takonata haka abun yayimatukar bashi mamaki
Lubcy takatsemasa tunani dacewa doctor kataimaka karabani da wannan bala in wlh zan iyah mutuwa
Yanda nakeji ajikina kataimaka kaciremun wannan ciwon"" yadago yana kallon Usman duk shisuke kallo suwaiba da labila dakumashi Usman din sunajirah suji tabakinsa
Yanisa agaskiya alhaji bansan mezancewa wannan al amarinba Abu kamar shirin film yanzu ciwonta yanuna kamar takonene harsuna fitarda miyagun ruwa
Tayiyu sosawarda tayine danhannu define dashi"" baidace kubarta tana sosawaba bari nasake wanke mata Amman karkubari tasosa zuwa safe zansa ayi awon jininta muga tayanda zamu bullowa lamarin
Yafita dasauri basuwani dadeba yadawo tareda wata nurse mai duty aka sake wanke ciwon akasa maganie saitaji Dan sauki har barci yadauketa
Saida tayi barci doctor din yajona mata wasu ruwan da allurai wadanda yakesaran zasu taimaka wajen make kurajen sukaimasu saida safe usman yace yagode
Bayan sunfita yasamu waje yazauna yakuramata ido gabadaya lubabatu tasauya kamar ba itah ba rayuwa kenan lafiya qalaufa yabarta amman yanzun yadawo yasameta gatanan dai
Labila ma gefe takoma tabuga tagumi kowannensu dakalar abunda yakesakawa aransa"" hargari yawaye lubabatu bata farkaba barcinta takeshaka
Khadija kam anacen anata shirin komawa Nigeria kaleed tunda safe yatafi gidan yadauki anwar sosai yanason yaron harcikin ranshi tunkafin yasan babansu daya yasan sosai zaiyi kewarsu idan sukatafi
Karfe bakwai nasafe tagama shiri danbataso tayi tafiyar rana motoci kusan guda bakwai akacika za aimata rakiya kamar wata sarauniya
Sunashiga airport akabasu waje ganin motocin mai martaba"" dama an gama shiryamata komai saibatun shiga jirki dansaura mintuna goma yatashi
Tayi sallama dasu tana kuka maimartaba yahadata dawata kuyanga zaharau dantarika taimaka mata da yaran tayi godiya sosai sukayima addua dafatan Allah yatsareta daga sharrin mutum da aljan
Tayita godiya jitakeyi kamar kartabar danginta yan uwa masu dadi"" kaleed yanagefe yana kallonta"" dasun hada ido saiya saukarda kansa
Matsawa tayi kusadashi tace kayi hakuri yayansu nasan kanajin wani Abu azuciyarka tayiyu haushin mahaifinka kakeji dukda kasan bashida laifi
Nidai inasake baka hakuri amadadinsa kayi hakuri naba hajiya number ta saika karba komai kakeda bukata kasanardani insha Allah zanyi kokarin ganin naturomaka dazaran angama komai zansanardakai koma nazo dakaina mutafi tare
Baice mata komaiba tajuya tawuce zainab tanakallon yanayinsa yasauya saitaji wani iri kallonta yayi yakawar da kansa gefe Sam bazai sanarda Zainab damuwarsaba
Yanaso saiyaga mahaifinsa tukun duk abunda zaiyi inhar babu ubansa awajen aidasauransa"" harjirginsu khadija yabace Asama kaleed baisaniba yayinisa wajen tunani
Muryar Zainab yaji tace ya muje tayi maganar tana zungurarsa da kafada "" yadansaki murmushi yace meyasa zakitureni inda nafadi kumafa???
Ta kwalalo ido 😳faduwar lafiya Yayana gudanawa nake dazan iya tureka saikace Wanda bayacin abinci🙄
Dariya yayi maidan sautii tace waiyaushe sukawuce??? Yayi maganar yana kallon gefensu dabaiga duka moto cin gidansuba
Tamere baki yaushe zakasan suntafi kanacen kana bakin tunaninka tamurguda baki daidai sunkai bakin motar yabudemata tashigà shima yazagaya mazauninsa ya zauna
Yana fuskantarta yace waye yafadamaki tunani nakeyi??? Tace baga zahiriba naganie ninarasa gane kanka tunsanda Anty khadija tazo kasauya kwata kwata
Sam kadaina sakemun fuska damekakeso inji da soyayyarka kokuma dakyaluwarda kakemuñ???
