Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
5 / 7
jikinta baaga laifinta ba? Saita datasaka abaya dayarufe jikinta don kawai tayafa gyalen?”nikuma nce maka zan auri yusuf ne? Ko na ce maka zanyi aurene? Basai ku aurar dani nagani ba” bai kulata ba yace “inna karta kara fita dawani shigan daya sabawa addini, wannan ai karamin hauka ne!” Yana fita tamike aranta tana cewa inga karamin beran dazai takurani , da tuntuni bakasan daniba saidana girma nasan darajana da mutuncina, tsaki tayi tamike akan kujera baccine mai nauyi ya kwasheta bata farka ba sai magrib tamike tadauro alwala tayi sallah sannan takunna tv duk da batagane mesukeyi don wani indian film ne tadai zurawa tvn ido sallama taji anyi anshigo tagane muryan anma tarufe idonta kaman tana bacci, yashigo yazauna ganin tana bacci yazura mata ido, yarasa yazaiiyi yanason aliya baikuma san meyasa takeson juya masa baya ba, saiyanzu yasan dalili da hussiena takirashi awaya yatabbata tazo tasami aliya ne, yadda yasan kishin aliya yasan saiyayi dagaske, ganin tanata runtse ido yaki ya tafi yasa tadanyi juyi [10/11, 8:01 PM] Adda Bena: Tuni ya tallafota bashiri tamike “meye haka zaka rikeni” saketa yayi awh dama idonta biyu dakyar takoma don taji kunyan abunda tayi. Cikin borin kunya tace “mekazomin anan, ilya yana nan baiyi nisa ba” “Ki kira ilyan ko kasheni yayi ba inda zanje yau saikin gayamin menamiki,aliya hussiena ba budurwa ta bace so ake ahadamu da ita naki babanta abokin babana ne alh.hamidu, tuni tazauna tareda zaro ido, don ta tuna cewa sufyan yace mata alh.hamidu shine wanda suke tare da mahaifinta ran ajalinsa, dasauri ta sake fuska donkar ya fuskan komi “to ni meruwana?” “Nidai don Allah kiyi hkr. Kezan aura kenakeso ke zuciyata take bida “nan yagama sumbatunsa anma aliya ko cikanka batace ba, yana fita tajawo wayanta sufyan takira yana dauka yace “menenee? “Kazo gida nasamu labarin alh.hamidu” bata saurayi mezaice ba ta kashe wayan cikin minti talatin saigashi ya iso “Aina kika samu labarin? Keda kike nanike a daki?” “Meruwanka? Yusuf yazo yana ban hakuri akan yan biyun dasuka min hauka ranan, wai yaran aminin sarki ne alh.hamidu” “Allahu akbar, duk bincikena banje kansa ba, don naga baida sarauta anma tazo gidan sauki, yaran yanbiyu ne? “Ae! Bazaka gane wanne bace hassana ko hussiena” “Tazo daidai zanyi soyayya da daya, kozan sami kusanci da mahaifinsu ko yakikace?” “Kayi da hussiena” “Munafuka don kihadani fada da yaronnan ko?” “Oho dai kaikasani” “Kedai ki tabbata babu wanda yasan alakanmu don anasani shikenan ansan kema yar galadima ce plans dinki duk zasu rushe” Ficewa yayi yabarta bai nufi ko ina ba sai fada fanni abdullahi da matansa, yasamu tarba sosai anan yagwada sa cewa yaga yar alh.hamidu kuma yanaso, abdullahi yayi farinciki inda yace wacce aciki? Sufyan yagwada cewa hassana yakeson aura, aikuwa nan da nan yafara murna yara masu hankali kayi saan mace dawannan yace su shirya daredare zasuje gun mahaifinta, Daredare suka sha manyan kaya suka nufi gydan alh. Hamidu wanda yakarbesu hannu biyu biyu, abdullahi yayi bayanin kudirin sufyan a matsayinsa na dan marigayi galadima, nan da nan alh.hamidu yace “hassan adamu? ” Abdullahi ya gyada kai tareda cewa “ae shi” “Masha Allah ashe zankara ganinka? Mahaifina aminina ne sosai, Allah yajikan rai” Dukkansu suka amsa da “ameen” “Ban isa naci amanar abotana da mahaifinka ba, donhaka in hassana ce nabaka!” Sufyan yanuna farincikinsa yakuma yi godiya ayayinda akace suzo washegari don