Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
3 / 7
36) Tace wlh babu wata er iska nace da zaka auro ta rike mini yara, dama niyyar aurenka kake yi shi ya sa zaka fake da son 'ya'ya tunda ni nace 2 sun isheni to ka auro matan duniyan nan wlh nafi karfinsu. Daga wasa sai ta maida zancen fada, saboda tsananin kishi dole ya fice ya bar mata gidan. Magungunan da likitan ya basu kin shansu tayi shi yasa aranar ciwo yayi mata dirar mikiya ga hayaniyar yara, suka zo suka dameta, ai kuwa haushin dadyn su sai ta huce akansu, yana falo yaji ihunsu, yayi sauri ya shiga dakin ya kamo hannunsu yana tambyar menen? Suhail ya nunata yace, mom ce ta yi mana bulala wai mu fita a dakinta. Suje duk inda za su amma bazai yiyu ina ji da kaina su zo su dameni ba, da wanne zanji? Ya fice da su yana cewa, ai ba su suka kar zoman ba ratayar ma ba abasu ba, ba zaki sake ganin su ba. Ya sami su Aneesa a kicin yace, aneesa gasu nan kada ku barsu su shiga gurin mamansu, suna damunta, ko me suke so kuyi musu, komansu yana dakinsu. Kwanan safeena uku bata zuwa ko'ina saboda tana karatu a university din Abuja, aranar wata kawarta tazo dubata, tym din ita da aneesa na dakin baccinta tana tayata gyaran dakin. Ta bar Aneesa a dakin ta fito falo gurin bakuwarta. Da jin hirar su kasan aminan juna ne. Safeena ta shiga zayyana mata cewa ciki gareta, kuma ita wlh so take ta cire shi don ba zata iya wahalar laulayi ba, ga karatu ga su Suhail sannan nan da en watanni ace ta haihu. Kawar dariya tayi tace, ai hkr zakiyi ki barshi tunda mai abin na son abinsa, kina dai ji yace zai dauki mummunan mataki idan kika cire masa ciki. Ke a tunaninki wane mataki zai dauka? Iyaka dai yayi fadansa idan ya gama ya koma fushi daga nan ba zai kai ko ina ba zai saulo, dan nasan hushinsa ba ya kai ko ina duk iya laifin da nayi masa. Kawar mai suna Aina'u tace, tace kinsan fa ya taba ce miki idan ke ba kya son yaran shi yana so kuma zai auro wata tayi ta haifa masa, ba kya ganin zai iya auri watan? 37) Dariya Safeena tayi tace, aure! Ai ina jin Ishaq shi da aure a duniya dai ya gama shi sai da ko a lahira, don idan yace zai aure nima zan dau mataki, mummunan mataki akan haka, zan yi adawa da auren babba ma kuwa, yara kam bani da ra'ayin tara su, kamar akuya, dole ya hkr da tsari na. Aina'u ta murmusa tace. In kuma Allah ya rubuta masa 'ya'ya da yawa ya zakiyi? Kinga dole kiyi hkr ki zazzage masa adadin su. In kuma baki so wata ta zo ta amshe ki. Ta tabe baki tace, kin fa san yadda bana son kishiya, ko sunanta bana son ji. Ni fa ko wata naga za ayiwa kishiya jin zafi nakeyi, ina jin ma na fi ta jin kishin abin. Balle ace ni kuma, kinsan Allah da ya kawo min wata gidan nan amatsayin kishiya gara ya aje macen banza a waje (kuji banza mtsssw) wannan bata dameni ba. Akan kishi kuma a gidana. In ma rabon yaran ne can ahaifa masa su awaje, da dai akawon gida. Kai! Ina ba zai yiwu ba ma, ai gara in mutu da in ga wata mace Captain ya kawo a matsayin kishiya. Kinsan Allah da shi da ni da ita zan iya halaka mu. Gara mu mutu gabada a huta