nakejinsa haba cikina haryasoma lalacewa lubabatu damamaki tace hadi nikake gayawa magana??? Kamanta alkhirinda naimaka idan kamanta intunamaka asanadina sajida tadaukeka aiki
Dabadan niba daharyanxu kanacen kana bara akan layi yace nasanda haka kuma tundahar kinsamu abun gorantamun bakida lada inharkinyine saboda lada
Bayankuma aiki namaki kika samamun aikin yaja tsaki yajuya kan motar zuwa gidan lubabatu wlh Dabadan kar hajiya taji nashuka maki rashin mutunciba takoreni dasaman titin nan zanjuyeki gabadaya motar nan tagumie kamar inashakar mushe karama mushe wlh saiyakama kuka aini nashiga uku idanhar nakaiki lafiya bankwanta asivitiba azoyimun barka wannan aisaiki tashi karamin gari da doyinki waima menene yake wari ajikinki koduk rashin wankane????🤔
Kuyi hakuri dawannan wlh bañsamun lokaci[truncated by WhatsApp]
☠ *HATSABIBIN BOKA!!!*☠
PART 2⃣
20
By gentle
lady💃🏽
Wannan tambayar taba la in bawa lubabatu takaici afusace tace ah rashin wankane kamar yanda uwarka takeyi
Baki yarike yace lala hajiya harda zagin uwata daga tambaya ??? Uwatafa tarasu aiyaka mata kidaraja tsohuwa kodama tana raye ballanata tamutu
Kodayake Wanda baisan darajar tasa uwarba taya zaisan tawanie lubabatu tace wlh idan kacikani da maganganun banza sainasa sajida takoreka aiki
Dariya yafashe da itah yace aike hajiya yanzun duniya tadaina yayinki dake dabola duk daya koyanzun akwai dalilinda yasaka Tacema amiyardake dankar kibata mata gida da doyi koyanzuma aikin barmata tsaraba
Amman wlh hajiya duniya tajuyamaki baya dayawa ace kof guda wannan al Marin yakwabe maki niharkin soma banie tausayima
Tace uwarka dakai datausayin!" Nace uwarka dakai datausayin tausayi yaci gidansu nizaka nunawa iskanci nalurah tunsanda nashigo motarnan so kake kaga bacin raina
Yasheke da daariya yace Allah mai iko u um duniya akace juyi juyi dakwado yaganshi aruwan zafi kintuna sanda kikecewa waike bazaki shiga motataba nakaiki gida saboda karamar motace
Ai abunkunyane aganki babbar hajiya dake kinshiga karamar mota yanzukuma gaki acikinta kinafadi hajiya mai kuraje kinga yanda kikakoma yanda kikasan horo ke horoma yafiki kyau gaskiya yakamata kisomayin bara ba kananun kudi zakisamuba baiko gama rufe bakinsaba lubabatu tayanka masa mari tabaya jikake tasss saubiyu tadaukeshi damari
Yasaki sitiyarin mota yadafe kumatunsa biyu saura kadan motarsu tafada rami saida yaji anayimasu oda Yakama kan motar yacigaba da tafiya baicemata uffanba saifaman kyacci yakeyi
Sunkai wani guri inda bamutane sosai yatsayarda motar yafito yayi tsayinsa yama bata baya yakunna sigarinsa yanasha
Yabar lubabatu cikin mota zafi kamar zaikasheta taturo kofar cikin masifa tace waikai mekamaida mutanene??? Yan iska irinka kome kazo kakaini gida idankai bakada aikin yi ni inadashi
Baiko kalletaba saida yagama zukar sigarinsa yabude motaar yace karba tanada gokai yawanketa da mari hudu yayimata Jere dajuna sannan yajawota kasa tafadi timm yacire bel dinsa yahau dukanta kamar yasamu jaka yace bani kikaa maraba??? Saikinsan kinmareni
Lubabatu tanata ihu babu maicetonta danbamutane wajen saidai yara saida yamata lis tana kwance tasuma yazuge wandonsa yakwarara mata fitsari yana dariyar mugunta
Motarsa yashiga yatuka yabarta nan lubabatu tafarfado tanata tsine masa kukanma yabacemata wai itah wani katon banza yadaka
Yarane sukasoma taruwa sunakallonta saisukahau yimata wakar mahaukaciya mahaukaciya maitutu ga Leda wasu su amsa mahaukaciya
Wani yaro yace fuskarta da munie sukace mahaukaciya""
