Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
Cikin lallashi yace autan Ummi zo nan ki gayamin waya tabaki Cikin kukan ta fada kan girjin shi Sai da yayi wani irin ajiyar hrt Cikin kukan Tace ya Ahmad tunda ka dawo baka kula ni ba Ka tabbayi kowa ni baka tabba yeni ba A hankali ya ronqofo kan kunneta Cikin Rada Yace ai Ke Aysha matuqar INA Raye a duniya toh INA tare dake ba sai Na tabbayi woni ba Amman kuma A yanxu lkci ya qarato mana Rabuwar Na gaba towa Da sauri ta daqo Cikin mmk ta zuba mai ido Cikin alamun eh gsky nake fada miki Yace gatar da nakeso ki min bayan rabuwar itace addu,a Cikin sanyi ya kuma kalli Yusuf yace biyaye Haka mukayi da kai Meyasa ka kasa cika min burina Meyasa kake yiwa Aysha tsawa har yau baka bar hantararta ba Cikin sanyin jiki yace Ahmad yanxu wannan ba shine matsala ta ba Ni kuwa itace matsalata Hannushi ya riqo Cikin kula ya kalli Abba yace Abba meyasa kuka dawo? bayan jikin Ahmad har yanxu na ciwo? Cikin nitsuwa Abban yace Yusuf Ahmad dinne ya matsa da Sai mun dawo Gida Toh a satinnan zamu koma ya fada yana mai kallon Ahmad din Kai ya geda mai Cikin cewa toh Allah ya kaimu lkcin Amin suka amsa baki dayansu Baba bello ne ya miqe gami da cewa toh duk Ku fito mu tafi masallacin maqqariba tayi A hankali Cikin hikima Ahmad ya rinqa qoqarin tashi Amman INA abin yaki Cikin sauri Adam ya kamo shi ya miqar dashi Fuskar Yusuf ko fal tsoro ya kalleshi Cikin tabbaya yace bakama iya tashi da kanka ne biyaye Sai in an dagaka?. Dry yayi wace tafi wuta ciwo a ranshi yace a ni kam INA tashi wlh kai matsalar ka kenan Sa ido Kai ya jinjina Dan gani quru quru Ahmad ke nunawa shi lfyarsa lau Daki Nenne suka shiga Cikin davara ya kalli Yusuf yace kai turomin maryama kaima jekayi taka al walar A a muje dai in samaka ruwan Kai ya Dan juya yace nave zan iya Malam turomin matata ita nakeson gani kafa San INA hannu kusan wata 3 fa ban jitaba bata jiniba gwara kai taka matar tana katararka Kallon shi yayi a gyatsine yace toh Ayu uwar jaraba bari Na turoma ita ni ban nemi dogon zanceba ka dai tuna a dakin Nenne kake . Eh ai nasani anan din nakeso Na sama mata jika da zai zame mata madadina kai Kuma ka samu abin gani a matsayina Cikin mmk irin mgn ganun Ahmad Yusuf din ya juyo yana kallonshi Ya bude baki Zaiyi mgn kenan Maryam ta shigo Cikin farin ciki Ahmad din yace yauwa maryama tawa zo nan zo yayanki yaji dumin jikinki Cikin qaunar mijin nata ta fada qirjinshi Hannu bibbiyu yasa ya ruggu mota yana sauqe numfashi Ita kam Maryam tama manta da wani Hamma Yusuf a wurin Shiyasa Cikin shogoba ta maqalo wuyanshi gami da furta mai I miss u so much my dear broz Cikin tau saya musu yace Allah ko? ehh mana ta fadi gamida narkewa a jikin shi Cikin Dan murmushi yace toh daqo daqo kanki ki gani ...... Yusuf kam dake tsaye yana kallon su ganin halin da Ahmad din ke ciki😳 yasa shi fita Cikin sauri har yana qoqarin faruwa.... Kuyi haquri masu karatu INA jin qorafe qirafenku kan batun Ahmad Dan Allah kukam kiyi haquri kawai Ku biyoni a hankali zakuga Yadda abin yake By garkuwan Fulani [4/9, 2:25 PM] β€ͺ+234 909 785 