Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
5 / 9
yayi kawai yayi murmushi yafita Usman shima murmushin yayi yajawo khadija ajikinsa yana Shafa bayanta sorry Deejarh bansan abun yataba mahaifiyarkiba kiyi hakuri badawata manufa nafadi hakanba kawaidai kinsan dole naji tsoro ace yarana zasuje wajen wannan axzalumin "" Dama saboda wannan ne yayanki yace bazaibawa maimata kanwarsaba khadija tagyada kai "" yace Allah sarki wlh yanada gaskiya nikaina zan iya cewa bazantaba bari Yayana su auri mai mataba Amman banida hujja tunda nima gashi an aureni Khadija murmushi tayi tashige jikinsa"" damadai sunyi missing din junansu danrabon dasu hada jiki tunkafin taje Niger Gashi Usman yashiryawa Daren saigashi yayi katari da labarin rashin lafiyar lubabatu daga rarrashi su Usman sai akazake yasunkuce abarsa zuwa dakinsa yaturo kofa Kaleed cikin takunsa yake taka matakalar yana sauka kasa sosai yake kallon yanayin gidan saiyake ganie kamar yanatare da mom dinsa acikin gidan Labila tana zaune saman kujerah tabuga tagumie tanajin takun takalma tayi saurin mikewa tana kallon kaleed kallon sama dakasa yayi mata yadauke kansa zaiwuce Tace ya kaleed"" chakk yatsaya saiyaji kamar zainab dinsace takirashi batareda yajuyoba yace wat!!cen kasan makoshi Kalmar tafito labila bataa damuba tace Dan Allah kayi hakuri Yace laifinme kikamun??? Nibakya cikin tsarin wadanda zansaka acikin tunanina dahar zandamu da abunda kikai inasodai kisan wani Abu koyayane wannan matar tagirmeki tunda har take auren mahaifinki baidace ko mugun kallo kiyimataba balantana hartakai kidaga hannu daniyar marinta agaban mahaifinki .yanxun kina tunanin shiyaji dadi ko itah taji dadi??? Labila kuka tasake fashewa dashi lallai tayi laifi babba yau ita dakanta tadaga hannu zatamari sahibarta"" kaleed yanaganin tasoma kuka yasakai yawuce abunshi Yana fita harabar wajen inda ake aje kujerah karkashin wata runfa maikyau yanufa yaja kujera yazauna wayarsa yaciro cikin aljihunsa Lambar zainab yakamo yadanna kira hartayi ringing takatse bata daukaba saida yasake Kira tadauka "" tayi sallama cen kasa kasa yaji muryanta dakaji kasan tasha kuka yace lafiya kanwata naji muryanki tasauya??? Taja ajiyar zuciya tace bakomai harkakai??? Yashafo sumar kansa sosai yanajin dadin iskanda yake kadawa maidadi "" yace nakai tundazu"" Tanisa shine ya kaleed koka nemeni"" guntu murmushi yayi yace afuwan abubuwane suka sha gabana"" tace bakomai kagaisheta ""nasan yanzun haka kuna tare Yasaki murmushi maidan sautiii yace aibaxan iyah magana dawataba muddin munatareda itah gatanan tafito dama tashiga daukomun wani abune korufe bakinsa baiyiba zainab takashe wayar kaleed mezaiyi inba dariyaba Aisha✍🏼 ☠ *HATSABIBIN BOKA!!!*☠ PART 2⃣ 26 By gentle Lady💃🏽 Sosai Zainab tabashi dariya sake kiran wayar yayi yajita kashe yayi murmushi sannan yakirah hassan suka gaisa Yace masa ya isa lafiya??? Yace qalau " yace dad nakira Kanwata yanxun naji kamar tayi kuka me akaimata??? Murmushi yyi yace mekamata dai""" kaleed yace nikuma??? Yace kaifa bakaika padamata Neman matarda zaka aurah kajeba"" aitun sanda kabar gidan nan ko magana batayiwa kowa """ kaleed ya murmusa yace zan rarrasheta ai Amman dad tadaici abinciko??? Bansaniba saidai katambayi mamanta"yace shikenan hassan yace yakasamu mutanen gidan??? Yashafo fuskarsa yace qalau suke saidai dayar matar batada lafiya dad bakaga yanda tazamaba wajen Neman duniya takai kanta