Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
6 / 7
duk abunda nakeyi, aliya wlh inasonki, dukkan kai nason dukkan ki, “jin abun yadawo sumbatu yasa sufyan yabashi gu, antyn abuja da inna dakuma yanuwa kakkani duk suna zaune ana jira likita yafito yace ansaka mata lafiya nima benaxir ina tsaye agefe inata adduan Allah yasa ayi aiki lafiya Bayan awanni kadan sai gashi likitan yafito sun bazama kanshi kaman zasu cinyeshi, anan yabukaci sufyan yazo nan da nan yusuf yabisu likitan zaiyi magana sufyan yace “badamuwa ana tare” binsa sukayi office suka zauna sannan yafara bayani “anyi aiki lafiya alhamdulilah jikinta kuma yakarba, yanzu bata tashiba don Allah duk wani abu na tashin hankali kar ayi agabanta, sannan inaga kar agayamata wa yabata kidney dinshi yanzu harsai ta warke,” anan sufyan da yusuf suka mishi godiya sannan yamusu bayani akan akwai nurse dazatazo tamusu magana, suka fito ahaka sannan inna tamike tareda tambayan sufyan yace anyi lafiya, dakin abdullahi yanufa don suyi magana anan yace masa ai anyi aiki lafiya anma bata farka ba, yayi murmushi sannan yace “ina rokon alfarmarka” “Na mefa?” “Don Allah kasamu kayiwa yusuf magana da duk wanda yasan maganan nan wanda kasan zai iya fadawa aliya, don Allah kar afada mata nina bata kidney acemata siya akayi, ” “Anma kasan dole tasani ko? Tunda yanzu bakamn da ba, dole kana yawan zuwa asibiti maganan gari baya buya” “Nidai kamin wannan alfarma abari sai bayan raina afada mata, don fada mata yanzu zaisa tafara diddigi banaso tagane cewa nine masoyinta dana guje mata,” “Ba gudu mata kayiba, ita tagudu maka kadena fadan haka” “A a nidai don Allah kar afadawa kowa maganan nan tawuce, karta sani” Dahaka sufyan ya yarda bayan fitowarsa yakira yusuf yamasa bayani anma yaboye masa dalilin dayasa abdullahi yayi haka shidai yusuf yasan cewa abdullahi na son aliya ne inbahakaba bazai taba bada wani fanni na jikinshi yazabi mutuwa akan rayuwa ba, dahaka sufyan yabarshi harzai fita yaci karo wani likita wanda haushinsu yakeji alokacin akan meyasa zasu yadda abdullahi yabada jikinsa, ba gaira a dlili ya makuro likitan tareda tambayansa dalili, likitan yana neman hanyan kwacewa karya mutu don numfashinsa daukewa takeyi, dayaga zai wahala yace “gimbiya falmata ce tahana mu yarda kabayar” ahankali yasake wuyan tareda cewa “mekace?” “Gimbiya falmata ce ta aiko da wasika akan duk wanda yacire wani bangare na jikinka abakin aikinsa” Sakeshi yayi yabar corridor din mota yanufa yayi wani wawan[truncated by WhatsApp] HALACCIN SARAUTA 26  benaxir  October 17, 2015  Hausa Novels  122 Views HALACCIN SARAUTA NA BENAXIR OMAR Ayadda ya isa kofan gate din sukansu dogaran saida suka matsamishi sunga yadda yashigo da motan, abude yabar motan da mukullin ajiki yashige cikin gidan a birkice fannin falmata yanufa a harzuke dogarai dasuke kofan gun suna ganinshi suka matsa masa don ayadda yazo kaman guguwa ne ta tunkudoshi tana zaune a falo rike da waya a kunnenta yashigo fuskarshi a daure bata taba ganinshi haka ba, tuni tasha jinin jikinta ta tabbata angaya masa, ajiye wayan tayi tana kallonsa,cikin hushi da zafin murya yace “inaso kibani hujjanki nashiga rayuwata, kibani hujjanki na takurani,” dakewa tayi duk da ta tsorata “bakayi girman da zaka yanke wani hukunci dakanka ba!, inbanda dolonci irin naka nadan fari tayaya zaka cire wani fannin jikinka a matsayinka na dan sarki, sannan kuma sarki anan gaba kace zaka bawa baiwa?!” Murmushi yayi wanda tafi kuka ciwo yace “yanzu na fahimci