ganin yarinya Ranan sufyan yayi bacci mai dadi ganin cewa yadauko hanyar bayyanar gaskiyan mutuwan iyayensa, Washegari yashirya cikin janfa ya sha turare sai kamshi yake suka nufi gydan shida abdullahi ayayinda aka musu iso, yana zaune kanshi a kasa gabanshi na fadi wanda shikanshi yarasa dalili tayi sallama ahankali muryanta cikin sanyi sannan tashigo, alokacin yadago yakalleta, tanada haske saidai bata da tsayi, kananun ido gareta anma tanada karan hanci, kyaunta dan daidai masha Allah, dama shi bai fiyeson bakaken mata ba, musamman wanda yafisu haske, abdullahi ne yatabashi tuni yadawo daga duniyan tunaninsa yafara amsa gaysuwarta, kanta a kasa a zuciyanshi yace “anma aliya munafuka ne, yanzu wannan salihan yarinyan zatace taje tamata fada?wannan ai daga gani ba ruwanta salihar macece, suka gaysa sannan abdullahi yafara neman sasantasu itakanta hassanan tana fara ganinshi taji ya kwanta mata arai, domin kuwa sufyan yahadu namiji ne awaye, mai kyau da kwarjini taji ta narke da sonsa awansu biyu suka fito tarako su har gate sannan yakarbi numban wayanta, suna fita daga gidan tashiga dagudu gun hussiena wacce take labe take kallonsu tsaf suka hau tsalle da murna , su hassana anyi mijin aure, Sufyan kuwa yaki daina murmushi shikam sonta yake, karfa yagagara cika aikinsa harya ajiyeshi a gydansa sannan yakara fitowa yataho gydan inna, yayi hakanne donkar abdullahi yasan gydan saboda bacin rana, aliya tana kwance yashigo “Adarennan yaya meza kacemin?” “Ke. Tashi! Sharri zakiyima hassana ko? Yarinyannan yar salaha da ita ba ruwanta, “Ko dai taje ta nutsu don kissa irin na mata nikam kabarni bacci zanyi” fannin inna yaje yaci yakoshi sannsn yafice” Washegari aliya taci wanka tsaf tashirya cikin atamfa dinkin yakarbeta sosai ba kadan ba, tana zaune, sallama akayi wasu dogarai ne sukace wa inna ana neman aliya a fada Hankalin inna yayi dubu yatashi tazo fannin aliya “mekika yi musu?” “Babu , suwaye?” “Daga fada ana nemanki” tayi tunani iya tunani tarasa meya hadata dagun, tafito a sanyaye s[truncated by WhatsApp] HALACCIN SARAUTA 21  benaxir  October 12, 2015  Hausa Novels  104 Views HALACCIN SARAUTA NA BENAXIR OMAR Gabanta fadi yake don babu irin tunanin dabatayi ko wanene ba, dahaka suka isa fada taga bayanda tasaba ganin mutane ba, andan cika sosai, fannin falmata aka nufa da ita inda taana ganinta ta taso ta wanka mata mari umma uwar soro ne tayi sauri taja aliya wacce tarike kuncinta cike da takaicin abunda yasameta batasan metayi ba ankafamata mari, falmata cikin fushi take cewa “duk wanda ke da hannu acikin wannan aikin kuhado min dashi,” ahanyan fita da itane taga sufyan da abdullahi suna tsaye ganinta da yayi yasa ya tsure anma bai gwadaba don kar wani ya tsammace wani abu, yaja abdulllahi gefe tare da tambayanshi meya faru? “Kasan harkan mata da matsala, nagayawa yusuf yabar yarinyannan saboda abunda zai jawo mata, mahaifiyarsa batada shariya, yaki yadda, yanzu yazo yakwanta ciwo tun ast week, anma ciwon yayi tsanani ne shekaranjiya wanda dogaransa sunce daya dawo daga gidan aliya ne yakwanta. Kuma sumbatu yake yana kiran sunanta, hakan yasa mahaifiyar tace ko aliya tamishi wani abune, wai mayya ce tanason cinye mata da, ” “Subhanallah” “Yanzu dole munemi hanyar fidda aliya daga wannan matsifan narasa meya dawo da ita garinnan” “Muje muga gimbiya” Suka nufi fannin gimbiya yakolo inda suka mata bayanin abunda ke faruwa hankalinta yatashi sosai, anma babu yadda ta iya bata isa tasaka baki aciki ba, don