Dankulanin dakakeyi inàjin sanyi araina kadaina saigahawaye sharr kamar anbude fanfo kaleed yakuramata ido yanaji kamar yajawota jikinsa ya rarràsheta
Amman babu halinyin hakan danzai iyah shiga wani yanayin dakyar ya iyah furtamata Kalmar sorry
Tadago jajayen idanuwanta takafeshi dasu tace menaji kafada ya kaleed hakurifa?? Atunaninka Kalmar hakuri zata iyah tasiri azuciyata??? Inazargin anyama bakasoma soyayya dawataba???
Ninakasa fitarda miji saboda soyyyarda nakeyi maka duk danasan kayimun nisa dankoda babu maxa aduniya bazaka taba aurenaba
Kaleed yace injiwaye yafada maki??? Karkiyi mamaki nangaba zamu iyah zama miji damata
Murmushin yake tayi tace hakan zai iyah faruwa ammanfa ashirmen tunani ko mafarki Dan babu inda natabajin Yaya ya auri kanwarsa
Kaleed yace inamai tabbatar maki za afara akanmu kisa wannan aranki watarana zansake tambayarki yakika ganie tabbas saimunzama miji damata wannan alkawarine yayi maganar yanatada motarsa
Baki sake take kallonsa danganie takeyi kamar yazare a ina yatabaganin wannan kwamachalar uwadaya ubadaya
Saikace wadansu jahilai aiwannan ko ajahiliya dakyar idan anyi hakan"" nikam nace anyikam tunda harma zamanin jahiliya DA zai iyah yingadon uwarsa idan mahaifinsa yarasu yadauki matar wacce tahaifeshi acikin gadon abunda akabarmasa
Lokacinda mata basuda wani yanchi saikuma shima yacigaba dakwanciya da itah zuwan musuluncine yahana wannan akayiwa mata gata Allahu Akbar
Allah mai iko Hakika musulunci bakaramar gata yayiwa mataba gashi yanzun saida kudi ake daukarmu
Tunda sukahau hanya baisake cewa komaiba saidai jefi jefi yakandan juyo yakalleta danyasan tana nan tana saka maganarsa acikin zuciyarta
Aisha✍🏼
☠ *HATSABIBIN BOKA!!*☠
PART 2⃣
6
By gentle
lady💃🏽
Itakuma taki takalleshi harsuka kai gida yana yin fkng din motar wajen da ake ajiye motoci "
Zainab tabude kofar tawuce yabita da kallo sannan yagirgiza kansa ita bakin gaskiyarta soyayya yakeyi
Aikoda ma iyayensu daya bazaitabayin soyayya dawataba koda yayima bawaidan xatakamo kafar sonda yakeyiwa Zainab ba
Saidai tasamu Kalar nata yafitarda rayuwa da aurema waje kusa ashedai soyayyarda sukeyiwa juna bata yan uwantaka bace soyayyace ta gaskiya
Shikanshi yadade yana mamaki yanda yake jin zainab aransa fiye daduka sauran yaran gidan"" idan sunatare bugun zuciyarsa har tsananta bugawa take
Murmushi yayi yashafo sumar kansa zanbaki surprise bazanbari su Abba sufadamaki komaiba har ayi auren gobe zansanardasu dankarma sufadamata idansukaga tashiga damuwa
Dariya yayi daya tuno da kishinta"" akansa akwai watarana dasukaje kanti siyayya dashi da yaran gidan harda Zainab
Sunsoma jidar kaya suna zubawa akwando saigawata kyakkyawar cika tabiyo tawajensu tunkafin takawo zainab tasoma kare kaleed duk gefenda yarinyar tayi saitaje takareshi dankar yaganta ko itah taganshi""
Shisam bailuraba saida yarinyar tabar wajen sannan tacigaba da diban kayanta"" wani turare yaganie mai kyau kwalin tiraren yaburgeshi
Yakarasa yadauka yana dubawa kamar daga sama yaji ankirah sunansa wanake ganie kamar Prince??? Yajuyo da kallonsa wajenda yaji ankirashi yasaki fara.a
Khairiya kece???kokuwa" tasake sakin fara a tace nice wlh yagidan yakwana dubu"" yayi dariya dubu kuma
Tarausayarda kai ah mana kamanta rabona dakai tunda nabar skull dinku yace hakane dama nangarin kike???
