ce daga Taimako ba shikenan ba?
Sadiq ya yi shuru kamar bazai yi mgana ba sai kuma chan yace" Tahir na fad'a maka Tausayin su na ke ji. Kuma ni wajen mahaifiyar su na ke zuwa matar na so na wlh."
Tahir ya yi wata Dariyar renin wayau kafin yace"Ta na sonka? Eh dole ta soka Tunda ta na son kaima ta jefa rayuwarka cikin gagari ta sanadin yarta kamar yadda ta jefa Sauran."
Sadiq bai Fahimci in da Tahir ya dosa ba shiyasa ya ce"Naji ka bar ni. Rayuwata ce ba taka ba Tahir."
Tahir yace"Kasan me naji a kan wannan yarinyar da Ahalinta?
Sadiq kai tsaye yace"Sai ka fad'a."
Ya fad'a hankalinsa na kan Allon Na'urar da ya ke kallo.
Tahir yace"ka na fita wani Mutum ya zo can u just imaging yarinyar da ka ke ma kallon yarinya karama auranta fa Biyu bazawara ce."
Sadiq ya yi shuru kafin ya Dago ya na kallon Tahir cikin mamaki yace"Me ka ce? Bazawara ?
Tahir yace"Yes ofCourse Bizet ba. Abunda zai kara baka mamaki ma shine Bayan mganar auran nata yarinyar ta na da wani abu a tare da ita na Dabam kuma"
Sadiq ya yi saurin cewa"Kamar na me?
Nan Tahir ya shiga zayyanemasa har da kari ya karishe da fad'in"An ce duk arzikin mutum in ya rabeta sai ya talauce in ma bai rasa rai ba. Mijinta na farko da shi da iyayensa sai da suka rasa komai nasu, na Biyun kuma ya na chan ya na jinya.
To wai yarinyar da ace itace silar karyan arzikin Ubanta ta yi kuma sanadiyar mutuwarsa da ciwon uwarta da duka Halin da suke ciki itace Sila kasan wasu haka Allah ke yin su da Farar kafa ba bu albarka ko wani nasibi a tare da su."
Tahir ya tsagaita ya na kallon Sadiq ya na so ya Fahimci yadda ya karb'i mganar sai yaga hankalinsa na kan abunda ya ke kamar ma bai ji abunda ya ke fad'i ba.
Kai tsaye Tahir yace"Baka ce komai ba?
Sadiq kai tsaye yace"Me zan ce maka Tahir?
Cikin mamaki ya ce"Baka ji mganata ba ne?
Sadiq yace"Na ji mana. Me ka ke so ayi yanzu?
Tahir ya gyara zama ya na fad'in"Ka yi nesa da su don Allah Sadiq. Ka na da wad'anda in wani abu ya sameka za su shiga wani Hali."
Sadiq ya yi kamar bai ji Tahir ba sai da shi ya gaji da jiran jin ta bakinsa ya kwace laptop d'in ya na fadin"Sadiq mgana fa mai muhimman na ke yi maka ka yi min banza"
Sadiq ya sauke ajiyar zuciya kafin ya ce"Tahir me ka ke so nace.?
Tahir yace"Au me ma zaka ce ka ke tambaya ta Sadiq?
Lafiyar ka Dukiyarka ka tseratar da su mana."
Sadiq ya goya hannayensa a saman kirjinsa lokaci d'aya ya na fad'in"To naga ai ni ba mai dukiya ba ne ballatana ace zan talauce."
Ya fad'a lokaci daya ya na kyalkyacewa da Dariya.
Galala Tahir ya yi ya na kallon Sadiq ganin ya na dariya kamar wanda ya fad'i wani abun dariya.
Tahir ya shaka da yasa a fusace yace"Sadiq abun dariya ne wannan?
nace abun dariya ne wannan?
Sadiq ya tsagaita da Dariyan ya na Fad'in"Gaskiya abun dariya ne Tahir. Ta ya ya zaka yadda da wannan mganganun kamar almara?
Daman mutum ya isa ya yi ma wani mutum wani abu batare da Allah ne ya yi masa ba?
Ya tambayi Tahir Lokaci d'aya ya na kallonsa. Tahir yace"Ba wannan bane, Ka fara tunanin janye jikin ka daga wannan yarinyar Sadiq in dai ba sonta ka ke yi ba."