3276‬: πŸ“πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡ NAYI NADAMA πŸ‘‡πŸ»πŸ‘‡πŸ»πŸ‘‡πŸ» MI WASMITI. page 6⃣4⃣to6⃣5⃣ Na Aysha Ali Garkuwa πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡ Ganin da sauri Ahmad ya hada bakinshi da Na Maryam yana mata wani irin kidi memmen kiss Yasa Yusuf ficewa Da sauri A ranshi yake cewa kome su Ahmad sukeji a jikin yara qanan nan ne Oho musu A daki kuwa tabbas Ahmad yayi missing din maryama haka Kuma ya nuna mata hakan a aikace Sosai yake ta kissing dinta tako ina Itama biye mai tayi Gaba daya sun mance da cewa a dakin Nenne suke Cikin buqa tuwa Ahmad yaja hannuta suka fada kan gadon Wasa yakeyi da iya son ransa Cikin zaquwa ya fara qoqarin zuge zip dinta Da sauri tace ya Ahmad a dakin Nenne fa Na Sani maryama Na San a inda nake Kiyi haquri yau kawai daga yanxu fashike nan Gaba daya ya birkice mata ala dole ya samu ya biya buqatar Sa Bayan komai ya lafa ne ya daddafe ya shiga toilet wonkan tsarki yayi yayi yishi Kuma suffatul kamal so hade da alwalarsa ya fito Tin da ya watsa ruwan a jikin shi yaji woni irin sanyi ya ziyarceshi gaba daya jikin shi Kuma yaji kamar an rufe shi da danyen fata A take jikin shi ya fara rawan sanyi Yana fita rigarsa ya dauka yana zurawa a jikin shi gaba daya jikin shi rawa yakeyi A Dan firgice Maryam ta matsoshi tana fadin ya Ahmad sanyi kake jine ? ko zazzabi ne ke damunka? Kai ya rinqa juyawa Cikin cijewar voice yace shim fidamin darduma Zanyi sallah a gida bazan i iya iya iya zuwa masallacin ba gaba daya muryar shi Sai fizga takeyi Da sauri ta shimfi da mai Yana tada kabbara Cikin ikon rabbi duk ya nemi sanyin ya rasa Ganin ya daina rawar yasa itama tafada toilet din tayi nata wonka Shi Kuma Ahmad yana idar da sallan gaba daya Yaji jikin shi ya sake A hankali ya rinqa jin suqar zuciyarsa Na tsananta Lkci daya zazzabi mai qarfin ya rufe shi ga tari Yana Cikin haka Maryam ta fito Da sauri ta nufi gunshi Dai 2 lkcin da ta isa a dai dai lkcin ya fara wani irin amai jinine yake amayarwa guda guda 😳😩😭😱 da qarfin ta riqoshi Cikin ki dimewa ta rinqa kiran shi ya Ahmad ka tashi tashi mu tafi asibitin Nenne Nenne kuzo wayyo Allah Na ya Ahmad Gaba daya ta rude Cikin tsoron Taji yana kiranta da qarfin Cikin fizgar mgn Yace Maryama je ki kiramin Nenne Na da Yusuf da Adam kiyi sauri kice Abba Na da baba bello su zo Cikin tsoron da kidima tafita a guje babban parlon ta nufa Gaba daya suna zaune shi gowarsu kenan Tana zuwa hannu Abba taje ta kamo Cikin Kasa mgn Sai nuna mai hanyar dakin Nenne take Cikin firgita Yusuf yace Maryam INA biyaye Na Ba mgn Sai komawa tayi ta kamo hannu Yusuf din tana ja Da qer tasamu ta iya bude baki tace Hamma Yusuf Ya Ahmad zai zai Bai tsaya ya qarisa jin zancen ta ba ya nufi dakin a guje Gaba daya suma suka rufa mai baya Yana shiga ya hanqoshi konce Cikin galabaita Yana ganin Yusuf din ya miqa mai hannushi yana mgn da qar yace biyaye Na zo zo gareni zo inji dumin jikinka Na qarshe Da sauri ya qarisa gunshi tallaboshi yayi ya ruqqumeshi a girjinshi Cikin kidima yace Baba bello mu tafi hospital Ya yunquro zai tashi