Wani yaro maidan girma cikinsu yace wlh wannan mayyace kukalli idanunta jajaye aikuwa gabadaya yaran wajen suka watse niesa da Itah suka koma sukahau jifanta sunaga manya gamanya
Wani mutumene yazo wucewa yayimasu tsawa gabadaya suka watse sannan yawuce dakyar lubabatu tamike tasoma takawa yarankuwa sukabita
Dama takusa dagida dankusan unguwarne Amman koyanzu akwai tafiya tunda batasaba tafiyar kasaba dole taji wuyarta
Usman yanakaiwa gidan ya aje motarsa yatasamma falon gidan yayi sallama yashigo su khadija suna nan inda yabarsu suka amsa masa sallama dayan kujerar dabakowa yaxauna yakwantarda kansa jikin kujera hannunshi daya yadafe kansa dayan yana rike da cikinsa
Yama manta rabonsa dacin abinci cikinsa yayi kukan yunwa haryagaji yadaina "" Sam komai yaficemasa arai haryanzu mamaki yakeyi ina lubabatu takezuwa hartakwaso wannan cutar yasandai batacika yawo sosaiba saikuma gida takirashi
Wata zuciya tace ah ah bahaka bane Aida masu gadi sun sanardashi khadija takalli labila"" sukajuya wajensa dakyar khadija ta iyah buda baki tace koyunwa kakeji inkawomaka abinci???
Yadan karkato yakalleeta saikuma yayi murmushi yagano fushi takeyi dashi Dan koyanzu fuskarta daure take magana" " yamaida kansa yana fuskantar sama yalumshe idonsa
Khadija tasake kallon labila itakuma tazungureta ahannu ma ana tasake tambayarsa
Murya kamar mairada tace dad"" baibude idonshiba Kuma bai ansaba tasake cewa dad"" batareda yabude idonba yace akwai matsalane???
Takalli labila itakuma tagyada mata kai"" tace ah"" saiyanzu yasake kallonta wannan karon babu murmushin afuskarsa yace inajinki meyafaru
Tadanja ajiyar zuciya tace cewa nai nakawomaka abincinka"" ?? Yasake gyara zamansa yace kinga alamar inajin yunwane konafadamaki dakaina???
Tarausayarda kai basaikafada ba ai ganinai kadafe ciki kuma rabonka dakaci abinci yaukwana hudu fa anayin rayuwa haka???
Yace hmm banajin yunwane gabadaya komai yaficemun arai""" khadija tayakuna fuska tace shikenan ina yanzu daga hospital kadawo
yasake komawa yakwantarda kansa yace ya akai kikagane??? Tace warin maganie naji wannan karonma murmushi kawai yayi saikuma shiru yabiyo baya
Khadija takauda shi run dacewa dad karamin tsaki yaja yace waimenene Dan Allah Khadija?? Nan zamanda kikaga nayi bakisan abunda yake damunaba
Tace Allah yabaka hakuri kamar tayi kuka dagajin muryanta kasan bataji dadin abunda yayimataba""
Shima yagane hakan yasake tashi zaune yace menene fadamun Amman dai Allah yasa bamaganar abinci zakisake yimunba
Shiru tayi saida yasake cewa uhun inajinki"" bandawani Abu khadija bazatasake maganaba Amman maganar tanada mahimmanci shiyasa tace dama sonake natambayeka anjima mushirya muje ganin mom
Hannunsa yana kan bakinsa yana kallonta baice komaiba
Tace please dad kacewani Abu mana koda bazaka barniba kabar sahiba taje
Katuna mahaifiyartace kuma tanada hakki da itah kamarkai Dan Allah kabarta tatafi dukda nasan itah bazataa iyah tambayarkaba
Amman inajinta duk da dare batakwana toilet takeshigewa tayita kuka kasan soyayyar Dada mahaifi sai Allah
Usman yakalli labila tayi saurin sanne kanta kasa tanawasa dayan yatsunta yamaida kallonsa wajen khadijar yace yanzun daga asivitin nake bansametaba!
Ancewai wata mata tazo damota tadauketa munyi nemanta bamugantaba "" yanxun gidanazo managani kotadawo nan ne Amman da alama banan tazoba kumanie bansan inazata shigaba dawan nan ciwon
Kuyi hakuri dawannan aiki nakeyi bansamu lokaciba
Aisha✍🏼
☠ *HATSABIBIN BOKA!!*
PART 2⃣
21
By gentle
lady💃🏽
Yadafe kansa dayaji yana Sarawa Khadija tace innalillahi to ina mom zataje ita dabatada lfy ????