baa haka, yazama dole tanemi mai ceton aliya hakan yasa tafito don zuwa ganin aliya wanda akasa a cage, aliya idonta ya kumbura yayi bul don tasha kuka, ita badamuwanta abunda suke mataba damuwanta shine yusuf yawarke ko zata gwada masa irin son datake mar, kodataga gimbiya tuni kukan yakaru,gimbiya ta yi umurni wa masu gadin dasu fice zatayi magana da ita suna fita tariko hannunta “Aliya meya faru? Kigayamin gaskiyan abunda kika sani” Cikin kuka aliya tabata labarin abunda yafara faruwa tundaga tsohon gidanta, zuwa haduwanta dasu hassana da hussiena dazuwamshi data koreshi da ilya, dakuma zuwanshi na biyu shekaranjiya kenan sannan tacigaba dacewa “wlh ranki shi dade ni ba mayya bace,jinina a tsarkake yake,” Gimbiya yakolo taji tausayinta anma babu yadda ta iya donhaka tace “bazai yiwu naceceki ba, dole dole shi zai ceceki idan yamike akan gado, inhar bai mike ba, zata iyasakawa a illata ki”hankalin aliya yakara tashi bata taba jin mutuwa zamzam haka ba, tagama tsorata tarasa ina zata saka ranta, gimbiya tasamu tadan lallabata kafin takoma fanninta ta ai akira bilki, ta umurceta datana kai mata abinci tace injita, takira abdullahi da sufyan ta bukaci suje suga jikin yusuf din ko zaagane meke damunsa sun nufi fannin sa, suka tarar da likita ne sai bayi guda biyu, sufyan yazauna yadan duddubashi kasancewar yanada dan ilmi akan lafiya,yakuma tambayi likitan shidai likita yace jininsa tahau abinda yagani kenan, sufyan yadanyi dube dubensa sannan yaja gefe yazauna kusa da abdullahi yana cewa “nifa inaga akwai abunda ke damunsa yana boyena, its lyk akwai weak heart, mezai hana akaishi asibiti agani, abdullahi ya amince da shawaran, nan da nan ya umurci da azo akai yusuf asibiti , falmata wacce take fanninta tuni tafaso dakin hankali a tashe tana cewa ” iiiiiina kuma zaku kaishi?” Daga yanda take jan maganan sufyan yagane cewa tabbas batada gaskiya, abdullahi yadaure fuska sannan yace “asibiti zamuje suduba jikin dakyau” “Babu inda zaku kaishi!” Cikin tsawa tafadi haka don saida hankalin bayin yakoma gun kowa ya tsaya jungum jungum, ganin basuda niyya yasa abdullahi yariko yusuf din dasauri sufyan yarikoshi alamun yabari karya rikoshi haka suka barshi akan gado suka fito domin kuwa falmata ta kasa ta tsare Bilki kuwa dataje kai abincin basu barta tashiga ba dole takoma tasanarwa yakolo abun yaci mata rai anma babu yadda ta iya dole ta san yadda zaayi a farkar yusuf kamin wani abu yasami aliya, sufyan kuma samu yayi ya lallabi abdullahi suka shiga gari babban asibiti suka dauko likita yazo da kayan aikinsa a fannin abdullahi yasauka wani daki da aka ware masa, suna jira dare tayi donsu cika aikinsu inhar basu magance matsalan adaren ba washegari zaa iya zartarwa aliya hukunci domin falmata tasa annemo hujjoji nacewa aliya mayyace kuma ita take illatashi inhar baakasheta ba yusuf bazai tashi daga sumbatun dayake ba,saida suka bari kafa yadauke sukaja likitan suka kaishi fannin yusuf suka rufo kofan, yayi bincike sosai yagano cewa kwaya aka bashi wacce tafi karfin kwalkwalwarshi hade da allura, saboda kasanceear aliya ce aransa yasa yake sumbatar sunanta, yadanyi dube dubensa sannan yace zaiyi alluran dazaiyi reversing dinshi, anmishi allurai kwaya biyu anma likitan yanuna musu cewa sai bayan awa hudu ko biyar yatashi hakan yasa dole suzauna agun, dukkansu babu wanda ya runtsa yusuf baitashiba sai hudu na asuba nan da nan suka lallaboshi yazauna suka watsa mai ruwa zai fara matsifa abdullahi yatoshe mai baki