dashi Kenan Yayi mgn da Dan qarfin yace biyaye barni barni a gida barni Na cika a dakin mahaifiyata a gaban idanta Hannu ya miqawa Adam Wanda tuni yaketa sharar qollah😭 Riqe hannun juna sukayi Cikin tsananin firgita Shi Kuma Yusuf ruqqumeshi yayi da qarfin kamar mai tsoron kar a kwaceshi kai kawai yake juyawa yana A a a a ba inda zaka Tafi biyaye muna tare Aysha ko riqe da hannushi daya Sai kuka take kamar ranta zai fita Cikin qarfin hali yace Abba Ku gafarceni ya kuma kallon Nenne da ta fara zama mai daqushewar tunani yace Nenne da sauri ta matsoshi Yace shin ba INA gaya miki cewar Allah da ya bakini ya fiki sona ba Nenne ya nake ga alamar kareya a idonki da qarfin ta riqo hannushi tace Na yarda Ahmad Na San Wanda ya bani kai ya fini sonka . Toh Nenne inko hakane addu,arku kawai nakeso Dan Allah kar ki bin da kuka Ina ita kam a NEnne tuni ta fashe da kuka A hankali ya juya kanshi gun baba belle mahaifinshi kenan Cikin murmushin qarfin hali yace Baba Na zan tafi Na barka Ga Nenne Na ka kulanmin da ita hannushi ya kuma riwewa Baba ka gafarceni idan Na taba yima wani laifin Cikin qarfin hali baba belli ya daga kanshi yace Ahmad baka min komai ba Kuma koda kamin Na yafe maka duniya da lahira Ahmad Allah ya bada Sa,an tafiya Cikin sanyi yakira Abba Abba Na kuka kake min ? Ya tabba yeshi Kai Abban ya jinjina Cikin kuka tsosai yace a a Ahmad kaina nake yiwa kuka Ahmad kaina nake kokawa Da qer ya daga hannushi ya goge qollah😭 da ke bin fuskar Abban yanan murmushi Cikin sanyi yace Abba Dan Allah INA da tabbayoyin da zan muku A yau dinnan Ku daure Ku bani amsar su Kai ya geda yace INA jinka Ahmad tabba yeni matuqar Na sani to zan gaya maka Cikin gajiyar hrt yace Abba meyasa kuka hanani Auren Aysha? Meyasa kukace Aure ya haramta a tsakanin mu? Abba meyasa kuka hadata da Yusuf bayan shi uwa daya uba daya suke da ita ? Kuma yaushe aka daura Auren Aysha da Yusuf? A hankali ya kamo hannushi yace wadannan sune tabbayo yin ka ? Ehh Abba Cikin sanyi yace toh Ahmad zan amsa makasu kamar yadda ka buqata Da forko dai Aysha yatace amman ba ta cikina ba cikin gsky da gsky ya nuna Dr Umar Ardo yace wannan shine mahaifin Aysha ma haifiyarta Kuma itace qanwata khadeeja wacce ta rasu Da sauri Adam yace Abba me kake cewa? Eh abinda dai kaji Na fada ya bashi amsa Cikin dimuwa yace kenan Aysha qanwa tace uwa daya uba daya Ehh sosai ma kuwa Nan ya fara basu amsoshin tabba yartasu Kamar yadda kuka Sani khadeeja qanwa tace uwa daya uba daya dama a cikin mu mu 6 ne maza 4 mata 2 a gurin maHaifi yarmu mu 3 ne bello Sai ni Aliyu Sai Khadija Itama inna yayan ta 3 Maza 2mace 1Ahmadu takwaran Ahmad kenan Sai hamisu Sai Aysha Khadija qanwata ita aka fara aurawa abokina Dr Umar Ardo bayan sunyi Aure Allah ya azur tasu da namiji shine Adam Sai hydar kamar yadda kuka Sani ana tare kuka girma da Adam Daga kan hydar bata Kuma aihuwa ba kamar yadda kuka Sani khadeeja Na matuqar qaunar Yusuf a ranta shiyasa tayi alqawari duk ran da ta haifi ya mace to matar Yusuf CE ta bashi duniya da lahira Ku Kuma bayan kunngama primary school dinki Sai aka sama muku