yace doctor mehakan yake nufi??? Wannan karyane ina matata zata samu wannan cutar bayankuma munada cikakkiyar lafiya
Wannan ba result din matata bane doctor"
Doctor lawal yace kazauna alhaji nasan dolene kayi mamaki nikaina nayi mamakin hakan Amman sun tabbatarmun da cewa result dintane Amman yanzu muje taredakai zandibi jinin dakaina muje dakin awon hardakai dankagani da idonka
Yamike yawuce Usman yakasa tashi daga zaunenda yake saida doctor din yadagashi suka wuce yanabashi baki kakwantarda hankalinka
Komai zaizo cikin sauki Dan cutar batayi nisa ajikintaba inhar zata kiyaye dokokinda zamubata zata iyah rabuwa da ita gabadaya
Usman yace kamadaina furta hakan ni matata qalau take shiru doctor yayi suka karasa dakin sunsamu hajiya tazo da Abdul aka sake diban jinin lubabatu sukawuce lab tare
Yakirah khadija sukawuce tare
Akasake aunawa yatabbata lubabbatu tanadauke dacutar HIV jikin Usman neyasoma rawa ina lubabatu zatasamu wannan cutar???
Yacewa doctor ya auna na khadija itama akadibi nata ita batasàñ meke faruwaba itama aka kawo nata result din batada cutar
Usman yashiga rudanie Ganin yashiga tashin hankali doctor yasa shima aka dibi jininsa aka auna
Tunkafin afadi sakamako Usman yasan yanama da ita danyayi Imanin cewa lubabatu bayar iska bace to inazatasamu wannan cutar sai idan shine yalakamata
Toshimadai baitaba Neman mataba"!!! Yasalam kuma yasan ba khadija bace tunda gashi an aunata batadà cutar
To ina lubabbatu tasamu wannan cutar??? Amsar wannan tambayar bazaisameta abakin kowaba sai lubabatu
Muryan doctor ce tadawo dashi hayyacinsa yana murmushi yace ina tayaka murna bakada wannan cutar acikin jininka
Usman yakalleshi da mamaki kaiyadyada masa yanuna masa result din Usman yakarba yana dubawa tabbas bashida itah
Lallai dolene lubabatu tasanardashi inda tasamo wannan cutar result din lubabatu yadauka dasauri yafita doctor da khadija sukabishi dakallo doctor"" usman yabashi tausayi
Lallai dole hankalinsa yatashi Allah ma yatsareshi baikwasaba"" itakuma haryanzu khadija batagane komai ake magana akaiba
Gaisuwa dafatan alkhairi agareku masoyan wannan littafin inasake tunardaku badan nishadi nakeyinsaba saidanku amfana inasonku sosai😍😘
Aisha✍🏼
☠ *HATSABIBIN BOKA!!*☠
PART 2⃣
14-15
By gentle
lady💃🏽
*MUMMUNAN LABARI*
Inada wata Yar uwa datayi aure totanada kishiya sosai nasan uwargidan bala ine da itah bataganin girman iyayen mijin"" atakaicedai komijin batadaukeshi abakin komaiba""
Sanda ya auri Yar uwar tawa da agidan mahaifinsa yake saiyayi gininsa danyatare tokunsan uwargida tanayin yan binne binnenta dankar ayi auren
Nikuma alokacin da akace uwargidan tazabi daki saitazabi na kurya akace Yar uwata tazauna nafari
Danaga rawarkan nata yayi yawa nace Yar uwata bazata zaunaba saidai wancen din datakeso ashetasan mugun abunda tayi
Bayan bikin wasu watanni suka shude sai tayi fadada mijin dama nafadamaku zaman hakuri yakeyi da itah naje garin alokacin nasamu tahaihu abun baizo daraiba alokacin duk Kalau suke da Yar uwata
Bayan lokacin sai Yar uwata tasamu ciki " cikin yanawata uku uwargidan tayi fada damijin haryakai yasaketa damakuma igiya dayane yaragemata
Shine tace tundahar yasaketa yakwana dasanin bashi bakara zamadawata matar dashi da aure saidai alahirah idan anayi
Yace yaji ai Allah yafita taje tayi duk abunda zatayi"" hmmm bayan barinta gidan dawadansu watanni sai Yar uwata tasoma rashin lafiya
Takumbure suntul akayita yawon asiviti abutakai har anasaida kayan dakinta ana mata maganie tunda mijin baida hali ciwo yacinye kudin