Tace ganinan munafuka gaba dayansu suka dago kai har Usman suna kallonta"" karasowa tayi gabansu tacewa khadija Ashe kinada wasu yaran bayan wadan nan???shine kikaboyewà kowa
Khadija tasanne kanta kasa batace komaiba cikin fada lubabatu tace tambayarki nake kinyimun shiru
Labila tace haba mom yaxakiyi mata irin wannan tambayar??? Bayan kinsan wadan nàn ne yaranta nafarko lubabatu tadaga mata hannu alamar tayi shiru tace sonakeyi najii daga bakinta gaskiyane ko karya
tarage murya kamar maishirin yinkuka tace abunda yasa nakeson nasani wadansu yarane biyu sukebani tsoro sune sukahanani barci alhalin inajin barcin khadija dagaske kintaba haihuwar wasu yaran bayan wadan nan ??
Usman da labila Khadija kawai suka tsurawa na mujiya murmushi tayi mai daukar ma ana biyu tace Wanda yafadamaki haka gaskiya najinjina masa domin wannan Karon baiyi karyaba
Alokuta dadama yanamaki karya ciki kuwa harda daurewar farinciki aduniya bayankuma kuntauye tawasu taya zakaji dadin rayuwa bayankuma kacutarda wanie???
Tanisa tabbas yaranane kokinji mamakine ??? Yayanane hassan da husainie zunbur Usman yamike tareda labila sunamata kallon mamaki Usman yace khadija kina nufin kinada yara bayan wadan nan tosu waye ubansu nidai nasan budurwa na aureki totayakuma zakice kinada Yaya aiwannan zancen iskane
Khadija tace yayankane sune yayun su anwar kayi lissafi lokacinda mukadawo nayo tsaraba tosune yaranda nahaifa
Murya tanarawa yace to to inakika kaimun yarana??? Tabuda baki kenan zatayi magana wayarta tasoma ringing tadauko wayar tadauka daguntun murmushi tana kallon lubabatu
Tanarayawa aranta komai yaxo adaidai Hartana tunanin tayaxata sanarda Usman yanxukam komai zaiwarware
Tanadauka tace kunkawo??? Yadagakai yanakarewa gidan mahaifinsa kallo saiyanxu yakedan tunu yarintarsa agidan yashaki iska yalumshe idonsa yabude sannan yace ah munkawo
Tace OK kashigo ciki yanxu yace OK sannan yatasamma kofar shiga gidan" """
Khadija ta aje wayar tanabinsu dakallo tana murmushi tace mom barikiga wani abun mamakin Wanda yafi wannan yauxakisake tabbatarda rashin nagartar hatsabibi yauzakisan shidin bakomai bane bai isah yayi abunda Allah baikaddaraba tun akaina yadace kiyarda makamanki
Domin kinga darasi sainaganie shidin idan zaitsira daga hannun yarana"" labila tace waimeyasa kikehaka sahiba mahaifiyatace fa kikegayawa magana
Khadija tajuya damurmushi tana kallonta tace nasani labila danma tana mom ne nakedagamata kafa dabadan hakananba wannan ko darajar kare bazatayi awajenaba
Afusace labila tadaga hannu zata mareta kawai taji anrikemata hannu kafin tajuya tagawaye kaleed yawanketa da mari yace aiwannan kare ma yafita Dan koshi baxai aikata abunda ta aikataba
Gabadaya kusan tare suka kalleshi Usman Wanda yamike danshi yaga lokacinda kaleed yashigo fuskarsa yahau shafawa kamar yanagaban madubi waye wannan maikama dañie ????
Labiila ma bakisake take kallonsa tanadafe da kumatu tasake juyawa takalli dadynta murya narawa tace dad... waye wannan.???
Lubabatu kanta tarude idan takalli Usman tajuya takalli kaleed kowannensu tambayace abakinsa """ komawa tayi tazauna tace yayansu zauna mana bamusu yasamu kujerah yazauna yadorah kafadaya akan daya
Ganin kallonda suke binshi dashi yasa yadauko wayarsa yasoma latse latse
Usman yakalli khadija yace Deejarh kinsamu arudanie kuma kimbarmu datarin tambayoyi azuciyarmu shin waye wannan???
Khadija tamurmusa tace dama inajirane naji kokai ko mom waninku yatambaya sannan infadamaku yanzun kai baka ganeshiba???
