaurinsu"" bayan wannan abun kuma atashi hisabi asameki da aikata wadan nan manyan laifuka mezakifadawa Allah???
Sharrin zuciyane??
Aikin shaidanne???
Shairin kawace???
Kwadayin duniyane???
Kokuma jindadine???
Acikin tambayoyin nan wanne kikeganin zakice shine yaturaki
Sharrin zuciya: kikasance kina gdun duk wani mummunan Abu da zuciyarki zata darsa maki tabbas kekanki kinsan Abu maikyau da marakyau
Aikin shaidanne: kikasance maiyawan Neman tsarin Allah daga sharrinsa aduk lokacinda kikaji yayimaki yaye yaye Wanda bana alkhairiba kiyisaurin fadar a uzubillahi minashshaidanir rajin
Ina Neman tsarin Allah daga shairin shaidan jefaffe""
Kikasance maitaka tsantsan da hudubar shaidan""..
Shairin kawance: rigakafi shine kiguji duk wata Kawa dabakiyarda da tarbiyartaba domin komai iliminki inhar bawani nufi na Allah ba zakiga kinfada tarkonta takaiki tabaro
Kwadayin duniyane; me akeyi da Kawar banza ta duniya??? Abunda bazai daureba har abada karkimanta karya ko zalunci cin amana ko ha inci bazaitaba kaiki ko inaba
Jindadine: haba Yar uwa ina jindadi yake anan kekanki idan kina mu amala da bokaye hankalinki bazaitaba kwanciyaba
INA kikaga kwanciyar hankali bakigida gashikuma kinshanya garinki arana kuma gashi anhada hadari Yar uwa kekanki zakifijin dadi idan kika kasance mace tagari maitakawa bake bayan kame kame
Hankalinki kwance bakida fargabar maganin yaci kobai Ciba idan kinaso ki mallake mijinki ba boka ba malam yabiki kamar bantee saikiyi masa biyayya kiguji Saba umurninsa yinayi bari nabari
Idan yanuna yanason Abu kinuna masa kinfishi son abun"" idankuma yanuna kyamar Abu koda kinasonsa aranki kema ki kyamaci abun harma kifishi kyamar abun
Ana mallake miji tahanyar siyasane iya magana hakuri yawan ibada iyah girki dakuma rike sirrin gidanki hakuri dakuma dangana da abunda mijinki yabaki hmmm wai babbar magana mata!mata!! mata!!! Inacikin jinsin mata Amman wlh abunda mata sukeyi wasu bazanyi jam iba kaidakaji kasan rashin ilimi yayi katutu akansu
Daka auri mace wacce batasan Allah ba batada ilimin Islam yafimaka ka kwanta Kaita barci wata matar Sam batada tausayi
Hardai wannan yanayin damuka samu kanmu Na tsadar rayuwa babu ruwanki da kawarki ko makociyarki kullum saitaci nama kokuma kaya masu tsada mijinta yake siyamata
Inaruwanki" inbanda hauka aikomai da matsayinsa kitsaya inda Allah ya ajeki wannan hassadace bakomaiba
Idan kinaso kikasance mai godiya ga Allah akoda yaushe karki kalli nasama dake kikalli nakasa dake idan mijinki yana siyomaki nama sau daya awata karki kalli wacce mijinta yakesiyomata nama duk sati kokuma kullum
Kikalli wacce mijinta bayasiyo mata nama daga sallah karama sai babbar sallah watama ko sallar bazata samuba saidai Wanda makota suke basu kuma duk dahaka sukace Alhamdulillah
Mezaihanamu furta hakan komai lalacewar gidanki kinfi wata koya kikasamu kanki agidan mijinki kigodewa Allah saiyasake baki wata ni imar Amman idan kina rainawa mijinkima bazaiji karfin sake nemowaba
Tunyana daurewa hartakai zuciyarsa ta kekashe yazama sai ahankali saikiyi tsuwar da tushe Yar uwata kizama maiyawan dauke nauyin dayake kanki kixama mai hakuri dakuma tawakkali
Duk matarda tarike wadan nan inajin tagama komai saikuma abunda baka rasaba yanxun mukeda damar gyarawa kiyi amfànie da lokaci tunkafin kiyi nadama marar amfàni sanda lokacin yàkuremàki
Allah kaganar damu gaskiya Allah yasa mufi karfin zukatanmu Allah yakaremana zuri'armu
Allah kanesantar damu daga cin haram Ameen kaleed yace Ameen mom bari naje nadan watsa ruwa inkwanta kafin asoma kira yayi maganar yana mikewa
Ya aje haleema yawuce haryanxu Zainab tana nan tsaye jikin kofa kaleed yaganta saiyayi kamar baigantaba harwaka yakeyi yana gyada kansa kamar wani kadan gare
Xainab ganin tayi yayi kiba yasake kamar bashiba yayi haske abunshi tome take bashi Yakoma haka??? Kishine ya turnuketa haryakusan barin wajen kamar kububuwa saigata ta bayyana agabansa
Yadago yakalleta yace ah kanwatace Ashe kina gida"" harara Tamaka masa tace aidole zakafadi hakan tunda kasamu wacce tafinie ya kaleed wlh kabani mamaki ace harzaka iyah kwana biyu batarreda kaji muryanaba saiyanxu nake kara karyata soyayyarda kakemun
Ta sharbe hawaye shikuma kallonta kawai yakeyi yarungume hannuwa yanata murmushi Wanda yake sake fitoda ainahin kyansa
Jintayi shiru tana sharar kwalla yasa yagyara tsayuwarsa yana rike kunkumi yace daga dawowana babu kosannu dazuwa zakitareni da tsarabar hawaye haba my love
Baki tamurguda masa tace aibani na aikekaba"" yarike