Harta haihu balafiya atakaicedai sai akamiyarda itah gidan iyayenta" "" batadade ba tace gagarinku naji mutuwarta kamar me😭 bayan kwana biyu yaronda tahaifa shima saiyabita
Bayan anyi zaman makoki an gama mijinkam baisake marmarin kara aureba saida aka kwashe shekara dawasu watanni
Yazo yayi aure suna zamansu lafiya matar tasamu ciki saiga ciwon marigayiya yabayya Na ajikinta kamardai yanda itama tasha wahalar hartahaihu akamaidata gidansu
Shine akakirah maimaganie kawunane dayaje gidan yanashiga dakin yace basuga hayaki yana fita takasan kujeraba
Sukace basuga komaiba yasa akadauke kujerar yace abashi maginie akabashi yafashe wajen yaballe daben dakin
Saida yayi Gina maizurfi saiga tarkacen kaya layu gashinkai waren takalmin Yar uwata da dankwalinta na atamfa mai golden da wani zanenta na engla"" da likafanie dasauran tarkace
Yacirosu sannan yace dole abata maganie Dan aikin yashiga jikinta akasoma karbarmata rubutu tunyaron yana jinjiri batakoma gidan mijinba harta yaye yaron
Batajima dakomawab saiciwo innalillahi wa inna ilaihirrajiun jiya bayan magrib aka kiranie akasanardani bayan la asar takoma wajen mahaliccinta
Inazakidamu duniya??? Menene ribar mace idan tacutarda Yar uwarta shinbata tunanin ranarda zatajuyo gareta?..
Meyasa mata basada hankali kawai bakin kishinki dabakin halinki kuma bakomai yake kawo hakanba sairashin tarbiya
Inada yakinin Tara bisa goma wadanda suke Neman maganie jahilaine basada ilimi uba anaso kasamawa yayanka uwa tagari wacce tafito gidan mutunci Yar datasan yakamata
Mai Ilimi da jahili basataba zama daya kaida kaga wani aikin kasan masani bazaitaba iyah aikatashiba barna darashin tausayi dakuma zalunci duka aikin jahiline shine kawai zai iyah
Zancenda nakemaku itafa tayi auren wani waje hartayi haihuwa biyu Amman saboda zalunci tahana tsohon mijinta shiyazauna data shi matar dama antusa dakarin kwana kunsan idan ajali yazo kobabu ciwoma sai anje
Ina baran adduarku kuce Allah yatonawa wannan matar asiri idan tanada rabon shiruwa Allah yashiryata idankuma batada rabon shiruwa Allah kasani kagaggauta nunamata abunta tun aduniya da itah daduk wasu matan masu hali irin nata Allah yawulakantasu kamar yanda sukeyiwa yan uwansu mata wadanda basujiba basu ganiba Allah yakaremu damu da zuri armu daga sharrin wadan nan matan ameeen
**--**--**--**--**--**-
Mahaifiyar lubabatu hannu tadorah akai🙆🏿 tafasha kuwa nikasaka??? Wlh bansakuba sainayi maganin ka macuci azzalumi sainaga karshenka dakai daduk maibaka shawara.
Ihu tasakeyi tasoma tikar rawa tanacewa yasakeni??? Baisakeniba " yasakeni??? kai baisakeniba "" tacire mayafinta tawurgar tacire dankwalin kanta tawatse gashin kanta
Waje tasheka dagudu lubabatu Ashe tasuma saboda tashin hankali"" tanafita tatasamma kofar asivitin dagudun tsiya""
Mutanenda sukaga fitowarta sukayi ihu akai Tara Tara aka kamata"" tace kusakeni inkasheshi kunajifa waiya sakeni???
Wlh bansakuba dole yazauna danie saikuma tafashe dakuka nacutarda rayuwarsa nabashi jinin hailana yaci acikin abinci yasha futsarina kuma yace zaisakeni ??? Wlh baisakeniba
Takuma shekewa da dariya tace Dan ubanku kusakeni ko insa akasheku daibayan daya inakallonku duk Wanda yakalleni saiyamutu
Saikuma tasoma gurnani tana turjewa saida akaimata allurah wani daki aka Kaita akadaureta da sarka
Lubabatu babu Wanda yasake bitakanta dan yanzu ko irin masu zama harabar wajen danshan iska sundaina saboda doyi suwaibace taturah kofar dakin hannunta yana Dade da hancinta
Takarasa bakin gadon tasamu lubabatu bata motsi takwalla kara dagudu tafito zuwa apishin lawal mijinta tafada jiki yana rawa yanaganin yamike yace lafiya suby meyakawoki nan??
