Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
2 / 7
muku ba idan bakyaso kuyi magana sai mu canza da wani. Muci gaba ko mu ajiyesa haka? MIJIN ARO 1**4 Ranar litinin Mahifin Aneeesa bai barta taje sch ba, tana gida har ya fita zuwa gurin aiki, ta shirya kannenta suka tafi sch, yayi saura daga ita sai mamanta a gidan. Ta tashi ta gyara gidan tas tayi wanke wanke zatayi wankin yaran sai maman ta hanata tace, Bar wankin nan masa kiyi wanka in aike ki tudun wada gurin Ummata. Aneesa da hanzarinta taje ta yo wanka ta shirya duk da ita Allah bai yo ta mai son kyale kyalen mata ba, ita ko kwalli bata sawa daga vaselin sai farar hoda sukenan kayarn shafarta, har kanwarta mai bi mata ta fita iya kalailaita ita kam duk wannan baya gabanta, don dai Allah ya bata kyau dan asaline shiyasa ko tayi kwaliyya ko baatayi ba kullum fuskarta tas zaka ganta. Maman ta gaya mata sakon maganar kudi ce na komawa asibiti yin hoto, shi Abbansu yayi biris da lamarin Aneesa tace, Mama ko in ranto gurin Hajiya tunda wata ya kusa karewa idan aka yi biyan basukan anko nana ba sai ki bata ba? Amma Umma sai in ga kamar kina takurata ne, Maman tayi murmushin takaici tace, karama to ya zatayi,? Ni nasan abinda yasa ba kya son zuwa saboda kina ganin idan na aike ki amso kudi gurinta ranta na baci ba wai bata da shi bane yasa take bata rai ko bata son bayarwa. haushi halin ko in kula da babanki ya mini shi ke damunta tunda ta san duk abinda zan nema gurin Abbanku baya rasa bane. bayarwa ne ba zaiyi ba, kin ga kuwa dole uwa taji zafin ba a kyautatawa diyarta ba$ kta kuma Hajiya ko na ranta idan na mayar mata ba amsa takeyi ba, shi yasa bana son zuwa, tashi dai kije gurin umman, ki gaishesu.Ta mika mata Naira Hamsin kudin mota ta amsa ta saka hjiba dinta ta tafi. Tana zuwa dai2 gidan hajiya ta hangi motar dan Hajiya da ke aiki a Abuja ya zo har zata wuce taji shai songaitwins da matarsa ke goyo.Alahyasaita ai tunda aka haifi Yaran take bala-n son su, lafiyayyu. farare kyawawa da su tamakar 'ya'yan turawa suke. Tun suna jarirai wani zuwa da sukayi suka kwana da za su tafi taje tayiwa Hajiya rada annne wai da su tafi da ita gidansu ta taya. Auntyn Abuja rainonsu, Hajiya ta dubeta Galala tace, saboda rainon su twins zaki bisu Abuja ki bari karatunki? Lallai wannan soyayya taki da yaran nan tayi girma, keMa Allah ya sa ki fara da twins din. tana jin hakan ta fyalle da gudu bata ma tsaya taga tafiyar en abujan ba. Rokon Allah ta dinga yi Allah ya sa taga aunty abujan aka zo, dan taga en 2 ai kuwa tana shiga taga yaran a cinyar kakarsu. Sallama kawai tayi a falon ta suri daya tana fadin Hajiya wannan waye na dauka Sultan ko Suhail? Hajiya tace kema kenan uwarsu baki gane su balle ni ina jin wannan ne Hassan. Aneesa tace yauwa ga sultan kenan. Ta juya ta soma gaida uwar yaran. dake zaune can doguwar kujera ta amsa mata da sakin fuska, albarkacin tana son yaranta kamar ta hadiye su, In baya ga haka ba kowa take wa fara'a a dangin mijin nata ba, shiya sa ba kowa ke shiri da ita ba. Hajiya kadai take shakka kuma ita kadai ke kiransu da sunansu na Asali Hassan da Hussain tunda aka haife su Hajiyan tace abar musu sunan su ita kuma uwar yaran ta. cewa mijinta wai kauyanci ne wannan sunan yayi common da yawa, tafi son sun unique shine ta zaba musu sultan da suhail, kuma haka kowa ke gaya musu. Akkala