Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
An dauko wannan littafi daga shafin https://taskarnovels.com.ng ku ziyarci shafin na https://taskarnovels.com.ng domin samun kayatattun littatafan hausa kama daga kan na yake yake dana soyayya Marubuci ko marubuciya zasu iya turo mana da littatafansu mu dora masu a shafinmu kyauta don masoyansu su rika Downloading a online, Sannan marubuta zasu iya turo mana da tarihin rahuwarsu da tarihin rubutunsu, dama sharhin littatafansu don masoyansu su gani kuma su karu da hakan Domin turo mana da littafi ko tarihin rayuwar marubuci ko marubuciya sai ayi mana magana ta whatssap da wannan nambar +2348140419490 A lura dakyau - kyauta muke saka littafi a shafinmu bama amsan ko sisin marubuci, duk wanda ya amshi kudinku da sunanmu babu ruwanmu, Alura dakyau - manazarta bama tura littafi ta private ku dena binmu private kuna neman mu tura maku littafi, duk mai bukatar littafi yaje website namu Alura da kyau - Littatfanmu suna fitowa cikin manhajoji uku ne PDF,TXT da DOC amman munfi amfani da PDF da TXT masu amfani da wayar android ko tablet ko computer zai fi kyau ku riga dauko PDF da DOC Masu amfani da kananan wayoyi java ko mara java TXT zakuna zaba don shine daidai wayarku This hausa novel was uploaded and downloaded from https://taskarnovels.com.ng You can download more hausa novels there Also you can send us your novel to upload it in our website for your fans to download it online It is free we do not charge for uploading novel Also if you are an Author be it online or Non online you can send us your biography including your book summary,commentary and others via this number +2348140419490 its free we do not charge for our services Note that - we do not charge for our services we uploaded novels and posted biography free, any person that collect your money in our name is your fault do not blame us Note that - pls readers stop calling us and be asking us to send you a novels we are not sending novels through whatssap or private our novels is public at any day, any time you can visits our site and download it Note that - our ebooks came as PDF,TXT or DOC format but the popular format are PDF or TXT, those with android or tablet or pc we suggest you to download PDF or DOC those with java phone or non-java phone we recommend you to download TXT This Novel is downloaded from https://taskarnovels.com.ng to download more hausa novels visits our site at www.taskarnovels.com.ng For feedback and support Facebook : https://facebook.com/taskarnovels Twitter : https://twitter.com/taskarnovels Telegram : https://t.me/taskarnovels MIJINA SIRRINA [7/4, 5:13 AM] El-hajj _©HASKE WRITERS ASSOCIATION (HWA)_ *​MIJINA SIRRINA​.....!*🌹 _(Labarin K'auna)_ **Based on a true life story** _*NA​​*_ *_​​UMMI A'ISHA​​_* _​Dedicated to Alh .I. Uba family​_ *_DA SUNAN ALLAH MAI RAHAMA MAI JIN K'AI,Rabbishrahli sadri, wa yassirli amri, yafqahu qauli.._* _Shafin farko nakine pherty b~b.._ *​1​* ~~~ "Oyoyo yaya kabeer...,oyoyo yaya kabeer.." Wannan shine ihun da yaran dake zaune cikin tsakar gida suna wasa suketa faman yi daidai lokacin da suka ga shigowar matashin saurayin wanda ke sanye cikin farar shadda kansa babu hula sai yar kyakkyawar suma da ya dan ajiye, Fuskarshi dauke da murmushi ya rungume yaran wadanda akalla zasu kai su kimanin guda hudu, Daga inda take acikin kitchen ta