Cikin muryar kuka tace naje dakinda aka kwantarda Anty lubane nasamu batamotsi batagama rufe bakintaba yaja abun awo dasauri yafita tabi bayanshi hartana hadawa dagudu
Yanazuwa yataba zuciyarta yaji tana bugawa sumane tayi ruwa yadibo yasoma shafamata take tasaukoda ajiyar zuciya tabude idonta tana kallonsu sannu kanhankali tatuno abunda yafaru
Saita sake fashewa da kuka suwaiba tace Anty Dan Allah kidaina kukan nan""" lubabatu ko saurarenta batayiba tacigaba da kukanta ganin hakan yasa lawal yayi mata allurar barci dantasamu natsuwa
Saida barci yadauketa sukafita dakin suwaiba saida tayi amai danbakaramin dauriya takeyiba saboda tanaganin mutuncin lubcy batajin zata kyamaceta kodakuwa kowama yagujeta
Bayan Usman yakoma cikin dakinsa baisake saukowaba su khadija sungama komai sunzuba Na asiviti dawanda zasuci taresukaci nasu dankofar dakin Usman arufe take
Ana kiran magrib Usman yasauko khadija tamike dasauri tace dad mungama shiryawa kaimuke jirah mutafi "" batareda yakalletaba yace zuwa ina???
Tace yahaka ??? Asibitin mana dama badanmuyi abinci kace mudawo gidanba?? Yace nayidake??? Kaitagirgiza tace Amman basai kayidaniba nasan abunda yadace
Yace tobazakuba yacigaba da tafiyarsa tasha gabansa dasauri tace dad wajen momfa zamuje bawani gurinba yakalleta kasa kasa yace nafiki sanin hakan
Kuma nace bazakiba saikifadamun menene alakarki da itah??? Khadija tarude dajin furucinsa tajuya kallonta wajen labila sutake kallo
Khadija tace please baban anwar bajimawa zamuyiba kayi hakuri idan bazakajeba mukabarmu mutafi
Tsuke fuska yayi yace waike yaushe nafara Wasa dake??? Har inace bazakuba kicigaba danacewa inadai nafiki kusanci da itah Dan matatace tokuma nine nace bazakiba karki sake yimun musu kawai kiyi abunda nace indai baso kike kiga bacin rainaba yana kaiwa karshen maganar yawuce yabarta
Baki sake tabishi dakallo"" saida yawuce tajuyo jiki bakwari tadawo wajen labila ga mamakinta murmushi tagani afuskar labila Sabanin taga damuwa
Tace sahiba lafiyarki kuwa ahanamu zuwa wajen mom kuma kiyi murmushi??? Tace tomezanyi sahiba??? Aikowa yasiyi rariya dole tazubarda ruwa tayiyu tasanadin hakan mom taga isha ra tatuba tadaina abunda takeyi
Akoyaushe. Khadija tana nunawa kamar Batasan komai agameda halin lubabatu ba aganinta cin fuskane tasanarda labila itama tasan halin mahaifiyarta
Tace hmm kedai kawai kice bakyason ran mahaifinki yabaci yanxu yazamuyi??? Labila tace mefa kawai tunda yace bazamuba muhakura zuwa gobe tayiyu yahuce Dan inajin akwai abunda akaimasa asivitin nan khadija tace kowama yamasa ai tsakaninsune baidace yashafi mom ba yanzun towaye zaikwana wajenta???