Tajuya wajen lubabatu kema mom bazaki iyah tunawa dashiba??? Tayi dariyar jindadi tace Alhamdulillah nadade inajiran wannan ranar alkawarinda nadaukarwa kaina zandawoda kaleed gidansu yacika
Takalli Usman tace wannan yaronkane kaleed gaban Usman yabada rasss lubabatu kam saisakin fitsariii nikam nace kamar amalala kullum saifitsari kodayake nadolene dantsabar firgita batamasan sanda yake fitowaba
Khadija tacigaba shine babban yaronka Wanda kafara Haifa da matarka tafarko ameenatu mace tagari wacce kukai soyayya ta gaskiya Allah yahada kanku yadasa maku kaunar junanku rana daya akasamu wasu shaidanu suka rabaku. Harsukai sanadin mutuwar matarka wacce kakegani tamkar acikin mafarki kukai rayuwa
Dad ba mafarkibane gaskiyane katabayin aure kuma wannan shine yaronka gabadaya maganganun Khadija sukarika yimasa kuuuwa acikin kwakwalwarsa jiyake kamar anamasa magana da muryoyi daban daban
Kunnensa yadade dahannuwansa biyu yarumtse idonsa dakarfi yace karyane!""" Karyanee!"karyane!""
Saikuma sukaga yasulale kasa sume Khadija tareda kaleed sukayi kansa labila da lubabatu tamkar mutum mutumi haka suka koma.
Khadija tasoma jijjigashi tana kuka kaleed yace samomun ruwa please dasauri khadija tamike hartana faduwa tadauko ruwa takawo masa yaballe murfin ya yayyafa masa Sannan yashafamai afuska
Usman yasaukarda sassanyar ajiyar zuciya yabude idonsa ahankali yakalli Khadija wacce fuskarta Duk tajike da hawaye tana masa murmushi
Yajuya dakallonsa wajen kaleed yalumshe idonsa hawaye sukazubo masa tagefen ido hannun kaleed yalalabo yarike kam cen kasan makoshi yace kaleed
Cikin sanyin murya yace Na am dad Usman yafashe dakuka kamarwani karamin yaro
Aisha✍🏼
☠ *HATSABIBIN BOKA!!*☠
PART 2⃣
22
By gentle
lady💃🏽
Shima kaleed baisan sanda Yakama kukan ba yarungume babansa khadija kam dadi yakumeta sai murmushi take tana sharar hawaye
Batayi kokarin hanasu kukansuba saida sukai mai isarsu Usman ne yayishiru yasoma sharewa kaleed hawaye yace ya isah haka kaleed
Kadaina kukan nan """ yajuya dakallonsa wajen khadija yace ya akai kikasan kaleed bayankuma bantaba sanardake inada wani yaroba
Khadija tadagakai takalli lubabatu wacce taketa rusar kuka kamar ranta zaifita tasanyau dai karyarta tagama karewa
Murmushi tayi tace Anty maimunatu tasanardani yace wacece kuma haka??? Khadija tace wacce tataimakeni lokacinda aljani yadaukeni agidan nan
Dasauri Usman yatashi zaune yace aljani kuma Deejarh meyahadaki da aljani kuma???
Murmushi tasakeyi tana kallon labila tace ranarda mukadawo Dubai taredakai nakwaso gajiya sanadin hakan barci yashureni banyi adduaba da asuba inaji kana bugamun kofa intashi inyi sallah duk sanda zaka tayardani take naketashi Amman ranar dayake Allah yarubuta kaddarata aranar zanbar gidan nan
Inaji kawuce nasake gyara kwanciya kamar Cikin mafarki naji mom tana kirana tace mumbanie narasa labila wannan Kalmar takarshe danaji wato sunan sahiba shiya firgitardani gashi kasan nakirata ranar bansametaba da abun nakwanta shiyasa inajin tafadi sunanta nazama tatsaye dagudu nafito inacewa meyasameta bangama rufe bakinaba najikamar anbugeni bansake sanin meke faruwaba saikawai nabuda ido naganni cikin gajimare anagudu danie kamar iska yadauko karmami
Nan take nasoma addua saigamu munyo kasa saura kadan nakai kasa naji anchafeni ashewata aljanace sunanta maimunatu
Cen gefe ta ajeni alokacin harnasake suma dantsananin iskar dake sama tana ajeni nafarfado sai lokacin naga wani katon Abu kamar jemage Amman yalinkashi girma sau Dari danyakai girman dakie
Shine yacesaitabashi ni zaisha jinina itakuma tace bai isaba daganan suka soma dauki badadi tacigaba dabasu labari dai bayan daya haryanda akai takona hayyanul xairi dakuma yanda akai tasan inda kaleed yake
Khadija kenan dukfa wannan labarin datake bayarwa batafadi sunan lubabatuba
