Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
watsa mata saida ta sauke kanta asanyaye takasa ko motsin kirki magana yayi cikeda gadara yace."Kada ki kuskura kije Kotu a haka kuma na haramta maki wannan kwalliyar matsawar zaki fita waje kije ki shareta umurni nike baki ba shawara ba."baijira cewar taba ya fita a fusace, Salma ce ta maye mashi baya suka shiga mota suka tafi saida suka biya ta wajen mahaifiyar su dan ya gaidata a cikin bedroom din ta ya isketa ta gama shiryawa itama cikeda ladabi ya gaida ta, ta amsa a takaice...itako Nazima kamar tayi kuka haka taji ta mirrow ta kalli dressing dinta cikeda Sacin rai tace."Wane hukunci zakai man da ya wuce saki daman shi nike bukatar saime wlh badan a gaban Salma kaiman wannan maganar ba Allah da ban goge kwalliyata..."Sumburar baki tayi ta bude Press dinta ta dako atamfa ta saka blue and pink color sai hijab mai hannun sannan ta fita ganin ta kusan makara. Koda Hajia Zaituna Buhari,tagama waya da aminiyar ta kuma kanwar Na'ima kallan Nizam tayi daka ganshi kaga mai damuwa,gutun tsoki tayi tace"Naji rashin kunyar da kaima yar uwa ta kuma da kanwar ka akan wannan sakaryar yarinyar dai ko?toh bari kaji muddin mukaje Kotu ka nuna ka mutu akan son yarinyar har ka?i sakin ta wlh ranka ne zai mugun Saci! kajini da kyau ni Zaituna Buhari ?a ga Hajia Aisha Maikaba kaf zuriyar Wakin mu bamu da raggo dan haka ni bazan haifi raggo ba dafatan ka fahimta.?" Rasa abin cewa yayi banda gyaWa kai da yayi alamar eh,awani sashen na zuciyar shi yana tunanin sanar da mahaifin shi halin da ake ciki dan baiji zai iya rabuwa da matar shi, dahaka yai mata sallama itama tashi tayi suka shiga mota tashi nagaba suna biye dashi har zuwa katuwar Spreme Court din atare duk sukayi parking daidai nan Nazima da kannen ta suma sunyi parking, atare suka gaida Hajia Zaituna amman ko kallan arziki basu isheta ba,shiko kallan matar tashi yayi yaga tabi umurnin shi kuma yaji daWn hakan saidai yana ganin bata kyauta mashi ba da take neman takardar saki har takawo shi Kotu, a gaban idanun shi Fadila da Hafsat suka ingije Nazima,su Amina ne suka tareta saura kaWan ta faWi buWe baki yayi zaiyi magana aiko Hajia Zaituna ta wurga mashi wani irin matsiyacin kallo,ba shiri ya haWe kalaman shi da haka suka shiga Kotun kowa ya hallara Alkali kawai ake jira,basu jimaba ya shigo kowa ya mike bayan ya zauna kowa ya zauna Court din tayi tsit kamar an mutu Alkali ya maida kallan shi wajen magatakardan Kotu yaba shi izini karanta case din da za'ayi shara akan sa yace...... _________ _Danginmu ne Silar Komai labari ne daya kunshi tarin sadaukarwa ta wasu masoya da_ _sukema junan su sahihin so.Nizamuddeen da Nazima masoya ne da suka fito a cikin wani irin dangi masu yawan son zuciya da zamba cikin aminci dangine da tarin yan ubanci yayi gaba a cikin zuriyar ta_ _Maikaba.ta zabi mijinta ya saketa saboda Dangin su ta zabi ta rabu da duk wani farin ciki da jin dadin rayuwar da suka gina cikin tsantsar so da kaunar juna,ta zabi tabar uban Wanta badan komai ba sai saboda Danginsu!miyasa ta zabi ta rabu da kowa nata duk akan_ _dangin su,wa'anne irin Dangi ne?minene Silar da zaisa ta nemi takardar saki a wajen mijin ta duk da irin son da sukema junan su.zata samu abinda take nema wajen mijinta?Wannan kaWan daga cikin shimfidar Danginmu ne Silar_ _Komai...ko minene Silar?duk wannan amsoshin bazasu samu ba saikin biyoni a cikin wannan labarin mai dinbin darasi da nishadantarwa._ _Yar uwa,garzayo kada ayi babu ke maza ki mallaki naki danjin dadin karatu cikin jin dadi da aminci akan farashi mai rahusa da arha #500 two post in a day.Via acct no 0777512438 Access_ _Bank Jamila Abubakar Bello show ur evidence via 08160508316._ _*Thank you>?p?*_ &&& *Sdeendtm* I'm sell data to all Nigeria network Thank you for contacting Sdeendtm! *BUY DATA FROM THE AFFORDABLE PRICE* *I'm selling MTN data with this cheap price* *MTN DATA PACKAGE* 500MB@===200 1GB@=====300 2GB@=====600 3GB@====900 5GB@====1,500 Dial *131*4# or *460*260# to check Data balance. *Validity 1 month* *Airtel,9mobile and Glo* *also available.* *Subscription for DStv gotv star time electric pay bills* *Whatsapp 08066268951 _____________ _Akwai ingantaccan maganin?