inda kika dosa, toh inaso yau kisa aranki bakida da , sarki kuma kike can kinemi wanda zai cika miki burinki, baiwa???? Itace ta nutsar dani, takuma ladabtar dani abunda ke kika gagara yi!” Yana fadan haka yajuya yafice, ji tayi kaman ya watsa mata ruwan zafi, salati tayi tana rike kirjinta, yau dan cikinta shine ke mata gori,haryazo corridor yaga jakadiya yasan ita aka aika tafadi sakon, daya makuro wuyanta wani kara tasaka domin a tsammaninta zata leka lahira ne, dakyar dogarai suka karbeta suma yakoma kansu akarshe rikeshi akayi don abunsan yafara dawo karamin hauka, kuka yakwanta wiwi yanayi a daki tunda tahaifeshi baitaba tur da halayenta irin na ranan ba, yayi wadaran da halin mahaifiyarsa akan meyasa bazata koyi nagari ba don itama nata suzama nagari, Matar abdullahi tafarka jikin nata da dan sauki gashi cikin mai laulayi ne, duk tadamu kishin mijinta yashiga ranta duk da yamata bayanin cewa arashin na mutane ne yabada nasa, toh ita tambayan anan shine yasan guda daya ne yasaura mishi akan meyasa zai bayar? Yana nufin zai mayar da ita karamar bazawara! Lallema duk tabi tadamu jira take yawarke don tasauke masa farillai da mustahabban rashin mutunci,aliya sai sha daya na dare tafarka da salatinta tafarka tuni sufyan ya kirkira su kowa yanufo gun dama abdullahi na asibitin, sai inna, yusuf kuwa yanacan shima bakanshi, bude idonta taga sufyan akanta duk tarame tayi kashin wuya, lebenta ya bushe idonta ya kumbura yayi jaa yariko hannunta yana murzawa idonsa fir akanta, dakyar tadan murmusa sannan tabude baki zatayi magana anma takasa, yace mata tayi shiru kartayi magana Allah yabata lfy. Inna ma sai faman tofa mata addua take taki motsawa daga baya kuma tamike ta dauro alwala tafara sallah tana addua Allah yadaga kafadun aliya, baccine yakara kwasan aliyan sannan yazauna agefe shima ya gyangyada sai asuba dayaji kiran sallah sai ya mike yafita dauro alwala yanufi masallacin asibitin, inna kuma a dakin tayi sallah, aliya sai karfe goma ta farka yusuf shima yashigo anma kana ganinshi kassan yana cikin damuwa,idonsa radau radau ya kumbura, yazauna agefenta itama kallonsa take yariko hannunta jikinsa yayi sanyi lao itakuma zafi kaman wuta, batayi magana ba har lokacin tagagara magana, yusuf kuwa shi dazaa cire zafin yakoma kansa dayafi kowa farin ciki, yazura mata ido alokacin likitan yazo dubata donhaka suka fita bashi wuri. Dawowansu dakin bayan likitan yagama yusuf yazauna agefe. Can dai aliya ta daure sannan tace “wayaban kidney dinshi? HALACCIN SARAUTA 27  benaxir  October 18, 2015  Hausa Novels  126 Views HALACCIN SARAUTA NA BENAXIR OMAR Bai amsa tambayanta ba yace “yajikin naki? karki kara magana” bata kara cewa komi ba, tana tunani ne taga waye yabata, taga yusuf garau donhaka tasan bashi bane, sufyan ma taganshi tasan bashi bane, taga inna taga antyn abuja duk sauran tsofi ne donhaka taciresu a lissafi, saikawai tasa aranta na siyarwa aka saka mata, nan tafara adduan Allah yasaka da alheri wa duk wanda aka samata kidney dinshi, yusuf yaki motsawa agefenta itakuma idonta zur akansa shima hakan jiyake kaman ya hadiyeta, inna ne suka shigo anma duk dahaka yusuf yaki matsawa saidai kowa yagaidata daga nesa, sufyan daya shigo yaganshi yasan meyakeji donhaka yajashi dakyar yace yaje yahuta ganin sufyan yadage yasa yusuf yanufi dakin likitan ranshi abace yatuna da tsohon bacin ransa, likitan yazaro ido don yaji labarin yusuf yasan mesuka aikata donhaka tuni yashirya dazuwansa , zama yayi akan kujera