don ba ma zan yarda in mutu ni kadai in barsu su ci gaba soyayya ba gara a yi mutuwar kasko. Ke aina"u kin ma san yadda nake son Captain kuwa? Ni fa ina jin ko uwar sa ba zata fini sonsa ba, ita dai ta haifamini shi, shi ya sa ma idan naga tana wani nan-nan da shi har haushi nake ji, sai in ga kamar zata raba mu ne, Aina'u tayi ajiyar hrt tace, safeena kenan lamarinki sai ke. Ni dai shawarata ki bar cikin nan baki san irin albarkar da yake tattare da shi ba. Aneesa na ckin dakin baccin safeena tayi zuru tana jin wannan zance mai kama da shirin film. Ita kam duk yadda take tunanin safeena ashe ta wuce nan, lallai duk wadda Allah ya hada kishi tare da ita ta shiga3. Ko da yake ma Ishaq baya da ra'ayin kara aure don basu taba jin ya furta ba. Tana dakin har kawar ta tafi safeena ta zo ta suka cigaba da gyaran dakin. Ita a tunanin safeena Aneesa bata jiyo hirarsu ba, kuma ko da ta ji ba abu ne da ya shefta ba, tunda ta san Aneesa babu ruwanta da abinda bai shafeta ba. 38) Ranar litinin Hajiya tayiwa Ishaq waya cewa Mamansu Aneesa ta haihu, amma yaron bai zo da rai ba. Sai dai lafiyarta lau. Da yake ma hajiya na gidansu Aneesa ne sai ta ba maman wayar suka gaisa da Ishaw yayi mata sannu da jiki. Da ya dawo gida da yamma ne ya kira Aneesa da sadiya yake gaya nusu. Aneesa duk sai ta rude ta soma sharar kwalla wai ita gobe gida zata tafi. Yace bayan na gaya miki maman lfiyarta lau, munyi ma magana da ita, baki yarda ba kenan? Tace ni so nake in ganta shi ya sa, yace zaki ganta amma ba gobe ba, saboda nine zan maida ki gida. Ina son zuwa nima amma sai ranar asabar, saboda gabadaya wannan satin ina da tafiye2 kuma ba ma kasar nan bane. Ki bari idan natafi gobe sai friday zan dawo sai mu tafi. Ba don san ran Aneesa ba ta hkr. Tunda babu yadda zatayi$ Ranar da zasu tafi kayayyaki sosai Ishaq din ya saya musu na kashin kansu, don a tafiye2 da yayi naa jigilar fasinja kasashe, acan ma ya siyo masu tsarabar abayoyi da takalma da jakunkuna masu kyau. Don har mama da Hajiya ya sayo masu takal wasu en india masu kyau. Ita ma safeena tayi masu dinkuna irin nasu na en gayu en jami"a don tare ma ta dauke su a motarta suka je gurin tailor ya gansu ya babbance awonsu, saboda sadiya tafi Aneesa jiki, ita Aneesa falen2 ce ajiki, kirjinta ne ke da cika da hips dinta. Suna hanyar dawowa Aneesa tace, Aunty naji kince siket za'ayi mana kala3, duka ne dubu biyar? Tace, a'a ko wani set ne dubu biyar, mu dinki a abuja akwai kyau, amma da tsada. Aneesa tace aunty mu a zariya ba zai wuce dubu daya daya ba, gashi telolinmu sun iya dinki sosai.. Babu wani babbanci dana abujan. Ko zamu amso ne mu bada a can zarian? Tace ku barshi kawai, kinsan mu nan Abuja akwai tsadar rauyuwa komai na abuja mai tsada ne. Shi yasa duk wanda kika gani yana zaune a cikin garin Abuja, to ya ci ya tada kai ne. 39) Da wuri suka baro abuja saboda ranar Ishaq zai dawo shi da su Suhail akayo tafiyar saboda rigimarsu. Sai sun biyo shi, ba arziki ishaq ya sha Safeena ya shirya su tunda ba kwana zaiyi ba, ko ma kwana ne ya kama shi ba