Sadiq yace"Wlh tallahi ba sonta na ke yi ba. Mganar kuma na janye jikina bai taso ba ban fara domin na daina ba Tahir."
Tahir yace"Sadiq ka na jin fa an ce ga abunda ke faruwa a rayuwar yarinyar nan. Daman ni tunda naganta ba ta min ba tsoron ganin Fuskarta ma na ke yi farin ta ya yi yawan da zai iya zama matsala."
Sadiq ya kara Bushewa da dariya kafin yace"ina ruwan ka da farinta. Fari ko baki wani hallita ne na ubangaji. Kada ka danganta haka da yanayin da Allah ya halliceta."
Tahir yace"Sauran mazajen da ta aura fa? Me zaka ce a hakan haka.?
Sadiq ya gyara zama kafin yace"Ni ban zan ce komai ba. Saboda ni musulmi ne na yi imani da Allah da Annabawansa tare da Sahabansa da Littafansa. Sannan na yi imani da Tauhidi da iklasi na kuma san akwai kyakyawan kaddara da Mummuna shiyasa bazan ce komai kan mganganunka ba Tahir, Basu da ma Tushe ballatana makama kai ma ban yi tsammanin jin irin wad'anan maganganun daga bakin ba Tahir."
Ya na gama fad'in haka ya karb'e laptop dinsa ya na fad'in"Ni ga Allah na Dogara nasan kuma shi ke aikata mai kyau ga bawa da akasin sa ba Mutum ba."
Tahir ya saki baki kawai ya na kallon Sadiq bai taba zaton zai iya Ture wannan mganar ba.
Sai yanzu da ya maida abun wasa yasan raba Sadiq da wannan yarinyar nan aiki ja ne.
Tahir bai hakura ba yace"Sadiq ba Rayuwarku d'aya ba. Ku na da tarin bambamce bambance don Allah ka bar su ana su Duniya kai ma ka koma taka Duniyan."
Sadiq ya amsa shi cikin Sakewa ya na Fad'in"musulmi dan'uwan musulmi ne Tahir. Kuma taimako ai ba laifi ba ne ni ban ga wata matsala ba aciki."
Cikin kumfar baki Tahir yace"To aure auren nata ka san da shi?
Ka daa garin Taurin kanka ka siya ma kanka wahala Sadiq."
Sadiq ya girgiza kai kafin yace"Abunda ya shafe su sai nace sai na sani? Nima ai ba su san komai a kaina ba, Kaga Tahir plz ka kyaleni da wannan mganar bata da asali ballatana Tushe."
Sadiq ya fad'a ya na cigaba da Sarrafa Laptop dinsa Wani Turkish Drama ya ke kallo shi ya ke kokarin kunnawa, sanda Yaji Tahir na fad'in"Ammh kasan akwai farar kafa acikin mutane ko?
Kamar Sadiq bazai yi mgana sai kuma ya Ture Na'urar gabansa ya na kallon Tahir na wani Lokaci kafin yace"babu Farar kafa a cikin Mutane Tahir. Kuma babu Farar kafa a musulumci Duk canfi ne kuma Canfi karya ne addini baizo mana da shi ba kai ko Maita ma Annabi bai sanar damu ba kambun baka kad'ai Annabi ya sanar damu akwai shi a acikin musulunci."
Ya fad'a cikin Tarin natsuwarsa. Tahir ya yi kasake ya kasa mgana.
Sadiq ya cigaba da fad'in" Babu wanda yasan gaibu sai Allah Tahir.
Allah Fa'alim lima yarud_ shine mai aikata abunda ya ke so alokacin da ya so. babu Canfi ko farar kafa a musulumci, lamyasiduna_ Babu abunda zai same mu a wannan rayuwar Illama katabullahi lana_ sai Abunda Allah ya Rubuta zai faru same mu.
Wahuwa maulana_ kuma Allah shine majibancin dukkan lamuranmu.
Wa'allallahi falyatawakkalu mu'uminun_Ga Allah kad'ai ne mu mumumai ne zamu dogara."
Sadiq ya karishe fad'a ya na kallon Tahir kafin ya Dora da fad'in"Saboda haka ka kiyaye irin wad'anan mganganun. Ko wani kaji ya na yi ka fad'a masa Allah shine masanin gaibu ba Mutum ba."