sannan yace yayi shiru yaji, cikin basira suka mai bayanin abunda ke faruwa sannan sukace hanya dayane don ceton aliya idan safiya tayi yacigaba da yadda yake inyaso idan antashi hukunta ta yafito yafadi gaskiya shikam tuni hankalinsa yatashi jin cewa aliya na cage saboda shi, zuciyarshi na radadi mikewa yayi waizaice yadaukota suka danneshi dakyar suka lallabashi ya yarda, kafinnan suka wuce fannin abdullahi don yin alwala sutafi masallaci alokacin ankira sallah Dasafe aliya idonta yacika ya kumbura ganin cewa yau komi zai iya faruwa da ita, taci kuka harta koshi ta godewa Allah,karfe goma saiga dogarai inda akaje da ita mahukunta, gurin da ake hukunta duk wanda yayi laifi acikin fada, ta sunkuyar dakanta ayayinda umma uwar soro taketa bayanin abubuwan da aliyan tadauka daga karshe tace “zaki fadi gaskiya ko ki fuskanci hukunci, ke ba baiwa bace da an miki hukunci mafi tsanani, sannan kinsan cewa hukuncin maita a masarautannan shine akashe mutum, donhaka kifadi gaskiya kisake yarima kisake kurwansa,donkar ki fuskanci tashin hankali, ” Aliya kuka take sosai yayinda take kallon sufyan wanda ke mata alamun tayi shiru anma tagagara ganewa shikenan itakam yau mutuwa tazo mata, ta ina zata sake yusuf, gashi mintuna kadan aka bata tasakeshi, kukan datake harya hade zuciyanta alokacin. Kawai saiga yusuf yashigo filin falmata it[truncated by WhatsApp] HALACCIN SARAUTA 22  benaxir  October 13, 2015  Hausa Novels  129 Views [10/13, 8:13 PM] Benaxir omar: HALACCIN SARAUTA NA BENAXIR OMAR cikin wani yanayi na fargaba tace “yarima?” Dasauri tanufeshi shikuwa yanufi inda aliya take ya kunce igiyan da aka daureta dashi, ji yayi kaman ya rungumota ko zatasan halin da zuciyanta take ciki anma babu yadda ya iya, tuni kuwa abdullahi yashigo filin shima riketa yayi suka dagota wanda kowa saida yayi mamaki kenan aliya tasan dukkansu? Bilki ce tanufesu don riko aliya, sufyan ma gun yanufa nan da nan akasata a mota yanufi asibiti da ita, yayinda falmata ta yi umurni da a watse nan da nan yusuf yace baigama ba yanada magana, hankalin falmata yatashi tasan cewa asirinta zai tonu donhaka takara daure fuska anma yusuf bai saurareta ba, yakira likitan dasu abdullahi suka kawo mishi da likitan da falmata takawo, yacewa likitan falmatan yamasa bayanin meke damunsa cikin tsoro yace “zazzabi ne da rashin bacci,”, yakalli likitan da sufyan suka kawo masa sannan yace masa “meka samu yake damuna?” “Allurai ne akayi ranka shidade da dan kwayoyi ” Yusuf yamike yahade rai tamkar sarkin dayake shirin yanke hukunci “kukama minshi harsai yafadi dawa yahada baki aka sashi abunda yayi,” nan da nan dogarai suka kamashi, anan yahado da tsohon da aka kama wanda yake cewa tabbas shi mai kama mayune kuma aliya ma mayyace ita tacinye iyayenta, dukka yasa aka kamasu sannan yanufi fanninsa wanka yayi da zummar yabi aliya asibiti saidai fitowarsa yatarar da mahaifiyarsa tana jiransa, bai kalletaba balle yanuna yasan tana gun harta gaji donkanta sannan tace “in nina haifeka kasakesu” Wani kallo daya mata itakanta saidata tsure bai kulata ba don tunda yake itakanta bata taba ganin bacin ranshi irin na ranan ba, kaya yasa yafito don ji yayi yatsani munanan halayyan mahaifiyarsa don batada hali ko kadan tabari son mulki da son zuciya yarufe mata ido, bayason halin mahaifiyarsa ko kadan yasan shima da halinsu daya anma haduwarsa da aliya yacanja, yadawo cikakken mutum yadawo mai tausayi yakuma san darajan dan adam, yanzu yasan meya keyi kuma ya gode Allah daya