Labila tace ai hajiya tazo nasan koda alhaji Yakoma dakyar idan zatakoma saitaga yanda jikin yayi kwana biyu muje muyi sallah kinji""
Kaitsaye bangaren khadija suka nufa Dan gabatarda sallar magrib
Aisha✍🏼
☠ *HATSABIBIN BOKA!!*☠
PART 2⃣
16
By gentle
lady💃🏽
Usman ranar shikadai yakwana itama Khadija kinzuwa tayi wai itah adole tayi fushi shima damuwarda yake ciki bayasoma tazo kusa dashi
Bayan kwana biyu doctor lawal yakirashi awaya yabashi hakuri akan yadawo kurajen lubabatu sun sake yin ruwa kuma tsutsotsin yanzun sun sake lunkawa
Wadan nan masu bakaken kaine ruwan jikinta zasurika tsotsa"" warinta yasake lunkuwa tunsanda allurah tasaketa take ta ihu duk tarude asivitin
Kuma anwanke mata ciwon Amman Sam bawani haske kamarma anasake karo ciwonne sai suma takeyi" tunjiya aketayimata allurar barci
Usman yace Toni mezanyi mata doctor dazaran naganta raina sake baci zaiyi kataimaka duk taimakonda yadace kayimata kayimata nizanbiya kudin Amman bana bukatar ganinta
doctor yayi shiru daga bisanie yace gaskiya iya taimakonda zamuyimata munyi abun yacitura yanzukam aikin karshe dole ayanke mata Kafa inhar ciwon nan yacigaba dacinta
Usman yanisa yace shikenan sainazo"" saukowa yayi daga sama yasamu su khadija zaune sunyi shiru yawuce abunshi ko kallonsu baiyiba
Wayar khadija ce tahau ruri tadauko yayansu taganie cikin fara a tadauka takara akunnenta tareda sallama
Daya bangaren aka saukarda ajiyar zuciya yace inawuni maman anwar tace lafiya qalau yayansu ya Niger??? Yace gatanan dai wlh gabadaya hankalina yadawo wajen mahaifina
Inason zuwa naganshi please idan babu damuwa shiru khadija tayi yakatsemata shirun yace please inacikin wani hali karkice ah ah yanada mahimmanci arayuwata
Khadija tanisa tace banki takaba ammanfa gidan ba lafiya tunranarda nadawo nasamu ankwantarda mom asiviti
Yace nibanada damuwa da itah kawaidai kicemun kawai nazo"" khadija tace shikenan saikazo idan kasauka kakirani saina tura adaukoka yace yauwa nagode
Lubabatu kam tasake kwamtsewa ganin kowa yajaye karyarta takusan karewa tayanke shawarar dole taga sajida
Da suwaiba tazo ganinta tace ta aramata wayarta takirah labila tace tadaukomata wayarta labila tace kiyi hakuri mom dad yace bazamuzo hospital dinba
Lubabatu tace shikenan kidauko wayaata kibawa driver saiyakawomun tace to tadauko tasamu muhd tabashi tace yakaiwa mom hospital yakarba yatafi
Bakin kofa sukahadu da Usman shikuma zaifitowa daga asivitin baiko kalleshiba yawuce shikuma saiyadauka baiganshi bane
Yawuce dakin Sam yakasa kohadiye yawu saida yamata yajiki yabata wayar yajuya yafita tacewa suwaiba tawarware mata hannunta daya
Tawar waremata takunna wayar low b3 matakekirah
lambar sajida takamo takirah saida takatse ba adagaba
Tasake Kira sannan akadauka hello tace sajida kina ina??? Tace ayya Kawata banagari wlh kinsan inashire shiren yin birth day na Dubai shine nakeshirya wajenda zamuyi dakomai dazamu bukata
Kawata zamu holefa danhaka kisan yanda zakiyi kitambayi sarkin ikonki Dan watadaya zamuyi anan nagakamar tsoronshi kikeyi
Lubabatu hawayen takaicine sukazu bomata gakudi ga lokaci Amman babu abun takamar wato lafiya
Komai kudinka komai mulkinka idan bakada itah saikaga kudin tamkarma basuda wasu amfanie
Sundade suna alwashin wannan birth day din Ashe bada itah za ayishiba saita fashe dakuka sajida tace nashiga uku menene yasakaki kuka Kawata Kodai akwai matsalane???
Lubabatu tace babba makuwa Dan Allah kitaimaka kidawo yau kisameni ina hospital sajida ina Neman taimakonki komai ya lalace kowa yagujeni harda yata mijina yahanata zuwa gurinda nake inason taimakonki kodan narama cin mutuncin da akamun
Sajida tace shikenan zakiganni kuwa sainazo taka she wayar Sam lubabatu tamanta suwaiba tana dakin Amman suwaiba batagano inda maganar lubcy tanufaba
Ranar sajida tabaro Dubai Amman koda jirginsu yasauka marece yayi shine tayanke shawarar tabari sai washe gari
Washe gari karfe Tara tashirya ta isah asibitin wayar lubcy takirah tayimata kwatancen inda zata sameta tunda tatunkari wajen tadade hancinta aranta tace menene yake doyihaka kodaima wanine yamutu ba asaniba
Tanaturah kofar dakin taga lubabatu sai kuda suke binta""" sajida ta kwalalo ido tace lubcy kece kuwa??? Takalli kanta tace nice sajida karaso mana
Sajida hannunta yana Dade dahancinta danyan hanjinta harmotsawa sukeyi Sam lubabatu bataji haushintaba waje tasamu tazauna dadan nesa da itah tace garin Yaya hakan tasameki lubcy???