Daga haka ya cigaba da abunda ya ke yi ya bar Tahir ya na kallonsa.
Ba domin wa'azin Sadiq ya wani Shigesa ba. Dole fa akwai ayar tambaya acikin Rayuwar yarinyar sai ace haka kawai komai ke faruwa kai ina da walakin Goro a miya. Dole sai ya yi kamar ya na yi Ko saboda abotan da ke Tsakaninsu da Sadiq ba zai taba bari ya saka Rayuwarsa acikin Tsaka mai wuya ba.
Tun daga ranar bai kara yi ma Sadiq mganar ba saboda yasan ko ya yi masa bazai Sauraresa ba.
Sai ma karin wasu ayoyon da za su biyo baya da tarin Hadisan da Sadiq zai rika gayamasa ya na fassara masa.
Kuma ya na gani Sadiq bai fasa zuwa gidan ba sannan bai fasa zuwa siyan wannan munafukin Danwaken da ya ke Tunanin koma wani Mugun abu ne ciki ta saka ma Sadiq din domin ta ja Ra'ayinsa a kanta.
Har so ya yi ya kira Umma ya fad'a mata sai kuma ya kasa. Ba sa taba irin haka da Sadiq ba duk da shima kamar dan gida ne bazai kyautu ya kai karar Sadiq gidan su ba.
Ya na cikin neman mafita ne Makarantar da ya ke Hidimar kasa su ka yi Hutu yace ma Sadiq zai tafi gida ko shima zai tafi Gusai? Bai tab'a zaton Sadiq din zai ce za shi ba. Ammh sai ya ce masa shima zai tafi gida ya yi sati biyu sannan ya dawo.
Tahir ya ji dad'i sosai tare da Fatan Allah yasa kafin Sadiq ya Dawo ya manta da zabiyar yarinyar.
Rana d'aya suka tafi kuma abunda Tahir bai sani ba Sadiq a daran ana gobe Tafiyarsu sai da yaje ya yi ma Amma sallama a kan zai je kauye zai jima kafin ya dawo.
Har Amma na fadin ko dai in ya tafi bazai dawo ba ne? Yace mata in sha Allahu zai dawo ai bai gama hidimar kasar ba.
Hasiya ta rakosa har waje in ba idanuwansa suka ga masa karya ba yaga damuwa da kewa acikin Idanuwantaa.
Ya na cikin motar zuwa Gusai ya ke tunawa da mganar ta cikin sanyi in da ta ke cewa"Ammh zaka dawo ko?
Kai ya gyad'a mata kafin yace"In sha Allahu SIYA."
Sai ta d'aga masa hannu alamun bye bye kafin tace"Allah ya kiyaye hanya. Ya kuma dawo da kai Lafiya ASSADIQ."
"ASSADIQ.."
Sunan ya daki zuciyarsa har sai yaji ya amsa acikin jikinsa. Lumshe ido ya yi ya na kallon siraran hannunta lokacin da ta ke d'aga masa hannu da Sanda ta juya siraran kafafuwanta ta koma cikin gida.
Sake Bude' idanuwansa ya yi yana jin wani iri aransa In da gaske ne auran Hasiya Biyu me ya faru da ita ta yi aure aure a kananun Shekarunta? Tabbas akwai wani abu shi kuma mutum ne da ba ya cika Takura ma Mutumin da ke tare da shi akan sanin wani abu na fanni Rayuwarsa.
Ammh zai so ya ji garin ya ya da kananun Shekarunta ta yi aure har Guda Biyu kuma ta na fitowa?
Ya tuna kwanaki har Amma ya taba ma tambayar Ko Hasiya Sikila ce?
Amma sai da tayi dariya kafin tace"Hala sirintar ta ka gani ko?
Haka na Haifeta lafiyanta kalau Abubakar."
Abun mamaki har ya kai Gusai duniyarsa da Tunaninsa akan Hasiya ne.
Acikin ransa Tausayinta ya ke ji tun kafin yaji me ya faru da ita. Tausayin yadda ta na karamar yarinya ta Fuskanci Kalmar Saki har sau biyu.
Da rana ya sauka agida.