damuwa zaiyi ba. Jikin safeena har yanxu laulayi take sosai, tunda har karin ruwan anyi mata agida, saboda yawan Amai. Aneesa a tsaitsaye ta gaida Hajiya tace bari taje ta duba jikin Mama zata dawo anjima. Ishaq ya dubeta yace ku tafi da su sultan nima gani nan shigowa, ku gaidata. Sadiya ta taya ta diban kayanta har sabon troley da Ishaq ya saya masu kowa babba, aciki suka xubo kayansu. Shara suka iske Maman nayi a dakinta Aneesa nayin sallama tayi sauri ta amsa tsintsinyar tana cewa Mama kece da shara har kin warware ina Aisha fah? Tace na aiketa sannun ku da zuwa, sannu sadiya kun sha abuja, ashe har da mazajena aka zo. An zo mana da cefane ko ni da Hajiya? Ta kamo su tana tambayrsu, sultan ya laluba Aljihuns ya dauko sabon kudi ya mika mata, yace gashi kudin cefanen. Da Mama da su Aneesa me zasuyi ba dariya ba. Shi ma Suhail ya kwaso nasa kudin ya ba mama akayi ta musu dariya. Su Aneesa suka gaida Mama da jiki. Aneesa ta kara da cewa ai ranar da Yaya ya fada mana kin haihu dan baizo da rai ba nayi ta kuka nace gobe gida zan dawo, maman tace ai kuka? To idan kika dawo me zaki yi mini? Tace abubuwa da yawa zanyi miki mama tunda na san baki da mai taimaka miki sai Allah, yanzun baga irinta nan ba sha naga tarar kinayi. 41) Ji dadi wai duk wanda Ya Ishaq yake sayo musu a Abuja ita baya mata dadin na zaria. Da yamma Aneesa ta fidda tsarabar jama'ar cikin gida ta tafi kai musu, ta shiga dakin Hanne ta durkusa ta bata su subulai da mayuka da turare, en matan dakin sun cikin dakin, uwar ta kada baki tace. Ai fa ansha abuja dole kuyo tsaraba, balle ana tayi musu dawainiyya da 'ya'ya ba dangin iya bana baba. Aneesa na jin haka ta yi saurin mikewa zata fice taji babbar diyar Hanne na cewa, ke ko mama ba dole ba gidan maiko, tafi tafi ma sai kiji wata babbar magana ta bullo hadin zaumuntar dole, ba dangin iya ba na baba. 'Ya'yan suka sheke da dariya. Aneesa da sauri har tana tuntube ta afka dakin Halima, 'ya ta mutanen Abuja tlfy na ganki a hargitse? Aneesa sarkin saurin kuka nan da manyan fararen idanunta suka antayo da hawaye. Halima tace gidanmu ko? Ai shikenan kin dawo za su fara halinsu da kina can abinki kamar kada ki dawo, dibi yadda kika yi kyau kamar wata baturiya, hankalinki kwamce a can, nan ko tsegumi da gulmace2 kadai za su tsangwami zuciyar mutum, kai wannan musibaa Allah ka kawo mana iyakarta $ yanzun me ya faru kuma? Aneesa ta share hawayenta da agefen hannunta ta gayawa Halima cin fuskar da sukai mata daga abin arziki. Halima tayi murmushi tace kai aneesa. Wlh kinso zubda hawayenki a banza ne, yanzun meye sabo a wajenki cikin halayyar Hanne da yaranta? Sharri ko bakin cikinsu wanenen baki sani ba. Ishaq dai abin arziki ya hada uwarsa da taki, har suka zama tamkar sun fito ciki daya, kuma 'ya'yansu dole kuyi zumunci. Har gashi muma muna cin tubarrakinku, ko da yake alheri halinsune, amma ai babu abinda da ba sayi mana na alheri kuma suna amshewa suna jin dadi, amma don butulci irin na mutumin yau, sai kuma sune za ayi wa hassada a bi su da kulli. Shi don Allah ina laifin wanda ke kaunar naka? Mu kam babu abinda zamu ce musu sai san barka. Allah ya ninnunka ma ishaq arzikinsa ya kara budo masa hanyoyin alheri, ki rabu da su ki share hawayenki, kada ma fatima taji wannan maganar ki barsu da sharrinsu. 