No wlh nazo wajen mama nane"" ina zaune abuja ne gidan mahaifina lokacinda nabar makaranta mamana sukasamu sabanie da babana shine tace nadawo gida
Kaleed yace toya karatun??? Tace nagama ai yanzun ina aikine"" yace Masha Allah sai aure ko?? Murmushi tasaki tace in Allah yaso katayani addua insamu kamilin mutun
Yace Allah yatabbatarda alkhairi tace Ameen zainab tanakaryo kwana tayi arba dasu tazo fuuuu kamar kububuwa tashiga gabansu tace ke malama menene hadinki da Yayana,??
Batajira tabata amsaba tacigaba tundazu naganki wato dukda kareshi danayi dankarki Ganshi dayake kedin manyace saida kikabiyo nan hanyar🙄
Khairiya kam tasaki baki saida zainab takai karshe takalli kaleed tace Prince wacece wannan?? Murmushi yayi yace kanwatace sunanta Zainab
Kiyi hakuri khairiya tanada matsalane"" tace ayya sorry fa Yar uwa"
Wani mugun kallo tawatsamata khairiya tasaki murmushi takalli kaleed tace Prince kabani numberka murika gaisawa
Yace bamatsala khairiya sakamun taki zankirah yasaka hannunsa aljihun wandonsa nabaya daniyar dauko wayarsa"" aikuwa zainab tafinciko hannunsa tajashi
Yace Zainab menene haka frnd Dinacefa"" ko kallonsa batayiba harsuka kai wajen motarsu gabadaya wajen su ake kallo barin ma khairiya
Suna kaiwa tasaki hannunsa dakarfi taace ya isah haka ya kaleed ya isah dame zanji darasaka danayi har abada kokuwa da kishinka nibazan hanaka yin soyayya ba tunda banda mafita akan hakan Amman banaso kayi agabana
Idan harkasan in munfito yawo yammatanka zakarika kulawa kadaina zuwa dani zan iyah kauda kaina akan komai Amman bandakai
Shi gaskiyar ma tahanashi magana murya cikin sanyi yace haba zainab kiyarda mana wlh skull kawai mukayi da ita bawai soyayya mukeyiba
Murmushin yake tayi tace naga alama ai tunda hartake Neman numberka karkamaidani yarinya mana aini nasan yanda ake soyayyya
Tajuya zatabar wajen yasha gabanta inakuma zakije???
Batareda takalleshiba tace gida zanje"" yace kayankifa kakara kabata ninayafe
Kakoma wajenta idan kungama siyayyar saika Kaita gida
Taraba gefensa tawuce tana sharar kwalla wannan wace irin masiface soyayya da yayanta uwadaya uba daya""
Kaleed yabita dasauri Amman taki tsayawa jitayi ankirah sunanta tadan Dakata saitaga wani saurayin tane mansir yanasonta sosai Amman duk sanda zaimata magana bata tsayawama ballantana ta sautareshi
Yanxu kam tayanke shawarar saurarensa kodan tacire kaleed aranta murmushi takirkiro tace mansir kaine '"
Yakaraso wajenta yana fara a jinyau haryasamu takirah sunansa yace ranki yadade nine"" daga inakike haka kedaya
Tashafo fuskarta tace wlh siyayya mukazo dayan gidanmu"" yace kungamane tace ah ah sunaciki nikaina yake ciwo gida zanje
Yace sorry my.Lady tomuje nakaiki gidan tace nagode suka karasa inda ya aje motarsa yabudemata gaba tashiga shima yazagaya mazauninsa yatada motar sukawuce
Duk wannan abun akan idon kaleed akayi nantake idanuwansa sukasauya launi daga farare zuwa jajaye tsabar kishi jikinsa har ciccirah yakeyi
Dasauri yafada motarsa yaja yabi su abaya
Yama manta tare sukazo dakannensa "" Sam basumasan yanabinsu abayaba harsuka kai gidan bayan yayi fkng yafito yabude mata kofa tafita haryanzu murmushine akan fuskarsa yaujinsa yakeyi kamar angafartamasa"" waishine yau har Zainab tashiga motarsa
Tace zanshiga gida indan kwanta nagode" yasake washe baki babu damuwa Allah yasauwake tace Ameen tawuce abunta yabita da kallo hartashige gidan
Kaleed ne yashigo da motarsa atsiyace kogama tsayawa batayiba yafito fuuuu yanazuwa yadaukeshi da mariii shi hankalinshi yana kan kofarda zainab tashiga yana tunani baimasan dazuwan kaleed dinba
Hannunshi dafe dakumatu yajuyo da mamaki yaga wanne mai tsautsayinne yakai hannunshi a fuskarsa sukai ido hudu da kaleed yashiga rudani danbaimanta abunda yama wani akan zainab ba mugun duka yamasa saida aka kwantardashi hospital
Aisha
☠ *HATSABIBIN BOKA!!*☠
PART 2⃣
7
By gentle
Lady💃🏽
Tuni yahade wasu yawu yasauke hannunsa daga kan kuncinsa yabuda baki daniyar yin magana kaleed ya chachumo wuyan rigarsa
Yace yausaika fadamun meyahadaka da itah"" yace bakomai sultan kasakeni mana muyi magana yayi maganar yana kwakwale hannuwan kaleed dasuke shake awuyansa Amman yakasa danmuguwar shaka yayimasa..