Tashere hawaye tace tsautsayi sajida nayi danasanin amincewa dakawa duk khairat ce ummul haba isin jefani cikin wannan bala in
Ina zaman zamana takaini wajen bokanta Ashe kaina nakarbowa maganie bakishiyaba kalli yanda nakoma"" itakuma tagujeni
Sajida tace wayakaiki lubabatu😳 kinmanta sharadinda *hatsabibin boka* yabamu farkon zuwanmu wajensa???
Lubabatu tace wlh ban mantaba saida nafadawa khairat komai gamedashi Amman tace in share bazaiyi komaiba
Sajida tace aikuwa taturaki ga bala I domin babu makawa *hatsabibin boka* bazai kyalekiba kehar itama bata tsiraba Amman taya akai kika amsarwa kanki maganie bayankince bakyazuwa wajen boka
Lubcy tace wlh karya nakeyi inayin hakanne kawai dannakawarda hankalinku kudauka bana Neman maganie
Sajida tace kinatsammanin koda kowa yayarda nidin zanyardane kawaidai nabikine ayanda kikace nan lubabatu takwashe komai tasanarda itah harkomawarta wajen bokan takaredacewa
Sanadin fyadenda wadan nan yanfashin sukai mana Ashe nakamu dacutar HIV tasake fashewa dakuka
Sajida tace bokan yacemaki bashine yayimaki wannan aikinbako??? Lubcy tagyada kai sajida tace tabbas babu makawa wannan ba aikin kowabane saina *hatsabibin boka*
Lubcy sauran kadan tafado dagasaman gado"" tace dagaske sajida???😳 Tace koshakka babu nayarda zaiyima fiyedahakan
Komai zai iyah aikatawa agareki tundahar kikataka dokarsa Amman kinyi ganganci gashi kinkai kanki kinbaro
Lubabatu tace nashiga ukuna 🙆🏿wlh daman irinhakan nayiwa gudu Amman khairat tazugeni gashi abunda tajamun sajida kitaimakamun inrabu dawannan ciwon ya isheni
Sajida tanisa tace yanzu hanya daya dole muje gidana inada madubin dayabanie sainakirah makishi kibashi hakuri lubabatu tasaki murmushi dukda zafin ciwon jikinta baihanata jindadi arantaba hartasoma kiyas ta tsiyarda zatashuka idanhar tawarke saitasa khadija mahaifinta yayunta Usman sunkwashi kashinsu ahannu motarda aketurah guragu datake dakin nantasaka lubabatu bayan tataimaka mata tasa kayanta
Asace tafitoda da itah tabaya tazagaya tabawa masu tsaro cin hanci tafita datai makonsuma tasakata amota dancemasu tayi kasar waje za akaita tanarufe motar tajata saigidanta..................
Aisha✍🏼
☠ *HATSABIBIN BOKA!!*☠
PART 2⃣
17-18
By gentle
lady💃🏽
Koda suka karasa gidan gabadaya motar tagume da doyi sajida takagarama sukai dangudu tayi bana wasaba"" bayan tayi fkng din motar tabudewa lubabatu tace toyanzu yakenan tunda nibanida abunda zanturaki???
Lubabatu tace zankokarta tamike dakyar tasoma takawa sajida tabita abaya tana dade hanciii saida takai falon sannan tatsaya "" sajida tace mukarasa ciki mana sukahaye sama
Inda sajida take ajiye madubinta wurine na musamman danyanda takejinsa ko rayuwarta batajie haka bayan lubabatu tazauna sajida tatafi dauko madubin
Jikin lubabatu harrawa yakeyi ganie takeyi tamkar sajida batayin sauri " takagara tayi ido hudu dashi dantasan matsalarta takau kuma duk tarabu dawannan ciwon wlh Wanda khadija zatayi da Usman saiyafi nata muni danyanzu Sam tajima yaficemata arai
Tanada bururruka aranta wadanda taketa kiyas" tawa zatayi inhar *hatsabibin boka* ya warkarda itah"" tana nan tana sake sake sajida tadawo tareda madubin tazauna kusa da itah hannu tasa tashafa madubin tareda kiran sunan *hatsabibin boka*
Rufe bakinta keda wuyaa saisukaga iska mai karfiiii tataso tamkar asahara suke kayan dakin sukasoma shawagiii tsayin mintuna biyar sannan komai yadawo yanda yake saiga *hatsabibin boka* yabayyana akan kujerarsa
Bayyanarsa keda wuya yasheke dawata mahaukaciyar dariya kaidakaji dariyar kasan dariyar muguntace dominkuwa tsabar dariyar harda hawaye yakeyi
Yadauke sa o i goma yana kyakyata wannan dariyar wacce takaramasa munie fuska uwa dorinar ruwa
Cikin abunda baifi second dayaba yagimtse fuska kaibakace shine yagama fesa wannan dariyarba maikamada kukan jakie yadago jajayen idanuwansa yakalli sajida yace menene dalilinki nakirana alhalin kina tareda wannan???