Murna wajen iyalan gidan Alhaji Sulaiman ba'a mgana.
Kada su Innani ta ji labari ta kasa zama ta kasa tsayuwa Magajij gida ya dawo. Abba baya nan sanda ya dawo ya gaji shiyasa shashensa ya wuce ya yi wanka. Kafin yaci abinci Tahir ya kirasa yace shima ya sauka gida Tun dazu ba su jima suna mgana ba suka yi sallama.
Salima ta kawo masa abinci ya ci ya sha sannan ya kwanta ya na warware gajiya."
******
Tafiyar Sadiq da kwana Biyu Adda ta zo Dalilin ta kira Adda Fati ta na tambayan lafiyan Amma. Ita kuma ta gayamata Ciwon da Amma ta yi kwana Biyu tsakani sai gata tare da d'aya daga cikin ya'yanta Isuhu Jauro.
Ko alama Adda bata nuna ma Amma da mganar tafiya da ita tazo ba Jauro nan ya barta ya koma sai da ta kwana sannan ta zaunar da Amma da mu tare da Adda Fati da Adda Rukayya.
Domin Adda Fati na zuwa tace ta Kira mata Rukayya jin Adda ke kira yasa ta zo da sauri a tunanin ta ba lafiya.
Sai da taga kowa lafiya har Amma sannan ta kwantar da Hankalinta.
Maganar da Adda ke fad'i ne ta girgizamu ba Shawara ba ce wannan karon tace Umarni ne zata Dauki Amma su koma gida.
Adda Fati ta zaro ido kafin tace"Adda mu kuma fa? Mu kadai anan ba mu da kowa fa"
Adda tace"Ba ku kad'ai ba ne. Ku na da mazajen ku sannan nan ne Tushen ku ga kuma Dangin Uban ku duk suna garin nan, Aisha kuma aure ne daman ya kawota kuma wanda ya yi silan zuwanta ba shi Tuntuni ya dace na tafi da ita mu zauna tare saboda ku na kauda kai. Ammh yanzu komai ya zo karshe Da Aisha da Hasiya da Habiba duka zan iya rike su, na saka Tuni an gyara muku muhalli ci da sha bazai gagaremu ba in sha Allahu."
Ta fad'a kai tsaye ta na kallon mu.
Cikin mu sai aka rasa mai kara cewa wani abu tun bayan mganar Adda Fati.
Adda ta kalli Amma da ta dukar da kai kafin tace"Wannan karon ba karb'an uzuri. In Hasiya ki ke ji ki daina damuwa achan ma zata samu miji in sha Allahu."
Adda Rukayya tace"Ammh Adda rayuwar ce ba d'aya ba kina ganin akwai takurawa gareki kema ki na Fama da kanki.?
Da Sauri Adda Fati tace"Eh nima shi na ke Tunani."
Adda ta yi mirmishi kafin tace"Ni fa da Aisha muka taso tun bayan rasa iyayen mu. Kuna tunanin bazan iya rike ku ba ne? Kamar yadda na tara ku suma yarana haka na Tarasu kuma suka bani goyon bayan Tahowa da ku kuma in sha Allahu sun ce baza su gaza ba, Naga nan din da ta ke zaune ba wani mai kula da ita. Dangin babanku kuma sun yi butulci da Hankalina ke chan a tashe gwara na Dawo da ita a kusa da ni zai fi min kwanciyar Hankali. Ba shawartanku na ke yi ba Umarni ne.
Ke Hasiya ku fara shiri kin ji ko?
Cikin sanyin jiki nace"To Adda."
A baya na fi kowa Murna da komawar mu gadan mallam mamman.
Ammh abun mamaki yanzu sai naji kamar in na tafi zan bar wani abu mai Muhimmamci anan to menene shi wannan?
Wata zuciyar ta tunasar da ni shi.
"ASSADIQ."
shine na ke jin wani iri ya ya zai ji in ya dawo akace masa ga in da muka koma? Maimakon na yi murna sai naji na kasa yin farinciki ko kad'an.
Ammah kuma ba ta iya ma Adda Gaddama ba tace duk yadda tace haka za'ayi.
Su kan su su Adda jikinsu duk ya yi sanyi haka suka tafi.
Washegari mun tashi da had'a kaya duk da bamu gayama kowa ba sukola muka ta shi da shi Tun Safe ni da Habiba.