sake lab'ewa saboda bata son ya ganta duk da sanin cewar dominta yazo gidan, sadadawa tayi ta buya a bayan fridge gamida leka kanta ta window ta yadda tasan bazai iya hangota ba, Ganinshi tayi rike da hannun Amira da waleeda kannenta sannan ga amir da husna atsaye sai faman jajja masa riga suke suna tsalle,manyan chocolate samfarin coconut chocolate ya debo daga cikin aljihunsa ya mimmikawa yaran, Sunkuyawa yayi wurin Amira saboda itace babba tafi su husna wayo, "Amira ina mama?" "Tana falon abba?" "Yaya NADIYA fa?" "Tana kitchen mama tasata aiki.." Murmushi yayi ya mike saboda yasan aduk inda take taji shigowarsa shiyasa ta gudu ta buya, Yana rikeda hannun su Amira ya bi hanyar da zata sadashi da falon Abba, Sai da ya tsaya yayi sallama mama ta amsa ta bashi izini sannan yasaka kai ya shiga cikin falon, Mama yasamu zaune kusa da abba suna yin hira gefe daya kuma kwanukan abincine da abban yaci kasancewar bai jima da dawowa daga wurin aiki ba, Su walida da amira na biye dashi har cikin falon sai da suka rakashi ciki sannan suka ruga da gudu suka fita,wuri yasamu ya zauna kanshi a kasa saboda kunya da kuma girmamawa, Ganinsa yasa abba sakin fara,a tareda mikewa daga kishingiden da yake ya gyara zamansa yana murmushi, "Kabeeru yanzu kake tafe? Barka da zuwa.." Cikin jin kunya da sose sosen keya kabeer ya daga ido ya kalli Abba, "Ehh wallahi abba, shigowata kenan dama nazo ne in gaisheku saboda kwana biyu ban samu damar shigowa ba.." Murmushi Abba yasake yi ya kalli kabeer din, "Haba kabeer har yaushene rabonka da gidan, nazaci ai jiyane kawai baka zoba amma ai shekaran jiya ma kazo kodai ka manta ne?" Maganar da abba ya fadice tasa mama tsoma bakinta tana dan murmushi amma fuskarta babu yabo babu fallasa, "To ai Alhaji tunda yasaba zuwa kullum jiya kuma baizo ba ai dole yaji kamar yafi sati daya rabonsa damu" Dariya abba yayi yakoma ya kishingida yana kallon kabeer wanda ya gyara zama yafara gaisar da mama, Shiru falon ya danyi nawani lokaci saboda shi kabeer nauyin mama da abba yakeji yanzu sam baya iya sakewa yayi hira dasu yanzu kamar da, Ganin yanata zaune shiru sai dai dan lokaci zuwa lokaci abba yana sakoshi cikin zancen da suke yi da mama yasashi mikewa, "Abba bari naje waje.." "To kabeer tafiya zakayi?" Abba yafada yana gyara zamanshi, "A'a ba tafiya zanyi ba waje zanje" Fita yayi daga cikin falon cikeda kunya, yana fita abba ya dubi mama yana fara,a, "Nasan dama ba tafiya zaiyi ba wurin mutuniyar tasa zaije.." Shiru mama tayi batace komai ba saboda ita kwata kwata bata son wannan maganar saboda wani dalili wanda ta barwa zuciyarta ita daya amma idan hali yayi zata bayyanar dashi ga abban shima yaji, ganin taki zancen yasa abba barin maganar ta hanyar shigo da wani zancen daban domin ya fahimci duk lokacin da zaiyi magana makamanciyar wannan wadda ta shafi kabeer da nadiya mama bata bada goyon baya. Yana fitowa daga falon abba cikin kitchen yawuce, a bakin kofar kitchen din ya tsaya saboda ganinta da yayi tsaye tana mopping bayan ta kammala share cikin kitchen din, Yarinyace yar budurwa wacce bazata wuce shekaru goma sha biyar aduniya ba, tanada hasken fata amma ba farace can ba, tana sanye da atamfa kalar koriya dinkin riga da zani, daga inda yake yana iya hango gashinta dake nannade cikin dan kwalin dake daure akanta, "Sannu da aiki.." Yafadi yana murmushi har lokacin yana tsaye akofar