.shiru sajida tayi batace komaiba " lubabatu ce tace uban hatsabibai tuba nake ninasan mailaifice agareka saboda nakarya dokarka Amman kayafemun wlh bazansake gigin sake aikata hakanba
Yasake bushewa dadariya yace dagabaya kenan aini bana yafiya kallinan yayi nuni da hannunsa akan wani katon madubin tsafi saigawani haske yabayyana
Hoton wata matane kwance akan gadon asiviti kafafuwanta sunyi tula tula duk kafadaya tayi girman randar ruwa jajir da itah kamar akwanta jinie yafito
Duk tsabar ciwone hannunta yalankwashe sannan kanta yayi tukuwa uku goshi yayi gaba kamar shantu bayama haka saikuma tsakiya dayatashi sama
sunraja a dakallonta duk da sudin basusantaba Amman suntausaya mata dandaganinta tanajin jikie""
*hatsabibin boka* yace wannan shine hukuncin duk wani Wanda yayi kokarin jadanie Cikin tashin hankali lubabatu tace wannan wacece???
Dariya yasoma shekawa sannan yace wacce tabaki shawarar kisaba umurnina kikarya dokata lubabatu tace nashiga ukuna wannan badai khairat bace?? Tasake kallon hoton tabbaskuwa itace duk da kamannunta gabadaya sunsauya Amman taganeta yanzun datajie yafada
Tafashe dakuka tace boka kayimun rai karabanie dawàn nan
Ciwon wlh nayimaka alkawarin bazankara kuskuren saba dokar kaba"" yace wannan ai shirmene dacen nine nasakamaki ciwon kishiyarki kikayiwa kuma dabakinki kikace ayimarar makari sai mutuwa
Duk dawan nan aikin nawane nima kamar yanda kikace saimutuwa lallai bake bawarke wannan ciwon
Tadorah hannu aka🙆🏿 tace nabani na lalace boka kayimun rai khairat kincuceni dayanzu inanan dalafiyata
Yace kimadaina bata yawun bakinki wajen yimun magiya wannan hukuncin shine yadace dake kuma wannan tsoratarwane gasauran masu zuwa wajena dansuguji sabawa umurnina
Kisanie kekanki kinada sa a Dan abunda naso nayimaki yafi wannan sa arki daya inakan wani aikine hankalina bayakusa da abunda zanyi maki saiyafi wannan munie kimaza kuma kibacemun daganie danbanason ganinki
Tasake fashewa da kuka tace yazanyi boka ciwon nan yakaini intaha bayabarina barci kuma idan nakwanta barci sainayita mummunan mafarki wadansu yara dawadansu miyagun namun jeje sunabina
Sukuma yaran suyitamun dariyar mugunta karshe sainafada wani katon rami boka katausayamun ko barcine nasamu kalli yanda nazama mijina yagujeni
Babana yatafi yasaki mamana saki uku agabana gashi tahaukace yayyuna suma suntafi yata mijina yahanata zuwa inda nake duk danasan itama dazaran tasan tasanadin zuwa karbar maganie nahadu dawan nan lalurar zatadaina kulanie
Katai makamun badan halinaba"" tsawa yadaka mata wacce tasaka lubabatu tasaki fitsari yace tunda kika saba umurnina babu wani sauran tausayi awajena wannan shine dokar tsafina kuma baxantaba karyataba saboda muddin nakaryata nikaina baxanga daidaiba ko uwata ta aikata badaidaiba hukuncine akanta banajin tausayin hukunta duk Wanda yayimun laifi kisanie