yanzun yaran sunyi shekra2 da haihuwa. Suhail shima ya taso daga cinyar Hajiya yana cewa Aunty nima. Ya mike hannunwansa wai shima ta dauke shi. Tayi dariya ta sauke sultan tace yi hkr da ma zan dauke ka ai. Mamansu ta danyi murmushi tace ya dauka yawo zaki tafi da sultan tunda ya ganki Da hijab, haka suke wannan kishin idan mai rainon su ta dauki daya shima dayan dole ta dauke shi. ta dauki Suhail din sai sultan ya fara kuka, haka nan ta hada su ta dauke su tana nishi saboda yaran kosassune. kujerar da maman su take ta akaisu ta zaunar da su tace, ku zauna anan bari in je in kawo muku chocolate zaku sha? Gaba dayansu suka amsa eh, ta zo gaba Hajiya tace, Hajiya bari naeTudu wada gidan Umma, Mama ta aike ni. Tace, to sai kin dawo ki gaida Umma, idan kin dawo ki biyo ta nan Yayanki na son ganinki. don tunda suka zo yace a kiraki, yaunxun kuma ya fita ganin abokin sa A GRA tace, bari nayi sauri in dawo. Tayi Rashin sa'a don bata sami Umman ba sunje dubiya asibiti, saboda haka dole ta zauna jiranta saobda muhimmancin sakon da zata amsa, tunda goben Maman zata koma asibitin. Har tayi azahar taci abincin ta dan kishingida sai wajen 2pm sannan Umman ta dawo$ Duka taji a gadon bayanta Umma nacewa, wacce raguwarce ke min minshari a daki, daga ci sai bacci, wannan ai sai ki firgita mtane da minsharinki. Ta tash tana sosa wajen, ni wlh kada ki karya min baya ki yiwa mijina asara, tunda kin san nafi karfin kwartakwashin mijinki. Haka suka yi ta barkwanci. Aneesa sai wajen 3pm ta bar tudun wada. abakin kasuwa ta tsaya ta sayi jakar Eclairs don ta kaiwa su Sultan da tayi musu alkawari. jikinta ne yayi sanyi tunda taga bata ga motar su a harabar gidan ba, ba dai sun tafu ba? kila sunje wani gurin ne ta san dai idan suka zo yawanci kwana sukeyi. Tana shiga Hajiya ke gaya mata sun tafi wai Yayanta ya dawo har can gidansu yaje akace bata dawo ba, kuma basu dade da tafiya ba. Taja tsaki tace, Amman ai naji haushi har chocolate din nan da nayi ma su Shuhail alkawari saida na tsaya na siyo musu, ni na dauka kwana za suyi, Umman ce na iske sunje dubiya shi yasa na dade. ta mikawa Hajiya ledar tace, ga ajiya nan duk ranar da suka dawo ko da bana nan ki basu. Ko idan daddyn su ya zo shi kadai ki bashi ya kai musu. tana amsa tana cewa, oh wadannan yara da a garin nan suke da sun san suna da uwa mai ji da su. Tayi dariya ta mike tace, Hajiya bari in karasa gida, zan dawo da yamma zanyi miki wani haddadden girki da aka koya mini. tace Yau laraba kada tayi girkin gidan nan da kenan? tace, to shikenan. zo ga sakonkinki inji yayanki. Tace daga kushin din can ki dauko kudi, Ta mika mata tace wannan yace ki sayi books din sch da kukayi magana, wannan kuma ki sayi kayan makeup. Ta amsa tayi godiya ta kara cewa, kai yayana da tsokana yake ni yaushe yaga ina kwaliyya? Daga vaselin sai hoda nake shafawa ai. Mama fada ta kama yi mata da ta isa gida akan ta dade da yawa, tace wlh mama Umman ce bata nan sunje dubiya, shine na jirata. ga sakon tace in gaisheki da jikin. idan da wata matsala ki yi mata waya$ tace kinga ma kudi nan dubu biyar Ishaq ya gaisheni ya bani, Ya dade muna hira yana jiranki, Hajiya tace masa kin shiga baya nan ko kun hadu? Tace sun tafi nima da zan tafi gidan Umma ne naga motarsa shine na shiga gidan, kafin in dawo har sun tafi, nima kinga kudaden da ya bani har da books din