Biyo dan'uwansu domin zumumci kuma da Taimako ammh Innani ta Tsare gaba ta tsare baya. Ko zuwa suka yi Innani zata tattare ta saka ya ba su kudi kad'an da ko na maida su gida bazai isa ba sannan ta hana su kwana acewarta shima Sulaiman ba kudin garesa ba Rufin asirin Allah ne.
Za'a iya cewa wani abun na Abba ya Tadda Hali ammh kuma da zugan Innani da irin Tarbiyanta.
Hauwa kadai ta ke bari Abba na tallafa mata itama haka take tsine ma shitu tunda yanzu matansa biyu kuma dukkansu suna ta Haihuwansu Hauwa ce aka bari cikin gorin dangin miji da kishiyoyi sannan Innani ta so ta raba auran Hauwa tace sai Shitu shima ya ce sai Hauwa daga karshe Innani ta fita batunta ta koma neman ma matan Sulaiman mganin Haihuwan Magajin gida.
Lokacin da Magajin gida ya zo Duniya komai na Rayuwa Alhaji Sulaiman ya gama mallaka ya yi karfi a sana'ar gwalagwalai sannan tare da Shigo da kayan wuta, da su kamfutoci a lokacin kuma ya'yan shi goma sha d'aya duka Mata ne innani ba inda bata shiga ba, ammh har alokacin Kum fayakum.
Umma ke da Shidda, Mama kuma na da Hud'u.
Surayya ce itace Babba, sai Suba'atu,Sadiya,Sa'adatu,Saddiqa,Sajida,Sai dakin Mama kuma Sa'ima ce babba sai sakeena,Saliha,da Shahida.
Kaf din su sunayensu da Harafin S ya fara kamar yadda na iyayensu ya fara Shiyasa ko a makaranta in za'a kira sunansu da SS Shinkafi a ke kiransu.
Kuma a zuwa Lokacin Innani ta Dawo Gidan d'anta da zama saboda ta ce ta rika lura da wasu abubuwan tunda har yanzu Allah bai kawo magajin gidan ba, Sai dai har alokacin bata Saduda ba Duk in da taji ana ba da taimako sai kafarta taje bata Hakura ba.
Umma ta samu cikin da tunda ta same shi ta ke wahala ba'a taba sanin ta na da Junnu ba sai alokacin suka tashi zabuban sai dai aka yi ta mgani Innani ce ta tsaya kan Umma alokacin ta rika kula da ita, sai dai ta sha Uban jike jike da Ruwan Rubutu a shashenta akayi renin cikin Sadiq wanda ko Innani bata sakama Ranta magajin gida ke tafe ba Ciwon Umma ya Dauke wannan Tunanin daga kanta.
Sadiq ya zo duniya cikin wani irin Hali da tsaka mai wuya Umma ta Haifeshi ba ta san wanda ke kanta ba, bata kuma san abunta ta haifa ba Kamar mahaukaciya haka ta koma ta na mganganu marasa ma'ana da kokarin tashi ta fita da gudu kamar wacce ta zare Abba ya so a yi na asibiti Innani ta hana Sannan Dangin Umma daga Gummi sun kasa mgana saboda ganin Kulawar Innani akan Umma sai suka kauda idanuwansa.
Tun da Sadiq ya fad'o duniya Daman Innani ta karbi haihuwarsa tace an samu Abubakar Sadiq,Magajin gida yazo tun kuma daga Lokacin Innani ta karbi Ragamar kula da Sadiq a hannunta tare da Umma Gabadaya.
Da abun ya ki yi ne tace za su koma Shinkafi da zama saboda nema ma Umma magani.
Abba ba shi da mafita saboda Umarnin Innani ne, haka ta koma Shinkafi da zama tare da Umma da Sadiq tana kula da Umma gefe daya ta na kula da Magajin gida. Shiyasa Sadiq yace Innani na da Muhimmanci a Rayuwarsa yana da wata takwas ta cireshi a nono saboda daman sai da Dubara Umma ke iya ba shi Nonon Tunda har Lokacin sai a hankali.
Shiyasa Sadiq ya gini da ciye ciyen abincin gargajiya tunda duk shi Innani ta rika Dura masa.