kitchen din, "Sannu da zuwa yaya kabeer" tafada ahankali sannan maganar ma tayi tane cike da kunya, "Yawwa sannu sarki aiki.." Tunowa da tayi cewar bata gaidashi ba yasata saurin dan rissinawa, "Yaya kabeer ina wuni?" "Bazan amsa ba har sai kin jiyo kin kalleni ido da ido.." Murmushi yasaki bayan ya furta mata hakan saboda yasan ba karamin aiki ya hadata dashi ba domin kunyarshi da takeji bazai taba barinta ta iya hada ido dashi ba... _*Ummi Shatu*_ [7/4, 5:13 AM] Humaira Khaleel: _©HWA_ *MIJINA SIRRINA.....!*🌹 _(Labarin k'auna)_ **Based on a true life story** _*NA*_ _*UMMI A'ISHA*_ _Dedicated to Alh .I. Uba family_ _Fatan alkhairi ga k'awata maryam qaumi, kina raina akoda yaushe yan matan shaddad.._ _*2*_ aishaummi.blogspot.com ~~~Jin abinda ya fada ya sata sake sinne kanta kasa tana kallon tiles din dake malale a kitchen din, "Bazaki gaida ni ba kenan in tafi ko?" Kabeer ya fada har lokacin fuskarshi tana dauke da murmushi, "To ba na gaisheka ba kaki amsawa" nadiya tabashi amsa tana mai sake juya masa baya dan kar yaga fuskarta, "Nadiya kenan wai wannan kunyar yaushe zaki dainata ne? Kullum idan nazo sai ki gudu ki buya alhalin nikuma saboda ke nake son zuwa gidan nan, duk ranar da ban gankiba idanuwana radadi da zugi suke yimin, kuma nazo sai ki hanawa idanuwa tozali da kyakkyawar fuskarki? Uhm nadiya? Dan jiyo mana.." Badan taso ba ta dan jiyo dakyar tana kallon kasa, "Kinga kyankyaso nan a bayanki.." Tun kafin ya karasa maganar ta dako tsalle tabar wurin sai gata a bakin kofar kitchen din kusa dashi, dariya ya fara yimata domin dama yasan tana mutukar jin tsoron kyankyaso shiyasa lokuta da dama yake tsoratata dashi, Ganin yanata dariya yasata gane cewar ba dagaske yake ba, Fuska ta bata, "yaya kabeer ashe dama tsokanata kake?" Dariya ya sakeyi ya daga mata gira, "Wasane matar yaya kabeer.." Hannuwa tasa ta rufe fuskarta cikeda kunya domin kowa adangi da haka yake kiranta tun tana yar jaririya har ta girma, kowa matar kabeer yake cemata, "Yau ina ka bar hular taka ka taho haka?" Sai da ya dan matsa kusa da ita sannan ahankali yace, "Wai duk zumudin zuwa ganinki ne yasani manto wayata da hulata adaki har sai da nazo nnpc sannan na ankara.." Dariya itama tafara yi masa, yayinda shikuma ya tsaya yana kallon yanda kumatunta ke lobawa, hakan ba karamin burgeshi yakeyi ba, "Kici gaba da dariyar bana son ki daina" Tsagaitawa tayi daga dariyar da takeyi, "Yaya kabeer na kawo kayi min assignment din biology? Skeleton teacher dinmu yace mu zana nikuma ban iya drawing ba" Makale kafada yayi,"nima ban iya drawing ba.." "Please yaya KB" Jin abinda tace yasashi kallonta tareda sakin wani tattausan murmushi, "Dauko nayi miki" "Yawwa yaya kabeer thanks.." Rabawa tayi ta gefenshi ta wuce fuskarta dauke da murmushi, juyawa yayi ya bita da kallo, yanzu SS 2 take a secondary school alla alla yake ta kammala domin so yake ya zama mijinta sirrinta, Yana nan a tsaye har ta fito hannunta rikeda pencil, cleaner da note book dinta sai kuma modern biology, tsayawa tayi ta bayanshi tana kallonshi domin a zahirin gaskiya yayi mutukar tsaruwa sam bashida makusa ko kadan. Babu zato ya jiyo nan tayi gaggawar dauke idonta daga gareshi, "Yaya KB gashi.." Tafada cikeda jin kunyarsa domin tasan yagane kallonsa ta tsaya yi, Hannu ya mika ya karbi books din hannunta sannan ya sakar mata wani murmushi, ahankali ya furta, "Ki ware