42) Da dare ne Maman Aneesa ke gaya wa Aneesa wani labari da ya razanar na da ita, Karama yau fa saura sati daya a daurawa Abbanku aure da wata bazawara anan cikin zariya take can bakin kasuwa take. Aneesaa ta dafe kirji tace mama aure? Yanzun abinda. Abba zai yi miki kenan? Alhalin ke da shi ba wata jituwa kuke ba, sannan zai karo wata a tsakaninku, me kika yi masa dai yi miki sakayyar kishiya? Mama tace, kash! Karama ban son jin haka daga bakinki ba, Abbanku yana da halin auren mace uku yanzun ya hadamu, ba shi da rashin wadata, kuma ni banyi bakin cikin aurensa ba, addu'ata dai Allah ya daidaita tsakaninmu, ya sa hakan zai zamo alheri a garemu dukkanmu. Ina fatan idan ta zo zaku riketa a matsayin uwa da kowane irin hali ta zo mu dogara ga Allah don shine shahidi. Dakins Aneesa ciki da falo ne, sai yace su koma dakin mamansu anan ne zai saka amaryarsa, Allah ya sa dakin maman falo ne da dakuna biyu ciki, sai tace su Aneesa su gyara daya dakin, ita ta dauka daya. Gaba daya gidan Abbansu ya saka akayi fenti har da dakin maman sai dai ko tsinke bai bata ba, ko ya canza mata na fadar kishiya ba. Hajiya Ishaq itace ta dinga tausar zuciyar maman duk da dai dama ba wai ta tada hankalinta bane. Hajiya ta bata kyautar wasu lafiyayyun kujeru sets da take ajiye da su awani daki a gidan. Wadanda masu ne kila ko amaryar ba zata zo da irinsu ba, nan da nan Halima ta taya su Aneesa aka fidda tsoffin kujerun mama aka zuba sabbin, ga leda da labule ta siya komai yayi sabo a falon. Da abbansu Aneesa ya dawo ya shigo dakin sai yayi sororo yana kallon dakin tayi saurin gaya masa inda kujerun suka fito labulai da leda ita kuma ta siya da kudin da Ishaq ya bata. 43) Tabe baki yayi yace, ai bansan ke 'yar gatan zuriar Hajiya ce ban tada hankalina inyi miki komai ba, nasan ba zata kyaleki haka ba. Murmushi kawai Mama tayi don ya san ita mai hkr ce, shi yasa ya fadi haka, kuma ya ma riga ya san ko da bata masa hankali ba, amma a zuciyarta sai da tace, oh Allah mutum bai rasa abinda zai kyautata mini inji dadi ba, amma don bai min hidima ba, ko ajikinsa, alhali shine ya cancanci yayi fiye da abinda Hajiya ke mini, amma babu ruwansa tamkar zaman Hajiya da zuri'arta nakeyi. Ranar asabar aka daurawa Abbansu Aneesa aure, kuma aranar ne da dare matar ta tare, wadda a yadda ya gaya wa maman cewa 'ya'yanta 3 mijinta tsarain mota yayi ya mtu ya bar marayu. ************* Zaman su Ya faro abin sha'wa kasancewar Fatima( mama) ta kama girmanta na babban su kuma su Aneesa kanninta sun maida amaryar tamkar uwa kullum ta rugumesu tamkar 'ya'yanta. Addua fatima a kullum take kada Allah ya aiko da baraka, a tskanin wannan zama nasu da amarya ta z da ita ya saje cikin 'ya'yan gidan tamkat nan aka haifeshi. Ashe tsuge bata kare ba wai , an sai biri an sayi kura, en hana ruwa gudu