Kawai labari tabasu Amman batanuna tasan Wanda yayi aikinba takai karshen labarin dacewa tunsanda nadawo nakeson zuwa Niger badanwai naga dangin mahaifiyata bane ah ah
Kawaidai inason inga kaleed danna sanardashi waye mahaifinsa"" sanda kacemun bazaniba bakaji yanda najiba dankuwa namatsu naganshi dannaji tacemun kamarku daya dashi saikuwa gashi naganie takai karshen maganar tana murmushi
Usman yayi shiru kamar mainazarin wani Abu Sannan yace tonidai iyah tunanina kaleed ba bata yayiba yana hannun hajiya kawaidai nawayi gari Sam naman ta dashi tome yakai kaleed Niger????menene yafaru danie harnamanta nataba aure nakuma manta komai kosaudaya bantabajin inada yaroba yakalli khadija alabarinki akwai alamar aljanar nan tasanardake waye yakeson ganin bayanki Amman baki fadamun kowayeba
Khadija shiru tayi akaro nabiyu takalli labila itama kuka kawai takeyi sosai tabata tausayi itama hawaye suka saukomata
Tasa hannu ta share takalli Usman tayi murmushi yake tace bata sanardaniba nima kawai labarin tabanie kuma tundahar nadawo lafiya Allah baisa kwanana yakareba aikomai yawuce kamanta kawai
Takalli kaleed Wanda yasaki baki da mamaki yake kallonta idanuwa talumshe masa alamar yabar maganar haka
Usman yace yahausar haka kinanufin batasanar dakeba khadija akwai abunda kike boyemun"" tace bakomai Allah Indai baso kakeyi inyimaka karyaba bata fadamunba
Yanisa shikenan nayarda Amman ina kika kaimun yarana yanzun??? Tace suna saudiya hannun kakan maimunatu
Yace tome sukeyi acen kinga akawomun yarana bana son suma ahakalasu tagyara zama tace babu abunda zaisamesu kayarda danie tunda sukashigo duniya tabbas saisun aikata abunda yakawosu Daganan koda mutuwa sukai banda takaici zanyi alfahari dasu domin sunyi jahadi
Wannan karon Khadija takai Usman bango yace jahadin mezasuyi??? Batareda shakkar komaiba tasanar dashi aikuwa yahauta da fada bakida hankali yaran nawa zakisa akai gidan boka??? tokan wane dalili???
Damani nasan akwai abunda kike boyemun Khadija kifadamun menene gaskiyar lamarin nan
Kafin khadija tayi magana sukaji muryan lubabatu tace nizan fadamaka!!! Dasauri suduka suka kalleta khadija tasoma girgizamata kai alamar karta fada""" Usman murya narawa yace kekuma???? Tasake matsar kwallah tagyada kai!!!!!
Inabaku hakuri wallah yau banida lafiya shiyasama banyi dadan yawaba
Aisha✍🏼
☠ *HATSABIBIN BOKA!!*☠
PART 2⃣
23-24
By gentle
lady💃🏽
Gaisuwa tareda fatan alkhairi xuwa gareki takwara *AYSHA MAILITTAFI* naga sakonki Kuma nagode Allah yabar zumuncii . kamar yanda kikai addua Allah ubangiji yasa duk mai makamancin irin wannan halin tatuba tadaina domin sihiri baya dorewa duk sanda kikazama muguwar mace maicutarda mijinki babu makawa akwai ranarda zakiyi kuka da idonki
Idankuma kinada rabon shiruwa idan duniya tayimaki juyin masa saiki saduda kituba kikoma ga Allah tunda sauran lokaci
Kokinsan Allah baya karbar tuban Wanda yake gargarar mutuwa??? Hakan yafaru da fir auna lokacinda yaga bala i kirikiri yasan bazaitaba shaba
Duk wacce take aikata ta asa idan taga mutuwa fili dafili waisaita tuba dantasan tata takare wannan tubar Allah bayakarbar irinta daza ta tsilge tasamu tafita zakasamu takoma ruwa tamkarma komai baifaruba hartamanta wancen Abu
Misali idan mutum yana aikata sabo sai rashin lafiya takamashi maitsanani zakajishi yanata alkawullah idan nawarke zanyi kaza zanyi kaza
Wanima zaice indai nawarke babu shakka sainayi azumie koyace dazaran nawarke nadaina Abu kaza Amman dazaran yasamu sauki duk wancen abun yamanta idanma yafadi kwaraine wani yaji
Idan yatunamasa wane kacefa idan kawarke bazakasake yin Abu kazaba kozakayi Abu kaza saiyace kai manta kawai zafin ciwone yasa nafadi haka bakomaiba
Allah yakiyashemu Allah yasamufi karfin zukatanmu ameeen Allah yakaremu daga shairin shaidan da tawagarsa ameen
Yace kekuma menene naki aciki ??? Kotasanar dakene abunda yasameta???