idanuwanki ki kalleni son ranki kidaina kunya saboda nidin nakine...." Fuskarta ta rufe da hannayenta ta juya ta nufi cikin kitchen tana cewa "kai yaya kabeer.." Murmushi yayi kawai ya nemi wuri ya zauna kan wani dan dakali dake zagaye da wasu flowers wanda yake opposite da kitchen din, Zana mata skeleton din yafara yi yayinda ita kuma ta kafeshi da ido tana daga cikin kitchen din bayan ta kammala mopping din da take yi, Kallonshi ta tsaya take tayi ko kiftawa batayi,dago kanshi yayi da niyyar yi mata magana nan ya kamata tana aikin kallonshi, Saurin kawar da kanta tayi ta juya zata koma cikin kitchen nan yayi gaggawar dakatar da ita, "Nadiya zo nan.." Tana rufe da fuskarta ta karasa gabanshi ta tsugunna, "Meye kike satar kallona?? Ba nace miki idan kina son kallona kawai ki kalleni kanki tsaye batare da kunya ba..?" "Nifa ba kai nake kalloba yaya kabeer" tafada muryarta na rawa dan jin kunyarsa, "To naji, idan nazana miki skeleton din ai basai nayi miki labelling ba ko?" Kai ta daga masa batare da tayi magana ba, Murmushi yayi yaci gaba da zanen, "to bani labari inji.." "Yaya kabeer nikuma wanne labari na iya bare in baka?" "Ko na makarantarku ma idan kika bani ina so.." "Ai makarantarmu babu wani labari acikinta" "Kedai kawai bakya son ki fada min labarin makarantarku..." Kafin ta bashi amsa mama ta zo daf dasu zata shiga kitchen domin dora tuwon dare, batare da mama tayi magana ba tasaka kai ta shige cikin kitchen, Ganin mama yasa hirar tasu takare sai aikin murmushi da suke aikawa junansu, Littattafanta ya mika mata ya tashi tsaye yana yimata wani murmushi wanda ita kadai ce ta fahimci sakon da yake son isar mata, Kitchen yabi mama yayi mata sallama ya wuce batare da yayiwa nadiya magana ba amma kuma yana ta kokarin aika mata da sakon bankwana ta cikin idanuwansa sai dai ita ta kasa kallonshi, tana tsaye tana satar kallonsa har ya fice daga gidan,wucewa tayi ta nufi dakinsu itada su amira, Akan gadonsu ta zube tana mai tuno yaya kabeer acikin zuciyarta duk da cewar har yanzu bai bude baki ya furta mata kalmar so ba amma tasan soyayya suke yi a boye ita dashi batare da sun bayyanawa junansu sirrin dake cikin zuciyoyinsu ba. *_Ummi Shatu_* [7/5, 3:35 PM] Ummi A'isha🏻: *MIJINA SIRRINA...!*🌹 _(Labarin k'auna)_ *_NA_* *_UMMI A'ISHA_* *HASKE WRITERS ASSO.* **True life story** *3* aishaummi.blogspot.com ~~~Note book dinta ta bude tafara kallon zanen skeleton din da yaya kabeer yayi mata, gefe daya kuma kamshin turarenshi ne yake tashi daga cikin littafin, Bin zanen kawai take yi da kallo tana murmushi wanda ita kanta bata san ko na menene ba amma kuma zuciyarta tafi aminta da cewar kawai na tsantsar farin cikine, "I love you yaya kabeer.." Tafadi ahankali tareda lumshe idonta,waleeda ce ta shigo cikin dakin da gudu, "Yaya nadiya kizo inji abba.." Ajiye littafin tayi ta dauki hijabinta ta fita saboda al'adar abbansu ce haka duk lokacin da ya dawo daga office ko kasuwa to tattara yaranshi yake yi a falonsa suyi hira masu wasa suyi wasansu yana zaune yana kallonsu masu karatu kuma suyi har lokacin sallar magrib yayi a lokacin ne kowa zai dauro alwala yajasu jam'i, haka sallar isha ma, wannan dalilin ne yasa su nadiya basa fita ko ina idan ba makarantar islamiyya ko boko ba sannan hakan ya haifar da shakuwa mai karfi a tsakaninsu dashi, Ahankali ta tura kofar falon abbansu ta shiga, kishingide ta sameshi