Ya taso ya gansa a Shinkafi ne tare da Umma da Innani, sai dai Abba da Sauran yan'uwansa na zuwa dubashi a kai akai ko da suke a shinkafi ba bu gatan da Sadiq bai gani ba Abba da Inanni kamar zasu lashe shi Saboda so da kauna in kana son su soka to ka so magajin gida sai suma su soka.
Umma sai da ta kusa shekara Biyar cikin wannan Halin sannan ta warke da taimakon magungunar musulumci,da addu'o'in malamai lokacin da ta warke ita kuma Sai Hauwa ta fara ciwo daga zazzabi ta fara sai rama kuma Sai Innani bata koma Gusai ba sai Umma ce ta koma Gidan Mijinta aka kuma bar ma Innani Sadiq a hannunta.
Shekara takwas ya kwashe a shinkafi sannan ya dawo gusai wajen iyayensa da zama tare da Innani wacce ta kasance itace komai na shi. Tun yana karaminsa ya ke da katon bangare shi kadai kuma ya mallaki komai da yan gata ke mallaka.
Sai dai shi ra'ayinsa ba shi kan Sauran Ra'ayin wadanda ke zagaye da shi.
Ra'ayinsa Dabam ne da na kowa sannan Rayuwarsa mai Sauki ce ba kamar yadda akayi Tunanin Magajin gida zai kasance ba.
Sultana Diyar Hauwa ce wacce ta Haifeta ko ganinta ba ta yi ba Allah ya yi mata rasuwa,Umma na ganinta ta ji ta na sonta ta Dauketa Innani ta Daurre mata Gindi Dole Shitu ya bar musu Sultana yasan Tijaran Innani bai isa ya musa ba. Dalilin da zamanta ya Dawo gidan su da Sadiq kenan Hannun Umma.
Sadiq tun yana karaminsa mutum ne mai sanyin Hali Tausayi da jinkai, ga Abba da mako da son abun duniya shi da Innani ammh kuma shi ba su iya masa gaddama. Tun yana da sha wani abu a duniya yasan ya taimaki wadanda ba su da shi, ko a hanya yaga mutum na neman taimako zai ce ka Biyosa sai gida sai dai Abba yaji sallama kuma ba shi da ikon cewa a'a kai tsaye Sadiq zai ce Abba a taimaka masa don Allah.
Sannan shi Yaro me da ke son zama cikin mutane ko da bazai Rabesu ba, ammh yana son zama cikin Anguwan da ke da cikowar Mutane shi dai ya kasance ya na ganin Mutane kowa na Harkan gabanshi.
Mutum ne da ke son Rayuwa daidai misali bai cika son Dora Rayuwarsa kan Babban mizanin da kowa ya Dauke shi ba. Ya san shi dan gata ne gaba da baya. Ba Iya Innani ba kaf Dangi kowa shi ya ke so burin shi ya farantamasa rai. Tausayinsa ya siya masa soyayyan Mutane tun kafin ya zama Saurayi su Baba Sammani suka rike shi kamar shine Abba Tunda in ka fad'amasa matsalanka to kaje gida ka kwanta ka gaddara ma matsalarka ta kare.
Ya na son Mutane da son yan'uwa mafi girman abunda ke ranshi Shine Tausayi Sadiq ba ya so yaga Mutane na cikin wani Hali ya kasa taimakawa baya so yaga wani cikin halin Babu ko Damuwa in dai yana da Halin taimakawa shiyasa in kaga Abba ya yi kyauta to Sadiq shi ne in yace ba'a iya Saba mganarsa Innani ta kan ce yi masa komai ya ke so tunda komai da ka mallaka na shi ne magajin gida.
A shinkafi ya fara Fimari dinsa sannan yazo gusai ya karisa secondary school dinsa wata makaranta ya yi mai hade da boko da arabi saboda son addininsa.
Yana da naci kan abunda ya ke so ya koya,yan'uwansa ba su so ya yi karatu ma a Nageria ba, sai dai kuma Uban gayyar baya Ra'ayin haka.
Sannan ga Mallam Taju da ya ke Daukan karatu a wajensa.
A makaranta suna hadda sannan in ya Dawo gida yana yi wajen Mallam Taju shiyasa cikin Lokaci ya samu ilmin da ko iyayensu ba su taba Tunanin yana da shi ba.