suna nan sun sa idanu, ba haka ransu ya so ba, Hanne da yaranta sun so ne ai sanadin amarya wulakancin da akewa fatima da 'ya'yanta ya ninka na baya sai ga shi suka ga akasjin haka, wannan abu yayi wa Hanne ciwo shiyasa taci alwashin cikin ire2 amakircinta sai tayi kutungwila ta haddasa rikici a gidansu Aneesa, wannan 'ya'yanta take gayan mat, kaji shirme, wai yaranta take batawa. Allah ka ganar da wanda ya kauce hanya, rashin lfya ya samo asaline wata ranata da Fatima bata nan, su Aneesa sun tafi makaranta hadda da suke xuwa a tudun wada wato Nurul tilawa, duk ranar asabar da lahadi, idan suka tafi karfe 8am sai 6pm suke dawowa. Naku akodayaushe: (Abduluk)MIJIN ARO 1**8 44) Gida ya rage da Basira amarya sai er diyarta, tana ta hidimat dora girkin rana saboda 1pm mai mashin zaizo ya dauko abincin da yake kawai su Aneesa makarantar. Hanne ta shigo gidan saboda taga abbansu Aneesa ma ya tada motarsa ya fita. Basira ta dubi hanne, tace lah sannu mamansu haula, hala en aike kike nema? Hanne ta tabe baki cike da iya haddasa husuma, tace yan aike? Ai 'ya'yan sasan nan basu aikuwa. Ai daga su sai uwarsu suke rayuwa, ko kin taba ganin yaran na shiga wani sasa balle a aike su? Ai gidan nan tsakanin ko da su ido, babu kamar mai kulu2 idon nan irin na uwarta. Mai hali irin uwarta da bata ganin kowa da kima, Basira tayi murmushi tace wa kenan? Hala aysha? Hanne tace wace aysha? Ai aysha ce tayo hali irin na ubanta ai tana shiga cikinmu, Wannan sumuma kashe din Aneesa miskila marar magana irin uwarta, cikinsu fal da mugun abu. Basira tayi murmushi tace, ni kam kinga kaf yaran nan ba wanda jinina ya hadu da shi irin Aneesa don tafi aysha hankali da nutsuwa ga ladabi da biyyaya, ko ubansu na fadin haka, aneesa bata da kwiuwa irin aysha. Nikam ita da uwarta basu da wani aibu bansani ba ko nan gaba ma gani tunda ban dade ba. Hanne tace ai kuwa nan gaba za su fito miki da halinsu na asali, amma yanzun ba zaki gane su ba, tunda ke xuwan yau ce, sai gaba zaki gane idan suka hadar miki kai su tasamma korarki cikin gidan. In banda ke wa aka bari ta shigo gidan, sai ya nemu abu kiji abu rigidi2 sai kuma kiji shiru, anbi dare an bi rana an hana auren kema Allah ne ya nufa ga rabo nan ma kila an samu, tunda jiya nake cema sa ina amarya, yace kina kwance massara ta rufe ki har ina masa tsiya yana dariya, kinga yanzun ko cikin gareki, idan baki sa'a ba sai an raba ki da shi. Ki bar ganin matar nan kamar ta Allah kullum cikin hijab zulum2 mugun abinda ke zuciyarta yafi karfin tunani. 45) Ita dai Basira shiru tayi bayan tace Allah ya kyauta. Sai Hanne tace, bari in koma gida dama na leko ne in ga jikin naki na dauka har yanzu kina kwance ne, ashe kin mike na dole kina bautar girki, ita da 'ya'yanta sun fice abinsu tunda sunga kin juri wahala ko ba girkinki ba dole kiyi, idan kina son zaman gidansu. Gwiwa ba kwari Hanne ta fita, tunda sam ba sami yadda take so ba, duk yadda ta dawo tsegumin Fatima da 'ya'yanta amarya Basira bai shiga kunnenta ba, amma duk da haka ta sha alwashin yau da gobe sai tayi