Idanuwansa harsun soma sauya launie masu aikin gidanne suka sheko dagudu zasu rabasu wani mugun kallo yawatsamasu take kowannensu yaja baya
Dan abunda sukaganie acikin idonsa yabala in basu tsoro kowayasan kaleed baruwanshi da fitina dazaran Kuwa anga yanafada tobashakka wanine yataba zainab..
Sunyi cirko cirko anrasa wazai kwaci mansir kamar daga sama Allah yakado hassan gidan ganin shi yasa maidagi yasheka yafadamasa sultan zaiyi kisan kai
Dasauri yakaraso wajen yace kai sultan kanada hankali kuwa??? Kasakeshi nace yazaka shakeshi haka ko nunfashi bayayi cikin huci kaleed yasakeshi yanunashi da yatsa yace wannan yazama gargadi Na nafarko akanka wlh duk ranarka kasake yimata magana bamawai saika dauketa amotaba kallontama idan kayi saina nakkasaka idan ka kiyaye katsirah da lafiyarka yawucee fuuuuu
.gabadaya suka bishi dakallo haryashige gidan sannan hassan yajuyo wajen mansir yace Kayi hakuri kaji sultan bayaso yaga kowa dakanwarsa yanada zuciya zai iyah yinkomai yafada
Kahakurah da itah gamata nan ko acikin gidan nan kowani gurin kasamu kafadawa mahaifinka yasanardani zantsaya maka danganin kasamu.
Mansir yayi murmushi yadan gurfana yace nagode Abba Allah yasaka da khairan nizan wuce yashiiga motarsa yana sake matsa wuyansa.
Maigadi yace aidole kamatsa wuya wannan gargadin aihar abada bazaka manta dashiba
Kaleed yanashiga gidan bangaren zainab yawuce yaturah kofar dakinta dasauri zaune take tahada kai da guiwa sai hawaye takeyi narashin dalili..
Jin anturo kofa yasa tadago dasauri tsammaninta mom ce saitaga kaleed saurin kawarda kanta tayi gefe yana kallonta yatako har inda take yaduka cikin kaushin murya yace abunda kikai kin kyauta kenan?.? Tace mekuma nayi??? Yace waye wancen saurayin???
Tayakuna fuska wai mansir??? Wani mugun kallo yamata bandamu dasanin sunansaba sonake naji dangantakarki dashi dahar zairage maki hanya kuma keharkishiga motarsa
Batareda tsoron komaiba tace saurayinane"" yazaro ido wat??? Tace saurayina tana murguda baki"" kaleed mikewa yayi yace kenan kina sonsa??? Tace dabanasonsa aida baxanshigo motar saba
Kaleed yagyada kai dakyau nixakiyi wulakanci agabana zakice kinason wani katon banza hannu tadaga masa tace ya kaleed katsaya iyah matsayinka kai yayanane wannan ba huruminka bane bakada damarda zaka takuranie nice nakeda damar zaben mijinda zan aurah kuma mansir yayimun shizan aurah
Kamar kaleed yakwalla ihu yaji saukar maganarta kamar ansoka masa mashi akahon"" zuciyarsa yaruntse idanuwansa sannan yabude dabadan zainab ce tafurta hakan da bakintaba dawanine wlh kowaye yau saiyakwana gadon asivitiii
Iska yahurar tabakinsa yace zainab dabakinki kike sanardani iyah matsayina??? Kodayake ba laifinki bane laifin wancen Dan iskan saurayin nakine kuma nagode kije ki aureshin din nima bandamuba yaja tsaki yawuce fuuuu hannu tadaga dasunan takirashi kuma saita fasa
Komawa tayi saraf tazube kasa kamar kayan wanki tafashe da kuka meyasa nace haka meyasa nacehaka""