tabaro yanzun harda cutar HIV ne da itah Yahau sallallami kunji aikin jahilci dama duk macenda zuwa wajen boka yaxama aikinta aikuwa baxatayi karshe maikyauba Allah yakaremu daga fadawa tarkon shaidan Allah yakaremana kunnuwan mu dajin sautinsa kaleed yace ameeen daganan sukacigaba damagana Lubabatu tana saman hanya tana kuka ko acikin mafarki bata taba tunanin wata makamanciyar rana irin wannan zatasameta ba Saiyanxu take danasani meyasa tunsanda labila take lurarda itah illar abunda takeyi tun alokacin yadace tabari yanzun menene amfanin nadamar batada amfanie tunda gashi tarasa komai.. Babu Wanda yacuceta sai iyayenta suda suka kasayimata tarbiya takwarai neman duniya kawai sukasama gaba"""" Koda takarasa gidan duk yayi kurah dagabakin kofa kadai zaka tabbatar unguwar shiru take babu mutane sosai haka tafito cikin motar tana tafiya dakyar tabude gidan sannan taja motar tashiga""" Tunda tashiga gabanta yake faduwa saitsoro takeji towandama bai iyah Addua ba aidole tsoro yakamashi Tanashiga falon taxauna"" tanata yan kalle kalle. daga bisani tadan gincira dantagaji dazaman Har magariba takawo jiki lubabatu batayi komaiba tanazaune tana karatun wasikar jaki jitayi kamar ana motsi bayanta dasauri tawaiga bataga komaiba saitaga anwurga tagabanta kamar mutun gashi gidan yasoma duhu ko nepa babu mikewa tayi daniyar fita saiga nefa takawo gabaya haske yagauraye gidan tasaukarda ajiyar zuciya sannan takoma tazauna duk datanaganin haske wani bangaren zuciyarta baidaina jin tsoroba tanazaune har akai isha duhu yagama mamaye ko ina harbarci yasoma dibanta danyanzun batajin masifar kaikayi kamar da Tasoma gyangyadi kenan saiga wutar gidan tasoma rawa kamar iirin anaruwan saman nan" "" firgigit lubabatu tafarka tahau yan kalle kalle ko mintuna goma ba ayiba kayangidan sukasoma rawa hatta fankar falon dakujeru rawa sukeyi saitaji Anfara cida gashikuma ba lokacin damunaba Cikin kaduwa tamike tayi kofar fita dasauri kafin takai akaja kofar jikake ramm akarufe dasauri takai daniyar rike marikar kofar saitagajini yana diga ajikin abun cikin tashin hankali tahau duba hannuanta kodai yankewa tayi bataga komaiba saitaji mutum abayanta Gabanta yahau dukan Tara Tara ahankali tasoma juyowa cikin tsoro da fargabar mexata ganie. Ihu takwatsa Wanda yakarade ilahirin unguwar duka hankalinsu ya tashi sunji ihu Amman basusan daga inda yafitoba Dalilin ihun lubabatu kuwa tanawaigowa tayi katari da samrat """" cikin mummunar fuska bakinta yajuye hakoranta zalan xalan taturo harshe yana dalalarda Jinie . .idonta daya asaman goshi dayakuma bisa kuncinta lubabatu tana kwamtsa ihu samrat Tashakureta ko kwakkwaran numfashi takasayi Sosai tashakureta lubabatu sai kakarin mutuwa takeyi dakyar tasamu takwakule hannun samrat daga wuyanta tafita dagudu tana bude wata kofa Ashe kitchen ne tafada aikuwa kamar walkiya saigakuma samrat tafito lubabatu tasoma jadabaya duk fawannan abun datake haryanzu kukatake takaici daya batasan yazatayi addua aba domin tatsira sai ihu takeyi tana Neman agajie Mutanen unguwar sunajin ihunta sunfito kofargida Amman basu shiga gidanba dansunganshi kulle da kwado suntabbatar bakowa cikin gidan watakil sautin daga wani wurinne daban Haka suka kare dube dubensu suka koma gidensu Amman basudaina jiyo iface iface ba" lubabatu tararumo wani kwano takwadamata akai kogezau batayiba Komai tasamu tajefa mata Amman gabanza tasake kaimata shaka cikin lalabe