Sai da yammah sai ga Adda Fati da mijinta. na zata yazo gaida Adda ne sai bayan sun Fati Adda ta kalleni ta na fadin"Fati da mijinta sun roki a ba su Habiba ta zauna tare da su saboda karatun ta. to ganin yadda ta damu yasa na amince sai ke ki shirya tare da ke zamu tafi."
Gabana sai da ya fad'i na kasa ma mgana Habiba na jin haka ta fara tsallen Murna, daman karatunta ta ke ji in ta koma chan ammh jin haka sai ta fara murna.
Amma ba ta ce komai ba sai dai a kasan ranta ni ta ke Tausayi.
tun jiya da Adda ta yi mganar nan ta ke ta nema min mafita ammh bata samu ba.
Habiba ta samu nata mafita saura Hasiya. Ita da Rayuwarta ke cikin Tsaka mai wuya ta na bukatar Farinciki da jin dad'i.
Ta na bukatar wata rayuwar da ta fi wannan da ta ke ciki.
*Littafin TSAKA MAI WUYA paid book ne, iya Book 1 ne free Pay N500 For BOOK 2,3. Regular group or VIP GROUP N1000. Via 0552179550 Jamila Umar gt bank.*
*Shedar biya ta wad'anan lambobin 09069067488 or 08032773332.*
*SPECIAL GROUPS Follow@Jamilaumarjanafty On AREWABOOKS mutanen mu na Niger za su Tuntubi Kausar Aglan nissa +22796562223 Nagode*
*Janafty*
*TSAKA MAI WUYA.*
*Wattpad:Jamilaumar315*
*Mallakar:Janafty*
*Arewabook:Jamilaumarjanafty*
https://chat.whatsapp.com/BARBh2begGc0KdlLEZDzhk
Ku zo ku yi sayayyarku tare da Yar Gidan Imam, inda za ku sami komai cikin sauki, tun daga kan kayan kicin, kayan yara,atamfofi da lesissika uwa uba da kayan gyaran jiki irin na manyan matan da suka San kan su,har counselling mu na yi yadda duk damuwar da ki ke ciki a game da aurenki da gyaran jikinki zaki samu solution. Ku dai ku shigo cikin wannan gidan na karamci kai tsaye domin more tagomashin da ke ciki.
*18*
Kamar wasa sai ga karamar magana ta zama babba, Adda ta dage tare da ni da Amma zata koma kafarta kafarmu tun ina ganin lamarin wasa har na sare na Saduda da cewa tafiya ta zama Dole.
Tuni har Amma ta sanar ma da matan gidanmu saboda rayuwa. An yi zaman Amana tun zamanin zaman mu acikin gidan nan ko cacar baki bata taba yi da kowa ba.
Mu ma haka babu ruwan mu tun ballatana ma da ba su cika Rab'ar mu ba, mu ma sai mu ka kama kan mu da Maraicin mu.
Adda Fati da Adda Rukayya matuka sun shiga damuwa. Adda Rukayya ta fi bani mamaki ita da ni ke ganinta ba ta damu da mu ba, sai ga shi ta nuna jimaminta sosai. Daman tun faruwar abunda ya faru a gidanta ta yi sanyi yanzu lafiya lau mu ke da ita sai dai duk da haka babu shakuwa Tsakanina da ita kamar yadda muka Shaku da Adda Fati.
Dukkansu ba su da mafita ne Gwara ma Mijin Adda Fati zai iya rike mu ni da Amma. Ammh mijin Adda Rukayya ba shi mutumci ko Habiban Adda ta ce zata rike wlh bazai rike ba. Mutumin da bai san kowa ba sai kan shi itama don ya na sonta ne shiyasa ya ke yi mata abunda ta ke so.
A baya ne na so na koma wajen Adda da abubuwa suka rikicemin ammh a yanzu kuma sai naji ba na son barin nan d'in. Amma ma ta gama iya nazarinta ta san ba mafita sai ta bar ma Allah duka zabinsa.
Adda Fati ta kira Ramatu ta sanar da ita ta kuma ce ta sanar da Inna Talatu. Washegari sai ga su sun zo Hankula ta she, Inna talatu ta ce"Yanzu shikenan kuma Amma zaki bar mu?
