Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
1 / 6
An dauko wannan littafi daga shafin https://taskarnovels.com.ng ku ziyarci shafin na https://taskarnovels.com.ng domin samun kayatattun littatafan hausa kama daga kan na yake yake dana soyayya Marubuci ko marubuciya zasu iya turo mana da littatafansu mu dora masu a shafinmu kyauta don masoyansu su rika Downloading a online, Sannan marubuta zasu iya turo mana da tarihin rahuwarsu da tarihin rubutunsu, dama sharhin littatafansu don masoyansu su gani kuma su karu da hakan Domin turo mana da littafi ko tarihin rayuwar marubuci ko marubuciya sai ayi mana magana ta whatssap da wannan nambar +2348140419490 A lura dakyau - kyauta muke saka littafi a shafinmu bama amsan ko sisin marubuci, duk wanda ya amshi kudinku da sunanmu babu ruwanmu, Alura dakyau - manazarta bama tura littafi ta private ku dena binmu private kuna neman mu tura maku littafi, duk mai bukatar littafi yaje website namu Alura da kyau - Littatfanmu suna fitowa cikin manhajoji uku ne PDF,TXT da DOC amman munfi amfani da PDF da TXT masu amfani da wayar android ko tablet ko computer zai fi kyau ku riga dauko PDF da DOC Masu amfani da kananan wayoyi java ko mara java TXT zakuna zaba don shine daidai wayarku This hausa novel was uploaded and downloaded from https://taskarnovels.com.ng You can download more hausa novels there Also you can send us your novel to upload it in our website for your fans to download it online It is free we do not charge for uploading novel Also if you are an Author be it online or Non online you can send us your biography including your book summary,commentary and others via this number +2348140419490 its free we do not charge for our services Note that - we do not charge for our services we uploaded novels and posted biography free, any person that collect your money in our name is your fault do not blame us Note that - pls readers stop calling us and be asking us to send you a novels we are not sending novels through whatssap or private our novels is public at any day, any time you can visits our site and download it Note that - our ebooks came as PDF,TXT or DOC format but the popular format are PDF or TXT, those with android or tablet or pc we suggest you to download PDF or DOC those with java phone or non-java phone we recommend you to download TXT This Novel is downloaded from https://taskarnovels.com.ng to download more hausa novels visits our site at www.taskarnovels.com.ng For feedback and support Facebook : https://facebook.com/taskarnovels Twitter : https://twitter.com/taskarnovels Telegram : https://t.me/taskarnovels *TSUMMA MAKUNSHIN CUTA* Wolf in sheep's clothing oumyasmeen Da sunan Allah mai rahama mai jin kai Dukkan yabo da godiya ya tabba ga Ubangijin talikai ya Ubangiji ka bani ikon rubuta dai-dai. GARGADI gargadi ban yarda wani ko wata su yi amfani da daya daga cikin shashi na littafin nan ba ta ko wacce siga indan kunne yaji jiki ya tsira Wannan littafin ƙirƙirarran labari ne duk wanda ya ga yayi dai-dai da rayuwar sa to ya dauka arashi ne. Bismillahir ramanir rahim Ina meson logo ko invitation card To ga dama ta samu Werleedert graphics design ta zo muku da graphic design na ban mamaki Invatation card VEDIO invatation Logo Banner Poster Menu Acount sticker Graduation stickers Business sticker Save the date Business flayer Birthday flayer Engagement Event program invatatin Walimah invatation Wedding invitation Vedon invatation