lubabatu tajawo wuka talumamata gefen wuyanta saiwukar talume maimakon taga tafadi saita tintsire da dariya Nantake tabace wata murya taji marar dadi tanacewa dagayau lubabatu kinyi Bankwana dajindadin ayanda tasanadinki narasa maatata Yayana matsayina kwanciyar hankalina duka nayi Bankwana dasu Kema yazama dole saikinrabu dasu narabaki da mijinki yarki mahaifanki narabaki dajindadi kisani bazantaba mutuwa nidayaba dole mu mututare yanagama fadar hakan saigashi yabayyana cikin mummunar shiga take lubabatu takwallah kara tazube wajen somammiya ************* Tunsanda kaleed yafita gidan yabar labila tana kukan nadamar abunda Taiwa Khadija Khadija anacen ana soyewa saida akayi kiran la asar Usman yayi wanka yasauko kasa labila tana ganinshi tamike kallo daya yamata yadauke kansa yawuce bakinta tatoshe saboda kukanda yazo mata shikenan maganar ya kaleed ta tabbata dad yana fushi da itane yana fita sukai cikibis da kaleed zaishigo sunahada ido kaleed yasanne kansa kasa Usman yayi murmushi yace inakaje tundazu??? Cikin jinkunya yace banyi nisaba nadan zagayane inga unguwar"" Usman yayi murmushi yace yazakafita kaida bakasan gariba karfa kabar gida kakasa dawoda kanka Kaleed yayi dariya maidan sautii yace bazan bataba dad yanzun ma tareda wannan maisurutun mukatafi Usman yace waye kuma maisurutu??? Kaleed yace Wanda yadaukoni airport"" Usman yace muhd kenan kaleed yagyada kai Usman yace jeka dasauri kayo alwala muje masallaci kaleed yace to sannan yashiga gida" Tare sukaje masallaci kowa yagansu saiya tambaya waye dankamar tabaci yace masu kaleed ne sukanyi mamaki inayashiga tsayin shekaru harsuma suka manta dashi saiyanzu wadanda sukasan amenatu suke tunowa da itah Shikuwa Usman cemasu yakeyi wajen Yar uwarsa yake shiyasa sukadaina ganinsa"" bayan sundawo sallah yakai kaleed hangarensa yayi wanka sukafita Yawo tare Saidare suka dawo kaleed Rabin hankalinsa yanawajen zainab danharyanzu baisake samuntaba Dadarema saida sukaraba dare suna firah labila kasa zama tayi acikinsu tashige bangaren lubcy idanuwanta duk sun kunburah saboda kuka ************- Kamar an mintsileta tamike zunbur tasoma kallon wajenda take tana kallon jikinta tatuno da dalilin sumarta kuka tafashe dashi tace nashiga uku meya aikeni gashi inacikin masifa waye zai taimakeni Kuyi hakuri kwana biyu bakujiniba banajin dadi kuma saigarashin nepa shiyasa nadaina hawama"" Nagode sosai da kulawarku gareni naji sauki sosai Allah yabar zumuncii ameeen Sakna Adam nagode sosai da soyayyarki agareni Salimat annuri naga sakonki nagode sosaiii Kema tauraruwace *Aisha mai littafai* nayi katari da sakonki banada bakinda zanyi jinjina agareki saidai nace nagode sosai dakulawarki Magana cikin sanyin murya yan uwana Allah yasa ba soyayyar novel kukemunba saboda duk soyayyarda aka dorah tubalinta akan wani dalili bamai dorewa bace Inaso duk Wanda zaisoni yasoni Dan Allah sannan yakinie Dan Allah duk Wanda yakesona Dan saboda novel banajin nidin zansoshi banasonma soyayyar tashi Kugina soyayyarku akan tubali nagaskiya wato saboda Allah har abada zakuga daidai bawai nishadiba inaso kufahimceni nagode nidai inasonkuu wlh saboda Allah badan wani daliliba Aisha✍🏼 ☠ *HATSABIBIN BOKA!!!