Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

bayyana mata ko ita wacece.
" Sunana anisat, ni yar sanda ce mai binciken manyan
laifukka kuma yanzu haka akwai abunda nake bincike a
wannan kauye naku saboda haka inaso ki bani hadin kai
dari bisa dari." Anan ta nuna mata ID card dinta. Ita kuwa
mairo batasan ko meye ID card ba iyaka dai ta karba tana
kallon foton anisa dake ciki.
PAGE 48
" Wai ko kun taba yin bako a wannan gari naku?" Anisa ta
tambaya.
Anan mairo tayi dan tunani mai zurfi, cikin kankanin
lokaci sai ta tuno da mutumin da suka gani jiya a wurin
rafi. Daga nan sai ta amsa da cewa. "E kwarai kuwa."
" Ina fatan dai zaki iya bayyana min ko shi waye!" Anisa ta
fada.
Anan mairo ta fada mata wannan mutumin da suka gani
jiya wurin rafi tare da zanen dake hannunsa na maciji.
Haka anisa ta cigaba da yiwa mairo tambayoyi ita kuwa
sai bata amsa take. Daga karshe sukayi sallama anisa
kuwa sai ta dauko cake ta bata. Mairo ta karba cikin
mamaki domin tunda take bata taba ganinsa ba. Da anisa
ta fahimci hakan sai ta fada mata cewa abinci ne. Haka
anisa ta shiga motarta ta manta ta karbi ID card dinta. Ita
kuwa mairo a tsammaninta an batane kyauta. Anan ta
kama hanyar gida tana tafe tana tsalle tsalle.
Bayan magrib ne mairo ta kaiwa dije ziyara. Anan ta
bayyana mata yadda ta gamu da wannan yar sanda anisa.
Da kuma kyautar data bata na hotonta. Sai kuma dan
cake din data bata. Da karfi dije ta karbe cake din ta
bantali dan kadan. Ai kuwa tanajin dadi sai ta finciko shi
iyakar hannunta. Daga nan kuma saita amshe ID card din
ta rataya a wuyanta kamar sarka. Ita kuma mairo bata
damu ba anan ta barta shi. Haka sukayi sallama mairo ta
koma gida.
Bayan sati daya da faruwar hakan, yar dawar da akaba su
dije sai ta kare. Sabida haka sai rayuwar da ta dawo. A
kowane lokaci dije kanyi bakin ciki sosai idan taga yadda
rayuwarsu take. Ba jin dadi balantana walwala. Saboda
wannan dalili sai ta yanke shawarar cewa bari ta gwada
zuwa rafin nan wata kila ko zata gamu da yar sandan nan.
Idan ta gamu da ita ta mata tambayoyi kila ta bata irin
abunda taba mairo wato cake.
Da daddare ne amma ba sosai ba. Sai dije ta fita ita kadai
da nufin zuwa rafin nan. Haka ta kama hanya tafiya take
da sauri kai kace wadda aka yiwa busharar wani abu. A
wannan lokaci yunwa ke damunta sosai domin rabonta
da abinci har ta manta. Babban abunda yasa ta yanke
wannan shawarar na tafiya rafi shine ko wata kila ta dace
ta gamu da wannan yar sandan wato anisa.
PAGE 49
Idan ta gamu da ita wata kila ko tamata tambayoyi yadda
tama mairo. To idan aka yimata tambayoyin kila ta samu
cake ko ta rage yunwar dake damunta. A haka ta cigaba
da tafiya ba sassauci. Sabida tsabar yunwar dake
damunta ko takalma bata dauko ba. A kasa take tafiya
bata damu ba. Bayan ta isa rafin ne sai ta tsaya tana
duban ruwa amma kowa babu. Wurin yayi tsit sai kace
makabarta. Anan dije ta duka cikin bakin ciki. Cikinta ne
ke wani murdawa saboda yunwa. Cikin rashin tsammani
sai taga an hasko mata haske. Tana dubawa sai taga mota
tafe wurinta. Anan dije ta mike cikin jin dadi domin a
zatonta yar sandan ce. Kaji wani abu, da takardar cake
din tazo.