Lubabatu tace ah ah Amman nasan komai Usman Hakika na aikatamaka babban laifi Wanda nasan dakyarne idan zaka yafemun
Nasan dazaran kaji bazakasake kallona da idon rahamaba taja ajiyar xuciya duk abunda yafaru agidan nan nice ummul haba isi
Nice nakesawa anakashe duk matanda kake aurah dakidaki lubabatu tasoma basu labarin komai harkawowa kan khadija
Usman jiyayi tamkar mafarki yakeyi "" tace wannan ciwon dayake jikina nice nakai kaina kuma alhakin khadijane yakamanie
Anan tasake basu labarin yanda akai takarbo maganie harwadanda sukaimata fyade dakuma yanda tafada maganin gabadaya wajen yayi tsit sautin kukanta kawai kakeji Dana labila
Usman kasacewa komai yayi danyashiga rudanie sosai
Takalleshi idanuwanta suna zubarda kwalla tace kayafemun Usman karkace zakarabu Danie wlh akankane komai yafaru soyayyarda nake makane tajawo hakan Kuma wlh nayi nadama
Wani mugun kallo Usman yawatsamata yace yanzu kikai nadama dakikaga komai yakwabe maki??? Tabbas nasan dazaki warke abunda zakiyi nangaba saiyafi wannan Allah nagode maka daka nunamata abunta tun aduniya wannan ciwon kadai ya isheki ishara dake dasauran mata masu hali irin naki
Tafashe dakuka tace Dan Allah kayafemun Usman wlh sharrin shaidanne
Murmushi yayi yace yanxun zakifadi haka baxancemaki komaiba duniyace gaki gata Allah sarki matata Ina zaman zamana da Iyalina saida kikazo kika tarwatsamun farincikina
Mikewa yayi yahausama dasauriii sukabishi dakallo baiwanie jimaba yadawo damabudan gida yajefa mata yace tashi kije gidana danake sauke baki nabakishi halak malak banason insake ganinki agidana
Kijecen kikarata"""lubabatu tahau kururuwa tace
khadija kisa baki yayi hakuri yanzun yazanyi dawan nan Ciwon katausayamun wlh inasonka bazan iyah rabuwa dakaiba
Usman yayi murmushin takaici yace Allah yawadaran wannan soyyayar taki wacce batada rana
Duk abunda kika aikata zuciyarki tabushe bakyajin tausayin rayuwa tayake kike tuna nin za aji tausayinki
Wlh koda bakida HIV baxansake zama dakeba kince soyayyarda kikemun ce takaiki wajen boka yanxun kinyi ba 1 ba 2
Datun farko kinyi hakuri kinrungumi kaddara tabbas danaje garinku na aureki Cikin mutunci kuma zanzauna dake
Duk abunda kika aikata lubabatu dakinyi hakuri dazaki samu abun nan cikin ruwan sanyi rashin hakuri dakuma garaje shine yake cutar mutane "" gashi yanxu duk abunda kike takamar kinsamu yakubuce daga hannunki kuma gayanda kika koma hakan zakimutu dawan nan ciwon
Lubabatu tace please Usman karkajuyamun baya kaima yanzun banida kowa Saikai ninasan koda naje wajen mahaifina bazai kalleniba gashi mom tahaukace
Kawayena duka sungujeni"" wacce nakeji da itah ma yautanuna mun iyakata
Usman yace kadanma kikaganie badai shaidan yabugamaki gangarsaba kintaka"" to wulakanci yanzun kikasoma ganie aiduk Wanda yasaka wani kuka bamakawa shima saiyayi kuka.