yana kallon labaran yamma a tashar AIT, can gefe daya kuma Amira ce da amir suke rubuce rubuce ajikin littafinsu na makaranta da alama home work suke yi, sai husna da walida daketa aikin mammatsa game wanda duk karar game din ta cika cikin falon, "Sannu da hutawa abba.." Nadiya tafada tana kokarin zama kusa da abban nasu, "Yawwa nadiya, kabirun har ya tafi ne?" "Ehh abba ya tafi yanzu bai jima da tafiya ba.." Shiru abban yayi ya maida hankalinsa ga kallon labaran da yake yi, ita kuma nadiya wurinsu Amira taje tasa ido tana ganin yanda suke yin home work din har mama ta shigo ta iskesu. K'arfe 9 nadare bayan su nadiya sun kammala cin abincin dare mama tace suje su kwanta domin har waleeda da husna sunyi bacci su amir ne kawai idonsu biyu, D'aukar husna nadiya tayi zuwa dakinsu ta kwantar da ita akan katifarsu sannan ta sake zuwa ta dauki waleeda taje ta kwantar da ita su Amira suna biye da ita, gyarawa amir wurin kwanciyarsa tayi ya kwanta sannan itada Amira suka haye gadon dake cikin dakin suka kwanta, Wayar mama dake ajiye a karkashin pillow dinta ta zaro ta yiwa yaya kabeer plashing, kusan kullum haka suke raba dare suna hira a wayar mama amma ita maman sam bata taba sani ba ita dai kawai tasan nadiya bata taba barin wayarta ta huta mutukar tana gida sai dai idan makaranta ta tafi to lokacin ne wayarta zata samu lafiya. Ko minti biyu da yi masa plashing din bata yiba ya kirata,da murmushi akan fuskarta ta daga wayar, "Yaya kabeer kaje gida lafiya?" "Lafiya lau nadiya, yasu mama?" "Suna nan lafiya" "Ya kunya?" Dariya tasa saboda jin abinda ya fada, "Yaya kabeer kenan kaima ai ya kamata ka rinka jin kunyata.." "Saboda me?.. " "Saboda na cancanci hakan.." Murmushi ya saki kafin ya bata amsa, "See you, idan a wayane kibi ki isheni da surutu amma idan nazo sai kiyi shiru ki kasa magana kamar wanda zan kamaki" Itama dariyar tayi, "to ba kaine ba" "Nine me?" "Kaine idan naganka sai naji nakasa yin maganar.." Dariya ya sake yi, "nadiya kenan.." "Meya faru yaya kabeeru?" Murmushi yayi saboda jin ta kirashi da kabeeru, "Kin ganki ko? Bakinki ya iya fadin kabeeru sake fada naji" "Yaya KB.." Dariya suka yi dukkaninsu musamman ma shi kabeer din wanda yake cike da nishadi cikin wannan dare, "Yaushe zaka zo? Zaka zo gobe?" "Yaushe kike son kara ganina? Duk lokacin da kike son sake ganina zanzo.." "Koda kuwa yanzu ne?" Ta tambayeshi tana murmushi, "Yes even now i shall come if you wish..." "To ina jiranka idan har dagaske kake zaka zo din" "Dagaske kike kina son ganina yanzun..?" "Kaji yaya kabeer da dawasa nake? Dagaske nake mana" K'arar bude kofa ta jiyo hakan yasata saurin dakatar dashi, "Ina zaka zo da tsohon daren nan?" "Sabon dare dai ba tsohon dareba,wurinki zanzo ki ganni" "To yi zamanka na hakura da wasa nake yi.." "Inama kiyi dagaske kigani idan zanzo ko bazan zoba" "Yaya kabeer kenan ai nasan zaka zo" Murmushi yayi, "to yaushe zan kawo miki budurwata ne ku gaisa?" Jin abinda yafada yasata mikewa da sauri bayan zuciyarta ta harba, nan taji wani shiru ya ziyarci cikin kunnenta duhu ya mamaye ganinta yayinda bacin rai ya lullube zuciyarta gaba daya. *_Ummi Shatu_[7/8, 6:42 AM] Humaira Khaleel: *MIJINA SIRRINA...!*🌹 _(Labarin k'auna)_ *_NA_* *_UMMI A'ISHA_* ® *HASKE WRITERS ASSO.