Anan ta falfala da gudu saida sukayi gab da gab sannan ta
tsaya. Kawai sai taga namiji ya fito a ciki. Dubawarta keda
wuya sai taga ba kowa bane in banda wannan namijin da
suka fara gani a ranar da santsi ya kwasheta ta fada rafi.
Anan ta mika masa takardar dake hannunta na cake. Shi
kuwa mutumin yana karba sai yayi murmushi. A nan ya
jawota inda motarsa. Yana bude motar sai dije ta leka
ciki. Ai kuwa a guje ta shige ciki domin ba kome in banda
abinci kala kala tare da irin cake din da takeso. Kwance
tayi ruf da ciki sai diba take tana kaiwa baki. Abinka da
sakarya batasan ko waye shi ba iyaka dai daga ganisa ta
shige motarsa. Koda yake ba laifinta bane, tsananin
yunwa ce ta jawo hakan.
Shi kuwa mutumin da ganin hakan sai ya tsaya cak yana
kallonta. Haka dije tayi cin hauka har saida tayi tatil. Daga
nan sai ta fito daga motar tana gyatsa. Fitowarta keda
wuya sai kunya ta kamata ganin mutumin na kallonta.
" Amma fa na gode sosai." Ta fada tana dubansa.
Shi kuwa murmushi yayi ba tare daya tanka ba. " Wai a
wannan gari kake?" Dije ta tambaya amma shiru bai
tanka ba. " Ni sunana dije kaifa?" Anan ya kara yin
murmushi baice kome ba. Anan dije ta fara tunani wai ko
baya magana ne. Can sai taga ya shiga motarsa. Anan ya
juya ya nufi inda ya fito. Haka dije tabi wannan mutumi
da kallo har ya bace mata da gani. Ita kuwa sai ta dawo
gida cikin mamaki. Haka kuma taja bakinta ta tsuke ba
tare da fadawa kowa ba harda mairo da take kawarta.
PAGE 50
A yau dije tayi bacci mai dadi domin tunbinta a cike yake.
Taji mutukar dadi na ganin wannan mutumi domin ya
bata abunda takeso.Iyaka dai abunda ke damunta shine
wai kuwa yana magana? To idan yana magana me yasa ya
kyaleta a ranar. A haka dai ta cigaba da tunanin cewa kila
baya magana. Saboda wannan abu daya faru sai dije ta
maida rafi wurin zuwanta a duk lokacin da takejin yunwa.
Sai dai bata zuwa sai a cikin dare domin mutumin a
lokacin ake ganinsa. Bata fadawa kowa halin da take ciki
ba domin ganin take idan ta fadawa su umma sukan iya
hanata zuwa. A kan hakan ne ta tsuke bakinta ko babbar
kawarta mairo bata fadawa ba.
A duk lokacin da taje yakan bude mota ta shiga har sai
tayi tatil da abinci. Kuma a duk lokacin da tayi masa
magana baya amsawa sai dai murmushi. A kwana a tashi
har suka fara sabawa da juna. Wataran idan tazo yakan
rungumeta yana mata wasa amma kuma baya magana.
Dije bata damu da duk abunda zai mata ba in har zata
cika cikinta. A wannan dalili takan bashi hadin kai suyi
wasansu daga nan kowa ya kama gabansa.
Wata rana a cikin dare bayan dije ta iso wurin. A
mamakinta bata ganshi ba. Sai da tayi tsayin kusan minti
talatin sai gashi ya zo. Ai kuwa kai tsaye ta shiga motar.