*☠ PART 2⃣ 27 By gentle Lady💃🏽 Cikin tsoro tadawo falon komai Yakoma yanda yake tamkar babu abunda yafaru kanta bako dankwali tayi hanyar waje dagudu dankuwa taraya aranta baxata sake kwana agidan ba kuwwa tasakeyi sakamakon kofarda taji da kwado tayita jijjiga Amman taki budewa saida tagaji Dan dole tahakura wajen taduke tana sana arta Lallai rayuwa juyi juyice waiyau itane anan kamar wata almajirah""" cikinta saikukan yunwa yakeyi wannan dalilin yasata komawa cikin gidan ba waidan ranta yanasoba Khadija tunda safe tahau hadamasu break Dan Usman yace kano zasuje da kaleed""" Bayan tadora abun karyawa tahau sama dakinda takesaran ganin labila"" tana kwance tsakiyar falon dakin lubabatu tanajin sallamar khadija tatashi zaune Amman kanta yanakasa Dan sosai take jin kunyar khadijan Fuskarta dauke damurmushi takarasa inda labila take zaune taduka sannan tadafata tace menene duk wannan kikeyi kindaina zama cikin mutane yanxun ne yadace kisabu dadan uwanki zamnki cikin dakin nan bayayimun dadi sahiba Labila cikin muryar kuka tace dan Allah kiyi hakuri abunda naimaki khadija tace mekikamun??? Aini dadima naji dayazama kinsomajin son mom aranki ai uwa uwace nibanga laifinkiba kuma banrikeki arainaba"""" labila tafada jikin khadija tace yazanyi sahiba na aiikata kuskure dukda nasan halin mahaifiyata kuma nasan naki Baidace raina yabaciba harnadaga hannuna daniyar kaiduka gareki kiyafemun kiyafemun tasake fashewa dakuka Khadija tace ya isa haka Mana nafadamaki nibakimun komaiba mezaisa kidami kanki kinga tashi kiyi wanka kafin nan nagama hadamana abinci saimuci Tayi maganar tana sakar mata murmushi bamusu tamike tashiga toilet sannan Khadija tafita takoma kitchen Kaleed yana kishingide saman gado waya tanarike a hannunsa tunjiya yakeneman layin zainab anacewa kashe take yanzun ma tashinsa barci kenan yadauko wayar dankam inhar batashigaba mom zaikira yace akaiwa Zainab Saigashi cikin sa a yanakira tashiga dasauri yatashi zaune jiyayi kamar angafartamasa Allah Allah Kawai yakeyi tadauka Hartayanke batadagaba''" saida yasake Kira takusa yankewa sannan akadauka """ yayi sallama ciki ciki ta amsa masa Murmushin gefen baki yayi yace kinkyauta abunda kikamun???? Shiru tayi yace shikenan tunda bazakiyi maganaba Dama nabugone insanardake"" mundaidaita dawacce zaan aura cikin satin nan zandawo saisu dad suzo sunemamun aurenta Kobakinsa bairufeba Zainab tafashe da kuka wayar yajaye akunnensa yahau dariya saida yayi mai isarsa sannan yagimtse yace tosai an jima kanwata gashi kiranta yashigo wayana Cikin kuka tace baxan kasheba wlh saidai tahakura kaleed yace haba yazakiyimun haka matar tawafa Kishine da ita banason ranta yabaci Tace kambu harma taxama matarka wlh nibanyarda ka auri kowaba "" kaleed yawaro ido kamar tana gabansaa yace sabodame zakicehaka ??? Gashinikuma inada bukatar kasancewa tareda ita Zainab tasake fashewa dakuka tace sokakeyi namutu ya kaleed mezaisa bazakayi azumiba mucigaba dazaman mu haka Yace tab nikam yanzun bazan iyah hakuraba saina aure ta!!! Gaban Zainab yabada rasss tace nashiga uku wannan wace iriin yarinyace Yace kamarki take danma nayimaki kara sainasamo mai irin sunanki"" zatayi magana saiga Usman yashigo dakin cikin shirinsa kaleed yana ganinshi yacemata sai anjima zankiraki baijirah jin mezataceba yakashe wayar Saikuma yasanne kansa kasa"Usman yayi murmushi yace yasunanta??? Cikin jinkunya yace Zainab Osman yagyada kai yace a Niger take??? Yace ah kanwatace yarsu mom ce Yasake yin murmushi yace tashi muje muci abinci saimu wuce dagabaya zamuyi magana"" kaleed yaji dadi sosai Dankaran kansa baxai iyah yiwa mahaifinsa maganar Zainab dinba duk da