da na fadan masa, shine yace na fada masa sunan ya sayo min ko zai aiko min da kudin in siya. Mama tace Allah ya saka masa alkhairi, ya karamasa budi, nikam Ishaq babu abinda da zance masa don ko bai zo ba garin nan in dai zai turo ma Hajiya kudi sai kinga nawa kason. washegari Maman da sassafe tayi wanka tayi shirin zuwa asibiti, tunda abbansu Aneesa ya ga tana shiri ya soma hade rai, saboda ya san zata tambaye shi kudin hoto, da ta ga haka sai bishi dakinsa tayi sallama a ciki2 ya amsa, sannan daga baya ko kallonta baiyi ba ya ci gaba da gyara wasu takardu, ta nemi gefensa ta zauna sannan ta sake gaida shi , ta dan dube shi tace, daman yaune zan koma sibiti kuma zanyi hoto daga nan, yace amma ain naga ya miki bani da kudi. abar maganar hoton sai karshen wata ko? Koko dole ne sai anyi hoto a haihu lfy? Ya kar maganar a hasake idanunsa kyam a kanta, Ta risinar da idanu kasa tace, nima da na hkr din sai jiya Ishaq ya shigo ya bani 5k shine zanje inyi hoto sauran kidin sai in sayi sauran kayan haihuwar da bamu syab. Dan Aunty. MIJIN ARO 1**5 Ya dan tabe baki yace, shikenan Allah ya taimakeki tunda dama kin matsu kiyi hoton, sai kije a dawo lfy. Ta mike gwiuwa a sabule saboda wannan halin ko'in kula da yake bata wanda tun asalin aurensu ba haka ta saba gani ba, ita anata hasashen idan zama yayi zama yau da gobe ne Ma'aurata ke fuskantar canji a tsarin zamantakewarsu ta fil azal, koko ta gundure shi ne yake mata haka? Ita kam ta rasa dalili, kila kuma wani abu take masa baya so, to in wannan ne ai ta sha tambayarsa sai yace shi batayi masa komai ba. wani tym din idan ya kuntuka mata wani abin yaga tana zubda hawaye sai duk ya damu yayi ta lallshinta da bata hkr wai shima ya rasa dalilin da yasa yake yawan bata mata rai. Ta taba gayawa hajiyan Ishaq sai tace ta dinga yawaita nafilar dare da tsananin addu'a insha Allahu komai zai daidaita, shi ya sa ta kae kaiwa Allah kukanta, ta rungumi shawarar Hajiya shine fa wani tym ta kan ga sauyi. kafin ya sake botsare mata, Haka dai zaman yake yau fari gobe tsumma. sannan gashi ya sa duk abinda aka ce kta ko Aneesa sunyi a gidan nan yake saurin hawa kai ya zauna, ya zama Gabar wadda bata juri zunguwa ba. tana shiga daki ta iske Aneesa da kofin shayi tana fifitawa, ta dubi Uwar tace, Mama ga tea din naki baki karya ba zaki tafi? Naga kina ta sauri. Ta mikawa Aneesa hannu tace bani to insha bana so in makara kinsan asiboitin daga can wuce gurin hoto gara tafi da uwri. Ta zauna ta soma kurban tea din, Naeesa ta dubi Maman tace, Mama kiyiwa Aisha magana tayiwa Yara wanka ni sai inji da abin karin shirya su, tunda ni Abba ya hanani zuwa sch idan suka tafi sain gyara. gidan inyi wanke2 Ta aje kofin tea din tace taso mini ita tunda tayi sallar asuba ta bi ta nade a gado tamkar tare da shi aka halliceta. ai dole ta tashi ta taya ki wankansu. kema ai ba zamanki kenan ba agida, ranar mon dole kije sch in kuma ya hana sai in gaya ma Yayan sasa, gaba ai da gabanta. Taje ta taso Aysha sai zumboro baki takeyi, tazo gefen Maman Ta zauna, Maman ta dube ta tace, ba zama zaki ba tashi zaki yi ki yiwa Yara wanka don ni asibiti zanje ita kuma karama aiki zai yi mata yawa saura na dawo tace min bakiyi musu ba. Haka aysha ta sirka ruwan wakan da zafin gaske tana shekwa Yaran suna tsala ihu, suna zabura saboda zafi. don taga Mama ta fita, kuma tayi