Shigarta keda wuya sai ya kunna ya tayar. Dije tayi
mamaki ko ina zai je da ita. Taso ta tambayeshi amma
data tuno baya magana sai ta tsuke bakinta. Iyaka dai ta
jawo kayan abinci sai kalaci take cikin jin dadi. A duk
lokacin da suka hado ido sai yayi mata murmushi saboda
hakan dije bata damu ba iyaka dai a tunaninta yana
yawon shakatawa ne da ita. Abu kamar wasa sai ga tafiya
tayi nisa har suka fita cikin garin dije bata ankara ba sai
faman shagali take da su cakes. Anan suka hau titi sai
gudu yake a tamanin. Sai da sukayi tafiya mai nisa sannan
dije ta dawo cikin hayyacinta. Anan ta gane cewa ba cikin
garinsu ne ba. Saman titi ne suke tafiya sai dazuzzuka
masu ban tsoro dake a gefen titin.
PAGE 51
Anan dije ta fara damunsa daya tsaya amma ina ko
kallonta bayayi. Tuki yake iya karfinsa. Ita kuwa sai ta fara
ihu tana bugunsa amma yakiji. Da dai taga bazata fita ba
kawai sai ta rike sitarin. Anan motar ta fara kalan keluwa
sai da kyar ta tsaya. Ai kuwa motar na tsayawa dije ta fito
a guje. Anan tayi arba da wasu mutane masu kirar
samudawa. Kowanensu sanye da bakaken kaya sun
lullube fuskarsu da bakin kyalle. Can sai ga mutumin
shima ya fito. Dije na ganinsa sai ta sheko ta rungumeshi
a tsorace. Shi kuwa hannunsa yasa ya bugeta can gefe.
Anan taga an miko mishi takobi. Shi kuwa cikin sauri ya
nufota. Dije na ganin haka sai ta rantama a guje cikin
dajin. Su kuwa masu bakaken kayan sai suka dafa mata.
Anan aka fara tsere tsakanin dije da wadannan mutane.
Sai halbota mata kibiyoyi suke amma duk a banza domin
bata samunta.
Suna cikin gudun ne sai suka tsaya wuri daya suna dube
dube. Wato dije ce ta bace musu da gani basusan inda ta
shiga ba. Sai da suka dade suna binciken wajen amma ko
duriyarta babu. Daga nan sai suka nufi wata hanya suka
tafiyarsu. Can sai ga dije ta fito. Ashe dama cikin wani
rame ne ta shiga sai ta sanya ganyayyaki a sama yadda ba
kowa zai gane akwai mutum a wurin ba. Cikin dajin ta
kara shiga sai faman gudu take tana mamakin irin
wadannan mutane da kuma abunda yasa sukeso su
kasheta. Bako shakka akwai ban mamaki a tattare dasu
domin gudunsu daban yake da sauran mutane. Idan suna
gudu kai kace akan iska ne suke gudu.
Haka dije ta cigaba da gudun a cikin daji sai da tayi nisa
sannan ta tsaya tana haki. To anan ne ta kara duban dajin
taga irin bishiyoyin dake ciki. Wato dajin ya kasance
wangameme mai ban tsoro. Ko ina itace ne dogaye masu
furanni. Haka dije ta cigaba da tafiya tana sauri ko zata
samu taimako. Sai da tayi tafiya mai nisa amma ko
kadangare bata hadu dashi ba. To anan tsoro ya fara
dabai bayeta domin duhun ya tsananta. Dakyar take
ganin inda take takawa.
PAGE 52
Dije tayi mutukar dana sanin kin yin hakuri halin gidansu
na talauci wanda ta tsinci kanta a ciki. Gashi yanxu ta jefa
kanta ga mahalaka. Babban abunda ke damunta shine
can a gida ba wanda yasan inda take balantana a kawo
mata dauki. Tana cikin tafiyar ne saita hango an kunna
wuta a wani wuri. Da sauri ta nufi wurin inda ta isko
mace da namiji a zaune sai firarsu suke. Tana isowa sai ta
fara yi musu bayyani cewa su taimaketa za a kasheta. To
abunda ya bata mamaki shine suma wadannan mutane
basajin hausa kamar wancan mutumin daya daukota.