amatseyake da son auren Usman yafita sannan kaleed yamike yadanyi ihun murna yanaushi Iska dahannunsa"" sannan yafita yasamu duk suna xaune harda labila dukda tanacikin Dari Dari kamar wacce tai karya tagaida kaleed ya amsa bayabo ba fallasa sukasoma cin abincin su bayan sungama khadija tarakasu hargaban motar saidataga tashinsu sannan tadawo gida Tayiwa su anwar wanka tabasu abincinsu""' tabarma xahara u su tadawo falo wajen labila ********* Motarsu kofar gidan hajiya tatsaya" yana murmushi yakalli kaleed yace kashiga gidan nan kace hafis nanan yace to sannan yafita Kaitsaye yashiga gidan yayi sallama hafis Kuwa yanagidan tareda hajiya " ya amsa sallamar sannan yace waye yashigo Kaleed yatura kofa yashiga tareda sallama abakinsa kusan taresuka kalleshi saigashi sunzama natsaye suna kallon kallo Bakin hajiya sai motsi yakeyi tace waye kai?? Kaleed ya yamutsa fuska yace dadyna yace nashigo nan ince ana sallama da hafis " hafis yace waye dadyn naka??? Kaleed yace idan kafita zakaganshi harzai juya saiga Abdul yafito daki yana cewa hajiya dubakigani nayizanen Baigama rufe bakinsaba yaga kaleed yace dad yaushe kaxo turo kofa akai da sallama Usman ne yashigo da murmushi afuskarsa kaleed yace dad kashigo """kusan taresuka hada baki wai wannan ne dadyn naka Kaleed yagyada kai kujerah Usman yanuna masa yace zauna kaleed. Daga hajiya har Hafiz jisukayi kamar wani Abu yabugarmasu kai sukace kaleed?? Hajiya tafashe dakuka tace inakashiga kaleed tsayin shekarun nan baka tabazuwa inda nakeba" Usman yaxauna yace hajiya kizauna Tazauna Amman batadaina kukaba tana kallon kaleed Usman yanisa yace hajiya saimu godewa Allah domin kwanan kaleed ne agaba dashima yaxama tarihi kamar mamansa Hajiya ta share hawaye tace banfuskanci mekake nufiba babangida meyasamu maman tashi?.? Usman yanisa wani Abu yaji yatokaremasa zuciya sau goma zaituna lubabatu ce taisanadin rabashi da matarsa saiyaji yasake tsanarta cikin zuciyarsa hajiya tace babangida waime yake faruwa kasanardani mana Saida yasake Jan numfashi Sannan yabata labari aitunkafin yagama hajiya xufa yasoma karyomata!"" Kuyi hakuri dawannan don Allah Aisha✍🏼 ☠ *HATSABIBIN BOKA!!*☠ PART 2⃣ 28 By gentle lady💃🏽 Hmm. Sister na naga sakonki "" kuma nagode Amman baki karanta abunda nafada sosaiba idankuma kin karanta baki fuskanci mena fadaba babu kuskure acikin maganata Duk abunda zakayi aduniya matsawar basaboda Allah zakayishiba baida amfani kwarai akwai Sanadi zaiyiyu inason wance saboda tayimun alkhairi kaza Amman kuma sonda nakemata saboda Allah ne.. Sister duk Wanda zaisoki akan wani dalili bawai Dan Allah ba dazaran kinrasa abun nan zaidaina sonki """ inason masoyanda kobayan raina zasurika tunawa Danie suna sakani acikin addua Akwaisu nasani kuma akwai wadanda kawai dannishadinsu suke sonki bilkisu shin zakiyi alfahari da masoyinki Wanda baitunaki saidan saboda wani Abu?? Dazaran fa bakyatare da abun shikenan soyayyar takai karshe ni aganina da irin wannan soyayyar karama rashinta Sosai inason masu sona saboda Allah nimakaina inasonsu saboda Allah kuma nakasance ina alfahari dasu sosai Bilkisu nagode kwarai banida kamarki kinsanfa ko shawara masoyinka shine yake baka itah gataki jinjinar👍 Tasoma sharar kwallah tace yanxun lubabatu wannan aika aikar tayi kamar ba musulmaba??? Habaa me akeyi darashin imani kamar waacce bazata mutuba"" Usman yace to hajiya idanke kinsan haka ai itah batasan hakanba . Babu