hadasa da aliya akullum yana kara kaunanta sonta daban ne, dasauri yakunna motan sannan yafice daga fadan, asibiti yanufa wanda aka kwantar da aliya wacce ta gigice, sufyan duk tunaninsa karya rasata, haushin duk yancikin gydan yakeji don gani yake aliya zata iya rasa ranta, Allah kadai yasan kukan dayake a zuciyansa, tunaninsa Aliya ce kadai tarage masa yazaiyi insun rabashi da [10/13, 8:50 PM] Benaxir omar: Aliya , donhaka duk tunaninsa ta tsaya cak yusuf ne yashigo a rude yana tambayan ina aliya, abdullahi ne yamasa bayanin cewa sunbata gado suna dubata,numfashi yaja yazauna yadafa kansa nauyi yaji kanshi yanayi, don shikanshi wankan dayayi ne ta taimaka masa yaji karfin jiki, sunfi awa azaune kafin likitan yafito nan da nan suka mike inda yace musu tasamu kidney problem don kaman anmata wawan bugi agun, kuma gaskiya dukka biyun sun lalace ana son acire kuma abata guda daya, bayan haka anason jini sannan kuma tabugu sosai akanta dole ajira aga farkwanta suyi adduan Allah sa tatashi lfy kar asamu wani matsala,sufyan dafa kai yayi ya tsuguna agun saiga hawaye suna zubowa, abdullahi da yusuf wanda shima ya rikice kallomsa suke, kishine yashiga ran yusuf akanme sufyan zai damu? Meye hadinshi da aliya? Atake yace likitan yacire nasa inyazo daya, anma sufyan nan da nan yamike tareda cewa muje aduba kidney din, da jinin , yusuf wani harara yasakar mishi domshikam ji yayi hankalinsa yatashi har bari hannunsa yake, likitan saiyaga kaman abumsun gasane, donhaka yace waye yafi kusa da ita? Yusuf yayi caraf yace “nine masoyinta” Sufyan bai kalleshiba sannan yacema likitan “muje ! Ni yayanta ne uwa daya uba daya!” Ba yusuf ba hatta abdullahi dake kallon su sai daya tsorata wayan hanninsa yasake a kasa, tunaninsa ya tsaya cak, ya cukumo sufyan “kai dabban wani gari ne? Don kawai kana sonta zakace kai danuwanta ne?” Inna wacce tashigo asibitin a rude taga sufyan wanda yakirata yamata bayani tanufo kansu dasauri tanacewa “sufyan ina kanwarkan take? Yau munshiga uku innalilahi” yusuf sakeshi yayi don ya mugun tsorata, azatonsa yasan wacece aliya ashe yaudaran kansa yake baisan komi akantaba, jan jiki yayi gefe tareda zama akan kujera yayinda sufyan yanufi dakin likitan don samun karin bayani gameda kidney dazai bayar inda likitan yasanar dashi cewa dukka biyu sunsami matsala sun lalace donhaka dole acire asamata wani ko guda daya tasamu tayi surviving, tunda har kumbura tanayi wanda sai alokacin shi sufyan yalura dahakan shidai yasan yaga tacanja baiyi tunanin wani abuba tunda baidade da ganintaba anan yace shi yayanta ne uwa daya uba daya aka bashi duk wani fike dazai cika, yasa hannu sannan yace afara duba jinin , jininsu yazo daya atake aka diba , leda biyu yabayar yakwanta don yahuta bayan kwana uku zaa cire kidney dinshi daya abawa aliya, har kuka saidayayi akan gadon, yanason yar kanwarsa Bangaren yusif kuwa yarasa mezaiyi murna? haushi?takaici? Dole dai yayi dukka dole yayi farincikin cewa sufyan yayanta ne ba aure a tsakaninsu balle yadamu , nabiyi kuma dole yaji takaici da aliya taboye masa asalin cewa sufyan yayanta, tabbas hakane abdullahi yasanar mishi sufyan dan marigayi galadima ne anma baitaba kawowa aliya ba, lallai shi soko ne, meyasa aliya taboye mishi wannan bayan yasan babban sirrin ta balle wannan, shidai yanzu duk yarude damuwansa tafarka Inna kuwa duk ta tsure duk yanuwa na nesa saidata kira tasanar musu, antynsa ta abj ma tace zata biyo jirgi ta taho washegari, anan yusuf yasan cewa lallai aliya