Kafin ya gama Secondary School ya Sauke Qur'ani sauran littafai ya Durfafa kowa ya san shi yana da Saukakkiyar Rayuwa. A kallo daya in kayi masa bazaka ce yana da wani gata ba saboda yana Daidaita Rayuwarsa daidai da ta kowa. An sha Fama da shi akan ya je waje ya yi karatun Likitanci ammh Sadiq fur yace baya Ra'ayi shi Quantity Surveying zai karanta masu kula da harkan Shimfid'a tituna kuma kowa yasan Ra'ayin shi ne gaba da na kowa hatta da Abba da Innani.
Suna ji suna gani ya tattara kayansu ya tafi zariya, in da ya samu Admission a ABU ZARIA zai karanta Ra'ayinsa.
Abba ya so ya kama masa gida ya zauna yace baya so a Hostel zai zauna cikin Dalibai yan'uwansa.
Wannan shine Mafarin Haduwarsa da Tahir kenan.
Tahir ya zo daga Daura ne d'an talakawa maraya da taimakon yayyensa da Kakarsa ya samu makarantar, Daki daya suke mafarin Zamansu kuma abokai duk cikin Dakin Sadiq ya fahimci Tahir ya fi su maida kai ga karatu, Su hudu ne Shi da Tahir sai Jabir sai Usman Muhammad Balarabe Mb kenan.
To har gwara Usman akan Jb da shima yaron mai kudi ne babanshi dan siyasa ne, kuma daga kano yake daga ganinsa zakasan ba karatu ya zo yi ba illah Shagala.
Da Farko Sadiq da Tahir fad'a suke yi kan gyaran Daki Tunda Sadiq baya son yaga Shirgi a Daki yana son Tsafta daga baya kuma sai suka zama abokai duk da ba Course daya suke karanta ba.
Cikin Lokaci kadan suka Fahimci Hallayan juna. Suna shekara ta uku Jb ya bar Dakinsu ya koma ya kama daki a wajen makaranta yana cigaba da watsewarsa.
Sadiq ya yi suna Abu zaria saboda Tausayinsa da taimakonsa Abba ya sha Biyama Dalibai kudin makaranta bai san iyaka ba. Sai dai Sadiq ya kirashi yace"Abba akwai wani a makarantarmu bai biya kudin makaranta ba gashi za'a fara Jarabawa. Abba zamu taimaka masa."
Abba ba shi da mgana illah yace"Za'a taimaka musu Magaji gida zamu taimaka musu in sha Allahu"
Tahir ko da Usman shekaran ta kusa da ta karshe duk Sadiq yasa Abba ya Biya musu kudin makaranta. Shi Usman dan gangare ne, yana da kokari sosai phamarcy ya karanta da suka gama ya samu Scoolarship zuwa kasar Ughanda domin cigaba da karatunsa.
Rabuwarsu kenan, Jb kuma daman Sadiq ya yanke alaqan sa da Jb Tahir ne ya kasa Rabuwa da shi.
Sadiq akan kirashi da sunan Alarammah Saboda Addininsa sannan masanin Qur'ani ne da Sauran littafai kuma yana cikin malaman MSS na makaranta yana kuma limanci a masallacin makaranta, Sannan duk karattukan da ake yi da Sadiq a ke shi Yazo karatun boko ammh kuma ya samu har da karin na addini kuma in ya koma gida Hutu ya rika Daukan Wajen Mallam Taju.
Sadiq ba bu abunda ya taba nema ya rasa a makaranta sai dai ma ya kyautar shine siyama marasa karfi Handout sannan ya dinga Rabon kayan abincinsa ga duk wanda yasan yana Bukata. Sadiq tausayinsa ga Mutane mai yawa ne.
Duk da Abba da mako da son abun duniya ammh Sanadin Sadiq yasa ya ke alheri a chan Shinkafi sai kiga Mutum na da lambar Sadiq ammh kuma ba shi ta Abba. Saboda abunda Sadiq zai yi maka Abba bazai iya yi maka ba shiyasa shi ba iya magajin gida ya ke ba, shi magajin kowa ne.
Shi kuma yasa Abba ya jawo yan'uwansa ajiki ya kuma ba da Kofar kowa na zuwa gidan Abba ayi zumumci.