nasara. Hakan ne kuwa ta kasance, don kuwa yawan shigiwan da Hanne takeyi a boye da wanda 'ya'yanta keyi sun wa Basira hudubar tsiya, ya soma tasiri a zuciyarta, saboda yanzu ta kai ga ranar da ba garkinta ba, bata taya Fatima ko tsinke balle idan Fatima tana uzurin fita, cewa tayi ba zatayi ba, duk mai girkin idan zai fita yayi abinsa kafin ya fita, kuma dole mutum ya dawo da wuri ya dora na dare, amma ita Basira daga baya Hanne ta zuga ta akan idan tana da girki anguwa ta kamata kada ma ta tsaya bata tym dinta wajen yi musu girki, tayi tafiyarta dole Fatiman tayi ko don cikinta dana yaranta, in dan gudar diyarta ne ta dinga tafiya da abarta, hakan kuwa akayi, ita dai Mamansu Aneesa ba tace komai ba idanu ta kawo ta zuba ma Basira tunda ta san zugata akeyi. Ga kara da take yawan kaiwa Abbansu Aneesa tace Fatima tayi mata abu kaza ba ya bincike sai ya hau kai ya zauna ya dinga fada, idan kuwa su Aneesa ne ranar sai jikinsu ya gaya musu, aysha ce kawai bata kai kararta saboda ta lura ita er gaban goshin ubance, kuma kota kai kararta ba ya daukar mataki, shi ya sa ta hkr Hanne tace ta daina, ta taya shi som Aysha zasu fi daidaitawa. Ranar wata monday su Aneesa sun dawo sch kenan ko abinci ba su ci ba, Basira ta fito ta dubi aneesa tace, Garin tuwonmu ya kare ga masara can a buhun bagco ki dauka ki kai mini sirfe da nika. 46) Aneesa tace, ina Iliya almajiri fa? Tunda safe da kin bashi da yanzun anyi nikan, tace banda dama baa uwar iyayi, ke kadai nake jira ki dawo ki kai mini, shi ai ba bawan gidanku bane da komai za'a ce sai shi. Kamar tace ga Aysha nan ai itace kasa da ita, sai dai tayi shiru saboda ganin Mama ta fito ranta a bace ta dubi Aneesa, tace ke karama! Basira sa'arki ce zaki fada ta fada? Ko ko shi Iliyan bawanki ne, to maza kiyi sallah ki ci abinci kije ki kai bana son rainin arziki. Allah ya sa Aneesa ma tayi sallah shi yasa tana tube kayan ta ta kewaya bayi ta wanke jikinta ta gyara kanta sannan ta fito ta danci abinci kadan, sai ta dauki ba buhun tana fitowa zauren gidansu suka yi kicibis da sagir ya dubeta, ya dubi buhun hannunta yace, Aneesa ina zuwa haka ne daga dawowarku sch? Tace wlh an aike ni ne, daga ina haka yace makaranta, na sauka anan dan kawai in ganki inji sanyi gashi kuma fita zakiyi. Tace, to ba gani ka ganni ba, ai kaji sanyin ko? Yace sosai ma, amma kuma ai ba ganinki kadai zanyi ba, hira nazo yi. Tace, sai ka jirani in dawo ai ba zan dade ba. Ya leka buhun hannunta ya ga tsabar masara yace, ba dai kace mai kai nika ba? Yace Haba haba, wlh kin wuce kaiwa tunda kina da kanne, kuma kuna da almajirai a gidan nan ni bani in kai. Amma gaskiyya ba zan yada kije bin layin nika ba. Yana kici-kicin amsar buhun ita kuma ta hana shi suna haka sai ga daya daga cikin yaran Hanne zai wuce cikin gida, ya tsaya yace k. Sagir ina wuni? Yace lfy lau, zo nan ina zaka? Ba ko ina, yauwa ta amshi buhun hannun yayarka kaje ka kai mata nika da sirfe yanzun nan ka dawo ina jiranka anan. Ya amsa jiki na rawa sagir ya ciro naira dari a aljihunsa ya mika masa ta fi, ita dai