Maganar yaranda sukemaki gizo amafarki bagizo bane gaskiyane sunanan tafe gareki kamar yanda sukafadamaki
Tace wayyo nabani mekuma zasuzoyi wajena?? menamasu??? Wlh ko acikin mafarki tsoro sukebani ballantana ingansu azahiri sanadin ganinsu danakeyi koda inajin barcine saina hanashi zuwa
*hatsabibin boka* yace nikaina nemansu nakeyi inharma zasuzo ashirye nakedasu nasan bakisan kosuwayeba abincikena Nagano yayan mijinkine
Lubabatu tace ai Usman bayada Yaya biyu maza masukama daya wadanda tahaifa dayane namijie
Yace abunda bakisaniba kokacinda nasa hayyanul zairi yadauketa yaje yakasheta kafin sukai dajin tafarfado shine suka fada kasar sin lubabatu tace haba nidai tunsanda naganta naji jikina yabanie anya ma mutunce
*Hatsabibin boka* yacigaba wata aljana tataimaketa tariketa agidanta tunzuwansu Dubai daciki tadawo haryatsufa tanacikin dajin
Babu yanda banyiba dannadaukota nakashe yaran Amman aljanuna koda sunje dajin basaganin komai sannan kuma ni inaganinsu a madubin tsafina nasan suna dajin
Sanda hayyanul zairi Yakoma domin cika aikinsa tayimasa illah sanadin hakan yarasa wadansu sassa masu matukar amfanie ajikinsa
Aranar tahaihu Yaya biyu Kuma sune nake nema yanzun haka ta aikasu saudiya saboda karna isah garesu ranarda tadawo gidanku bayan kinsuma dakanta tashiga dakinki tadauko madubin tsafinda nabaki aljaninda yake gadin madubin takonashi da addua
Yayi wani murmushin mugunta yace nasan zakiyi mamaki dakikaji nazauna ina sanardake abunda bakisaniba kidauka nasaukone kodaya inafadamakine domin wani babban tashin hankalinda zaki riska
Kuma kisanie yanfashinda sukai maku fyade ninenan nasa aljanuna suka jagorancesu zuwa dajin dansu ba ma abota zuwa dajin bane nayihaka ne domin kisamu tsarabar zuwa wajen boka
Magana takarshe kisanie hayyanul zairi zaidawo gareki tareda aljaninda yake gadin madubi dakishiyarki takona domain basa yafiya duk abunda akaimasu saisun rama
Yamaida kallonsa wajen sajida wacce kanta yake kasa tunsanda suke magana yace kekuma dagayau banaso kisake kirana inhar badaliline dakeba maikarfi idankuma kikasake bazanfadi hukuncinda zanyimakiba
.saidai nayi danhaka kiguji mummunan hukunci yasauka akanki"" yanagama fadar hakan yasheke dadariya kamar bakinsa zaidare gida biyu take hayakiii yatashi sama batt yabace
Sajida tamike zatadauki madubin lubabatu tace please Kawata kisake kiranshi kibashi hakuri niyazanyi inrabu dawan nan guyabar
Sajida tace rufamun asiri lubcy kinajinfa abunda yafada Toni taya zankarya dokarsa nikaina inajin tsoron yayimun hukunci irin naki kinga tashi inmiyardake asiviti dankar azonemanki ba asamekiba
Lubabatu tamike dakyar gatakaicin ciwo nacinta gashi *hatsabibin boka* yaki saurarenta!![truncated by WhatsApp]
☠ *HATSABIBIN BOKA!!*☠
PART 2⃣
19
By gentle
lady💃🏽
Lubabatu jiki asanyaye tamike tasoma takawa ahankali tana tafiya tana waigen dakin sajida tanaji kamar tabugeta tadauko madubin ita inazatayi dawan nan ciwon???