* *_4_* aishaummi.blogspot.com ~~~Hannu tasa ta danne zuciyarta gudun kada ta faso ta fito waje, "Nadiya... Yanaji kinyi shiru ko bazaki gaisa da budurwar tawaba?" Ajiyar zuciya ta ajiye ahankali, dakyar ta iya sassaita tunaninta tayi magana ahankali, "Yaya kabeer me zai hana ingaisa da ita idan har ka kawo min ita?" Dan murmushi yayi mai kayatarwa kamar yana gabanta tana kallonshi, "Ina fata dai har zuciyarki kika fada ma'ana da zuciya daya.." "Yaya kabeer kenan.." "Nadiya kenan, nadiya yanmata" Murmushin dole tayi kafin tayi magana, "Yaya kabeer nafara jin bacci gashi kaga gobe zanje school" "Nadiya nifa da wasa nake yimiki banida wata budurwa so karki dauka dagaske ne.." Duk da cewar taji dadin maganarshi amma sai ta basar, "Kaji yaya kabeer da wani zance, to idanma dagaske ne ni ba abin in tayaka murna bane?? Sanyayyen murmushi ya saki, "Hakane to balle ma ba dagaske bane da wasane" Itama murmushin jin dadi da farin ciki tayi, "Shikenan tunda kaji tsoro ka sauya magana.." Yar dariya yayi wadda har tana iya jiyo sautinta, "Nayarda naji tsoron..." Juyi nadiya tayi taja bargo ta dan rufe rabin jikinta, "Yaya kabeer zan barka haka yanzu saboda kasan gobe zan je makaranta" "To ya nadiya babu komai, Allah ya kaimu goben sai kin jini" yafada cikeda tsokana, "Ok tom bye bye" tabashi amsa bayan ta lumshe idanuwanta, katse wayar tayi lokacin da taji yace "bye bye good night and have a nice sweet dream" Addu'ar kwanciya bacci tayi ta shafe jikinta, da tunanin kabeer bacci yayi awon gaba da ita. Washe gari da misalin karfe biyu nadiya ta dawo daga makaranta dama ba makarantarsu daya dasu amir ba su akusa da gida suke ita kuma nadiya makarantarsu da dan tazara da unguwarsu, a gaggauce ta shiga gida tana shiga tasan cewar yaya kabeer yana gidan saboda taji kamshin turarensa sannan ta hango takalmanshi a kofar falon mama dan haka bata bari kowa yaji dawowarta ba ta wuce dakinsu ta ajiye school bag dinta ta fito ta shiga kitchen, Abinci ta zuba ta zauna tana ci kamar ance kalli window tana kallon wurin tayi ido biyu dashi tsaye yana kallonta yana yi mata murmushi, Sunkuyar da kanta tayi tadaina cin abincin, murmushi kabeer yayi ya saki karfen dake jikin window din, "Kici abincinki dama kawai nazo ganinki ne, bari natafi inyaso sai nadawo da yamma lokacin kin gama laumar.." Bai jira abinda zatace ba ya juya yawuce, murmushi tayi ta tashi ta leka sai da ta tabbatar da cewar yatafi baya gidan sannan ta koma ta dauki abincinta ta nufi dakin mama tana tafe tana cin abincin, A falo tasamu mama tana shirya husna da alama wanka tayi mata, "A'a kekuma yaushe kika shigo? Jibeki kina tafiya kina cin abinci, keda zaki yiwa wani fada amma kece meyi" Zama nadiya tayi saboda mama kamar yayarta take sam batayi kamada mahaifiyarta ba kai idanma ba sani kayiba zaka zaci ya da kanwa ne domin kamar yadda abba yake jansu ajiki haka itama maman ke jansu ajikinta musamman ma nadiya domin kowanne abune yake damunta to ita take fadawa sannan idan shawarane ma da ita take yi, "Hajiya mama kenan wallahi wata yunwa na debo kuma ina zuwa sai na iske yaya kabeer agidan shine nagudu kitchen na buya acan nazuba abincin nafara ci, yanzu kuma da ya tafi shine nadawo nan dan kisan nadawo.." Tsayawa da shafa man da take yiwa husna mama tayi tana kallon nadiya, "Nadiya wai menene tsakaninki da kabeer ne?" Nadiya jin maganar tayi tazo mata a bazata dan haka tayi shiru tagagara bawa mama amsa wanda har sai da mama ta maimaita mata tambayar sannan tayi gaggawar zakulo