makaran ta a bauchi Inda kukaje kun Sani sai hutu ke dawo daku hutun ma Sai shekara shekara Kuna js 1 khadeeja ta samu Cikin Aysha Cikin ikon rabbi ta goya cikinta lfy ta aihu lfy Tana aihuwa ta kira mahaifinmu tace ta aihu Kuma ta samu ya mace tace Kuma yarinyar yar nan matar Yusuf CE Na bashi duniya da lahira Bayan awa daya da ahuwar jini ya yanke mata a take kafin minti 30 tace ga garinku A haka mukayi kuka muka haqura bayan wata biyu aka aurawa Dr Umar Ardo goggonku Aysha tana zuwa da shekara data ta haifi Maryam Inda itama Kuma tace ta bawa Ahmad ita amatsa yin mata Dama a lkcin Kuma da aka haifi Aysha Nenne Ku ta aihu yaro ba rai tsaka ninsu sati 3 Shiyasa Sai ta karbi Aysha ta shayar da ita kaji dalilin da Aure ya haramta tsaka Ninka da Aysha kunsha nono daya mahaifiyar kace ta Sha yar da ita har tsawon shekara daya da woya 6 kafin ta yayeta Batun daura Auren Aysha da Yusuf Kuma a lkcin kuna India a inda kuke hada digri dinki Na forko A lkcin Aysha Nada shekara 13 Bappa Yaya yayi woni irin ciwon da ya firgita mu Gaba data muka karaya to a nanne yake cemana batun daurin Auren Aysha da Yusuf a lkcin yasa aka daura Auren a tunanin Sa kar ya mutum bai hada Auren ba mu zo muqi cikawa khadeeja wasiyar da ta bashi Tarin da ya sarqafe Ahmad ne ya tsaida Abba daga lbrin da yake basu Da sauri Yusuf ya talla boshi Cikin azaba ga aman jini da yaketa kwarawa Murya Na rawa yace Yusuf kaji ko kaji abin da nake gaya maka Na tabbata Su Abba bazasu hada haram taccen aureba Cikin sanyi da daukewar numfashi ga wani zufa da yake ta keti mai Yadamqo hannu Aysha ya kamo Na Yusuf ya hada su wuri daya ya tura hannu Aysha Cikin Na Yusuf din da qer Cikin wahala da fixgar numfashi yace... .. Gaisuwata gareki Hajiya Ramatu Allah ya jiqan mahaifinku da rahamaπŸ‘πŸ» By garkuwan Fulani [4/9, 2:25 PM] β€ͺ+234 909 785 3276‬: πŸ“πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡ NAYI NADAMA πŸ‘‡πŸ»πŸ‘‡πŸ»πŸ‘‡πŸ» MI,WASMITI page 6⃣6⃣to7⃣0⃣ Na Aysha Ali Garkuwa πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡ Cikin carkewar murya yace Biyaye Ga amanar da zan bar maka. Sai kuma tari ya Dan carkeshi Hannushi Yusuf ya riqe da qarfi ya kai kan qirjinshi .. Tarin yayi sosai kafin ya da lfa gaba daya jikin shi ya sake idansa duk sun fiffito kan goshinshi Sai zufa ke tsatsafo a take fuskarsa ta dauki sheqi da qelli A wahalce yaci Gba da cewa Ban saniba Yusuf ko zaka iya karbar amanata ?ban saniba ko zaka iya riqemin amanar tawa ? Ban saniba ko zaka iya Sa farin ciki a rayuwar Aysha ? Yusuf kam tamkar icce ya zama a wurin ya kasa koda qifta idan shi Sai zuciyarshi dake bugawa Da qollah😭 da ke bin fuskarsa A hankali ya daqo hannushi ya shere hawayen dake bin fuskar Yusuf din ya kamo hannu Aysha ya jawota kanta ya daura dai2 kan qahon zuciyarshi Cikin rawan murya yace Aysha kiji bugun zuciyata da zanyi Na qarshe a duniya Ki ji lkcin da sonki a matsayin matar Aure zai bar jikina kiji lkcin da numfashi zai rabu da gangar jikina A yau zaki gsknta cewar kece bugun zuciyata Kanta ta daura kan qirjinshi ta Saki kuka mai ban tausayi Tana ya Ahmad