tanada gata, anma meyasa suka barta take bulayi agari? Abdullahi kuwa ayanzu yatabbatar da inda yasan aliya. Tun randa yafara kallonta yasan cewa yasanta awani gu!, tabbas itace kanwar sufyan wacce suke wasa da ita ya kyalla yace yana sonta, wacce yanemeta yarasata, akacemasa tatafi abuja dazama, wacce itace first love dinshi, ba shakka itace shiyasa duk lokacin dayaganta cikin wani hali baya sharewa saiya taimaketa, tabbas itace innalilahi yazaiyi? Yanzu yafarajin sonta danye, ruwa tsundum yadawo, yazaiyi da yusuf? Yazaiyi yatabb[truncated by WhatsApp] HALACCIN SARAUTA 23  benaxir  October 15, 2015  Hausa Novels  105 Views HALACCIN SARAUTA NA BENAXIR OMAR Tunaninsa duk yajuya, alokacin suka nufi fannin da aka kwantar da sufyan abdullahi ne ke zaune agefensa inda yake zura masa ido sufyan yayi murmushi sannan yace “karka damu, zageni kawai raina baxai baci ba,” hakan yasa abdullahi ya makeshi dakarfi tareda cewa “soko, wawa!ka cuceni wlh, kacemin harda ita a rasuwa meyasa ka boyemin tana raye?”sufyan bai damu da zagin ba yace “yazama dole ne,dole in boye wa duniya wacece ita, ko so kakeyi itama abimin ita akashe?” Shidai abdullahi baice komi ba yasan cewa abun yanaciwa sufyan rai shiyasa baiyi wani rikici ba har suka sallameshi daga bed rest din dasuka bashi alokacin sukaje dubata, tafarka anma ta jigata sosai, har ranta taji haushi asalin haushi taji don tabbas tasan cewa tanada matsalan kidney tanemi nasayarwa ko zata siya asaka mata tafasa daga baya acewanta kar tazo tafara ciwo bata cika burinta ba, gwara tagama idda cika burinta kafin ta kwakulo wani ciwo gashi yanzu sun nemo, kuma sunaso sucire tasan duk yadda zatayi suhakura bazasu hakura ba dole tabari su saka, fatanta Allah yatada kafadunta don ta cimma burinta Sufyan ne da abdullahi suka shigo dakin ta tsaya ne taga ko zataga yusuf bata ganshiba nan da nan zuciyanta ya sosu sosai, abdullahi kuwa saiyake ganinshi kaman bakon mutum agareta, kaman bakon fuska, tayaya zaifara fuskantarta? Shikam yadawo ruwa tsundum!, zama sukayi agefe sufyan yariko hannunta cikin tausayi, yanason kanwarsa gani yake itace sauran bangaren jikinsa, ganin basuda niyya magana ta bude baki da kyar sannan tace “meye haka kaman na mutu!” Sufyan yayi murmushi tareda cewa “bazaki mutuba ko raina zan iya cirewa nabaki don na sadaukar dakaina agareki”abdullahi hawaye ne ke zuba masa a ido anma yanata kokarin yaga yadanne yashare saboda kar agane, duk lokutan dasuka kasance tare suna yara yatuna, yatuna lokacin daya mata alkawarin zama da ita ko wani hali na rashi ko samu, yamata alkawarin taimakonta cikin kowani hali ko da kuwa zai rasa ransa ne, cikin sanyin murya yace “yajikinki?” “Dasauki ranka shi dade” a karo na farko kenan dayaji wani iri data kirashi haka yasan ada takan ce masa “yayana” bazai iya zama ba bai amsata ba yafice yabar dakin waje yafita yashiga motarsa kuka yafarayi sosai, tunda yataso yayi wayo baiyi kukan dayayiba, nadama duk ta isheshi, toh ni benaxir damuwan meyakeyi? Aiba laifinsa bane, yusuf ne yashiga dakin alokacin inna tagama jimaminta tana zaune itama agefe shidai sufyan yaki motsawa, yusuf yazauna agefe tareda cewa “yajikin?” Bata amsa shiba anma ta gyada masa kai, hakan yasa yaja gefe yazauna duk yadamu, likitan ne yashigo don dubata bayan dube dube yace sufyan yazo su gwada kidney dinshi, yabi likitan inda sukaje akayi scanning aka duba kidney dinshi da lafiyansu sannan ko shima zai iya badawa wani bayan dogon bincike likitan yakirashi kanshi