sannan yace masa “inaso infarajin bayani daga farko meyasameni , me kuma kuka shuka da gimbiya kuka min karya!, ” yayi gyran murya sannan yace “yarima duk abinda yafaru kadaukeshi kaddara tun asali dana dubaka kai kanka bakada ishesshen lafiya, abubuwan dakake sha sundan maka lahani kadan, kidney dinka basu da lafiyan dazaka bawa wani, ana cikin haka kuma mahaifiyarka ta isar da sakon karmu cire, dafatan zaka fahimceni” yusuf bai ce komi ba yatashi yanufi kanshi fitsarine likitan baiyi a wando ba domin ya mugun tsorata yusuf yariko kwalan rigansa sannan yace “daga yau duk abunda yashafi aliya, babu wasa aciki inaso kasan dahakan” Juyawa yayi yabar office din dakin da aka kwantar da abdullahi yanufa idonsa biyu yanaso asallameshi anma likitan yace bayanzu ba saiya kara samun sauki donhaka duk asibitin tahau masa kai, Yan biyu ne hassana da hussiena suka shigo kowacce taci kwalliya dakin da abdullahi yake aka nuna masa suka gaysheshi da jiki sannan suka ajiye ledan hannunsu yusuf yafita alokacin, harzasu wuce abdullahi yace kucika ladanku mana ku gayda aliya, hussiena kaman tace a a anma tana kunyan abdullahi donhaka tace masa toh, dakin da aka kwantar da aliya suka nufa, idonta biyu bakowa a dakin sai inna suka gaysheta kamar abun arziki sannan suka nufi gadon aliya hassana tagaidata yayinda hussiena ke mika mata sakon harara, aliya murmushi tayi don tasan dalili, can dai hussiena takalli tareda cewa “anma kinsan yarima yayi asaran kudin tara? Ace wannan zaicire sauran kodan shi kwaya daya yamika mata? Dasunan soyayya? Mayya duk yaran sarkin kin mamaye” inna ce tanufo kansu tareda katseta tanacewa “kuyi hakuri baason daga mata hankali” aliya ce ta katse ta tareda cewa “wani yarima?” Hassana taja tsaki tareda cewa “wanne kuwa abdullahin dakika nakike wa” wani nauyi taji akanta kaman ansauke mata dutse (Kuyi hkr kumin uzuri for today , ciwon ido ya matsoni kar na muku typing shirme lols, and plx masu tambaya ko benazir macece ko namiji letz make it these way , ni Macece, a 20yr old single lady, nd plx masu dropping numbansu a blog dina kudena plz HALACCIN SARAUTA 28  benaxir  October 21, 2015  Hausa Novels  111 Views HALACCIN SARAUTA NA BENAXIR OMAR Fita sukayi adakin suka barta da bugun zuciya har cikin ranta ta tsorata kwanyanta yafara caji, tasan haka kawai mutum bazai cire koda yabayar ba, wani zuciyan tace yanzu haka tsabar zumuncin dake tsakaninku ne, harta bar maganan ahaka saikuma ta tsorata data kara tunawa sunce guda dayan data rage masa yabayar, inna ce tariketa ta kwantar da ita anma aliya ta gagara kwanciya duk ta tsure hankalinta yatashi tuni tamike a tsaye tana cewa “inna nikam ko dai zanfita ne? Ina yaya?” Duk a gigice take hakan yasa inna tarikota tareda cewa “kwanta, barin kira miki yayankin” fita tayi don tanemo sufyan bata ganshi ba donhaka saitayi magana da nurse daya don su samu sudubata a lokacin shigowansu jikin ya rikice aliya duk ta tsorata sosai nurse dinne ta rikota itakuwa duk ta gigice dakyar aka kwantar da ita wani irin kuka take mai shiga zuciya tana kama jikin inna, “inna kitaimaka kinemomin yayana” batasan meye matsalarta na, anma ta tsorata bashiri tafita duk da batada tabbacin ko zataga sufyan din filin asibitin tanufa tazaga bataganshiba donhaka takoma ta dakin abdullahi tanufa ganinshi azaune a rikice tace “yarima ina sufyan? Kataimaka ka nemoshi munshiga uku aliya” agigice yamike yacire kalulan hannunsa sannan yace “muje” dagudu gudu suka nufi dakin alokacin aliya ta bankade