Wani yarene suke wanda batasan kome suke fadi ba.
Koda sukaga dije a galabaice ta zube kasa sai nishi take
dai dai. Sai macen ta tallabota tana mata fifita. Dije najin
suna magana amma batasan abunda suke fadi ba.
Anan suka kashe wutar dakeci. Ita kuwa macen na rike da
dije har saida suka kai wata yar bukka. A cikin bukkar an
gyarata sosai da kayan alatu. Anan ta kishingida dije
saman gado sai fita take mata. Ana cikin hakane sai ga
wata mace ta shigo bukkar. Anan ta kurawa dije idanu
bata ko kyaftawa. Daga nan kuma sai suka fara wata
magana da wannna matar dakema dije fita cikin wani
yare. To bayan sun kare sai matar ta juya ta fita. Haka
shima namijin sai ya bita. Anan aka bar dije da mai mata
fita.
Bayan wani dan lokaci sai dije ta farfado. Hankalinta ya
fara dawowa. Anan ta kalli matar amma batace kome ba.
Ita kuwa matar sai murmushi take mata. To anan ne ta
lura da zanen macijin dake hannunta irin na wancan
mutumin data hadu dashi a rafi. Anan dije taja da baya a
tsorace. Ita kuwa matar na ganin haka saita rungumeta
tana sumbatar ta. Tun dije na kokarin ta kubce har takai
ta tsaya wuri daya saboda abunda takeji yana shiga. Anan
ta mimmike kafafuwanta saman gado sai wani nishi take.
Ita kuwa matar sai matsar jikinta take duk inda taga
dama. Daga nan dije bata kara sanin abunda ya faru ba.
PAGE 53
Firgigit ta farka. Anan ta ganta cikin wani daki mai duhu
an daure kafafuwanta da hannayenta. A mamakinta ba a
cikin bukka bane. Hasalima shi wannan daki kamar a
cikin gida yake, sai dai shi wannan wane gida ne kuma ya
akayi tazo nan? Anan dije ta rasa abunda ke mata dadi
domin a halin yanzu tana tsaka mai wuyar sani. Batasan
inda takeba kuma batasan abunda ke iya faruwa da ita
ba. Bako shakka hakuri shine maganin zaman duniya, duk
wanda bai yi hakuri ba to bazaiga hakuri ba. Wato da ace
dije tayi hakurin talaucin da suke ciki da irin hakan bai
faru ba. Amma sai gashi kwadayinta na son abun duniya
ya kaita ya baro.
Bude dakin akayi a hankali. Can sai aka hasko mata fitila.
Tanaji sai taga an tallabota an azata saman kujera mai
tayu. Ita wannan kujera da an turata sai ta fara tafiya. Ai
kuwa anan aka fara tura dije saman kujerar sai ihu take
tana neman taimako. " Waye kai? Me kakeso a gareni?"
Haka ta cigaba da fadi amma ko jinta bayayi. Da sauri ya
nufi wani lungu da ita. Sai da yayi tafiya mai nisa sannan
ya tsaya a kofar wani daki. Anan dije ta tabbatar da cewa
lallai yanzu a cikin wani gida ne ba bukka ba. To amma ya
akayi taxo gidan?