bazaka mutuba numfashi ka bazai bar gaggar jikin ka ba Toh ya zanyi dole zan tafi Na barku Hannushi ya daqo ya kalli inda Maryam ke Durkushe Sai Kuka take jikinta duk bari yakeyi Cikin qarfin hali da kawaici da haquri da jarumta irin Na Ahmad Ya miqa mata hannu Cikin sautin qarfamata zuciya yace Maryama zo Maryama zo Maryama zo masoyi yata cikin kuka ta tsura mai ido tana kallon yadda yake fizgo numfashi Amman wai a hakan yake qoqarin sata farinciki Hannu ta Sa ta kamo nasa Cikin sakin wani irin numfashi ya jawota ya daura kanta kan daya gefen qirjinshi A hankali yace Maryama tawa kin zamani Na zamake Komai zanyi in babuke bazan ji dadiba Maryama kontar da kanki a jikina inji dumin jikinki Na qarshe Maryama matso gareni ki ga fitar raina a take Sai ga wani irin tari mai qarfin ya turkeshi numfashin ya fara fizqa in ya shaqa baya fitarwa da qarfin yasa hannu daya ya qara damqe hannu Yusuf da Aysha da ya hada wuri daya Ya Sa daya hannu Kuma ya damqi hannu Adam Wanda tuni yake kuka kamar mace Kuka 😭😭😭😭😱sosai Maryam da Aysha keyi Nenne ko miqewa tayi Cikin dimuwa kamar wacce hankali ya bar jikinta zata fita Da qarfin Cikin tarin yace Nenne kiyi haquri zaki rabu dani Nenne ki kalli Rabi,u a madadina Baba bello ne ya matsoshi Cikin qarfin hali da jarumta irin ta maza Sai kai yake juyawa yana cije lebe Yace Ahmad Na yafema duniya da lahira ubangiji ya maka raya Allah ya sadaka da Mala ikun rahama Ahmadu Cikin cijewar voice ya rinqa maimaita mai LA ila haillah muhammadura sulillah s a w Cikin sanyi ya karbi Kalmar shahadar da maifinshi ke mai Abba da yake ruqqume dashi kanshi a kan cinyarsa Da qarfin ya ruqqumeshi gami da rumtse idanshi Yana fadin innalillahi wa ibailaihi raji um A hankali Yusuf yaji hannun Ahmad ya saki nashi Cikin zaro ido ya kalli fuskar Ido Cikin ido Sukayi Murmushi Ahmad din yayi Cikin sanyi yace Biyaye ga amanar Aysha Sai kuma ya daura da Kalmar Shahada Idanshi suka koma suka kafe murmushin da yayi yana kan fuskarsa Dr Umar ardo ne ya rinqa mai mata kullu nafsin za ikatul maut Nenne dake gefe cikin gigita tace shike nan Ahmad kaima kabi yan uwanka Ahmad Na rabu da kai Sai kuma ta saki wani irin kuka mai ban tausayi Gaba daya dakin ya rude Hatta Abba kuka yake sosai ringume da gawar Ahmad din Adam kam Tuni ya fada kan Yusuf Cikin riqe hannushi Yana Shike nan Yusuf Ahmad ya tafi ya barmu Yusuf mun rasa Ahmad Sh kenan yanxu dagani Sai kai Yusuf Ahmad ya tafi ya barmu Maryam kam da Aysha qaqqame qawar sukayi Cikin firgici da rudani Suke kuka kamar ransu zai fita Baba bello ne da Dr Umar ardo sune suka samu Dan qarfin jikin miqewa baba bello kam Nenne ya kamo ya ruggume Cikin rawar murya yace haba ruqayyatu kar kibi Ahmad da kuka mana shin baki ga Rahamar da Allah ya mishi ba cikawafa yayi da kalmar shahada Allah sarki Nenne Sai fafawa tayi jikin mijinta ta rinqa kuka mai ban tausayi Cikin kuka Abubakar ya riqo hannu marya da Aysha da nufin ya jasu su fita Da qarfin Maryam ta fada qirjin shi Cikin n kuka tace ya Abubakar da gaske ya Ahmad ya rasu Na rasa ya Ahmad Kai ya rinqa juya mata yana zubda