hak ne don Aneesa tayi magana su yi fada tana jin haushin ta tasheta abarcinta, dan ta san babu abinda Aneesa ta tsana. irin kukan 'yan kanneta, ita kuma ta san abinda aysha ke nufi sai kawai ta shareta ta cigaba da aikin gabanta. Tana durkushe tana wanke2 bayan ta shirya kanneta suna daki, suna karyawa sai ga Aysha ta fito daga dakin ABban su da Uban kayan Wankinsa a tunanin Aneesa yau Aysha ce zata kai masa gurin mai wanki da guga na layinsu, har tana mamaki. Aysha da ko bokitin ruwa bata iya daukowa awaje wai kunya takeji ita adole ga budurwa, shine yau sai gata da tilin daurin wanki, da mama ce ta aiketa da an sha korafi da zumbura baki. 'wsai Aneesa taga Aysha ta dire wanki agefenta tace, sako daga Abba yanzun zai fito zakiji bayani. murmushi kawai tayi tasan yau itace mai kai wankin kenan, to meye sabon abu a gurinta, kaya ko yafi wannan zata dauka don ita bata dauki kanta akomai ba, tunda ko ruwa ne idan nasu ya kare kuma ba na famfo zata fita ta debo a makwabt. Abbansu yace tunda kin zama baiwa agogo sarkin aiki, to ga wanki nan daga yau na daina kaiwa gugda ke zaki dinga yi idan sun bushe ki goge su... Ki goge da dutsen gawayi. ya ciro dari 3 ya mika mata yace, Gashi nan ki sayi sabulun da sitati. Ta amsa hannu bibbiyu ba tare da wani bacin rai a fuskarta ba tace, Insha Allahu kafin ka dawo zan wanke in goge. Adawo lfy Allah ya bada sa'a. kafin ya fice ne ta bishi da wannan addu'ar bai amsa ba yayi ficewarsa abinsa. Da yake Allah yayi Aneesa mai zafin Nama kuma sam bata da kasala, ta saba da kazar2 shi ya sa kafin 10am har ta gama wanke2 ta share dakin Mama da Na Abban tare da hada ruwan girki. Ga kayan da yawa 15sets cikin ikon Allah kafin 12pm har wasu sun fara bushewa, Allah ya taimaketa akwai wutar nepa sai kawai ta fara gogewa$ Tana cikin gugar ne taji bugun gidansu ta san kannenta ne suka dawo, tana bude musu suka rungumeta Jafar yace, Aunty yunwa nakeji kin gama abinci? Tace naga jafar ai na sanka chop2 ne. Sai da ta canza musu kaya sannan ta shimfida musu tabarma a inuwa ta xuba musu abinci suka soma ci. ita kuma ta koma aikinta. Can taji ana knockn kofa tace Amira je ki bude kofa kila mama ce$ A madadin Maman taga ashe kanin hanne ne ubansu daya( matar baban sasa) yana zuwa koda yaushe gidan shima ya zama kamar dan gida. Ta gaishe shi yace Ina Aneesa fah? tace tana dakinsu tana guga$ Ya karasa ciki ya iske Aneesa, Ta dube shi tayi murmushi tace, a'a dan uwanmu kana garin nan kuwa? ko hutu ne ya boye ka? Yayai murmushi yace wani hutu ne ga dan makaranta, ke ce ma yar hutu tunda nazo gidan nan sau 2 ana ce mini kina nan bakya zuwa makaranta. kinga ai kce 'yar hutu. Tayi mrmushi, dole ta sa banje sch ba amma ran monday idan ka zo kamar wannan tym in bazaka ganni ba ina sch . Yace gaskiya ki din daina fashi, gaki da brain amma kina son ta dakushe ki ma 'ya'ya na asara. Ta harare shi saboda tasan don ya tsokaneta yace haka shi fa nan dole sonta yake yi, ita kuma tana ba tym din luv bane yanzun a wajenta, bayan haka ma kanin Baba hanne ne babbar makiyarsu ita da uwarta, ko da yake ba halinsu daya ba, kuma shi ubansu ne daya ba wani shiri suke sosai ba da baba hannen, tunda shi dan uba ne kuma acewarta yana mata katsalandan tunda idan yazo gidan dole suke aje narkewar da da sukeyi su fito rai bace suna aikin gidan, ita ganinta yana takurawa yaranta