Aneesa tana tsaye tana kallon ikon Allah, ita kam tasan in baya ga 'ya'yan Hanne na tsoronn sagir babu yadda za'ayi salisu ya kai nikan nan, ko da kuwa uwarsa ce ta aike shi, sai ta bashi lada yake zuwa, in ma bai gama ba ko ta bashi ladan ta bishi da lallashi ba zai je ba, idan kuma ya amsa to yana fita zai aiko yara da aiken ya gudu abinsa, idan abin da za ayi anfani da shi gurin girki ne, har sai wani ya siyo ta hirka bai dawo gidan ba don sangarta, to ana gama abincin zata sa aje anemo shi, wai ya zo ya ci abinci, ko ita da kanta ta dauka gyale ta tafi nemansa. 47) Suna nan a zauren suna hirarsu ta masoya, su Haulata suka fito za su fita. Yayi daidai da dawowar Salisu daga kai nika, agabn idonsu ya mikawa Aneesa nikan sannan ya ba sagir sauran chanjin. Suka gaida kawunsu suka fita, ba su dade ba sai ga su sun dawo. Aneesa na ganinsu ta san tsugudidi ya dawo da su, tym din da suka fito za su sake fita suke ce mamanmu tace in ka gama ka shiga zata baka sako can gida. Ya daure fuska yace, daman kun dawo ne ku gaya mata na zo gidan ban shiga ba gurinta ba? Ku dai ba kwa rabo da tsegumi, Haula tace mu bamu gaya mata ba dama tana neman salisu ne, daya shiga yanzun shine yace ba yawo yaje ba, kainme ka aike shi idan karyane ta tambayemu. Shine ta atambayemu, muka ce eh zaka zo kana zaure. Ya gayara fuskarsa yace, to naji kun kyauta, shima salisun daga yawonsa ya dawo na aikeshi, shine zai fake da cewa ni na aike shi, ita kan Aneesa ta san wannan kai mata nika da salisu yayi sai ya janyo jidali tsakaninta da Hanne har da mamansu. Bayan sun fita ta dubi sagir tace, bari inje in kai nikan cikin gida, kaima kaje gurin kiran da aka maka. Ai kuwa yana shiga yayarsa tayi kicin2 dai rai tace, meye dalilin da za a aiki Aneesa dan ita shaffafiya da mai ce zaka amsa ka ba dana don shi bawa ne, ita kuma tafi karfin a aiketa dole ita ga budurwa, in banda kinibibi ina kanneta da ba a ba su ba sai nawa yaran. To wlh ahir dinka kada ka kuma yi mini haka, in hutu kake nema mata ai da kaine ya ya kamata ka zo ka dinga zuwa mata aiken, tunda ka zama sullutu. Yayi murmushi da yake shi mai barkwanci ne, kuma ba shi da surin fushi, yace ni ba don zakice na zama sakarai ba ai, da na dawo gidan nan ko don in dinga tayata ayyukan da naga take sha kullum. Taja Uban tsaki, au abin ma wasa ka maida shi? Tunda ka maisheni abokiyar wasanka, to ni zan gamu da Aneesan gobe idan aka aiketa ba zata kai ba yarana ba, sanin halin yayarsa tasa yasa ake barkwancinsa gefe ya soma magana ta fahimta da fadin gaskiyya da ya ba mata akan zumuncinsu da ta riga ta tarwatsa. 48) Allah ya hanne a bar maganar wasa, Aneesa ko ba soyayya tsakanina da ita ai er uwar salisu ce, ta jini ko ni kawunsa bance yaje mata aike ba zai iya zuwa mata ba, idan tace yace gaskiyya in ma da wani abu tsakaninsu da iyaye bai kamata ku dinga saka 'ya'yanku a ciki ba, saboda zumuncinsu kuke ruguzawa tunda idan ki ba zu kuyi ba tsakaninku, su dole ne suyi zumunci da juna tunda alakar jini ta hada su, kuma alakar jini wlh ta tafi gaban wasa, xumunci