tayanda zakihada jahili damai ilimi" idan mutum yanada ilimie akwai Dan dama dama koda zaaiyi barnar maisauki zaiyi Hafis kuma shiko magana ma kasayi yayi danshi mamakima yake wai lubabatu ce tayi wannan danyen aikin hajiya tashare hawaye tace yanzun ina lubabatun take,??? Inafatar bagidanka kabartaba danwannan annobace zama da itah babban hadarine Ohh ni binta Allah sa yaran nan karsuyo wannan mugun halin dabakin kishi. Suka amsa da Ameen Usman yasanarda itah yanda sukai yabata key din tsohon gidansa wanda yake saukarda baki Hajiya tace aikara haka Allah yashiga tsakaninmu da wadannan mutanen ameeen."" Suka cigaba da tattauna maganar lubabatu Allah sarki shiyasa akeson bawa komai zai aikata ya aikata abun kwarai Tokuwa har abada bazaitaba tabewaba ina amfanin badi barai yanzun duk Wanda yaji abunda ta aikata saiya la anceta hakan ynada dadi Su Usman basu Bar kanoba saikusan goshin margib sunsha yawo kaleed yaga gari suna kaiwa kaduna ana kiran sallar isha i Alwala kawai sukayi sukawuce masallaci "" bayan an gama sallah Kaleed yariga Usman fitowa danyanxun hankalinsa yana wajen zainab Gashi yace zaikirata baikirataba yanzun zatasamu damar cewa yamanta da itah Kaitsaye dakinsa yanufa saman gado yazauna sannan yadauko wayarsa yakamo number ta yadanna calling""" Tasoma ringing batadauka ba saida takusa katsewa akadaga""" yayi sallama maimakon ta amsa saita fashemasa da kuka Gabadaya kaleed yarude yace innalillahi Kanwata lafiya me akaimaki waime yasa kuka bayayi maki wahala?? Dan Allah kidaina kukan nan wlh banason jin kukanki harciki zuciyata nakejinsa please kitaimaka kiyi shiru kinji waye zaibata maki rai alhalin kinada kaleed dinki ahannu Haba tawan kodai nine naimaki laifi??? Kiyi hakuri sarauniyata baza asake ba saiyanxu tayi magana Dan maganganunsa sunsa taji Dan sanyi sanyi aranta Tace ya kaleed nidai kadawo hakanan Dan Allah sonakeyi naganka"'' ido yawaro yace rufani mana annurin zuciyata yaushe nazo dahar zance indawo kwana dayanefa kawai nayi . Tace waine awajenka ko?? Aini kam kwanan nan daya jinsa nakeyi kamar wata daya inason ganinka please kadawo hakanan..cikin muryar kuka tayi maganar Kaleed yadafe kansa bayajin dadin kukan nan nata kokadan yana konamasa rai""" yace naji kidaina kukan nan"" ta share hawayenta tace zakadawo goben ??? Shiru yayi saida tasake magana yace zeena! Bangama abunda yakawoniba kiyi hakuri zuwa sati daya Dan Allah aigashi muna waya kullum nikaina nayi kewarki Baki ta tabe kamar yana ganinta tace wlh bawani kewana dakayi Dazunfa cewa kayi inbari kakirah nayita zaman jiranka saiyanzu katuna dani kana cen wajen wacce tafinie Kaleed yace ina kanwata aibabu wacce tafiki awajena duk fadin duniyar nan yasake gyara kwanciya kinsan ana iya sake mata ko budurwa Amman baxaka iya sake Yar uwaba saboda jininku daya kawaidai xan aure tane dantana sona Ya kaleed waime yasa bazaka fasa auren nan ba please muzauna warmu ahaka yashafo kansa yace bazan iyaba Tace sabodame?? Aransa yace saboda kece matar Amman afili saiyace nariga nayimata alkawari banaso tadaukeni makaryaci Kokinason akirah kaleed dinki mayaudari??? Tace saime kowazai kiraka cen badai agabanaba kuma ni nasan kai ba mayaudari bane nidai kadawo Yayana wlh bandako lafia Zaiyi magana akaturo kofar dakin tareda sallama"" ya amsa sallamar yace shi go labilace tashigo kanta yana kasa tace ya kaleed dad yace kazo muci abinci hannu kawai yadaga mata alamar to tajuya