ne, bata san gata yake musu ba, shi ya sa ya zame musu kadangaren bakin tulo abarka ka bata ruwa, har suna suka saka masa aboye da sunji sallamar sa za su ce ga kawu sa'idawa nan, ko suce kawu takura. Ya dan gisnte dariyar da yakeyi, saboda hararar da Aneesa take masa yace, don nace 'ya'yana to naki ne ke kadai, inace mu 2 zamu haife su? Tsaki tayi kawai ta cire iron din daga wuta ta tashi ta fice ta bar masa dakin saboda zancensa ya bata kunya, dama wanka take son ta shiga kawai sai ta sirka ruwanta ta shige bayi, taga duk ayyukanta har miyar dare ta daura. Tana fitowa tayi alwala ta shige daki, har ya kusa gama gugar ma da takeyi, ta tsaya sororo. tana kallonsa yayi kamar bai san shi take kallo ba ai jo tayi yace,kin sa fa ni bawanki zan zama idan mukai aure, shiyasa ma tun yanzun zan fara bauta miki, ke er hutuce Tace tym din sallah yayi a gara kaje kayi, ya karasa goge wandon sannan Ya cire iron din ya mike tare da zuba mata ido, yace bari inje inyi sallah in dawo yau akwai latest labari ko ba kya son ji? tace idan na alheri ne ina so amma idan na yan matanka ne jami'a akara gaba da shi. Dariya ya kama yi sosai har da rike ciki ita kam kallonsa kawai takeyi, sai daya gama sannan yace, Ni wlh ban taba sani ana sona haka ba har da kishina, lallai zan zo in kama kaina kada tsautsayi ya sa a ga ina magana da wata ayi min bulala. Ficewa yayi ita kam ta bishi da harara tana cewa, kishi? lallai ashe zan wahala idan akanka zanyi kishi wanda yan matan jami'a ke rububi. Juyowa yayi yana gab da ficewa yace bari in dawo kema zan gaya miki yadda ake ta rububi akanki. Kafin ya dawo tayi sallah ta shirya cikin doguwar riga ta zauna tana cin abinci sannan ya dawo ta na ganin ya shigo tayi sauri mikewa taje ta kawo masa nasa, don tasan yana iya saka hannu yace sai sunci tare. Ita kanta yanzun a tsorace take saboda dan yinin da ya shigo yayi yayarsa tana iya jin haushi ko kaji wani zance ya fito. Gaba dayansu da yara suna tsakar gida ne sukaji sallamar mama tana ganinsa da fara'a tace aka sagir yau kaine a gidan? Ya risina da fara'a ya gaisheta. Yara kuma suka rungumeta suna mata oyoyo ita Aneesa ta isa ta amshi jaka mama tare da yi mata sannu da zuwa, dukansu daki suka bi Maman har da Aneesa suka bar sagir ya kelo yace, Mama ni zan wuce, tace au zaka tafi to ka gaida gida da su goggon da Hajiya. Aneesa ta danyi jim sannan ta biyo shi tsakar gidan sukayi sallama ya tafi. A daki mama take shaida mata yadda ya kasance a sibitin, tayi hoto sun tabbatar yanzun komai lfy tunda sungyara yaron kwanciya. Aneesa tayi murna da jin haka don bata son Mama ta samu matsala ko kadan. Aneesa sun fara shirye shiryen zana xams dinsu ta JSSce hakan ne ya sa ta zage damtse gurin karatu da bada himma zuwa wajen sch saboda dama ita mai himma cema shi yasa duk wani kuskure da zatayi mata sanadin hanata zuwa sch. Gashi a tym din cikin Mamanta ya tsufa, dole suka raba aikin gidan ita da Aysha ba don ayshan ta so ba, duk da dai itama ai wannan tym din tana tausayawa Maman wahala da take ciki. Ranar talata Aneesa ta dawo sch daidai gidan Hajiya ta hango motar Ishaq, kamar ta shiga ta gaishe shi, sai dai ta wuce abinta, don ta san in dai ba sauri yake ba zai shigo gaida Mama balle yadda ya san bata cika lfy ba shiyasa ko waya yayi sai ya tambayi lfiyarta, har kude ya aje musamman gurin Hajiyarsu