Yamike yakalli kaleed yasaki murmushi yace taso muje sama bamusu yamike Usman yaja Hannun khadija yawuce
Saida yayi taku uku yatsaya batareda yawaigoba yace kafin nasauko karnasameki agidan nan kibar ganin nayimaki dasauki wlh darajar yarki kikaci yanakaiwa nan yawuce abunshi haryanzu yanarike da hannun Khadija kam sunagaba kaleed yana bayansu.
Lubabatu kuka takeyi maiban tausayi labilace tatako indatake jiki sanyaye kamar wacce kwai yafashewa aciki
Gaban lubabatu taduke tasake fashewa dakuka cikin kuka tace mekika aikata hakan mom??? Meyasa kikabi rudin shaidan kika aikata manyan laifuka harda kisa mom
Lubabatu tace kiyi hakuri wlh yanzun nayi nadama, labila tace tunyaushe nake sanardake kuskurenki tunbayauba nake nunamaki illar zuwa wajen boka
Wannan ranar nake gudu tazo Amman bakijiba saida kikacigaba gashi ranar tazo kinyi nadama aloakacinda nadamar batada rana
Bazance Allah bazai yafemakiba Dan Allah gafuru rahimunne Amman saiyaduba zuciyarki yatabbatar dagaske kikeyi bawuyace tasaki nadamaba
Koda Allah yayafemaki mom wadanda kika cuta basu yafemakiba danbasa duniya
Yanzu gashi kinga illar yarda da makaryaci dubi yanda kika koma atunaninki soyayyace tunfarko tasaka yakemaki aiki??? Kodaya danshi yabacene shiyasa kuma yabatar daku danyasamu abokan shiga wuta
Menene ranar haihuwar irin wadan nan mutanen aduniya domin kare yaronka dagafadawa mummunar sana a makamancin wannan satane kokuma fashi da makami uwa kikasance kinacin abunda yakasance na halak karkiyi yaki halat yaki haram
Uba yarika tsaftace dukiyarsa daga cin riba bangaren kasuwancine ko sana ar hannu !" Sannan idan zaiyi aure yasamawa Yayansa uwa tagari
Aduk lokacinda zaitara da iyalansa yatabbar yayi addu a idanshi baiyiba kekiyi saboda duk lokacinda wani zairaya dare tareda matarsa shaidan yanakusa
Danyarantse shikuma duk sanda za kayi jima I damatarka totaredashi zakuyi tare zaku saka alkalaminku danashi kazuba maniyinka shima yazuba idan alokacin Allah yakaddaro Daren zakusamu karuwa kaga kenan Dan nakane kuma nashaidane
Shizaisa kaga anhaifi yaro kangararre gagare yagagari kowa har iyayensa baya shakkar kowa idan akaturashi islamiyya yayi wajen wasar banza
.
Kai wani yaron dakaganshi kasan irin shaidanne saikarantsema shaidan yayi rainonsa danbashida imanie kokadan kazo kahaihu kahaifawa mutane bala i adoron duniya
Hartakai uwa tana kuka tana Allah wadarai da haihuwarka tace dama barinka nayi nahuta dawan nan bala in wannan babban kuskurene awajenki
Kisani wannan ma kaddararkice tayiyu kema akwai abunda kika aikata sai Allah yahoraki Tawan nan hanyar
Kinazubar masa dahawaye bakisan wani babban bala ine kike sake jefa rayuwarsaba tunkinayi bayansa kinayi gabansa
Dazaran yayi Abu kihaukuka kina ni asabe wannan yaro ka asheni kamar dandan Allah banie wa iyaxubillah kinanufin dandakika roka Allah yabaki kenan bazaibaki nakirkiba?? Wannan izgiline babba
Sannan kukanki agabansa zaisa zuciyarshi ta kekyashe yaga yasa nahaifiyatai kuka aikuwa komai zai iyah
Idan kuma kina aibatashi sannu kanhankali zaisake lalacewa irinsune sukezama miyagun yanfashi marasa imanie sutareka sukarbe kayanka sannan sukasheka babu shakkun komai aransu
Basa tunanin haduwarsu da Allah totaya zasuji tausayinka bayan basajin ta iyayensu zuciyarsu tabu she babu sauran imanie ajikinta
Wanda yakeda dansauran imanin shizakasamu koda ance yakashe wani inyan uwansa sunbada baya saiyabarka
Kinga kinhaifi annoba keya gagareki kinbarwa duniya Manzon Allah Annabi Muhammad (S A W) saiyakoyar damu adduar da zakayi domin gujewa shaidan "" *Bismillah Allahumma janab naa'shaidana wajanie 'shaidana marazaktana ""