amsa ta bawa Maman, "Mama babu komai kawai zumunci muke yi tunda ni yar uwarsa ce shi dan uwanane" "Nasani nadiya, amma bayaga wannan bana son wani abu ya hadaku muddin ba zumunci bane" "Amma mama saboda..." Katseta mama tayi bata barta ta karasa abinda take son tambaya ba, "Ya isa haka bana son tambaya, ki maida hankalinki kawai kici abincin da yake gabanki" Shiru nadiya tayi taja abincin taci gaba da ci tana ta sakar zuci saboda bata san dalilin mama na rashin son wani abu ya hadata da yaya kabeer ba amma Koma dai menene sannu ahankali zata tambayi Maman.... *_Ummi Shatu_* [7/8, 6:42 AM] Humaira Khaleel: ® *HASKE WRITERS ASSO* *MIJINA SIRRINA...!*🌹 _(Labarin K'auna)_ *_NA_* *_UMMI A'ISHA_* *5* aishaummi.blogspot.com ~~~Bata kara bi takan maganar ba suka cigaba da hirarsu ita da maman har ta kammala cin abincin da takeyi ta tashi tabar falon ta koma dakinta tana rikeda wayar mama, lafewa tayi akan gadonta suna yin waya da yaya kabeer, sun dauki lokaci mai tsawo kafin suyi sallama nadiya ta tashi ta shiga wanka ta fito ta shirya tasaka uniform din islamiyyarta domin karfe uku suke tafiya su dawo karfe shida na yamma, Hannen kannenta ta kama suka yiwa mama sallama suka tafi, sai da misalin karfe shida da yan mintuna suka dawo, dawowarsu tayi daidai da zuwan yaya kabeer shi da wani abokinsa, Nadiya bata bari sunga fuskarta ba tafara gaidasu, "Baiwar Allah ya kiketa boye kaine kamar marar gaskiya,kodai bakida gaskiya?" Abokin yaya kabeer din yace da ita, "Kabarta kawai musty domin yar kauye ce" yaya kabeer yafada cikin barkwanci da tsokana, ita dai nadiya shiru tayi musu tana jinsu sai dai ta lura wannan abokin na yaya kabeer wanda aka kira da musty sai faman binta da kallo yake, duk inda ta waiga sai taga yanata kare mata kallo, Ganin haka yasa ta takura ta shige gida yayinda yaya kabeer ya mara mata baya, A soron gidan suka tsaya kowannensu fuskarsa dauke da murmushin kauna, "Yaya kabeer ina ka samo wannan abokin mai shegen kallon tsiya?" Dariya maganarta ta bashi dan haka ya fara darawa yana kallonta, "Wai musty? Abokinane unguwarmu daya sannan tare muka yi karatu dashi" Dan karamin tsaki taja, "Allah na tsani mutum ya tisani agaba yayita kallona" "To yanzu dai nayi laifi tunda har na kawo wanda yayi miki abinda bakya so, ayi min afuwa..." Murmushi tayi, "ni ai ba laifi nace maka kayi minba amma dai wannan abokin naka gaskiya ya fiya kallo da yawa" "To ai nabaki hakuri" "Nahakura" "To zan iya tafiya?" Yace da ita cikin tsokana, "Zaka iya mana yaya kabeer..." "To fara shiga gida nagani" Wucewa tayi tana murmushi ta shige cikin gida sannan shima kabeer din ya juya yafita. Fuskarta dauke da fara'a ta shiga cikin gidan, zaune ta tarar da mama da kannenta tana yimusu shari'a wanda kusan kullum aikin kenan amir da amira kamar zasuga hanjin cikin junansu, "Ke kuma a ina kika tsaya su Amira suka rigaki shigowa?" Mama ta tambayeta idanuwanta akanta, "Mama yaya kabeer ne ya tsayar ni wallahi.." Shiru Maman tayi ta mayar da hankalinta gasu amir taci gaba da yimusu sulhu, yayinda ita kuma nadiya ta ajiye jakar islamiyyarta ta shiga kitchen domin ta jiyo tuwon da mama keyi ya fara kauri alamun ya kama, Itace ta karasa girkin sannan ta fito daidai lokacin abbansu ya dawo nan kuma dukkaninsu suka dunguma zuwa falonsa kamar yadda suka saba. Tunda musty abokin kabeer yaga nadiya yaji ta kwanta masa arai domin yarinya