wai da mama ta fara nakuda ayi maza direban Hajiya ya kaita asibiti don baya son ta haihu a gida kada asami matsala. Zata shiga gidansu kenan sukayi kicibis da diyar yayar Ishaq din. sukayi wa juna murmushi Aneesa tace kamar fa in shiga gidan Hajiya da naga motar Yaya sai dai na wuce$ Tace kuma shi ya aiko in kira ki Mama tace kina sch, amma ta san kina hanya. Aneesa taka hannunta mu koma ciki in cire Uniform dina sai muje. in kaji kira samu ne balle kirian irin na manya masu keta hazo kullum. Suka fashe dariya. Doguwar riga kawai ta saka da hijab ta so taci abinci sadiya ta hana wai taci a gidan ay,Alh ytiakt tayi sallah a sch. A harabar gidan suka hangeshi yana ganawa da dafifn mutane, dattijai da matasa masu son ganin wanda duk xuwa sai yayi da gaske yake kwatar kansa a gurinsu, shima sai in sallah aka kira amma duk sai ya sallami kowa da bukatarsa da ya zo da ita, sannan yake shiga cikin gida, shi yasa matarsa bata bari suyi masauki a gidansu da hade dana Hajiya, sai dai su sauka ahotel. Amma idan shi kdai ne nan sashensa yake kwana, yafi son ga shi ga Hajiyarsa. Allah yayi Ishaq mai jama'a tun yana yaro. Kitchen din Hajiya Aneesa ta nufa ta shige ta debo abinci a plate sannan ta shiga falon, ta iske su zaune. Hajiya na ganin ta da palte a hannu tayi dariya taceN Hala dawowarki kenan taje ta taso ki agida ba? Tace da kyar ta barni na cire uniform, ta hanani cin abinci wai yaya ishaq na kira na, kila kudi zai raba mana, ta bi ta dameni in taho yanzun. Hajiya tace kinji kyale wannan 'yar wautar cikinki ya dauka, In bakuyi sa'a ba kafin ya shigo gidan nan sai an kusa magriba. Aneesa tace, ina ce yau zai koma naga ranar aiki ce gobe. Hajiya tace wani wani taro suka zo aviation nasu na matuka jirgin sama, gobe da safe ne taron a goben zai koma, Yanxun ma da aviation din zai tafi to jama'a sun hana shi tafiya. Aneesa tace ni na rasa yadda suke sanin Yaya ya shigo garin nan, kuma kowa ba zai zo haka ya tafi ba. Allah ya karawa Yaya budi, Hajiya tace ameen, to in bai taimakwa wanda baya da shi ba , yayi me? wanda ka bayar shine rabonka na lahira, wanda kaci kayi kiba idan ka mutu tsutsa ta burge shi, idan ma baka ci ba ka tara ma 'ya'ya da jikoki duk hakan take, yaya ma Allah ya baka na kwarai ne za suyi maka ddu'a, shi ya sa nake ba shi kwarin guiwar ya taimakawa kowa ba 'yan uwa kadai ba. Yamma tayi sosai sannan Ishaq ya shigo gidan. Ya dubi Aneesa yace, Aneesa yaushe kika shigo, tun dazun nace sadiya ta kiraki. tace Yaya tun tym na shigo dan kana waje da jama'a ne, Kazo lfy? Ya su Suhail? Yayi murmushi suna nan fly kullum suna damuna wai su zaria wurin Hajiya ko suce Auntyn Zaria, sun ganeki sosai Yaran nan. Tace Allah sarki Yaya yaushe zaka kawo su? Yace ba su ne za su zo ba, kune zan turo driver ya dauke ku ke da Sadiya, kuna gama jarabawa kuje can kuyi mana hutu, suka kalli juna da Aneesa da sadiya su kayi murmushi, saboda duniya babu gidan da suke xuwan irin gidansa sannan babu yaran da suke so tamkar su lashe irin yaransa don Aneesa tym din suna jarirai har lasar Kyan kafafunsu takeyi ta tsotsi Jajayen labbansu, ita dai jinsu take tamkar ta su. ) Ya dubi Hajiya yace, Hajiya kinji ni shiru ko? ina gurin jama'a. Me zan samu inci anjima idan na dawo sallah? tace ban san me kake so ba, amma anyi birabuskon shinkafa miyar ganye ko tuwo kake so? Yace ayi min