tafita kaleed yace Kanwata inazuwa zankiraki anjima Tamarai raice fuska tace bayan muna fira zakatafi waime yasa baxasu Barmun kaiba darana bakahutaba yanzuma dadare haka Yace toyazanyi daddy nanefa" baisan sanda yafurta hakanba" tace haryazama dad awajenka tunda zaibaka yarsa ka aura shikenan saikadawo Taka she wayar murmushi yayi sannan yamike yafita yasamesu zaune saman dinner shi kawai akejira yayimasu sannu dahutawa sannan yazauna Usman yace kaleed munje sallah tare dakai shine kataho kabarni inata warar idon nemanka Ashe gida kazo Yasosa kansa yace ah wlh'"" khadija tace bisimillah bayan tagama zubamasu Aisha✍🏼 ☠ *HATSABIBIN BOKA!!*☠ PART 2⃣ 29 By gentle lady 💃🏽 Bayan sungama cin abinci kaleed yamike yayimasu saida safe usman yace baxaka tayamu firaba"" Idanunsa yashafa yace barci nakeji dad nagaji dayawa,"" yace shikenan kaje kakwanta saida safe kaleed yace okay dad night yawuce abunshi haryana hadawa dadan gudu khadija tabishi dakallo tana murmushi Usman yana kallonta shima murmushi yayi labila ce tamike itama tayimasu saida safe tadauki sapna tawuce su anwar sunawajen zahara u itama sapna batajin dadi shiyasa takawota wajen khadija Yanxun khadija harmantawa takeyi tanada yaya dantunsafe idan tabasu abincinsu batasake ganinsu saikuma idan sunji yunwa" Bayan labila tawuce Usman yadan jingina jikin kujerah yana kallon khadija yace mekika fuskanta akan kaleed naga kinbishi da murmushi akwai magana dauke abakinki Dariya tadanyi mai sauti tace bakomaifa kawaidai yabani dariyane nasan babarci yakejiba"" Osman yasaki murmushi yace nima nasan haka yasake matsowa kusada itah yace kinsan Zainab dinsa??? Tace mezaihana tunda kanwatace yace anyihaka kaleed yafadamun ai khadija tace aisaikaji soyayyar tasuma sufa ada kafin natafi cen sunason junansu sosai . Saidai su tunaninsu babu aure tsakaninsu tunda iyayensu daya shi idan yaganta dasaurayi yahau zuciya itakuma idan taganshi da budurwa ranar babu Wanda zaiga fara arta saitayi kwana biyu bataci komaiba ... Saiyaakoma rarrashi'"" usman yace toyanxu tasani? Khadija tayi shiru daga bisanie tace bana tunanin yasanarda itah Usman yayi shiru daga bisanie yace zanso ace labila tasamu miji dasai ayi bikinsu lokaci daya Amman nalura batako kula samari bansan zatakeson zamaba Khadija tace kamar yanda matarka tazama kamanta alkwarin mu da itah ainice zanzaba mata miji shiyasa batakula samari Usman yarike baki yace hakane namanta toke waye zakibata??? Tace yayana Amman haryanzu bansanarda itaba inajiransa yadawone"" Usman harcikin ransa yaji dadi sosai''' yace Alhamdulillah Allah yatabbatar mana da alkhairi"' khadija tace Ameen Usman yamike yace tashimuje kinji anbarmu anan gashinima nasomajin barci tana dariya tace katabbata barcin zamuyi ko?? Yace Sosai Amman saimun gama .....😉yakanne mata ido daya"" tana dariya suka wuce sama Kaleed kuwa yakwana yanajan tsaki dankoda yakoma yakirah wayar Zainab kin dagawa tayi karshema takashe wayar Shima jefarda tashi yayi yakwanta"" yadade kafin yasamu barci yadaukeshi ************* Bayan kwana biyu jama ar unguwar da lubcy take suka soma takurah duk dare basa samun isashen barci saboda ihunda sukeji kuma yanxun sungano tacikin gidan ihun yake fitowa Amman kuma babu alamun akwai wata halitta mairayuwa acikin gidan Wannan dalilinne yasaka suka dunguma zuwa gidan Usman dansu sanardashi abunda kefaruwa""" Suna kaiwa gidan shikuma yafito tareda kaleeed zasuje office