qollah😭ya jata suka fita Ummi CE ta matso Cikin kuka tasa hannu ta rufe mai idanshi Su Usman da Rabi,u kam da abdul dama tuni suka koma parlon kuka suke kamar yara Ummi CE ta miqe gami da kamo hannu Aysha da nufi su fita Tana janta Sai gani tayi tayi yuu Sai fadawa kan Yusuf tayi a sume cikin firgita Ummi ta rinqa kiranta tana jijjiga ta Amman ina Goggo Aysha CE tayi tunanin debo ruwan ana Dan shafa mata a fuska Amman INA ko matsi bata yiba 😱😫dimuwa. Da firgici da tsoro mai matuqar tsananin su suka sauqa kan rayuwar Yusuf inda ya zama tamkar mai Ciwon mantuwa Lallai kuka ma Rahama ne Shi kam Yusuf yau yake buqatar kuka a rayuwarsa Kuma a yau kuka ya mai tsada Zuciyarshi ta kasa tuno komai qoqol warsa Kuma gaba daya ta tsaya bata aiki kanshi da jikin shi duk jinsu a juye sukeπŸ™ƒ Ido kawai Yusuf ke binsu dashi Sai hannushi da yasa ya damqi hannu Ahmad din Su Ummi yake klo Cikin zare idon fuskar Aysha yabi da idonshi Cikin yanayin rashin sanin abin da akeyi Hydar ne ya zo ya ciccibi Aysha yayi dakin Ummi da ita kamar gawa Yusuf kam yana zaune a gun riqe da hannun gawar Dr Umar ya ja Abba ska fita tare Fuskar Ahmad din ya zubawa ido Sai ya juya ya kalli Adam dake durqushe a gefen shi yana ta kuka A haka har zuwa tsawon wani lkci Allahu Akbar Lbrin rasuwar Ahmad Ta kasance tam kar sauqan aradune a zuqatan yan uwa da abokan arziqi Lbrin ya zama tamkar sauqan qanqarane ne a jikin mutane Kafin wani lkci gida ya cika tab da yan uwa da maqota da abokansu Baba Ahmadu ne da Dr Umar Suka shigo Daukar gawar Dan Aje ayiwa gawar wonka ayi mata sutura a kaita makoncin ta Cikin tsoro baba Ahmadu ya daqo yana kallon yadda dr Umar ke ta yin qoqarin cire hannu Ahmad Cikin Na Yusuf Amman ....... Allah sarki rayuwa Dan Adam Dan mutuwa nima kaina Aysha Ali Garkuwa rasuwar Ahmad ta zame min fami a zuciya ta ta famimin rasuwar yan uwana shiyasa wlh bazan iya ci gaba da typing ba har Sai zuwa gobe 😭😭😭 By garkuwan Fulani [4/9, 2:25 PM] β€ͺ+234 909 785 3276‬: πŸ“πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡ NAYI NADAMA πŸ‘‡πŸ»πŸ‘‡πŸ»πŸ‘‡πŸ» MI,WASMITI page 7⃣1⃣to7⃣3⃣ Na Aysha Ali Garkuwa πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡ Amman gsky Baku kyautamin ba masu karatu ya kamata ace tsakaninmu Marubuta da ma karanta a ringa yiwa juna uzuri Daga jin Ahmad ya rasu Sai wasu suka rinqa qananan maganganu wasu harda kirana a woya Wai meyasa zan kashe Ahmad ai wanna NAYI rashin imani Haba masu karatu kukam kuyi Haquri maNa Ku Biyoni A hankali ai zakuga yadda zan tsara mana abin masu bina ta prvt chart kowa da irin qorafin da yake min Dan Allah mu rinqa yiwa juna uzuri Wasu harda cewa ai gwara akashe Yusuf😫 Ina Baku haquri wasu nace Na sasu kuka sosai karku damu zakuyi dry a gaba fiye da yadda kukayi dry a baya zaku Sha nishadi fiye da zatonku Ku dai Ku hira Yusuf ya shigo hannuπŸ˜πŸ˜˜πŸŒπŸ™ˆπŸ˜ Jan hannu Yusuf din yakeyi yana qoqarin rabewa a na Ahmad din shiku ma Yusuf Sai damage hannu da yayi yana mai zuba musu ido Kamar zaucecce a hankali Dr Umar ya zauna kusa dashi Cikin tausasa zuciyarshi yace Yusuf saki hannu Ahmad