Zuciyata meyasa bakida hakurine" ya kaleed bai chanchanci haka daga gareniba komawa tayi takwanta tacigaba da kukanta harbarcin wahala yadauketa
Kaleed saidai yabawa driver key yace yadauko yaran danbayajin zai iyah driving acikin wannan yanayin
Bangarensa yatafi yafada saman kujera maganganun zainab kawai sukemasa kuwwa akwakwalwa "' yarasa yazaiyi yaji dadi tabbas saiyajima wannan gayen duk sanda idonsa yahadu dashi
Tsaki yaja waimezaisa indami kaina ba itah tace tana sonsaba ni menene nawa aciki??? Wata zuciya tace saboda kana sonta
Saurin girgiza kai yayi yace wannan soyayyar karyace karyakike zuciyata meyasa zakiso abarda kikasan taharamta agareki kitsaya iyah matsayinki banason kina wuce gona da iri
Jiyayi kamar ana mintsilar masa zuciya yadafe kansa kamar yafasa ihu yasoma kiran innalillahi wa inna ilaihir rajiun sannu sannu yasamu zuciyarsa ta danlafa"" yatashi yawatsa ruwa yawuce masallachi
Daga kaleed har Zainab saida sukayi kwana dayinie basuci abinciba kaleed Sam bazai iyah fushi da Zainab dinsaba tunranar baisake shiga cikin gidan ba saiyau
Harya gama zamansa baiga wurgawartaba hardare su mom sunyi kamarma basusan sunayiba" "" washe gari dasafe dayashiga gidan bayan yagaida su yamike zaifita hassan yatsaidashi
Yakoma yazauna kansa yanakasa kiran sunansa yayi sultan" yadago Na am Abba """ yace waikai menene matsalarka da kanwarka
Kaleed yasaki murmushi yace bakomai abba "" murmushin su yayi namanya yace itama hakan tace amman nalurah dakai da itah bakwacikin walwala hardai itah kwananta biyu banda ruwan tea batashan komai gashinan yau tatashi sai amai taketayi yanzun doctor yabar gidan nan yasaka mata karin ruwa ""
Dasauri kaleed yadago kansa yace zainab din"" amman meyasa ba afadamunba "" mom tace waye zaifada maka bayan kanata fushi kogidan nan rabonka dashigoshi kwana biyu
Mikewa yayi yawuce haryana hadawa da sauri "" sukabishi da kallo hassan yace kinga abunda nadade ina fadamaki
Wadan nan yaran soyayya sukeyi dankawai sunsan babu aurene atsakaninsu suke kaucewa Amman zukatansu sunsan gaskiyar lamarin
Nidai dazakibari kawai musanarda shi gaskiya kada mushiga tsakanin soyayyarsu tace me kake so kace malam Amman kasan sarai inhar yaron nan yasan bamune muka haifeshiba zaishiga tashin hankali
Hassan yatari nunfashinta yace wannan dayake ciki batashin hankali bane??? kinsandai karfinda soyayya takedashi axuciyar Dan Adam
Rashin iyayensa zaiyi masa sauki akan yarasa soyayyarsa tayiyuma zaiga iyayensa "" tace Kanada shedarda zaka bayar wacce zaigane iyayensa da ita
Shiru yayi tace tokaganie kawai kazubawa sarautar Allah ido muga yanda zaiyi inhar zainab matar sace Allah yasaka iyayensa su bayyana
Idankuma ba aure atsakaninsu mubar maganar nan kamar yanda mukabarta tunfarko kaiyagyada yace shikenan Allah yazabamana abunda yafizama alkhairi
Kaleed yanakaiwa kofar dakinta yaturah kofa yashiga da sallama idanuwanta rufe suke kamar tana barci Amman hawayene suke sauka gefen kumatunta.