ce mai hankali sannan kuma mai nutsuwa gata da kunya da ganin girman nagaba, gani daya da yayi mata yasashi kamuwa da sonta dan haka batare da ya shawarci abokinsa kabeer ba ya samu mahaifinsa yayi masa maganar nadiya domin shi dagaske yake sonta bada wasa ba sannan son aure yake yimata ba na yaudara ba shiyasa ma yake son mahaifinsa yaje ya tambayo masa aurenta, Aranar da ya sanar da mahaifinsa aranar yaje ya samu baban nadiya daf da lokacin sallar magrib, kasancewar abba mutum ne mai karrama bako sai da ya karrama baban musty sosai ya fito musu da ruwa sukayi salla kamar dama sun san juna sannan baban musty yafadawa abba abinda ke tafe dashi, Shiru abba yayi kafin ya cewa baban musty zai tambayi nadiyan ko tasan musty din inyaso duk yadda sukayi da ita zai kirashi a waya ya fada masa, anan suka yi exchanging din phone numbers dinsu abba ya shiga gida, Lokacin da yashiga falonsa nadiyan ya samu ita da mama suna cin tuwo tare, su kuma yaran an zuba musu taliya suna ci, Sai da abba ya bari sun gama cin abincin sannan yayi gyaran murya yace, "Nadiya zo nan" Kusa dashi ta koma ta zauna, "gani abba" "Bakon da nayi dazu saboda ke yazo.." Ras,ras gaban nadiya ya fadi saboda bata san abinda tayiba, "Abba laifi yace nayi masa?" Murmushi abba yayi, "Ba laifi kikayi masa ba nadiya, yazo nemawa dansa aurenki ne, sunan yaron wai Mustapha abokin kabeeru ne yayanki" Ba karamin faduwa gaban nadiya ya sake yiba, nan fuskar musty ta bayyana acikin zuciyarta lokacin da ya kafeta da ido yana yi mata wannan kallon kurullar.... *_Ummi Shatu_* [7/11, 7:58 AM] Ummi A'isha *MIJINA SIRRINAH...!*🌹 _(Labarin K'auna)_ *_NA_* _*UMMI A'ISHA*_ ® *HASKE WRITERS ASSO.* *6* aishaummi.blogspot.com ~~~Shiru nadiya tayi saboda bazata iya fadawa abba cewar yaya kabeer take so ba, "Nadiya ya naji kinyi shiru ne?" Muryar abba ta dawo da ita cikin hayyacinta, "Abba babu komai.." "To Mustapha dai ya turo mahaifinsa tunda babu wata matsala zan sanar dasu inyaso yafara zuwa har kusamu ku daidaita" "To abba" ta fada kanta akasa, ita dai mama tana zaune tana jinsu amma har akayi aka gama batace ko uffan ba, Mikewa nadiya tayi ta fita zuwa dakinta gaba daya tama rasa abinda yake yimata dadi acikin zuciyarta, gashi bata son fadawa yaya kabeer domin gudun sakashi cikin damuwa,please call me ta tura masa nan take ya kirata, "Yaya kabeer yau ban ganka ba" "Nidinma yau ban samu ganin fuskar gimbiya nadiya ba amma nasan dalili.." "Wanne daliline?" Ta tambayeshi cikin dokin jin abinda zai fada, "Yau naje unguwa ne sai dazunnan nadawo shiyasa ban shigoba, amma gobe sammako zan dako da sassafe inyi karin kumallo da kyakkyawar fuskarki" Dariya abinda yafada ya bata dan haka tafara dariya, "Kaji yaya kabeer da abin dariya sai kace wani abinci da zakace zakayi karin kumallo da fuskata" "Ni ai kinfi abinci, da ace za a ajiye min ke inyita kallonki to da na tabbata bazanji yunwa ba.." Wata dariyar ta sake yi har tana kokarin fadowa daga kan gadonta, "Yaya kabeer zaka sa cikina ya fashe dan dariya gashi dama naci tuwo na koshi dayawa.." "Wai wai, wai, overfeeding kikayi ai? Oya tashi ki fara exercise ina jiyoki daga nan" Tashi tayi tana dan murmushi, "Allah yaya KB jina nakeyi nagaji nidai ban son exercise dinnan.." "To yi tsalle guda goma ina kirga miki, oya fara" Tsalle tafara tanayi yana kirga mata har sai da tayi guda ishirin sannan

Chapter 1 of 20