Zaku neme ta a kan wannan number +234 901 257 6569 Episode 1 Wata iriyar iska ke kadawa garin yayi ni'ima abinka da lokacin damuna ga kuma sanyin yammaci gyara kwanciyar ta tayi tana kallon waje tana tunanin anya kuwa yau ba za'a yi ruwa juyawa tayi tana cewa ai ina zaune a gurin nan idan naga an fara yayyafi na ɗauke masa kayan sa rufe idanuwan'ta tayi bacci na fusgarta a haka har ya kwashe ta. lokaci ɗaya ruwa ya kece kamar da bakin kwarya da sauri ta tashi tana zare idanuwanta tayi fiki fiki ga kayan ya ZAHID nan a zube akasa farare ne tas amma saboda ruwan da ya kece ga kuma akuyoyin nanne sun dawo daga kiwo suna neman malaɓa sun turmusa mai su sunyi wani irin baki ga rariyar bayi ta toshi dazu yake cewa idan ya fita zai nemo me gyara ya duba yaga me ya toshe musu ita sun hadu da kwatar bayi da ƙasa sun koma launin milk irin dark milk din nan me kama da ruwan ƙasa kuka Areej ta saka domin tasan yau me rabata dashi sai Allah ga nanne bata nan ta tafi ƙauye anyi mutuwa. wata ƙila ma ba yau zata dawo ba rasa ina zata saka kanta tayi taji dad'i dif ruwa ya ɗauke dafe kirji tayi jin alamun tafiya daga soro tamkar wata munafuka ta leko kan'ta ido hudu sukai dashi yana sanye da riga da wando jeans shi mutum ne me kyankyami dan haka ya shiga cewa joud joud tamkar wata wacce ake tuhumar ta da laifin kisan kai sai share gumi take tace '' sun tafi makaranta basa nan.., lokaci ɗaya ka kalli hanyar bayi farin gani yayi da kayan sa da suka koma wata kala abin kyankyami bazai iya mai da kayan nan jikin sa ba cikin takaici yace '' ke zo..., jikin'ta ya soma rawa ta zo gaban sa ta tsuguna tace '' gani.., ɗauke ta ya yi da mari sai da ta kifa kuka ta saki cikin ɗacin rai yace '' kina cikin gidan nan dan tsabar rashin kula da abin da ya dace ki bar min kayana suyi haka maza dauko su ki saka ruwa da hypo ki wanke su.., Cikin kuka tace '' bamu da hypo ɗazu najwa ta wanke mana kayan makarantar mu.., ganin irin kallon da yake mata da sauri ta hadiye sauran zancen ta ta tashi ta fara ɗiban kayan ta zuba a botiki juyawa yayi ya fita. tana kuka tana wanke kayan nan nanne bata , bata wanki joud ce ke yi ko najwa hannun ta ne ya fara ciwo amma bata dena ba jin sallamar nanne da sauri ta ɗago ta tawo a guje ta rungume ta , ta saki kuka cikin tashin hankali nanne tace '' auta waya taɓa min ke.., kuka ta ƙara rushewa dashi tace '' yaya ZAHID ne na kwanta bacci ban sanu ba kayan sa suka zobo suka ɓaci..., share mata hawaye tayi tace '' kiyi hakuri kinji auta zo mu shiga daki.., binta tayi har suka shiga daki zama tayi ta cire mayafin'ta tace '' yau baki wanka ba ko.., zumburo baki tayi ta kauda kan'ta ajiyar zuciya nanne ta saki tace '' auta auta kazanta ko tun kina jaririyar ki bakya son wanka bakya son a taɓa miki kanki Areej rayuwa za tayi haka kuwa..? wata ran fa gidan wani zaki maza tashi ina da ragowar ruwan zafi a flask nayi miki wanka na wanke miki kai tunda bakya son zuwa gidan kitso ni nayi miki., rufe bakin ta ke da wuya Areej ta saka kuka harda ɗora hannu aka ta saki ihu sosai take wage baki take zuba ihu nanne zuba mata ido tayi tana kallon ta , tashi tayi ta fita tsakar gida tana shure shure ta zauna a cikin ruwan nan cikin sauri aunty jamila ta shigo tace '' Areej lafiya kike kuka..?, ina nanne ta dawo ne ...?, da hannun ta ta nuna mata daki nanne fitowa tayi tace '' jamila mun wuni lafiya..?, nanne ina wuni kim dawo lafiya ya hakuri...?, cewar jameela. Alhamdulilah tafiya qalau hakuri