Tarame kamar wacce tayi ciwon shekara anciremata Karin ruwan ahankali yataka zuwa saman gadon yazauna
Tunsanda yashigo kamshin turarensa duk yagame dakin wata natsuwa taji tasaukarmata
Sunanta yakirah Zainab bata amsaba shima baidamu data amsaba yace am so sorry"" saikuma yayi shiru" zuwa sudewar seconni yace please my sister""
Saiyanzu tabude idonta tadorasu akan fuskarsa tace sorry for wat?? Yacije lebensa nakasa yace Zainab nasan kinsan akanme natsani naganki cikin damuwa
Murmushin gefen baki tayi tace ada kake gudun haka ya kaleed kasan natsani naganka dawata komai zakayi kayi amman bagaban idonaba
Tunfarko Kaine kasabamun dasonka kasan bazaka daureba meyasa baka jayeni daga jikinkaba tunkafin nafara sonka nadade ina kyarar zuciyata Amman saitacemuñ nahakurah ita taga Wanda takeso
Wlh dadayanda zanyi nacire zuciyata danayi tuntuni dankawai nabar wannan shirmammiyar soyayyar Mara kangado da tushe inama zam mut"" bakinta yarufe dasauri yace karkice haka idan kikace haka nikuma mezance zainab???
Nayarda da maganarki nine nayi wauta danajaki jikina Amman nikaina bansan ya akai hakan tafaruba yaran gidan nan babu Wanda nakeji ajikina sama dake
Nabarwan nan akan kodan kece kanwarda nasoma samu Amman zuciyata tafara karyata hakan hartakai nakanyi munanan mafarkai akan alakata dake wannan shiyake sake ingizanie akan tubalin soyayyarki
Zainab wlh babu abunda yake tsakanina da khairiya kiyarda dani kinsan bazanyi maki karyaba dankawai nakare kaina
Wannan bahalina bane dakinji firarmu da itah babu ta soyayya kawaidai karatu mukai tareda itah shekararmu daya acen tabar makarantar
Lokacinda nayi rashin lafiya kullum itah take kaimun abinci hospital harnawarke kokadan batataba nunamun tana sonaba matsayin Yaya tadaukeni dantace mamanta itah tafara Haifa tanason yaya Wanda zairikayi mata fada idantayi madaidaiba !!
Danhaka kikwantarda hankalinki indai kaleed dinkine dagayau ko abun hannun mace bazanciba inhar bayan gidan muba kowanda yafito daga hannunki hakan yayimaki
Cikin ido yake kallonta itama shitake kallo wadansu kibiyoyine suke fita tajikin idonsa sunashiga idonta
Aisha✍🏼
☠ *HATSABIBIN BOKA!!*☠
PART 2⃣
8
By gentle
Lady💃🏽
Saurin sauke idanuwanta tayi yajaye hannunsa daga bakinta yace mom tace kindaina cin abinci"" tagyara kwanciyarta tace aikaima haka""
Yajuyo dakallonsa wajenta yace wayafadamaki banacin abinci" tace gazahiri naganie duk karame ""
Murmushi yayi yace aidolene kinkuwaji yanda naji maganganunki??? Aranar wlh nafison asa sabuwar wuka ana yankan naman jikina tsoka tsoka da naji wadan cen kalaman saura kadan nahaukace
Tace nashiga uku hauka Yayana?? Yace sosai kokina mamakin hakanne?? Batace komaiba to indai har mamaki kikeyi tokigwada watarana kiga idan ban haukaceba
Tace bama zansakeba ya kaleed banaso ka haukace yace dagaske??? Tagyada masa kai tana murmushi
Yace tashi nataimaka maki kiwanko bakinki kici abinci bamusu Kuwa tatashi yarikata yakaita toilet tawanke bakinta sukadawo dakin
Yazubamata abinci yanabata abaki sunafirah kafin dare da kaleed da zainab sunware kamar basuba tundaga ranar kaleed baisake gigin yiwa wata maganaba idan sunatareda zainab
Inma yahaduda wacce yasani sauri yakeyi yaboye karma taganshi
********
Yasaki murmushi ya laso busassun labbansa babu shakka saiya razana Zainab idan yahada wannan planning din Dan ihun murna yayi sannan yafito motar yabi sahunta danya rarrashi abarsa
**--**--**--**--**--**-
Khadija koda daya darabi tabuga suna airport din kaduna bayar Usman takirah tayita ringing ba adaukaba takirah ta labila mahaka