Bayan sun shiga dakin ne sai ta ga cewa ashe mutumin
nan ne wanda yayi sanadiyar shigowarta dajin. Anan ta
kura masa ido sai harararsa take. " Macuci azzalumi me
kake shirin yi dani, kuma nan inane ka kawoni." Haka dije
ke fadi cikin bakin ciki amma shi ko damuwa bai yiba
iyaka kallonta jikinta yake yana murmushi. Anan yazo
yana shafa fuskarta a hankali. Yana cikin hakane dije ta
gatsa masa cizo. Sai da yayi kara sosai sannan ya fadi. Ai
kuwa tashinsa keda wuya ya gabza mata mari sai da ta
kife saman kujerar. Daga nan ya jawota ya aza saman
kujerar. Cikin fushi ya kara gabza mata wani marin. Daga
nan kuma sai ya dunkule hannu yana dukanta kamar
bazai barta ba. Fuskarta ya nunnuga sai da ya mata jina
jina kafin ya fita dakin cikin fushi. Anan yabar dije cikin
rauni mai yawa jini sai tsiyaya yakeyi. Kai da gani kasan
taci wuya domin gaba daya fuskarta ta canza ko ina sai
jini ke fita.
PAGE 54
Haka dije taci gaba da zama a wannan daki sai nishi take
dai dai. Saida aka dau lokaci kawai sai ga matar nan data
gamu da ita cikin bukka ta shigo. Anan matar tazo kusa
da ita. Hannuta rike yake da wani karamin akwati. Cikin
murmushi matar taxo kusa ga dije. Daga nan saita bude
akwatin ta dauko wani kyalle. A hankali tabi fuskar dije
tana shafe jinin dake tsiyaya a fuskarta har saida ta tsanar
da ita tsab. Tana kammalawa sai ta fita. Fitarta keda wuya
sai ga wannan mutumin na farko ya shigo. Cike da
murmushi ya shigo yana duban ta. Anan dije ta done kai
ko kallonsa batason yi. Shi kuwa sai ya tallabo fuskarta ya
kura mata ido. Can kuma sai ya kyaleta. Wata yar
karamar yukace ya fito daga jikinsa. A kirji ya soka mata
sai da tayi kara sannan ya fito da yukar. Anan ya jawo
yukar a gefen jikinta har saida ya keta mata riga yadda
ana ganin kome a fili.
Jifa yayi da yukar sai kallonta yake kai kace mussa taga
nama. Hannunsa ya dora saman jikinta sai shafawa yake
ko ina. Kafin kaceme sai ya jawota jikinsa. Ita kuwa dije
ba yadda ta iya domin a daure take. Da mutumin yaga
kamar idan tana daure bazai iya yin abunda yakeso ba sai
ya dauko yukar ya kwanceta. Anan dije ta kyaleshi sai da
ya shagala yana warwasawa kafin ta manna masa cizo a
kunne. Ihu ya kurma yana dukanta ita kuwa taki sakinsa.
A haka suka fara mulmule mulmule cikin dakin amma
dije taki sakin kunnen saida ta guntule shi. Daga nan saita
tashi ta dauko kujerar nan mai tayu. A kai tayita rafka
masa har saida ya suma. Anan ta fita dakin a guje ta
barshi cikin jini.
Gudu take iyakar gudu amma ta kasa ganin karshen gidan
domin ko ina lungu ne. Tana cikin gudun ne saita jiyo
ihun wasu a cikin wani daki. Sai dai ba damar shiga
domin wasu samudawa ne rike da makamai a kofar dakin
sai kai da komo suke. Anan dije ta labe tana tunanin
yadda za a yi ta shiga dakin domin ganin ko su waye ke
ihu. Can sai taji kamar an yi magana a cikin dakin. Kawai
sai samudawan suka shiga ciki dama su biyune. Ita kuwa
dije sai ta bisu jikinta na karkarwa.
PAGE 55
Labewa tayi bayan wata kujera tana duban abunda ke
faruwa. Wasu mata ne biyu aka sarkafe a gina jikinsu duk
jini ne. Sai wani mutumi mai siffar ban tsoro rike da
gatari yana magana da wadannan samudawan da suka
shigo ciki. Wadannan mata duka yan garinsu su dije ne.
Dayar itace nana wadda suka hadu da ita a gulbi tana
wanka. Dayar kuwa abokiyar nana ce, akan kirata da
ladiyo. Anan mamaki ya kashe dije koya akayi sukazo
wannan gida? Tana kallo sai taga mutumin ya ajiye
gatarin yabi wadannan samudawa biyu suka fita tare.