dole suyi shi tunda Allah ne da kansa yayi maganar zumunci dole suyi shi tunda Allah ne da kansa yayi maganar zumunci kuma duk wanda baiyi shi a duniya ba, dole zai yi shi alahira, to ba gara ayi shi tun a duniya ba cikin dadin rai da kaunar juna. Tunda rayuwar duniyar 'yar kadan ce ta lahira tafi ta duniya tsayi nesa ba akusa ba, itace mara iyaka. Tayi murmushin da bai kai ciki ba, tace sagir kenan, in dai wa'azinka akansu Aneesa ne na riga na saba jinsa da dai akan wani abu ne kila zan dauka, amma banda wadancan gara ma ka kyayeni, tun kafin namu zumunci ya baci ni da kai. Yayi murmushi a ransa yace, in dai zumunci ne da ke ai da tuntuni ya lalace da ace ina daka ta taki, in banda ni cikin en uwa wa yake jurar halinki, har cewa ake yi ba ni da zuciya inji en dakinmu. Yace ai ni da ke zumuncimu babu mai raba shi, tunda ko alahira sai munyi shi, wannan zumuncin yaran nan nake son ki kule musu shi gam2 tinda dai kece babba a gidan nan. Inbanda Goggo ita kam ba a sata alissafi, tunda mara lfy ce amma Allah yanxun kece uwar gidan nan. Ko shawara za ayi dole a ce kece kan gaba. Ta tabe baki, naji nasiharka yaya sagir, ka tashi ka tafi. Yayi dariya ya kwanta bisa doguwar kujerarta yace, ni ba yanzun zan tafi ba sai naci tuwon dare. 49). Tsarin zaman gidansu Aneesa yanzu ya chanza kwata2, babu wani kwanciyar hankali, saboda Basira yau gobe yasa ta dauki zugar Hanne dadin munafuncinma, yaran hanne yanxun dakin Basira suke wuni en matan. Duk ranar girkinta ba yin abinci yadda za'a koshi, in ma miya ce ta kara kana cin abinci to baka isa ta kara maka ba, sai dai ka ci gaya ko ka hkr da abincin, mama da ta lura da gayya Basira keyin hakan sai tana dafa musu wani idan basu koshi ba, nan ma Basira ta gaya ma maigidan, yace sam bai yadda akara yi masa girki 2 ba. Idan mutum bai koshi ba ya hkr, wai sharri ne kawai za ace a gidan sa ba adafa abincin isasshe. Sai mama tanayin miya ta ajiye idan basu koshi ba sai su siyo biredi suci da miya, anan ma ta kai masa tsgeumi yayi ta fada wai munafinci ne... Mama sai dai ta shige kuryar daki tayi ta kuka don bata da wanda zata gaywa, yayai mata maganin abin sai Allah shi yasa ta kai masa kukanta. Yawanci idan lamarin gidan ya ishi Aneesa, in dai mama bata da girki ranar sai ta gudu gidan Hajiya abinta tayi kwanciyarta ta huta, saboda gidan bata isa ta kwanta ta huta ba, abbansu na ganinta akwance zaice mazata tashi taje ta ya auntyn su aiki, to akan taya aikin watarana sai ta kai kararta tace tayi mata kaza ba daidai ba. Tana kwance bisa kujerar hajiya idanuwanta na bisa Tv da remote a hannunta tana latse latse daga karshe ta kamo tashar saudi qur'an, tana kallon yadda yara kanana ke kwararo karatun qur'ani cikin murya mai dadi ga tajweed sun fiddawa. Tana tallabe da goshinta tana sauraron amma idanunta a rufe, har hajiya ta fito daga dakin baccinta, tazo gefen Aneesan ta zauna tana cewa, jikine ko garin ne yau naji ki ba surutu ne balle dan girkin da ake mini, me ya faru? MIJIN ARO 1**9 50) Aneesa ta girgiza kai tace, ba komai

Chapter 3 of 7