nurse din tana cewa akaita gun sufyan, abdullahi ne yakomota yariko hannunta sannan yace “aliya kikalleni” kallonsa tayi agigice tarude anma yadda ya zura mata ido tuni taji wani nutsuwa yashigo mata, ya kwanto mata, hannunta na bari tace “yariiiiiim” “Shhhhh karkiyi magana kiyi shiru” Shirun tayi kaman yadda yace addua yatofa mata sannan yace wa inna insha Allah bazata kara firgita ba, zama yayi dirsham agefenta acewarsa sai sufyan yazo zaitafi, wata nurse ce tashigo tareda rokonsa yakoma daure fuska yayi kaman yaga malaikar mutuwa yana cewa ba inda zanje kuma karta nima takurashi, hakan yasata fita don tasanar da manyanta, inna tayi tayi dashi yamike yafice anma yaki yarda, tuni tafara nadamar kiransa anma abdullahi yakafe, aliya kuwa tana jingine a kwance tana ta tunani, tarasa tayaya zata tambayeshi inkuma yabata da zuciya daya ne fa? Yazatayi? Wani irin nauyinsa takeji yanzu fa duk gadaranta akwai kidney dinshi ajikinta, ita damuwanta sufyan yazo ta tambayeshi gaskiyan alamarin, Sunfi minti talatin ahaka kafin yashigo, shigowarsa yasamu aliya tayi bacci abdullahi na gefenta, tuni yanufo kansa, “kaida bakada lafiya kazo gadin wata marar lafiyan?” “Kai nake jira kadawo, firgita takeyi shiyasa nayi hakan” sufyan ne yajashi suka nufi dakin da aka kwantar dashi, sannan yadawo dakin da aka kwantar da aliya sannan yazauna cikin mintuna kadan saiga bilkisu dama sufyan yaroka abarta tafito don sunfi sabawa da aliyan yakolo ta amince, shigowan bilkisu dole tajira aliya ta tashi bayan farkwanta alokacin sufyan yanufi gun abdullahi , aliya naganin bilki ta wangale baki sanin cewa zuwanta bana banza bane bayan bilki tamata jajen yajikin sannan tamika mata wani takarda tare da cewa duk abunda kikeson sani yana cikin nan, Allah yabaki saa, bashiri tafice don tsoro takeji Aliya ta paki idon inna tasaka tacikin bargo taboye sannan takoma ta kwanta, can dai tamike tasaka akasan katifan tamayar ta kwanta, Bayan sun watse daredare anbarta da inna wacce tabude baki sai bacci take, taciro takardun tabude hotuna ne tsoffi dakuma wani enlarger karami, mahaifinta ne da alh.hamidu mahaifinsu yan biyu saikuma sauran biyun su uku, da mahaifinta dawani wanda take kyautata zaton cewa shine dan biyun mahaifinta hussieni sai alh.hamidu gabanta ne ya tsananta fadi, ta mugun tsorata asaninta tace bilki ta bincika mata alakan alh.hamidu da fadan gidan kusancinsu ta bakin tsoffin bayin dasuka san kan gydan, karshe kuma ga abunda bilki takawo mata, tasan bilki batayi makaranta ko ilmin dazatayi wannan binciken ba, dole akwai wanda yasan sirrinta, waye toh? Sufyan? Inhar shine toh bazai bawa bilki ba dakanshi zaiboye. Abdullahi? Tasan abdullahi bazai taba kawo aikinta ba, don baigama sanin alakarta da sufyan ba balle abunda yakawota(a tunaninta abdullhi baisan cewa ita kanwar sufyan bane), yusuf? Salati tayi tabbas yusuf ne shine kadai namijin da yasan sirrinta , amma meyasa yataimaketa? Nanma dai tagodewa Allah damuwanta burinta yakusan cika, yanzu dole tasami hanya da alh.hamidu don taji daga bakinshi meya sani, tunda duk shine mafi kusa acikinsu Batayi bacci ba har asuba nurses sunzo sun dubata suka fice ana idar da asuba bacci ya kwasheta, abdullahi ne yashigo dakin don ganinta inna tana wuridi yadan zauna agefe, idonsa ce tahango mai takarda, jaa yayi don yaga menene (Salam, akwai batu jiya dayayi ta zagawa akan na rasu, ba ni bace wata benazir muhd ce yar nasarrawa, nagode ga dumbin masoyana dasuka kira donjin lafiyata, duk wanda aka