Harkunya takeji wannan mugun doyi bakin motar suka kai sajida takwalawa driver nagidan kirah tace yayi sauri yamiyarda itah asibiti cikin wata motar tasaka lubabatu tayimata Allah yasauwake
Lubabatu tace toyanzu saiyaushe??? Sajida tayakuna fuska tace saiyanda hali yayi danni anjima kadan zankoma Dubai bangama abunda yakainiba maybe zandawo next weak"" Allah yasauwake
Tasakai takoma cikin gidan lubabatu tabita dakallo wasu hawaye masu zafie suka zubomata"" takaici nadama danasani babu abunda baizo mataba abokanta dasuke Sonta sunayin nan nan da itah saboda lalurah tasameta shine zasu gujeta
Kodayake mijinta ma yagujeta balantana su Ashe Duk Wanda yake kusa dakai yana lallake maka munafukin Kane
Bazaka gane hakanba sai idan wani abu yasameka jisajida menene batayiwa sajida ba duk yawonda suke zuwa itah takedaukar nauyin komai dazasu bukata Amman itane take Dade hanci saboda doyinda jikinta yakeyi
Usman yana hanyar zuwa hospital Dan yagama shirye shiryen fita da lubabatu kasar waje domin sunada kayan aiki sosai tayiyu tasamu tarabu dawan nan ciwon yanzu Sam tafita ransa Amman babu yanda zaiyi albarkacin yaransa dasuka Haifa da itah dole yanema mata maganie daga haka zai sauwakemata
Komai takeso zaibata Amman zamada itah yakare shiyanzu koson ganinta bayayi haryakai hospital din yana sake sake aikuwa sunsha banban danfitarsu kenan da sajida Usman yazo
opishin lawal yasoma tafiya yayimasa bayanie yace aiko yajidadi dan gaskiya abun atausayamata. Ne dantanajin jiki tare sukafito zuwa dakinda aka kwantarda ita
Suna bude kofar sukaga wayam tare suka kalli juna doctor yace to inakuma tatafi??? Kamar sunhada baki wajen fadin haka
Doctor lawal yafito Usman yabiyo bayanshi daki daki akayita nemanta ba agantaba haka sukayita tambayaa koda wani yagansu
Wasune sukace tabbas sunga wata mata tafita da itah cikin keken guragu akaje akatambayi masu gadi sukace tabbas wata mai bakar mota Amman cemasu tayi fita da itah za ayi kasar waje ""
Lawal yayita fada yace yaushe zakubari afita damarar lafiya irin wannan batareda annuna maku takardar sallamaba lallai kuna wasa da aikinku Saikusan yanda zakuyi kukare kanku danmuddin ba agantaba kuntashi aiki
Usman yamarasa bakin magana lawal yace Yakoma gida yaganie idan baisameta cenba sai asan matakinda za adauka yabar asivitin zuwa gida
Khadija suna zaune falo da labila tana bawa su anwar kamu saiga kiran kaleed da murmushi afuskarta tadauka tareda sallama daya bagaren aka amsa tace badai kana nufin harkun kawoba yayi murmushi munyi saurine tace ah mana""
Yace nikuwa naga kamar mundade ma tace naturo driver nasan yanakan hanya yace gawata farar mota naga ta tsaya kusa danie
Khadija tace ah shine saikazo
Yace OK yakashe wayar muhd yagama fkng din motar yafito yana kallon kaleed yace ikon Allah ashedai da gaskiyar hajiya alhaji yanada kani maikama dashi.
Yakaraso wajen kaleed yabashi hannu suka gaisa"" yacemasa yahanya?? Kaleed yace alhamdulillah Kaine akaturo kaje danie??? Yace ah nine hajiya tacemun kai kanin alhajine danaganka zanganeka gashikuwa Ashe haka kuke kamadashi
Saidai kawai kanuna masa kaidin sabon jinine kaleed yace ko??? Muje haka rana tana dukana muhd yace halan daga kasar waje kake?? Yayi maganar yana budemasa gaban motar yashiga
Kaleed yace meyasa kacehaka??? Tonaji kace rana tana dukanka kasan turawa sune basason rana mukan airana tagama duma mamu munyi lubus"" kaleed yayi murmushi yace daga gidan kankara nake dangarinmu koyaushe sanyine cikin ba a yayi maganar
Muhd yace haba saihaka Dan farin naka yabaci tolallai saidai karika yawo dalema dankuwa kafin kabar garin nan saikakoma kamarni sai in bajimawa zakayiba
Nima dakake ganina sanda nazo garin nan bazaka nunamun fariba kaleed yayi murmushi kawai yamaida kansa akan motocinda suke kaikawo saman titin
Suna kaiwa hospital din lubabatu tacewa driver yakaita gidanta Dan itah haryanxu bata tabbatarda maganar boka ba cewa yaranda suke bata tsoro amafarki yaran khadijane Amman shine tasheka masu karya tace wani waje tasamu kanta
Driver yace haba hajiya meyasa tunfarko bakisanar daniba saida nakawoki nan nifa hakuri kawai nakeyi wannan doyin yadameni
Tunsanda nadaukoki