Kaji sakeshi a yanxu ba wani gata ko Alfarma da zamuyi mishi sama da mu kaishi Cikin qabarinshi Baiyi mgn ba bai Kuma sakiba Sai zuciyarsa da ta rinqa bugawa da qarfin qarfi Hannu nashi ya jawo ya dawowa kan qawar yasa yatsunshi ya rinqa bude tafin hannu da Yusuf do ya damqe Shi kam Yusuf kallon shi kawai yakeyi So ya yake yaji shi shima a mace ko zaiji wani a bu a ranshi ji yake dama haukacewa yayi A hankali zuciyarsa ta fara tuno mai abinda kalaman baba Umar ke nufi a take Kuma Sai jikin shi ya rinqa karkarwa A haka suka samu suka dauke gawar Cikin kuka Adam yabi bayansu Shi kam Yusuf a wurin ya zauna kamar dasashi akayi Acan Kuma akayiwa gawar duk abin da ya kamata kafin ma gari ya waye anyi komai an gama Washe gari da safe wannan lbrin ya iski Anuty Sadiya Duk da mijinta ta ya ji dashi akayi komai Amman ya rasa ta INA zai fara kawo mata wannan zance Sai da safen yace ta shirya suje gida Su gaidasu A mota ta kalli mijinta Cikin sanyi tace Abban Yumin. Na,am ya amsa mata Cikin sanyi Sai kuma tayi shiru gamida dafe qirjinta Hannushi yasa ya kamo nata yace Kin kirani kin Kuma yi shiru Kai ta daqo ta kalleshi Cikin rawar murya da alamar kuka zatayi Tace Abban Yumin Zuciyata Na tsinkewa tsoro nakeji ban San meyasa ba tun jiya nakejin faduwar gaba A hankali ya jawota ya manna ta a jikin shi cikin fargaba yace ki rinqa addu,a ki Kuma kasance mai yarda da gaddara Dai dai nan yayi parking a farfajiyar gidan nasu A hankali ta zame jikinta ta fito Cikin tsoro da firgita ta bude idanta da kyau ganin gaba daya harabar gidan a cike yake da mutane a take qafarta ta fara rawa Cikin tsoro ta juyo gareshi tana Abban Yumin me ya faru me kake boye min Hannushi ta riqe tana jijji gawa da qarfi tana ka fada min INA Abba ban ganshi anan ba Allah sarki ita Sam bata kai tunanin ta kan qaninta ta rasa ba Rabi,u dake gefe ne yayi saurin isowa gareta durqushe wa yayi a gaban ta Cikin kuka yace Anuty Sadiya ya Ahmad ya tafi ya Ahmad ya tafi ya barmu Ido ta zaro Cikin tsoro Sai kuma tayi Cikin gida kai tsaye dakin Nenne ta nufa Can ta hango Ummi da sauri taje gaban ta ta fada Cikin kuka tace Ummi Me nakeji Ummi meya samu Dan uwana wayyo Allah wayyo Dan uwana wayyo Nenne Na wayyo cikina Ummi shike nan Na rasa Dan uwa Adam ne ya kamo hannuta Cikin kuka yace Anuty Sadiya mun rasa Ahmad Anuty Sadiya Ahmad ya tafi ya barmu Gaba daya suka ruda parlon kakace ta tashi itama Cikin kuka ta kamo hannu Sadiya Da Adam tayi Cikin daki dasu Suna shiga Sadiya ta hango Yusuf Wanda tun jiyan bai tashi a wurin ba sai sallan asuba da ya tashi yayi da taimakon hydar Tana hoggo shi ga Nenne a gefenshi Tana riqe da hannushi tana fadin Haba Yusuf kayi mgn mana Yusuf katashi kaje qun baqin da sukazo yi maka gaisuwa Haba Yusuf fushi kakeyi da yin ubangiji ne Shin ase bazaka rungumi qaddara ba Yusufa mufa musul Maine Shi kam Yusuf ido ya zubawa Anuty Sadiya Ita Kuma gabanshi tazo ta durqusa ta kamo hannushi ta kifa kanta kan cinyarsa ta saki wani kuka mai ban tausayi Tana kuka tana fadin Yusuf ya zamuyi Allah shi yabamu Ahmad Kuma shi ya dauke shi

Chapter 10 of 25