tayar ma hankali ko yashiga wani damuwa ina rokon afuwa don Allah nidai ina raye, Alla[truncated by WhatsApp] HALACCIN SARAUTA 29  benaxir  October 22, 2015  Hausa Novels  106 Views HALACCIN SARAUTA NA BENNAXIR OMAR Jawowan dayayi yaga bangon envelope ne donhaka sai ya ajiye agefen pillow, yana zaune har yusuf yazo mikewa yayi yafice don tun randa yusuf yaje yacemar yagode baikara mishi magana ba. Har abdullahi zaifita yusuf yace “tsohonka na memanka” gabanshi ne yafadi dum donyasan ba maganan dazaamishi saina maganar bayar da kisney dayayi shiyanzu matarsa yake jin tausayi karya mutu su gaza kulawa da ita da dan cikinta, dakin yanufa yatatara abunda zai dauka yafice gyda yanufa yayi wankarsa matarsa duk ta tsorats don tasan baa sallameshiba yadawo, ta so tabashi abun karyawa baikulata ba yafice don ganin sarki mai ran karfe baisameshi ba don yana bacci dole yahakura yakoma Yusuf kuwa zama yayi dirshan agefenta ya tsura mata ido. Tadawo gangar jikinsa tadawo wani gurbi arayuwansa itace tsoka da jininsa, tadawo tamkar bugun zuciyanta domin duk numfashin datayi sai yaji kaman daga jikinsa ne, bata farkaba sai takwas na safe likitan yaga warkewanta dawuri yakuma ce taci abinci sosai wanda ada ruwan lipton suke bata da abu mai ruwa hankalin kowa ya fara kwanciya banda na aliya damuwanta su sallameta awannan asibitin don tasamu tafita ta cimma burinta, sufyan ne yashigo alokacin yusuf yashiga gari anan ta mai bayani sannan tabada takardun daya karanta shima ya yarda da magananta nacewa saita gun alh.hamidu, donhaka yace zai danne damtse don yasamu kusanci da mahaifin hassana, alokacin kuma ta tambayeshi ko yasan dalilin dayasa abdullahi yabata wani bangare ajikinsa, bayaso yatada mata hankali donhaka yace “kinsan abokina ne, amintan dake tsakaninmu yabi,” bata gamsu da bayaninshi dama yasan bazata yarda ba, zatamai wani tambayan ya tallafota tare da cewa ta kwanta tayi bacci, hakan yakara tabbatar mata akwai dalili yusuf ne zaigayamata, saidai tatuna guntun kishin shi donhaka ta share, tuni ta gargade zuciyanta da kartayi binciken dalili balle yadawo mata tashin hankali, Dagari yama wayewa abdullahi yakoma gun sarki inda a tunaninsa fada zaimasa. Yamasa fadan kuwa sosai tareda cewa inhar kanaso ka gwada hallacinka kamata yayi kasiya, yanzu kai zaka iya mutuwa duk lokacin da jikinka ta gaji da wannan injin, nan dai abdullah yasha fada anma daidai da second daya baitaba nadamar abunda yayi ba, Satin aliya daya aka sallameta tuni takoma gida ankara gyra fanninta tasan aikin sufyan ne da antyn abuja wacce aranar tawuce abj, duk da tadawo gida mutane basu dauke kafa ba. Don gaydata alokacin sufyan yasami kusanci da nahaifin hassana tuni yashirya randa zaimasa tambayoyin hotunan yadiba sannan yaje gydan, hassana ta tarbeshi sannan tamasa iso bayan sun gaysa sai sufyan yayi bayanin meya kawosa tareda hotunan ya ajiye mai,alh. Hamidu yayi murmushi sannan yace “dama nakai shekara sha biyu inajiran rana irin ta yau, ranan da yayan cikinsa zasuxo don jin bayani saidai nasan ku biyune, ina kanwarka? Kaje kadaukota itama tanada hakkin tasan meyasami mahaifinta” sufyan yace toh tareda ficewa gyda yaje ya kinkimo aliya a mota yamata bayani tuni jikinta yayi sanyi domun ta tsorata sosai, suka koma inda suka sameshi kamar yadda sufyan yabarshi yafara dacewa “iyayenku yan biyu ne masu son juna dakuma matukar kama, hakan yasa shakuwa a tsakaninsa, sarauta da son mulki shiya shiga ransubwanda shaidan yazo yashiga tsakani , bazan