a sunkuye yana cewa “kayi hakuri sufyan, bazaka iya bawa aliya kidney dinkaba saboda kaima naka basuda isheshen lafiya,” wani dogon salati inna tayi sufyan kam daskarewa yayi agun, yagagara motsi shikan hankalinsa yatashi, yazaiyi da rayuwansa? Anan yafara rokon likitan yakawo dabara ataimakawa yar kanwarsa anan likitan yakawo shawarar akira yusuf, nan da nan suka kirashi atake ya amince zaibayar inda akace yashiga don amasa scanning shima, bayan ankammala likitan yace washegari zasuji result tunda dare yayi, hankalinsu duk yatashi innace ta kwana a asibitin abdulahi da yusuf suka koma gyda, ko yusuf dayaga falmata zata dameshi fitowa yayi yabar masu gidan, Washegari karfe tara anty ta iso asibitin yusuf, abdullahi da sufyan suma duk suna gun, likitan yakirasu inda yabawa yusuf hakuri cewa “yusuf you are not a donor donhaka bazaka iya bataba, kidney dinta bazai karbi naka ba” tunda sufyan yake baitaba fuskantar tashin hankali irin wannan ba baisan sanda yafara fidda hawaye da gumi ba, yusuf kam kuka yake wiwi, yarasa yazaiyi anan duk suka fito abdullahi yagagara tafiya, hankalinsa yatashi office din yakoma tareda cewa “dr. Kidney dina guda dayace tayi saura, ko akwai hanyan dazan iyabata ? Tunda kunce agobe kukeso!,” Likitan yakalleshi alaman mai tababben hankali sannan yace “kayi hakuri kanaso ka mutu ne?” Cikin tsawa abdullahi yace “meruwanka da mutuwa ko rayuwata! Kagayamin hanyan dazanyi”cikin tsoro likitan yajawo files dinsa sannan yace “Inhar zaka bada sauran kidney dinka zakadawo bakadashi ko daya, toh munada dialysis machine wanda yake aikin da kidney yakeyi, dashi zakana amfani har lokacin da jikinki zatayi resistn ,” abdullahi yayi hamdallah sannan yace duba kagani ko zan iyabata inyaso kacire ayau dinnan kanemo danwanka zanbiya ko nawane, kusamu kusamata kozata sami lafiya, sannan karka yadda kafadawa kowa!” Likitan ya tsorata shikam yakasa gane kansu, gashi dai danuwanta bazai iya bada nashiba, yusuf kuma falmata ce ta aiko wa asibitin wasika cewa karsu yadda su dauka nashi susawa wata banzar bawa ko dukkansu zasu rasa aikinsu, hakan yasa duk suka tsorata suka cemasa nasa bazai karbu ba, ga abdullahi mai mata anma ya yanke shawaran yahakura da duniya, dahaka yaduba yaga komi daidai atake yayi magana da likitan dazasu cire, adaren ranan suka cire masa kidney dinshi kwaya daya, masha Allah sadaukarwar soyayyaya da cika alkawari tabbas abdullahi yanuna nagarta da hallacin sarauta, yanuna cewa inhar baicika alkawari a matsayinsa na masoyinta ba albarkar sarautar gydansu zaisa yacika, yagwada mata cewa agydansu yatashi da nagarta, baimanta da alkawarin tun suna yara ba yau yacika. Yacika mata alkawarinsa nacewa zai tsaya agefenta, zai taimaketa koda kuwa zaizama ajalin rayuwarsa, acikinmu mutane nawane suke cika alkawari????????? Sufyan kuwa yana wata duniya daban don neman kidney dazaasa wa aliya shida yusuf sai kiransu akayi aka sanar dasu abdullahi yabayar yusuf dayake tuki saidayayi wawan reverse yatsaya sanin cewa abdullahi kidney dinshi dayace tarage suna nufin yabada wannan? Lalle kam akwai rikici, abdullahi nason al[truncated by WhatsApp] HALLACIN SARAUTA 24 & 25  benaxir  October 16, 2015  Hausa Novels  137 Views [10/16, 7:54 PM] Benaxir omar: HALLACIN SARAUTA NA BENAXIR OMAR sufyan ne yarikeshi tareda cewa “wuce muje” bai iya tuka motan ba hakan yasa sufyan yafito dashi yakoma yafara tukawa asibitin suka koma dasauri suka shiga, alocin matan abdullahi kuka take sosai hankalinta yatashi