da godiya daga cewa ta tashi nayi mata wanka shine ta zauna tana wannan uban kukan yawa wanda na dake ta.. Nanne ta faɗi haka cikin jimamin halin Areej ɗazu ma tana bacci ta fita da ace idon ta biyu tabbas sai ta bita irin yaran nan ne masu ƙawa zuci bata iya zuwa ko ina kullum tana katarar ta bata yadda da kowa sai ita. Aunty jameela tace '' to ai wannan ne sauki ne ZAHID yana waje bara na kirawo shi ke wacce iri ce a rana sai kiyi kuka yafi sau bakwai.., dif tayi jin ance za'a kirawo ZAHID ta share hawayen ta tace '' uhmm aunty jameela Wallahi bata yi min wanka a hankali ta dinga dirje min naman jiki na kuma jiya har ganyen magarya ta tai min tsarki dashi kuma da zafin sa ta wanke min kaina dashi shine yau ma wai zata wanke min, dan Allah ba ana yin kwaskwarima ba tai min mana dole sai tai min wanka.., ubanki za ayi miki ba wanka ba wankin da na saka ki kenan kika zauna kina yiwa mutane fitsara zaki tashi ko sai nayi ball dake ina wankin da kikai..?, dashi tayi jikinta duk ruwa ta labe a bayan nanne tana zare idanuwanta Nanne tace ''sannu tunda ta zama tamola ai dole ka buga kwallo da ita,zahid wallahi ka kiyaye ni wannan yar yarinyar zaka saka wanki ka taɓa ganin ta wanke ko da da pant din'ta ne..? ƙasa yayi da kansa yace '' nanne idan.., kafin ya ƙarasa tace '' bana son jin komai yi tafiyar ka.., Aunty jameela ta dunkure mata kai tace '' yar yar baka me kirar tifa.., kuka ta saka tana share hawayen ta nanne tace '' kiyi shiru auta ka'aba ma baka ce da masu zubin taliya yar murji gwara kosasshen mutum.., dariya aunty jameela tayi tace '' nanne dan Allah ki dinga rufewa yar nan baki kukan ta yana tada min me kano..., taɓe baki nanne tayi tace '' aini a gidan nan ba sarka na sakawa kowa ba dan haka kofa a buɗe take duk me son fita ya fita wannan yarinyar tawa tafi karfin ku.., murmushi aunty jameela tayi tace '' uhmm uhmm nanne ba'a san inda rana zata fadi ba .., zaro ido nanne tayi tace '' wani a'a wallahi sai dai a wani gurin badai anan ba kuje can ku ƙarata.., wanke kafarsa ya gama yi sannan ya dauko mukullinsa dakin sa a zaune yake ya juya ya bude dakin sa ya shiga bayan ya ajiye ta kalminsa a kofar dakin nasa. yana shiga ya kunna fitilar wayar sa da yake dakin yana da duhu sai kamshi ke tashi a hankali wayar sace tayi ringing da sauri ya daga ganin masoyiyar sace abar kaunar sa karawa yayi a kunne ta sakar mai kukan shagwaɓa lallaɓata ya fara yi yana cewa '' sweet me ya faru wane ya taɓa min ki sai inda karfina ya kare..?, wani kukan ta kara fashewa dashi tace '' sweet kaza nake son ci wallahi yau tun da safe nake jin kwaɗayi gashi mama bata da kudi ga kudin ankwon nan shiru kuma kasan mun kusa bikin bayan sallah ne ga zumi na karatowa.. Dan shiru yayi ya shafa sumar kansa yace '' Wallahi a dai yanzu bani da kudin da za kici kaza saidai kudin da nake hadawa zan baki na anko idan shi zan baki sai na baki kinsan lamarin rayuwar ne sai addu'a ba sosai ake samu ba idan kinga muna samo lokacin jarabawa ne ta ESSCE za azo a siya secrect card kinga ga makaranta da nake zuwa bana na samin damar zama a CAFÉ din sosai ba kamar da ba., tamkar yana gaban ta , ta hade ranta tace '' zaka fara ko ..? ni wallahi na rasa me yake damuna mace kamata na tsaya ina soyayya da wanda idan bukatar dubu dari ce ba zai iya yi min ba .., tana gama fadar haka ta kashe wayar ta hankalin sa ne yayi masifar tashi yana mugun son juhud yar shuwa , Allah ya ɗora mai sonta duk da mutane da dama cewa suke jummai