taba fada muku waya kashe iyayenku ba saidai ina rokonku dakuyi hakuri, ku yafewa kowaye ne, ku manta, don tsananta bincike baya jawo komi sai bacin rai,” sufyan da aliya duk sun kagu suji bayani anma sai waazi yake akarshe yace “ranar karshe da mahaifinku da hussieni suka gana adaki kafin hussieni yabar gari, bawanda yake gun sai ni danake falo suna daki abunda naji kuwa shine hussieni yace ko duniya zata juya saiya mulka garrinnan, yayinda hassan ya musanta , hussieni kuwa yace su zuba sugani” donhaka kuhakura da binciken haka” sufyan da aliya sunyi sunyi anma mutum kam ya gunshe baki a bacin rai suka fito suka fice, hassana wacce tashirya don soyewa da masoyinta sai karar mota taji yafice, .gyda suka isa inda akarshe suka yanke shawarar dole mutum dayane yazama ansansu[truncated by WhatsApp] HALACCIN SARAUTA 30  benaxir  October 23, 2015  Hausa Novels  99 Views HALACCIN SARAUTA NA BENAXIR OMAR tuni suka fara tunanin hanyar dazasu je su sameshi ko shi yazo, Washegari sufyan yaje gun alh.hamid tareda rokonsa ko akwai hanyar dazaayi asamu hussieni yazo, yace mishi hanya daya ne kadai zaisa hussieni yazo, in ance mishi anga ajiyan mahaifinsa, ajiya ne wanda kakanku yayi wa hussieni haryau baasamu ba, donhaka dole kusamo wannan hajiyan don hussieni yazo, sufyan ya amsa da toh anma shi tuni ya shuka dabararsa, wasikar jaki yayi yasa aka tura inda yake fadawa hussienin shine dan hassan kuma ga ajiyarsa a hannunsa, yayi hakkanne don baida kudin dazaice zaije bayan haka baisan yadda kanin mahaifin nasa zai karbe sa ba, gwara yajawo shi yazoshi duk da taimakon alh.hamdiu yanemi address din yatura Aliya ta warke garau haka ma abdullahi rayuwa tacigaba da gudana musu, duk da aliya ta dan ja baya da yusuf anma tana sonsa , daidai da kankanin lokaci sonsa baitaba raguwa mata ba, abdullahi kuwa yanzu da taimakon injin bature yake rayuwa, yariga daya cire rai wa duniya don yasan wahalarshi tazo karshe, Acikin wata biyu wata rana sai labari ta iso sufyan cewa ga hussieni yazo gari, ya tare ne agydan alh.hamidu hakan yasa aliya da sufyan suka shirya tareda inna don zuwa gayda shi, kasancewar sunsaba da gydan shigansu sunyi mamaki don kammanin mahaifinsu ne sak a fuskan hussieni sai yanmata guda biyu wanda duk daga kallonsu ansan yan biyune, zasuyi saan aliya, kyawawa dasu suma kammanin mahaifin suka dauko, hussieni ya tarbesu sosai a matsayin yayansa, aliya taji dadi ganin cewa itama gata da yanuwa tuni suka saba da yanbiyun, sunsha tadi sosai sai can dare sannan su aliya suka dawo gyda Washegari sufyan ne ya koma anma wannan karon duk acikin gyda suke, alh.hamidu da hussieni suna falo donhaka sufyan yashirya don yaje yatambayeshi yarike hannun kofan zaishiga yakasa kunne donjin mesuke fada, Alh.hamidu yace “kasan cewa yarannan sundameni maganan mahaifinsu sai tsananta bincike suke, ni bansan mezance musuba, kasan dai bazan bude baki nace musu hussienin mahaifinsu shiyasa akashe mahaifinsu don samun sarauta” “Nagode daka rufe maganan baka furta ba, ni bansan tayaya zanyiba, nayi nadaman abunda na aikata gashi idan ina kallon yaransa duk sai naji na tsargu mussaman macen, itace na cuta da maraici, hakika son zuciya da zugin shaidan su suka sani na aikata abunda nayi,yanzu kunsamamin ajiyan ne? Don da wannan ajiyan zan iya karban sarautar sarki bana galadima kawai ba, nadawo gida bazan koma ba,” Sufyan dake rike da hannun kofan yasake jiki a sanyaye yafice batareda kowa yasaniba, gyda gun aliya yanufa yashiga tana bacci don