tuwon semo sai in ci da miyar, Yamma tayi da anyi min kubewa danya. Hajiya tace da ka sani ka gaya min a waya ko ka aiko amma, yanzun ladidi ta gaji sosai tun rana take tsaye a kicin$ Aneesa tace Yaya in yi maka girkin? N iya miya mai dadi har da tuwon, wanda kaci rannan a dakin Mama ma ni nayi shi fa. Yayi murmushi yace Kai Aneesa ni kam ban taba jin labarin kin iya girki ba, nasan dai kin iya wainar flour da shasshaka da meye ma dayan? Tayi saurin cewa Allah da gaske nake na iya girki ka tambayi Hajiya ma ko ita ina mata, kuma yayi dadi. Ya juya gun Hajiya dake sauraronsu tana mursmushi, Hajiya wai da gaske 'yarki ta iya girki? Kada tayi min in kasa ci ta sani neman restaurant a daren nan. Hajiya tace don iya girki 'ya ta iya, amma tun da ka fara ko kwanto to ba zan yarda ta yi maka ba don kada yau hannunta yayi gardama, kace dama bata iya ba. Yayi Murmushi yace, dama kawai bata iya ba, amma bari tayi min ai daga gwadawa jirgin sama ya tashi. duk sukayi dariya. Aneesa da murnarta ta nufi kicin saboda Allah yayi ta mai son girki ce, shi yasa a duk tym din da ta shigo gidan Hajiya bata da tashar kallon sai ta girke2, kuma duk abinda ta gani sai shiga kitchen din Hajiya ta gwada, don ta san Mamansu ba zata juri wannan shirmen ba, a cewar hajiyace mai bata dama tayi duk abinda take so, ko da babu abun girkin yanzun zata tada driver ko ladidi ta aike su su siyo. MIJIN ARO part 7 35) Ta hana shi magana don kuwa Allah yayi mai son yara ne. Tun tym din da ta sami cikin su suhail tamkar ya maida ta cikinsa haka yakeji. Balle tym din da akayi scanning akace en 2 ne duk boys. Sai ya ninka kulawar da yake mata da ko yaya ta yi mosti sai yayi mata sannu da tace uhum zai ce menene ko me kike so? Haka da aka haife su sun sha gata iri2. Ta dube shi tace, Captain yanzun meye abinyi? Yace meye ko abinyi illa mu godewa Allah da kyautar da yayi mana. Ta gintse fuska gaskiyya ba zan iya wannan wahalar laulayin ba. Ga shi na irin na su Suhail ne tym din babu wuyar da ban sha ba. Su 2 ina kwanciya asibiti duka2 shekarunsu 3 ne fa, ina laifin ma su sami shekara 5 zuwa 6. Ni kam gaskiyya ba zan juri wahaka ba gara tun wuri musan abinyi. Ya daure face tamkar ba taba dariya ba. Ba yace me kike nufi? In zubda gudan jinina yabi kwararo? Sam ba zai yiwu ba. Haihuwa da kika ce ba zaki sake ba sai su Suhail sun shekara 5. Kika ce zakiyi plannin wannan kin matsa mini ne na uarda da yake Allah ba ayi masa wayo ko dabara kuma ba ayi masa dole kinga gashi baki cika shekarun da kike so ba ya baki cikin. Maganar cire shi kam babu ita ba da yawuna ba. Kuma ko da wasa kada kiyi gangancin cire mini ciki wlh zan dauki mummunan mataki a kan hakan. Likitan ya shiga bashi baki. Pls captain be a man, kada kayi fushi kasan halin mata su tunaninsu karami ne. Ka bari kuje gida sai ka lallasheta. Kowa zuciyarsa a kuba suka dawo. Safeena kam tun asali ma bata so sukayi haihuwar fari ba da wuri ba, saboda bata son hayaniyar yara, sai gashi Allah ya hada da en 2, har cewa tayi daga kansu ta gama haihuwa, shi kuma yace haihuwa yanzu ya fara bayan su wasu en biyun na nan zata kara tace. Ba dai ita ba sai dai ya auro wata tayi ta haifa masa yaran, sai yace ai kuwa dai auro duk sai ta hada da su sultan ta rike duk zai bata kyautar su. Sai cewa tayi wlh babu wata er iskar da zata shigo mata gida.....

Chapter 2 of 7