Fitarsu keda wuya sai dije ta fito bayan kujerar ta nufi
wurin su nana. Ai kuwa nana na ganinta sai ta fara ihu a
tsammaninta mutumin ne ya dawo. " Kiyi shiru mana
kada suji. Bari na kwanceku." Inji dije.
Anan nana ta jiyo tana kallonta. " Dije, me ya kawoki
nan?" Nana ta tambaya." Yanzu ba lokaci bayani bari sai
mun fita." Dije ta bata amsa. Anan ta dauko gatari ta sare
kacar da aka dauresu da ita. Sai gasu sun fado kasa
timmm. Saida yar karamar kura ta tashi saboda nana mai
jikice sosai. Ita kuwa ladiyo ko motsi batayi saboda ta
dade da suma. Anan nana ta goyata. Ita kuwa dije sai ta
dauki gatari ta jagoranci tafiyar. Gudu sukeyi dakyar suna
lalube a cikin duhu. Gidan ya kasance katon gaske sai
kace gari. Ga lunguna birjik. Dakuna kuwa ba a magana
domin ko ina sune hagu da dama.
Suna cikin gudun ne sai suka iso wani wuri da mutane
sunyi sahu sai tafiya suke suna waka. Dukkaninsu sun
sanya kaya jajjaye. Ba a jin abunda suke fadi cikin wakar
domin wani yarene suke fadi. Kayan da sukasa sun
lullube dukkan jikinsu yadda ba a ganin kome in banda
fuskarsu. Anan su dije suka labe suna kallon ikon ALLAH.
Mutanen hade suke maza da mata sai tafiya suke a cikin
sahu. Shi kuwa shugaban tafiyar shine a gaba yana
jagorantarsu. Mutanen bari biyu ne. Rabi a gefen dama
rabi kuwa a hagu. Sai shugaba a can gaba. To a tsakiyar
wani irin makeken maciji ne wanda tsawonsa yafi a kirga.
Haka kuma fadinsa sai kace daki. Macijin na tafiya cikin
kasaita yana wangame baki.
PAGE 56
Anan dije ta gane cewa wannan macijin shine aka zanawa
wannan mutumin da ya kawota dajin. Kuma irinsa ne ta
gani a hannun wannan matar ta cikin bukka. To indai
hakane kenan wannan maciji alama ne na cewa
kungiyarsu daya. Bayan wadannan mutane sun wuce sai
su dije suka bi wata hanya sai faman gudu suke ba
kakkautawa. Basuyi wani nisa ba sai nana ta gaji. Anan ta
ajiye ladiyo domin ta huta. Ita kuwa dije sai ta kasa zama
ta kasa tsayi. Iyaka taje ta dawo gabanta sai faduwa yake.
Kai da gani kasan a cikin tashin hankali take.
" Wai meye wannan abu? Ke bazaki zauna ba?" Nana ta
tambaya.
" Ai bazan iya kome ba a yanzu har sai mun fita daga
wannan gida." Dije ta bata amsa.
" To wai ke yama akayi kika shigo wannan bala i alhali
bakya yawo?" Nana ta tambayeta.
" Hmm. Da kenan. Yawo yanzu kam......" Anan dije tayi
shiru domin jin wata mata ta fito daga wani daki sai tafiya
take kwas kwas kwas. A haka matar tabi ta wurinsu ta
wuce amma bata gansu ba domin sun manne jikinsu a
bango. Gashi kuwa wurin tsananin duhu ne dashi. To
bayan matar ta wucene sai suka tashi suka nufi wata
hanya. A wannan lokaci ba gudu sukeyi ba. Sassarfa ce
sukeyi domin sun fara gajiya da gudun. Har dai nana da
take da jiki baya bari ta motsa sosai.
" Gaskiya na gaji da goyon nan fa." Nana ta fada.