Dubai yar duniya ce ba zata taɓa bashi yar ta ba ajiye wayar sa yayi ya fito ko me ya tuna sai ya chanza kaya kawai da wanka zai yi da dauki wayar sa ya chanza takalmi ya leƙa tsakar gida nanne tana yiwa Areej wanka tayi tsit da ace baya nan da makota ma sai sun san da yin wankan nan ta gyara ko ina tsaf akuyoyin ta ma ta mai dasu gurin su idan ba kwana za kai a gidan nan ba , ba zaka taɓa sanin ana kiwon a kuyoyi ba da sassafe ake sakin su bayan an basu abinci da yammaci su dawo shigowa yayi yace '' nanne zan fita wa'yannan kayan a bawa wani na hakura da su.., da sauri Areej ta rungume nanne tace '' nanne rufe ni kar yaya ya ganni ba kaya., murmushi nanne tayi tace '' to shikkenan zan bawa Nabeel ya rage su daman naga kayan nasa sun fara mutuwa Allah dai ya buɗa muku ya dafa muku.., amin ya Allah yace juyawa yayi ya fita tace '' Allah ya tsare hanya amin ya ƙara cewa ya fita cikin sauri da yake gidan jummai Dubai dillaliya yana bayan gidan su dan haka cikin mintoci kalilan ya isa aika yaro yayi yace '' ana sallama da juhud.., ba jimawa yaron ya dawo yace '' wai tace ka shigo.., to yace ya shiga sallama yayi jummai da take zaune daga ita sai shimi ga tulin kayan mata da na shafe shafe a gaban ta , ta amsa tace '' wa'alaikis'salam a'a Abdallah kai ne..?, cikin jin nauyin ta ya durkusa yace '' ina wuni mama.., lafiya qalau mun wuni lafiya kaganni jin wannan iskar na tube na saka shimi kasan idan akai ruwa wani zubin gari zafi yake barin idan ba me yawa bane irin dai wannan wanda ya zo gangara.., kansa yana ƙasa yace '' haka ne wallahi ina juhud take..?, hmmm mutuniyar taka tana nan wai tayi fushi nace aikuwa zan kiraka takanas nayi maka faɗa ni da nake cewa abin nan duk ɗaya ne ai kwaryar sama ce take dukan ta ƙasa , idan bakai mata ba wazai mata..? ehyi malam Abdallah na hanata kula kowa saboda kai to kaga idan kuma kana hanata abubuwa nayi mata adalci kenan da na hanata kula kowa sai kai cewa nake ai wannan abu dan liman ne dana na'ibi na baka juhud halak malak kayi yadda kake so da ita shi ne zaka tila min kasa a ido. shiru yayi yana sauraran ta yace '' insha'Allahu zan gyara amma mama nina wallahi bani dashi bawai haka kurum na hanata ba jiya ma tsiran dubu hudu na siya mata yau to bani dashi.., yanzu malam Abdallah koni ai na cinye tsiran dubu hudu balle juhud wannan farar fatar da kake gani tana burge ka ba karamin kuɗi take ci ba me auren juhud sai me hali ko me karfin zuciya irin dai kai.., murmushin karfin hali yayi shi wannan son zuciyar ta shi yake hada shi da su dan mutunci suna da kirki amma akwai son zuciya ajiyar zuciya ya sauke yace '' hakane yanzu tana ina .., tana cikin daki juhud juhud fitowa tayi da wani material me tsada a jikin ta sai zabga kamshi take murmushi yayi mata tace '' shigo ciki mana yawa wani bako.., tashi yayi ya shiga zama yayi akan kujera yana bin dakin da kallo murmushi tayi tana murza zoben hannun ta tace '' duk fushin da nake dakai idan na kalle ka sai hankali na ya kwanta naji damuwata ta hayaye.., dan matsawa yayi yace '' ko zaki koma daga can.., ɓata rai tayi tace '' kamshin turare na ne be maka ba ..?, ah wallahi yayi min sosai kinyi kyau ya faɗa yana dauke kansa da ya fara juya mai yana tsoron sabawa Ubangiji amma tun ba yau ya lura ba tarbiyar juhud da tashi ta banban ta ita gani take ba wani abu bane waye warta ta danne ilimin addinin'ta amma a hakan gani yake zai iya gyara ta , ta koma yadda yake son ta. fita tayi ba jimawa sai gata