(?let's go my fans?p?_ ```Free page ya kusa karewa=? ? hanzarta ki mallaki naki kada a baki labari=??``` ____________ Bayan kowa yayi uzurin gaban shi,aka fara dawowa daga hutun ta?aitaccen lokacin da Alqali ya bada,wannan karon Kotu tayi cikar da ko a karon farko batayi irin shi ba harda kawayen Nazima na makaran ta duk sunzo labari ya karaWe gari sai zancen shari'ar akeyi,shiko Nizam yana zaune a masallaci sai addu'a yakeyi akan Allah ya Waura shi akan wannan shari'ar yanaji a ran shi matuqar ya rabu da Nazima komai zai iya faruwa dashi,wasu irin kwalla masu dumi suka samu damar ziraro mashi kamar wani karamin yaro,abokin sa Zaharadden keta bashi hakuri yana tausasar shi da dadaWan kalamai masu sanyaya zuciya sunjima a haka sannan suka kama hanyar komawa Kotun saboda lokaci ya gabato.Koda ta Nazima shigo Kotun banda aikin kallan ta ba abinda akeyi wasu na gwada anata zinWen ta kamar wata barauniya haka ake gwadata jiki a matukar sanyaye ta zauna duk ta tsargu,tsakanin kannen Nazima da Nizam ji suke kamar su babbakama junan wuta banda kallan tsana ba abinda suke jifan junan su dashi kowane a cikin su ya samu mihallin sa ya zauna danko Hafsat da Fadila wani matsiyacin kaskantaccen kallo suke watsama Nazima saidai ta sunkuyar dakai kamar bata ga abinda suke mata saidai su Amina da Khadija ke ramawa bata taba cewa tsakanin su akwai wata alaqa atsakanin su,Kotu ce tayi shiru Alkali sakamakon shigowar Alqalali bayan kowa ya mike aka gaida shi ya zauna sannan kowa ya zauna sake gyara glass din idon shi yayi ya gyara zaman shi,ya bada izinin cigaba abatar da Shari'a ana fara shari'ar bada jimawa ba sai ga Nizam sun shigo suma,batare da bata lokaci ba Alqali yai gyaran murya yaci gaba da cewa."Kamar yanda muka Wauki hutun takaitaccen lokaci muka dawo,Kotu zataci gaba da gudunar da shari'ar ta akan tsari da doka dan haka Kotu na bukatar ganin lauyan wanda ake ?ara Barister Nafi'u Hassan Nakowa bissimillah."Tashi yayi yace."Ya mai girma mai shari'a zanso wannan Kotu mai dinbin daraja da tabani dama ingana da mai ?ara Hajia Nazima Abdulhamid Maikaba."wani irin bakin ciki ne ya soki zuciyar Nizam take,yana takaicin yaji an kira mashi matar shi a gaban kotu kowa na kallon ta a banza koda yake ita taja komai,dahar ta kawo case Court....itako Nazima tana fitowa ta shiga gun amsa tambaya ta tsaya,a hankali Barrister Nafi'u ya tsaya gaban ta yace."Hajia Nazima zanso ki gayama Kotu cikkaken dalilin dayasa kike son mijinki ya sakeki,bayan i?irarin da kikeyi na kin tsane shi kuma baki son shi,ko kinada wata hujjar bayan wannan ikirarin da kikeyi."?Da sauri Barrister Mukhtar ya mike yace."Objection my lord bai kamata abokin aikina ya dinga tada jijiyoyin wuya ba,dan tace bata son mijinta kuma ta tsane shi wannan kadai ma ai hujja ce,ranka shidade duba da Nazima ba yarinya bace tasan right din kanta ina rokon wannan Kotu mai alfarma zata jama abokin aikina kunne nagode ya mai girma mai shari'a."Alkhali yayi shiru kamar mai nazrin wani anu sannan yace."Korafi bai ?arbu ba Barrister ya zama dole Nazima tafaWa ma Kotu dalilan ta na bukatar saki daga wajen mijinta,dan tace ta tsane shi dole tana da hujja,cigaba da aikin ka Barr Nakowa."cikeda jin dadi yace."Godiya nike my lord,malama Nazima gareki ko kinada wata hujjar da zaki gamsar da Kotu."? A sanyaye ta maida dubanta ga Alqali tace."Ya mai girma mai shari'a ina da dalilin dayasa nike neman saki wajen mijina ko wannan kalmar ta DANGINMU dana ambata shima dalili amma yanzun ya zama dole in faWama Kotu dalilina,kodan samarwa kaina mafita....Kamar yanda kowa yaji dangan takata da Ya Nizam ya kasance mijina kuma mafi so da kauna a gareni amma baya saidai a halin yanzun banjin son mijina a cikin zuciya ta."Numfasawa tayi taci gaba da cewa."tunda Allah yasa Ya Nizam ya taso a cikin family dinmu ya kasan ce mutun ne mai Waukar girma da gabata ga kamun kai,ya kasance mutun ne mai karamci da sanin darajar ?an uwan shi,har Allah yasa muka fahimci junan mu,akai mana aure,bakaramin kulawa yake bani ba,bantaba samun matsala da mijina ba ya tsare mani duk wani hakki da Allah ya daura mashi ya sauke mashi bai rageni da komai ba asalima zan iya cewa ba macen data

Chapter 5 of 14