nan da nan magana yazaga gari, har fada tunda yakolo take hankalinta baitaba mummunan tashi irn na wannan karon ba, a gigice tabar fadan ta umurceta da akawota asibitn, kuka take sosai alokacin data iso asibitin yacika tam, mutane saisukaja gefe kawai suna kallon ikon Allah, yakolo ne ta bukaci tashiga dakin anan likitan yasa aka shigar da ita, don yace mata dan nata yanada jiki mai kyau tun awa biyu dasuka wuce idonsa biyu, hankalinsa akwance duk da zafin ciwo dake damunsa, cikin zafin murya da raunin zuciya tace “meyasa zakayi haka abdullahi? Baizama dole don zaka gwada mata kana sonta kasa rayuwarka a hatsari, haba abdullahi yanzufa kai rayuwa batada amfani agareka zaka iya mutuwa akoda yaushe aduk lokacin da jikinka tagaji da wannan injin, haba abdullahi!!” Tunda yake baitaba jin mahaifiyarshi takira sunanshiba yasan cewa ta tabu matuka, donhaka yamika mata hannunsa tarikoshi gam kaman bazata sakeba “tun ina karami kin koyamin muhimmanci rikon alkawari da cika alkawari, a tarbiyan gidanmu na sarauta natashi naga mahaifina yana cika duk wani alkawari daya dauka , meyasa nima bazan kwatanta hakaba? Shin bakimin kwadayin aljanna? Shin bakimin kwadayin rahaman Allah? Don Allah ki kwantar da hankalinki, nasan ina son aliya anma cika alkawari shine musababbin bata sauran kidney dina, inban bataba duk nan babu mai bayarwa, sufyan nashi ba lafiya, yusuf kuma nazo wucewa naji gimbiya falmata ta aiko ace mishi karsu yarda subada na yusuf ko abakin aikinsu, kuma nasan cewa ko batayi magana ba bazaitaba yiwuwa yusuf yabada nashiba, tunda kinga yana shaye shaye bazai yiwu ace kidney dinshi lafiya lao ba, annemi nasayarwa baasamu daidai nataba, dole nacika alkawarin dana mata nacewa koda raina zanbayar don naceci rayuwarta, kitaimaka ki bano kwarin gwiwa don insamu inwarke, mutuwa kuwa inna mutu lokaci nane babu wanda yake mutuwa ba lokacinsa ba, ” yakolo kuka take sosai tareda hamdala azuciyanta tana godewa Allah dayabata yaro mai ingantarcen tarbiya, mai kyan hali tunda take bata taba ganin abdullahi yayi alkawari yasaba ba, mutum ne mai daraja dan adam, taja numfashi sannan tace “nagode sosai daka fahimtar dani, Allah yarayamin kai yabaka tsawon rai yataimakeka,Allah yadaga kafadunka” anan tamike tabar dakin kuka yacita sosai balle matarsa karshe gado aka bata anan likitan yasamu tanada ciki ga murna ga bakin ciki, yusuf kuwa yana makale a gefen dakin tiyatan dazaayiwa aliya, yaki motsawa azamansa agun falmata tasa akirashi yakai sau biyar daga karshe tashi yayi yawanke dogarin da mari saida aka fita dashi yace karsu dameshi, sufyan kuwa zuwa yayi yasiyo abubuwan dazaa bukata na abdullahi da matarsa, Mai martaba sarki yaji bakin ciki sosai musamman da falmata tace masa wa baiwa yabada kidney dinsa, shikadai a fada yarinka fada, daga baya ne da yakolo ta koma gida dakyar a kukan nata sai ganin mai martaba tayi akanta yana shigowa yafara fada akanme zatabarshi yafita haryaje yabada jikinsa ganin yadda yake fadan tasan cewa falmata ta shuka wani makircin anma yazatay? Dole tamai bayani hakan yasa tazaunar dashi tamai bayani dalla dalla tana kuka yaji tausayinta sosai yakuma ji son dansa yakaru, rungumarta yayi yana lallashi [10/16, 8:21 PM] Benaxir omar: HALACCIN SARAUTA NA BENAXIR OMAR Yusuf kuwa tun yana jira yaji bazai iyaba, kuka yake wiwi sufyan yafara lallashinsa anma duk dahaka yusuf yagaza yana kuka yana cewa “aliya kitashi, namiki alkawari bazan kara shan wani abuba, aliya na nutsu nadaina

Chapter 5 of 7