Kafin ma Amma ta ba ta amsa Adda ta karb'e da cewa"Ba ta bar ku ba. zumunci ai Allah ya riga ya had'a. In bukatar hakan ya ta so zamu zo. Kuma in wani sha'ani ya taso ko auran Hasiya duk za ku zo in sha Allahu."
Daganan Inna talatu tasan Adda ta riga ta yanke hukunci ba mai tada wannan mganar. daman ta dad'e ta na so ta Dauke Amma d'in ta koma wajenta.
Ni kuma Ramatu sai nanata tafiyarmu ta ke yi ta na fad'in"Yanzu Hasiya in kika tafi ya zan yi? Kinsan fa ba ni da wata kawa wacce ta wuce ki."
Cikin sanyin murya nace"Zamu rika waya Ramatu kada ki damu ba bu abunda zai sauya."
Ramatu ta yi tagumi ta na kallo na ina yi ma Noor rawa ta na bangala Dariya.
Cikin muryan kamar za ta yi kuka tace"Hasiya sai na ke ganin kamar rayuwar zata yi miki wahala. nan aka haifeki kuma anan kika ta shi chan kuma bakon waje ne a wajen ki. Akwai chanjin Rayuwar da kafin ki saba sai kin sha wuya."
Mirmishi na yi kafin nace"Zan saba Ramatu. a yanzu dai banga irin rayuwar da Hasiya bazata iya zama acikin ta ba."
Ramatu tace"Ni da zaki amince da na yi ma Nura mgana tunda ina da Daki sai ki zauna tare da mu."
Ido na waro ina kallonta kafin nace"Ramatu anya ki na da Hankali kuwa.?
Ramatu tace"Ras na ke Hasiya. Allah da gaske na ke in kin amince na yi masa mgana sai ki saka baki mu lallashi Adda da Amma"
Dariya na yi kafin yace"A'a ba da ni za'ayi wannan aika aikar ba. Bazai yu yu ba Ramatu ai ba mutuwa zan yi ba, Wajen zama kawai zan sauya kuma zumuncin mu na nan har Abadan"
Ramatu sai ta kasa magana sai kallona ta ke yi cikin Rauni. Da alamun so ta ke yi ta yi kuka ni kuma sai naki kallonta na cigaba da yi ma Noor wasa ina fad'in"Kinga Noor ta kara wayau sosai."
Ramatu ba ta ce komai illah tagumin da ta zabga ta na kallo na.
Noor ce ta fara kuka na tashi na goyata na fara zagaye dakin Maman Boy da ita ina jijjigata.
Sai ji na yi Ramatu tace"Shikenan sana'ar Danwake ya tsaya?
Juyowa na yi ina fad'n"Ya jima da Tsayawa tun kafin zuwan Adda rabo na da yi."
Ramatu ta sauke ajiyar zuciya ganin yadda ta damu yasa na karisa na zauna gefenta ina Dafa kafad'arta Lokaci d'aya ina fad'in"Ki daina damuwa ba mutuwa fa zan yi ba."
Ramatu ta kalleni kafin tace"Ko ba mutuwa zaki yi ba. Zaki yi nesa da ni ko?
Sai na kasa mgana zuciyata sai naji ta matse ni kaina ba na son yin nesa da su musamman wani da zuciyata ta saba da shi.
Cikin fitan hayyaci nace"Ni kaina ba na so na yi nesa da shi Ramatu."
Ban san me na fad'a ba sai ji nayi Ramatu tace"Shi wa?
Kallonta na yi ina tunanin me na fad'a.
Ganin haka yasa Ramatu tace"Shi waye baki son ki yi nesa da shi?
Ajiyar zuciya na sauke Ramatu ce wacce ba abunda na ke boye mata ita D'in Sirrina ce kamar yadda na ke Sirrinta.
Cikin sanyin muryata da ta kara yin kasa nace
" ASSADDIQ..."
Ramatu ta bud'e ido ta na fad'in"Assadiq kuma? Na ina?
Mikewa na yi jin Noor ta fara kuka ina jijjigata nace"ina wanda kwanaki ya taimaka ya kai Amma asibiti?
Ramatu ta yi shuru kafin ta ce da sauri"Na gane shi wannan Saurayi baki dogo ko?