Mamaki taji sosai to duk suna ina??? Sake gwadawa tayi Amman basu daukaba karshe saidai sukadau tashar mota takashe kayansu da itah da zahara.u zuwa gida"" ana saukardasu tabashi kudinsa "" maidagi yazo dasauri yasoma jidar
Kayanta yanashiga dasu cikin gidan "" sauran kayan Zahara.u tadauka suka karasa ciki da sallama suka shiga khadija kam gabanta saifaduwa yakeyi
Maigadi zaifita takirashi yajuyo tace ina mutanen gidan suke??? Naga duk yayi kurah??? Yace suna asiviti Amarya
Tayi saurin tarar numfashinsa tace asiviti waye baida lafiya??? Yace hajiyace wlh Amarya idan kika ganta saikin tausaya mata takoma kalar tausayi nidanaganta wlh tashi rugawa nayi dan kamanninta gabadaya sunkoma na aljanu
Hannu khadija tadaga masa bawan nan jawabin nasakaba wanne asiviti suke""??? Yace ai hajiya muhd yana nan bari nakirashi saiyakaiki
Tace to kayi sauri tasaka zahara u tagoya anwar sukafito muhd din haryafito yabude mata baya sukashiga yatayarda motar zuwa asivitin
Lubabatu kuwa tundare da akawanke ciwon nan batasakejin kaikayiba saida safe anagama sallar asuba tasoma fizge fizge acikin barcinta sakamakon wani mugun mafarki datayi
Tanacikin daji tanagudu wadansu namun jeji sunbiyota cikinsu harda masu tashi sama cikibis tayi dawani wagegen rami fadinsa zaiyi fadin kofar gari zurfinsa kuwa zaiyi gaba ashirin
Yanaci dawuta balbal wutar tayi harso harsama dawani zaimatsa kusa dawutar ba shakka wannan wutar zata daye masa fatar jikinsa saboda bala in zafinta bama saika shigaba
Faduwa tayi tafasa ihu tana Neman agaji daga damanta wutace hagunta kuma gawadan nan mugayen halittun kowanne yabude wagege bakinsa
Lubabatu takwamtsa ihu tace bakowane awajen nan ??? Ataimakeni wazai taimakamun"" wadansu kananun yara taganie zaune suna wasa Amman babu alamar tsoro atare dasu kamarma basuga wadan nan hakittunba dasauri tamike tatunkaresu hartana kirewa tana faduwa
Gabansu tafadi guiwa kasa tana rusar kuka tace kutaimakeni zasu kasheni taresuka dago ido suka kalleta saisuka bushee da dariya gabadayansu dariyarsu tasoma amsa kuwwa acikin jejin wadan nan miyagun namun jejin suka sauka kasa Suna kallonsu
Lubabatu tasoma jadabaya dan dariyarsu tasoma tsoratata zuwa kamar mintuna biyar suka tsaya da dariyarsu take sukasoma magana
Ke axxalumace ke macuciyace Ashe kina tsoron mutuwa??? Dakina tsoronta dabaki aikata miyagun laifukanda kika aikataba
Kisani ranar bakincikin ki zatasoma dagayau duk abunda kikadade kina shukawa lokaci yayi dazaki girbeshi da hannunki yanda kika cutarda babanmu kema zaki dandani kadan dagacikin abunda kikayimasu
Dagake har bokanki karshenku yaxo mune zamuyi ajalinku bake bawarke wannan ciwon harkimutu sannan bakar azabarda zakitarar akabarinki talunka wannan dakike ciki saudubu zakiyi mutuwar wulakanci bayan kingama tonawa kanki asiri duniya tayi Allah wadarai dahalinki kibarwa kanki abunfada dake da zuri arki
.
Lubabatu zufa kawai take kanta yakulle yaran taresuke magana kamar computer sunakaiwa nan bat sukabace
Lubabatu tasoma waige tanacewa kuna ina kudawo kufadamun kusuwaye meyasa zaku kasheni kufito kusanardani menaimaku zaku cutardani wadan nan namun jejinne suka tasomata tasomaja dabaya Sam tamanta daramin dayake gabanta
Labila taganie tasheko dagudu tace mom kiyi addua"" cikin tashin hankali tace ban iyaba labila mezance?? batagama rufe bakintaba tazunduma cikin ramin zafinda tajine yasakata kwalla mahaukaciyàr kara!!