" Ki daure mana tun da bazamu yar da ita ba. Mucigaba
da zaga yawa watakila mu samu hanyar fita." Inji dije.
Suna cikin maganar sai ladiyo ta fara tari. Anan suka ajeta
gefe suna girgizata ko zata mike. Ai kuwa cikin sa a sai ta
bude idanu.
" Kai, meke faruwa ne?" Ladiyo ta tambaya.
" Yanzu dai ba wannan ba. Tashi mu cigaba da tafiya." Inji
nana.
"Hala ina su lami?" Ladiyo ta tambaya.
" Bamu sani ba. Amma mu bincika ko ma gansu." Nana ta
kara fada.
" Au, ashe baku kadai bane. Kunada yawa kenan?" Cewar
dije.
" Ai su biyu kawaine bamu gani ba. Wato lami da rabi."
Inji nana.
" To me zai hana mu bincika ko zamu gansu?" Inji dije.
" Nima abunda nake shirin cewa kenan." Cewar nana.
PAGE 57
Anan suka tashi su uku sai faman sauri suke ba mai yarda
a barshi baya. Suna cikin tafiyar ne sai sukaji motsin wasu
a gabansu. Anan suka manne a gina suna jira suga ko su
waye. Can sai ga wasu samudawa sun tallabo wasu mata
biyu akan kafada. Matan ko motsi basayi kamar matattu.
Bayan sun wucene sai su dije sukabi bayansu domin suga
ko su waye. Haka suka cigaba da tafiya cikin sanda idan
sukaga kamar zasu juyo sai su labe. Cikin wani daki suka
ajiye matan daga nan suka fito suka tafiyarsu. Su kuwa su
dije da karfi suka fada cikin dakin. Cikin sa a suka tarar da
wadanda suke nema wato lami da rabi. Sai dai ita lami rai
yayi halinsa domin har sun yanke wasu sassa na jikinta.
Anan nana ta fara kuka na tausayawa zuwa ga abokiyarta.
Su kuwa su dije sai faman lallashinta suke. Sai da kyar
suka ciyo kanta.
" Hamir ya cucemu, ya cucemu daya kawomu wannan
gida." Nana ta fadi cikin dana sani.
" Hamir kuma? Wai har yanzu baku daina wannan sana a
taku tabin maza ba? Kenan a can kuka hadu dashi." Dije
tace tana dubanta.
Anan nana tayi shiru batace uffan ba. Ita dai tasan
abunda ta aikata ita da kawayenta wanda shine yayi
sanadiyar kawosu wannan gida. Anan suka tallabo rabi sai
fifita suke mata. Sai da suka dau lokaci sunayi sannan
hankalinta ya dawo jikinta. Suna ganin ta mike sai suka
nufi hanyar fita daga dakin. To kafin su fita ne sai sukaji
takun wani kamar yanason shigowa ciki. Cikin sauri suka
lallabe suna jiransa. Ai kuwa yana shigowa suka yi masa
taron dangi. Mai bugu nayi mai cizo nayi har suka kaishi
kasa. Anan suka fita dakin suka barshi kwance cikin jini.
A wannan lokaci tafiya suke kamar wadanda aka yiwa
charge domin duk wanda suka hadu dashi to sai sun
masa jina jina. Sai dai idan sukaga mutanen nada yawa to
sai su labe har sai sun wuce. Amma daga mutum uku
zuwa kasa duk wanda suka hadu dashi to sai sun ji masa
rauni. Haka suka cigaba da gudu a cikin gidan amma ko
alamar karshe basu gani ba. Duk inda suka duba lungu
ne. Haka kuma dakunan gidan sun kasance daki cikin daki
har ba adadi. Wannan abu kan mutukar rudasu sai su
rasa shin wai gaba sukeyi ko baya.