tace mai haka kawai takejin faduwar gaba da ciwon kai yace tayi bacci inta tashi tasameshi agydan alh.hamidu, zura mata ido yayi hannunsa na bari yana shafa gefen fuskanta, farkawa tayi tazauna tareda cewa “yayah” bai amsataba yafara kokarin share hawayensa, tunda take bata taba ganinshi awannan yanayun ba, tuni jikinta itama yahau bari “yayah! Meya faru? Waye ba lafiya?” Hannunsa na bari yariko nata yarungumota kuka yake sosai mai tsananta zuciya, tuni tafara itama duk da batasan dalili ba, cikin yanayin tausayi yace “aliya hakika agarin bincikenmu yau mun bincikawa kanmu tashin hankali, aliya alh.hussieni shiya sa aka kashe mahaifinmu” tsak ta tsaya tana kokarin daidaita numfashinta anan wayan sufyan tayi kara cikin yanayin tausayi yadauki wayan, “hello, naam” Salati taji yafarayi yamike cak “abdullahi? Innalilahi!! Innalilahi wainnailaihirajiun!! Gamunan zuwa! Innalilahi!” Fitsari tasake awando wani kuka yaci fuskanta, gabanta ya tsananta fadi, “yayah meya sameshi?” Baikulata ba yace “shirya mutafi” dankwali kawai tadauka tabishi, nima benaxir gabana yana fadi nabishi don ganin meya faru! HALACCIN SARAUTA 31  benaxir  October 24, 2015  Hausa Novels  132 Views HALACCIN SARAUTA NA BENAXIR OMAR Mota ya fizga dakarfi sai alokacin aliya taga jikinta ajike anan ta tabbatar da aefa fitsari tayi anma wayake tanan yanzu, tunda kayan jikinta ba nunawa zaiyi ba goran ruwa tagani a motan tabude ta watsa ajikinta, fada yanufa dasu suka sami gurin acike, dakayar yasamu gun parking yana tafiya aliya tabi sahunshi fannin yakolo suka nufa wacce babu matsaka sinke ancika, tundaganan jikin aliya yayi sanyi komawa tayi tazauna, agefe wasu hawaye masu zafi suka fara bin kumatunta sufyan ne yakamo hannuta suka shiga shima dataimakon hauwau. Wacce tanuna cewa su yan gida ne suna shiga dakin acike agefe aliya ta tsaya sufyan yakarasa gun, abdullhi ne akwance agun macecce, duniya inazakije damu, mun aikata alheri mun mutu munbarta, dole kowani rai mamace ne, sufyan durkusawa yayi agun tuni dogarai sukayi gefe dashi don baabarin kowa kusa da gawan. Yakolo ma ba kanta dakyar aka danneta, aliya kuwa wani kyalli kyallu take gani a idonta tuni ta fizge dankwalin kanta tajuya dagudu zata nufi kan gawan rikota akayi, tuni sufyan shima yamike yarikota yusuf wanda ke can kuryan daki tuni yafito ganin aliya tuni ya nufa kanta rikota akayi anma yadda kukasan karfin aljannu gareta wani fizga datayi bashiri suka fada tabaya kan abdullahi tanufa zata budeshi anma nanma dogarai suka kara rikota, tuni umma uwar soro tace a fice da ita, daukanta cak akayi akafice da ita, wani irin kuka takeyi wanda duk mai kallonta sai ya tausaya mata, itakanta tadawo abun tausayi , sumbatu takeyi “yarima meyasa zakamin haka? Yarima meyasa zaka tafi baka amsamin tambayoyin dake raina ba? Kasan cewa sanadina kamutu anma baka gayamin hujjanka ba! Innalilahi wainna ilaihi rajiun!” Kuka takara fashewa da, yusuf ne yajata, yasa aka nemo bilkisu tarikota suka koma gefe acewarsa akaita fanninshi harsaitayi shiru kafin tashigo cikin jamaa, Anyiwa abdullahi wanka yadda ake kowani mamaci, abdullahi kuwa yasha fatan alheri agun alumma, iyayensa sun sakamishi sunkuma nema mishi aljanna, hatta mtanem gydan dsuke karkashinsa suna aiki kowa alheri yake fada akan abdullahi, duk wanda yazauna da abdullahi yasan mutum ne mai tausayi, marar son fada, mai son gaskiya, mai adalci mai kuma bin hakkin dan adam, matarsa da mahaifiyarsa sunbada kyawawan shaidu suma akansu, a inda sarki