Aisha✍🏼
☠ *HATSABIBIN BOKA!!*☠
PART 2⃣
9&10
By gentle
lady💃🏽
Tasoma sosar jikinta saboda tsananin zafinda tajiii take tasoma bata aikinda akamata Usman yana masallaci labila ma tafita tanabin jam i ana gama sallah suka taso tunkafin sukai dakin sukaji ihunta gabadaya yakarade asivitin
Dagudunsu suka shiga dakin Usman yana gaba labila tana bayansa" sunashiga suka rirriketa labila tasoma kuka tana mom meyasa kikeson jiwa kanki ciwone
Sai alokacin hankalinta yadawo jikinta taga abunda taiwa kanta saita fasheda kuka dasauri Usman yafita Kiran nurse allurar barci akayiwa lubcy
Dasafe da doctor yazo yaga abunda tayi yatabbatarwa Usman indai anason ciwon nan yawarke dole adauremata hannuwa dangudun sosawarda takeyi tanamaida aiki baya
Usman bashida zabi yace ayihakan"" hakan akayi kuwa aka dauremata hannuwa tunda akawanke mata ciwon tasamu sauki batasakejin kaikayinba saida karfe biyu tasake yin mafarki da yaran
Wannan karon kamar mahaukaciya takoma Tanata ihu tana jijjigar gado kaikai takeji kamar bala I babu halin sosawa anacikin hakane su khadij suka isah hospital din
Koda suka kai kofar dakin mutanene sunyi cincirando duk da kofar arufe take cen tahango labila tana kuka dasauri takarasa wajenta tace sahiba
Labila tadago dasauri tana ganinta tafada jikinta tana kuka tuni idanuwan khadija suka kawo kwallah"" tace kiyi hakuri kidaina kuka addua zakiyimata insha Allah zatasamu lafiya
Sannu kan hankali tasoma rarrashintaa hartasamu tayi shiru"" likitocin dasuke dakin da lubabatu take sukafito doctor lawal yasa akadibi jininta akaje lab domin asake aunawa yace duka cutarda take jikinta arubuta dansu San taimakonda zasu bata
Alokacin tasamu saukin zugin dansaida akawanke ciwon dole akabarshi sake ba asa kadaba duk Wanda yake dakin karfin haline kawai yakeyi Dan saboda mugun doyinda dakin yakeyi
Karfe uku dangin lubabatu sukazo harda yayyunta Amman saida Usman yayita basu hakuri dancewa sukai subaruwansu tunda takeda lafiya bata nemesuba saiyanzu dabatada lafiya Ashe sunada rana
Usman yayita basu hakuri yace karsu dubi abunda taimasu sutaimaka suzo dakyar " suka amince sukace zasuzo koda sukazo har barci yasoma daukarta Amman tana kinyi
Danbataso tasake mafarki da wadan nan yaran tanaganin yangidansu kunya takamata dukkansu basuyi mintuna goma dakinba suka fita mahaifintane kawai yadan jima aciki
Yana fitowa kawai yayi waya Aturo masa wadansu likitoci turawa da gaggawa"" dukkansu ciwon lubabatu ya firgitasu""
Bayan angama komai akafitoda sakamakon gwajin jininda akayiwa lubabatu doctor lawal yaduba hankalinshine yatashi yayita maimaita abunda yaganie yadago yakalli Wanda yakawo sakamakon yace katabbatar wannan result dintane?? Yace ah
Shiru yayi yadafe kansa daga bisanie yace kiramun alhaji yace OK sannan yafita lokacin su khadija suka shiga dakin sosai itama hankalinta yatashi
Daganin yanayin da lubabatu take ciki saiyanzu Usman yaganta yace wayakawota asibatin??? Tacemasa driver
Zaiyi magana Wanda aka aiko kiransa yashigo yasanardashi yace masu yanazuwa yafita "" zuwa office din"" doctor din yatura kofar yashiga da sallama yadago yakalleshi yana amsa masa sallamarsa yakarasa doctor lawal yanuna masa kujera yace yazauna jiki sanyaye yaja kujerar yazauna
Danganin yanayin doctor din yasan akwai Matsala yatattara ragowar natsuwarsa duka zuwa gareshi
Shiru yayi yakasa magana dazaran yadago kai yakalleshi saikuma yayi shiru"" Usman yace kayimagana mana doctor nikasani cikin rudanie
Kasanardani meyake damun matata danna nema mata maganie banason ganinta cikin wannan rashin lafiyar
Doctor Lawal yanisa yace agaskiya dangane daciwon matarka bamuga wata cuta dazata haifarmata dawan nan ciwonba saidai abunda mukasamu wanda bashi mukayi zatoba yayi matukar dauremun kai
Yadauko takardar yana dubawa nayi mamaki sosai danaji wannan cutar wai ajikin matarka yayi shiru Usman takardar hannunsa yakarba yana dubawa jerin ciwarwatanda suke jikinta
Batada ciwon sugar Amman akwai hawan Jinie akwai maleria akwai ulcer nakarshenne yatayarwa Usman hankali yamike yana Zare ido