((( بشم الله. اللهم جنبنا الشيطان؛ وجنب الشيطان مارزقتنا)))
Mom neyasa kikai haka meyasa"" tasake fashewa da kuka lubabatu kamar ranta zaifita tace kidaina kukan nan haka labila abunda na aikata rudin shaidanne dakuma Neman duniya namanta Duk abunda yake rabonka saika sameshi duk hadamarka baxakataba cin rabon waniba
Aisha✍🏼
☠ *HATSABIBIN BOKA!!*☠
PART 2⃣
25
By gentle
lady💃🏽
Ninasan na aikata babban laifi Wanda kowayaji saiya kwana yana la antata"" kiyafemun labila domin nasan nacutarda rayuwarki sosai
Labila tace mom yanzun kinga illar miyagun abokai ko??? Ada idan inayiwa kawayenki rashin kunya harzagina kikeyi
Kina tunanin sunfini sonki bayankuma bahaka bane ni inagujemaki fadawa halakane
Duk abunda kikai nasan kinayine saboda Abu uku nadaya soyayyar dad dakike ikirari kinayi gashikuma yanzun sanadin zuwa wajen bokan kinrasashi rashi nahar abada
Nabiyu saboda dukiya idan mijinki yamutu yazama kece kawai zakimallaki duka kadarorinshi toyanxu ina wannan burin??? Kinrasa komai
Na uku kinaso acikin kawayenki ace kinfi kowa yanxun gashi sanadin zuwa wajen boka yajamaki kinrasa wannan darajar babu Wanda yakeson zuwa kusa dake
Kawayenkin yanzun inasuke??? Ina bokan yake ayanxu??? Allah shine kawai zakidogara dashi shine bayagajiya da bawansa aduk sanda kika rokeshi zaibiyamaki bukatarki batareda yagindaya maki wasu sharadiba ko yaushe ko a ina kinada garantin rokon Allah
Mezaikaiki wajen wani kato fasiki"" lubabatu tace dangirman Allah labila kidaina maganarsa wlh natsani inji anama tunamun dashi nidai inarokonki kiyafemun
Labila tashare hawayenta tana girgiza kai tace bakiyimun komaiba mom " tamike tashi narakaki gidan
Lubabatu tace ah ah kizauna wajen mahaifinki idan kikabinie zakisake jefa rayuwarki acikin hadari
Tabonda naiwa rayuwarki ya isah haka kihau sama kidaukomun key din motana labila badan tasoba haka tadauko mata key tarakata harbakin Mota tashiga tafita daga gidan tanawaigensa tana hawaye labila tabita dakallo tana sharar kwallah
Su khadija bangaren Usman suka shiga cikin falonsa "" saman kujera suka zauna Usman dadi duk yakumeshi
Khadija sai sharar hawaye takeyi dansosai mom tabata tausayi"" Usman sunata firah da kaleed yana bashi labarin Niger dakaratunsa ""
Yakandan juya yakalli khadija haryanzu batadaina kukan ba karamin tsaki yaja yace waike lafiya kiketayiwa mutane kuka???
Shiru tayi yatabe bakinsa atunanina komai nayiwa wannan matar baidace kiji haushiba kinsan abunda ta aikata yafigaban atausaya mata
Khadija tace nasani dad Amman ai sahiba zakayiwa kara katausa yamata kodan yarta murmushi yayi kinanufin hukuncina baiyiba kenan
Yagirgiza Kai iya tausayawar dazanyimata kenan yakikeso inyi darabani da yarona datayi kokuma rabanie da matata???
Khadija shiru tayi yadanyi Jim sannan yawaigo gareta yace maganar yarana kifadawa antynki tadawomun dasu ne banyarda akaisu wajen wannan bokan ba
Khadija tayi saurin dago kai takalleshi yagyada kai yanxun Deejarh duk rashin Imanin mutumen nan harzaki yarda kibada yaranki
Arasa wazaiyi jahadi saisu haba kiyi tunani mana " khadija ta share ragowar hawayenda suka zubomata tace inazanganta???
Tunda bamutum bace dad?? Yanzun bazaka sadaukar da yarankaba domin kaceci dubbanin jama a??? Rayuwa nawa kasan wannan mushurikin ya salwantar ciki harda mahaifiyata tafashe dakuka maitsuma zuciya. Take usman yaji hankalinshi yatashi""
Dasauri yamike Yakoma kujerarda take kaleed tashi yayi yasauka waje"" Usman yanakiranshi yadawo waigowa