dakanshi yake jawabi amfanin zuwa duniya kenan, kazamto nai kyautatawa mutane , kazamto mai tausayi karkace don kafi karfin wane, ko wane yana aiki akasanka ka wulakantashi , kasani cewa shaidun duniya shine shaidan lahiranka, muguji duniya muzamto masu shiri akowani lokaci don ziyartar kabari, musani cewa aikin damukayi duk yana cikin littafanmu, yakuma yi jawabin cewa kar mutane suce don abdullahi yabada kidney dinshi shiyasa yamutu, wannan bahaka bane lokacinsa yayi, daya bada da bai bayarba dukka Allah yayi zaimutu yau, kuma mutane susani cewa akullum idan aka tambayi abdullahi maganan kidney dinshi da dalilin bayarwa yanada hujjojinsa anma babbar hujjarsa itace yayi alkawari kuma a matsayinshi na dan musulmi, na wanda yataso cikin mutunci da daraja a matsayinsa na balagagge wanda yasan hukuncin marar cika alkawari hakan yasa yacika alkawarin, kuma shi sarki yana alfahari dashi hakkika abdullahi abun koyi ne, Allah ya sa mucika da imani Ansamu ankaishi makabarta kafin sudawo aliya tasuma yakai sau uku, haka kawai takejin haushin kanta gani takeyi kaman itace musabbabin dalilin dayasa abdullahi yarasu, dakyar aka mata alluran bacci tasamu ta kwanta Sufyan kuwa abun duniya tamasa yawa dawanne zaiji, mutuwan amininsa kokuma bincikowan dayayi cewa hussieni shiya kashe mahaifinsa da mahaifiyarsa, dawani ido zai kalleshi duk yaga missed call dinsu anma bai dauki ko daya ba, atunaninsa basuda abin fada mashi gun inna yanufa yatarar tana kan sallaya tana ganinshi tashafa addua tareda cewa “sufyan ya akaji da hakuri?” “Alhmdlh” “Allah yajikanshi yamishi rahama” “Amin inna, dama nazo muyi maganane akan alh.hussieni” “Inajinka” “Kinsan shiya kashe iyayena shiyasa kika boyemin ko?” “Hmnm abdullahi kenan, rasuwa fa aka maka yakamata kayi hakuri ai yanzu ko” “Yanzu nakeson kifadamin amsata” “Nasani. Sannan alh.hamidu ma yasani, munga babu amfanin gayamuku ne,kuma nagayamaka anan nagayamaka, sufyan kadaina bincike, addininmu ma batason irin wannan binciken, tasar da kwantaccen magana,ana zaman lafiya kunje kun binciko abunda zai hanaku zaman lfy, yanzu dakasan cewa shine mezakayi?” “Lallai inna kinban mamaki, tambaya kikayi mezanyi? Kotu zamu shiga!, bazan hakura ba harsai anyiwa iyayena adalci, kina nufin muna ji muna gani ankashe iyayenmu a banza kenan? Da ke! Da duk wani wanda yakeda hannu aciki wanda yasani da komi duk sainakaiku kotu, zaku fuskanci hukunci ” Baikulataba yafice duk da ta tsorata tana kokarin yimasa bayani, fada yakoma har lokacin ance aliya bata tashiba ganin yusuf yayi donhaka yaje shima yazauna agefensa, yusuf na zubarda hawaye yace “kasan dalilin da yabata kodan shi?” “Nasani” “Menene” “Don yamata alkawari zai kareta koda ranshi zai cire yabata” “Bayan haka” “Yana sonta!! Itace mace tafarko daya fara so a duniya” Yusuf dama yasan dahakan yana son ya tabbatar dinne, ajiyan zuciya yayi wanda shi sufyan yagagara ganewa ko na farinciki ne ko na bakinciki Acan cikin fada kuwa fannin falmata jakadiya ce tashigo tana murmushi, falmata ta kalleta itama murmushin take, jakadiya tafada kasa tana kirari Sai ke Jaruma a cikin jarumai, jaruma acikin jagororin ma jagoranta Idan akaji ance kasaita in anduba kin cancanta taimako dare zuwa rana kin sabayi wa al’umma mai dukiya mai ran karfe Mai kudi uban matsiyata baki fushi ko anzage ki Baki zagi ko anzageki ja muje kece gimbiyar magimbiyata kara masu kece babbar su Mai girma agidan girma sannan kuma matar mai girma,uwar gida a gidan mai girma,Mai

Chapter 6 of 7