da robar ruwa da ta lemo ta ajiye mai da glass cup tace "' bisimallah ka jika mako shin ka..," Alhamdulilah yace yana kallon ta sai wani bankaro mai kirji take gata daman ba karamar mace ba wannan abubuwan ne suke rudar maza suke mata layi. ɓata rai tayi tace '' mama mama.., da sauri mama ta shigo ashe wando ne a jikin ta three quarter kannan yaci kananun kalba ta ƙari tace '' juhud me ya faru kike min kiran hukuma ke kenan bakya girma..?, turo baki tayi gaba tace '' mama kinga wai ba zai sha ruwan da na kawo mai ba.., maida gashin ta baya tayi tace '' haba kai kuwa ZAHID yawa ba gidan ku ba kaki cin komai a duk lokacin da ka zo.., murmushi yayi yace '' bana jin ƙishi ne amma next time insha'Allahu zan tawo banci komai ba sai kunce shi wannan haka yake da ci.., ya ƙarshe maganar cikin barkwanci. dariya mama tayi tace '' a'a ba za mu gaji da kai ba., ta fada tana fita daga cikin dakin gyara zama yayi yace '' yanzu me kike so ayi.., far tayi da idanuwanta tace '' uhmm bani da wata bukata hankalina ya kwanta nagan ka daman na fadi haka ne domin ka zo nasa baka dashi, Allah dai ya buɗa maka ka samu abin yi, muyi aure.., cikin jin daɗin maganar ta yace '' amin ya Allah Nagode sosai Allah ya bar min ke.., murmushin jin dadi tayi tace '' amin ya Allah., hira sukai sosai sannan yayi mata sallama ya tafi, fitowa tayi tana danna wayar ta , ta zauna a kusa da mama tace '' mama yau zaki fita ne..?, gyara zaman kayan ta tayi tace '' a'a ba inda zani so nake yi kafin na tafi Maiduguri na siyar da wa'yannan kayayyakin to kinga kwana biyu ba wani kaya ma da aka kawo min kuma mutuwar auren nan yinta ake yi bara na kirawo hajiya shatu muji gurin ta ko da kaya kinsan an bani cigiyar kaya to wallahi bana so suga gazawa ta.., ajiye wayar ta tayi tace '' kuma fa hakane ni ma nan da anjima zan fita.., Hajiya jummai Dubai ta dauki wayar ta , ta soma laluben number hajiya shatu cikin saa ta shiga sai dai har ta gama ringing ba'a dauka ba tsaki tayi tace '' tsiya ta da Hajiya kenan wallahi sai ta tafi sabgar gaban ta , tabar wayar ta ba tare da ita ba yanzu karki yi mamakin tana gida bata dauke ta ba , ta fita.., Mama hakuri za kiyi bara na koma daki na kwanta kafin lokacin fitar tawa yayi juhud ta faɗa tana tashi daga zaman da tayi shiga cikin daki tayi ta kwanta ruf da ciki wayar ta , ta dauka tana dannawa gajiya tayi da danna wayar ta ɗaga katifar ta , ta dauko wata kwalba buɗe ta tayi ta kafa a bakin ta tas ta shayen ta ko guntu bata bari ba kwanciyar ta , ta gyara ta limshe idon ta da yake mata dishi dishi cikin yanayi na mutuwar jiki tace '' mama idan karfe tara tayi ki tashe ni., ta komar da idon ta , ta rufe wani bacci me dad'i ya kwashe ta. Wannan kenan. shigowa yayi yana cije lips din'sa fuskar sa duk yanka wata yar ƙaramar huka ce a hannun sa nanne da take madafa ta leƙo tace '' a'a hafizu yau kai ne a gari..?, Cikin yanayin rikakkun yan daba yace '' eh wallahi nanne me zan samu kinga ciki na yawa anmin yasa ni wallahi ba ka fito ba daga gidan yarin nan abincin ma da zaka samu kaci cikin kwanciyar hankali babu sai an tada kura.., cikin mamakin kalaman sa nanne tace '' kai hafizu yanzu abincin kurkukun ne yafi na gidan mahaifin ka..?, harshe ya zaro ya lashi hukar hannun sa yace '' billahilazi yafi na nan gidan har fa dabge ake mana ke ba ra in tela miki Lokacin da na tafi lagos nanne tamu ta gargajiya me cika min cikina alkur'an kare ake ɓangare mana yaji kayan hadi ji za kiyi kamar kina cin