Wanda ya rakamu dakin da ku ke ciki lokacin da aka kwantar da Amma?
Kai na gyad'a mata batare da na yi mgana.
Ramatu ko mikewa ta yi jiki na rawa ta iso kusa da ni ta na fad'in"Gayamin naji. Ya ce ya na son ki ne?
Ta fad'a lokaci d'aya ta na Dafa kafad'ata. Sai ta ba ni dariya da sai da na Dara cikin Dariyan nace"Wani irin so kuma Ramatu?
Ramatu ta harareni kafin tace"To in ba soyayya ba me yasa baki son nesa da shi? Kuma ma ban da abun ki Hasiya ai garin masoyi ba ya nisa."
Mirmishi na yi kafin nace"Ba fa soyayya mu ke yi ba. Tun bayan taimakon da ya yi mana sai muka saba yana zuwa gidanan sosai wajen Ammah. To cikin sati nan da ya fita ya zo ya yi mana sallama zai tafi kauyen su shine abun ya ke damuna zamu tafi bai sani ba Ramatu."
Ramatu ta kuramin ido cikin mamaki kafin tace"Sai ki kirasa a waya ku yi sallama"
Kai Tsaye nace"Ba ni da lambarsa."
Ramatu ta yi shuru ba ta yi mgana ba.
Ni ma na yi shuru na wani lokaci kafin nace"Ko Amma ta damu tace da ta san da tafiyar da ta yi masa sallama."
Ramatu tace"Ba a nan garin nan ya ke ba?
Kai tsaye nace"Eh shinkafi ko yace sunan garin su."
Ramatu tace"Bazamfare ne kenan"
Ban amsa mata ba ta cigaba da fad'in"Damuwarki akanshi ta ba ni mamaki kad'an Hasiya."
Kallonta na yi kafin na yi mgana ta yi saurin Tareni da cewa"Daga gani kina jinsa kusa da zuciyar ki ko?
Kamar wata gaula haka na gyad'a mata kai ina fad'in"Ban san meyasa ba. Ina yawan tuna shi sannan ina jinsa sosai a cikin wani lungu acikin zuciyata."
Ramatu yar dariya ta yi kafin taje ta zauna ta na fadin"Fata na Allah yasa shima ya na jinki a cikin zuciyarsa kamar yadda ke ma kike jinsa."
Sai alokacin na Fahimci inda ta Dosa da Sauri nace"Ke ba fa wannan ba. Kawai taimakon da ya yi min ne yasa na kasa manta alherinsa."
Ramatu tace"Nima na sani."
Daga haka bata kara mgana ba ta bar ni ina Tunanin mganarta.
Ramatu wai ta na Tunanin Ina son ASSADIQ Ne?
Tuna haka yasa sai da gabana ya fad'i Haramun ne na so wani acikin Rayuwata in dai zan yi duba da Halin da ni ke ciki to aure ko soyayya ta Haramta a gareni ni Hasiya.
Kawai girman Alherinsa na ke Tunawa tare da kirkinsa natsuwarsa da taimakonsa zuwa garemu yasa zuciyata ta bashi waje na musamman.
Ammh ni kaina nasan Assadiq ya fi karfina ko a kafad'an gwada tsara bazan iya tsayawa da shi ba.
Saboda na kauda Tunanin haka acikin Zuciyar Ramatu yasa na kalleta ina Fad'in"Kin samu Labarin Salisu kuwa? Ya jikinsa?
Ramatu tace"mun yi mgana da Musbahu kwanaki yace da sauki ya na tafiya da Sanduna guda biyu."
Kai na gyad'a a hankali kafin nace"Allah ya kara masa lafiya."
Ta amsa da Ameen. Daganan muka yi shuru kowa na ta sake sake, ita daga baya Mijinta ya kirata sai na fita na ba su waje suna mgana ta waya.
Sai Dare Ramatu da Inna Talatu suka tafi da Niyar sai jibi in zamu wuce za su zo sallama.
Gabadaya mun gama had'a kayan mu. Adda tace komai kada mu bari Isuhu zai dawo gobe ya samo mana motar da zata kwashe kayan duk da ba su da wasu yawa.
Habiba kuma
All Chapters
Font Size
16px
Background
Progress
Chapter 20 Chapter of 24