ganin mutanen yasa yatsaya yana kallon su sukayiwa maigadi magana Osman yace barsu sukaraso khadija takoma Cikin gida suka karaso hannu yabasu suka gaisa yanayi masu kallon sanie Amman yamanta inda yasansu danyadade rabonda yaje unguwar yadaina sauke baki agidan saidai hotel bayan sungaisa wani daga cikinsu yace sunana alhaji kabeer munzone akan maganar tsohon gidanka Osman yace ayya nikam naga fuskar sanie kuwuceto mana yayi maganar yanayimasu iso falon baki yakaisu yasa aka kawomasu lemu daruwan sha"" bayan sunsha ruwa aka sake gaisawa Wanda yace sunansa kaberr yayi gyaran murya Alhaji Usman wani bakon al a marine yakefaruwa agidanka kwana biyu abun yana damunmu mudamuke kusa dagidan takai yanxu kobarci bamayi damu da yaranmu"" Usman yagyara zama yace me yake faruwa danshi Sam yama manta lubabatu tanagidan Alhaji kabeer yanisa yace kullum dadare wani irin kuka mukeji agidan da ihu da kururuwa bamasamun barci saikusan asuba dafari bamudauka daga gidanka abun yake zuwaba saidaga baya mukagane"" daga gidan kukan yake fitowa Munfi saran aljanune kokuma fatalwa dankuwa duk sanda mukaji kukan ana Neman dauki kuma komenene macene danmuryar mace mukeji koda munzo kofar gidan kulle muke samunsa da tsohon kwado sannan ga yana duk ta baibayeshi banda tsatsarda yayi Kagakuwa babu alamun da za ace mutum ne aciki munfidai zargin fatalwace Usman yayi shiru aransa yanacewa tokodai lubabatu bataje gidanba??? To Amman inazataje badaita koma garinsuba"" alhaji kabeer yakatsemasa tunaninsa yace mafita daya mexaihana muje kagani kokabari saida dare muje Dan dazaran anyi magrib duhu yasamu abun kefaruwa Usman yace ah ah basai dare yayiba ninasan mutumne agidan Amman baxan tabbatarba danbansaniba kotaje kowani gurin takoma Sukahau kallon kallo yace alhaji badai mutum ba gaskiya gidan baiyi kamada akwai mutaneba Usman yace banki tatakuba kutashi muje ingani inhar bansameta agidan ba sainasa ayiwa gidan karatu sainabadashi Sukace hakanma yayi gabadayansu suka mike kaleed dama yana wajen mota yanajira Usman yace yashiga suwuce Mota daya suka shiga sukuma sukashiga tasu suka dunguma zuwa unguwar....... Kamar yanda suka fada aikuwa haka Usman yatarar gabadaya yanace akofar gidan babu alamar akwai mutum aciki Sukace kagani ko dama munfadamaka "" Usman yace abun nan da mamaki aikoda Dadewarda akai ba ashiga gidan ba baidace yayi yana hakaba kubamu Aron wani karfe abuge kwadon Wanine yatura yaronsa gida dagudu akaje akasamu abun bugu aka balle kadon suka shiga cikin gida kaleed ne yatsaida yara dangaba daya unguwar tacika harda mata anaso aga menene acikin gidan wasu harcewa suke kilantama tsafi yakeyi Usman motar lubabatu yasoma cin karoda itah itakanta gabadaya yana tazagayeta yana tafiya yana waigen motar harsuka bude gidan Kaisaikace kangon gida danyanace ako ina bakasaran akwai wani Abu agidan makotan sukace lallai bakomai agidan nan saidai infa fatalwace Usman dakunan gidan yasoma bi daibayan daya """ harsuka gama zagayensu basu lura da lubabatu ba wacce take yashe kofar shiga daga gefe Bayan sunfito Usman yana waigawa gefen yana dube dube yaganta dasauri yakarasa wajen hannu yasaka yatabata tareda Kiran sunanta Tazaburah tatashi zaune tafasa ihu "" ihuntane yajawo daukacin mutanenda suke niyar fita gidan gabadaya sukajuya dagudu danjin ihun suka koma inda suka hangi Usman ciki kuwa harda kaleed dasauran yara Tanayin ido hudu da Usman tatashi

Chapter 5 of 9