ta wahaidu kazar larabawa idan kuwa na zauna a gu ba wanda ya isa ya zauna a buga caca kai bariki tayi a rayuwa ke rayuwar agege karkashin gada ba abin da ba'a samu idan dare yayi mu bazaza makabartu sabuwar gawar da aka kawo mu tone tsinanniya tas mu kwashe yan kuɗaɗen mu idan kuma babu mu dauki kaya sai kuma muci mushe musha ruwa.., kai kai kai hafizu kanka ɗaya kake wannan zance ina bacci nake jin tashin muryar ka wata mata ta faɗa tana fitowa daga ɗaya kofar da take kallon bayin nanne. haɗe rai yayi yace '' iyamu bana son ciki da annamimanci ke nake bawa labari ne ..? nanne wannan matar da kike gani duk wani hali da muka shiga ita , taja mana kema wallahi ki dena yarda da ita Alkur'an tsumma ce.., da sauri nanne ta tashi tace '' haba hafizu wannan ba mahaifiyar ka bace kake jifan ta da mugayen kalamai.., iyamu kuka ta fashe dashi tare da kifa kan'ta a kafaɗar nanne tausayin ta ne ya kama nanne ta soma rarrashin ta kwafa hafizu ya saki yace '' wallahi nanne ankar saboda kina cika min cikina ya saka duk abin da naga zai cutar dake da ya'yan ki nake nuna miki hanya amma ke bakya andasata (understand ) ba ruwa na jizos ba Allah mabane an'aike ne ankar ankar itama waccan zan tela mana tafi ta daga sabgar rocas yasin ko na sabule mata tafar cikin ta tas nayi mata ƙaramar tiyata.., Hafizu ya zaka tafi mahaifiyar ka , tana cikin wani hali Nanne ta faɗa cikin wani irin yanayi. Chak ya tsaya ya juyo yace '' yasin nanne dan kece nifa na ma manta da wannan sunan ke kike tuno min dashi ne idan wani ne ya fadi wannan sunan da sai dai yaga haƙoran'sa suna yawo a ƙasa tas sai na cire mai su tofa dan kece nake raga miki.., shege tsinannan ne karka raga mata dan ubanka wallahi hafizu ka kiyaye ni. iyamu ta faɗa cikin ɓacin rai hmmmm iyamu iyamu wallahi ki guji ranar da zanyi wa kowa na gidan nan zindir har kura ta cewa da kare maye gwara ni ba zambo cikin aminci nake yi ba kuma wallahi ido na idon wannan abin sai na hako shi duk ba ke kika samu a cikin bala'i ba. rarrashin ta nanne take yi dakyar tai shiru sannan suka zauna nanne tace '' hakuri za kiyi da lamarin yaran nan kowa da yadda Ubangiji ya tsara mai rayuwa idan aka saka hakuri da juriya sai kiga Ubangiji ya kawo afuwa be kamata ki dinga tsine mai ba kina la'antar sa iyamu kama ta yayi ki dinga tausasar zuciyar ki tare da faɗa masa magana mai daɗi. sai kiga ya shiryu ya bi kan turba kukan nan da kike mai ba ƙaramin bala'i bane a rayuwar sa dan Allah ki dena jifan sa da mugayen kalamai. ajiyar zuciya ta sauke tace '' Allah yana gani ba saboda dashi nake kuka ba nanne kalli irin maganar da yake fadi wai bana zama dake tsakani da Allah..., kara rushewa tayi da kuka taci gaba da cewa ai saiki zargi wani abin a zuciyar ki tunda zuciya bata da ƙashi idan ba kyautata miki ke da ya'yan ki ba me zanji a rayuwa ta iya so da kauna kin nuna min shi idan na musguna miki dai-dai da rana ɗaya sai Ubangiji ya kama ni haka dazu abin da jamila tai min banji dad'i ba wai na dauko farar alawa na bawa Areej ta karɓe ina kallon ta , ba komai nasan ba laifin ta bane irin maganganun da hafizu yake yi ne shi ya saka zargi ya shiga zuciyar ta ni kuwa ina zan saka kaina kowa yana yi min wani irin kallo me cike da ma'anoni kala kala duk kuma hafizu shine sanadi. kama hannun ta nanne tayi tace '' karki damu wallahi ko ɗaya matsayin ki yana nan a zuciya ta Allah ya dada shirya mana yaran mu.., kuka ta ƙara rushewa dashi tare da rungumar ta tana cewa

Chapter 1 of 6