PAGE 58
Wani lungu ne suka shigo. Tafiya sukeyi amma kamar a
cikin ruwa suke tafiyar. Sai daga baya suka gane cewa jini
ne ya cika lungun gaba daya kamar anyi anbaliyar ruwa.
Suna cikin tafiyar ne sai suka fara jiyo karagin wani abu.
Kai dagaji kasan wannan abu zaiyi ban tsoro domin wani
gurnani ne yake marar dadi. Suna cikin tafiyar ne sai
sukaji ladiyo na ihu. Anan ta fadi kwance. Wani abune ya
laulaye kafarta sai janta yake iyakar karfinsa. Anan su dije
suka kai mata dauki suna jawota amma abun yaki
sakinta. Saboda tsabar karfinsa ya janyeta. Anan sukayi
tsaye a tsorace kowane sai kalle kalle yake. Can sai sukaji
an jefo musu wani abu. Ai kuwa suna dubawa sai sukaga
sassan jikin ladiyo an yankata guntu guntu. Kai daban,
kafa daban. Kome daban. Ganin wannan abu ya mutukar
tsorata su. Ita kuwa dije batasan lokacin data yar da
gatarin data dauko ba. Anan suka juya baya da nufin
gudu. Kafin suyi nisa sai sukaji suma an laulaye
kafafuwansu.
Anan aka fara jansu suna ihu sai faman rike gina suke. Ba
yadda basu yiba domin su tsira amma ina sai da abun ya
janyosu. Ai kuwa suna kawowa gab da abun sai dije ta
gane cewa wannan macijin ne da suka gani dazu shine ke
jawosu da halshensa. Anan ya wangame baki da nufin
suna fadawa yayi musu cin gyada. To kafin su kai ga bakin
nasa ne dije ta wankala ta dauko gatarin data yar, saida ta
saita da bakin shege ji kake kimissss. Anan macijin yayi
kururuwa ya balla a guje. Daga nan sai suka tashi suna
nishin wuya. Wata hanya ce suka nausa suna tafiya
dakyar. Bayan sun dan yi nisa sai suka kai ga wata
katanyar kofa. Anan suka daga kai sama amma basuga
karshen tsawonta ba. Kofar ta kasance mai karfin gaske
domin karfe ne aka narka kafin ayita.
Ba yadda basu yiba domin ganin sun bude kofar amma
gam taki budewa. Saboda haka sai suka yanke shawarar
su hau samanta. Ai kuwa nan take suka dane dama
tanada matattakala. Sai da sukayi nisa saman kofar.
Kadan ne babu su kai ga karshe sai ga masu bakaken kaya
sun iso wurin. Ko wane rike yake da kwari da baka. Sun
lullube fuskarsu da bakin kyalle ba a ganin kome. Anan
suka fara sakar musu ruwan kibau su kuwa su dije sai
suka kara kaimin saurinsu.
PAGE 59
Duk da kasancewar nana mai jikice amma haka ta
takarkare bata yarda an barta bayaba. Ita kuwa rabi a
wannan lokaci ta fara gajiya sai nishi take dakyar. Wasu
daga cikin masu bakaken kayan sai suka dane kofar suna
bin sawun su dije. To a wannan lokaci ne aka sako wata
kibiya. Cikin rashin sa a ta shige hannun rabi. Anan tayi
kara ta saki kofar amma kafin ta fado sai nana ta rike ta
da hannu daya. Anan nana ta nuna mata data daure su ci
gaba. Can kuma sai aka kara sako mata wata kibiya. A
wannan lokaci fadowa kawai tayi domin kibiyar ta huda
wuyanta. Su dije na kallo amma ba yadda suka iya. Haka
suka tsallake suna jimamin rasa abokiyarsu. Anan suka yo
kasa sai taka matattakalar sukeyi har suka kawo kasa.
Daga nan suka diro. To

Book Chapters
Chapter 1Chapter 2Chapter 3Chapter 4
Chapter 5
Chapter 6

Please Login or Register in order to submit comment