Shi kuma ya saka Tsarin zuwa Shinkafi zumunci da kuma in sha'ani ya tashi Duk bala'in Innani bata iya ma Magajin gida shi ma kuma ya Fahimci har da Jahilci ke damun Innani shiyasa ya ke kokarin Gyara mata in tayi kuskure.
Maganar auran sa da Sultana kuma Umarnin Umma ce, Sannan Innani ta Dora Burinta shi kuma Umma da Innani suna da Daraja a wajensa shiyasa batare da Tunanin watarana zai iya shiga tsaka mai wuya ba ya amince.
Sultana ta taso ne da mganar Sadiq shine mijinta a bakin kowa. Yarinya ce shiyasa ba zata daura mizanin komai a yanzu ba ammh Abu daya ta sani Sadiq shine mijin da kowa yasan zata aura hatta iyayenta sun sani da Yan'uwanta, ta na zuwa Hutu ganin su ammh fa In innani ta yi ra'ayi har a yanzu Innani Tsine ma Shitu ta ke yi tace bakincikinsa da na matansa ya yi Sanadiyar Rasuwar Hauwa kulu.
Sadiq ya zabi ya yi karatu a zariya saboda Dalilinsa na zama in da Mutane ke harkokinsa ya yi kuma rayuwarsa kamar yadda daidai da yanayin da ya ke so Rayuwarsa ta kasance sannan ya zabi zama a Hostel saboda halinsa na son Mutame da mu'amala in da Mutane suka fi yawan zama.
Bai cika son zama gidan su ba saboda anguwa ce da ba ta cika Hayaniya ba. Allah ma yasa yana da yayye mata kadaici bai cika Damunsa ba in dai yana gida to kowa Burinsa ya faranta masa.
Suna kaunarshi kamar yadda ya ke kaunarsu. Duk da Mama na taba kishi da Umma ganin Innani ta fi sonta sannan ita ce uwar Magajin gida ammh bata isa ta raba kan ya'yan gidan ba. Ba bambamci Tsakaninsu duk Daya suka Dauki junansu musamman Sadiq ko da ya ke karami a acikinsu yana da kyakyawan Tunani mai kyau tunda ya karanta kuma ya gani.
Bayan Sadiq Mama ta kara Haihuwan Salima da Siyama wacce itace karama daga ita aka rufe haihuwa agidan Siyama ta zama autan Gidan. Sadiq kuma ya kasance Autan Umma Shalelen Abba da Innani.
Dukkansu matan sun yi aure a garin Gusai, Suba'atu ke aure a kano sai Saddiqa da ke kebbi.
A dakin Mama kuwa Sa'ima da Sakeena suma suna Gusai ne suna aure. Sahida na aure a katsina ita kuma Saliha na auran yaron yayar Mama ce suna garin Ibadan da zama in da ya ke aiki a kamfanin Dangote.
Kuma kowacce ta na jin dadi agidan da mijinta sun kuma hayayyafa da ya'yen su turbarkallah masha Allah.
Lokacin da Sadiq ya kamallah makaranta cikin yan'uwan sa ba wacce ta so ya yi bautar kasa a zariya ammh kuma Tunda yace chan zai yi ba su da tacewa barin ma Surayya da suke kira Big sis taso yaje kasar waje ya yi karatun liktanci tare da kanin Mijinta Sadiq yace baya ra'ayin haka.
Da farko Har Abba da Umma sun Amince Innani ma ta samu ta shawo kanta ammh A'a din Sadiq kad'ai ya isa da ya Rusa komai.
Dole a kabarshi ya tafi zariya again Bautar kasa. A wannan karon ma Abba yaso ya siya masa gida yace shima baya Ra'ayi sai haya ya kama da Farko a Daura Tahir ya so ya yi nasa Hidimar kasar ammh Ganin Sadiq ya koma zariya shima ya nema ya koma Saboda Abotan da ke tsakaninsu ta yi nisan da har Ahalin juna sun sani.
Sadiq yadda ake son shi yasa ko Kashi ya kai gida ya ke da Daraja. Shiyasa Tahir ya ke kamar dan gida a gidan su Sadiq duk kuma abunda Sadiq yace ayi masa Abba ba gaddama ya ke yi masa. Ranar farko da Tahir yazo yaga irin gatan da Sadiq ke ciki bayan sun koma Zariya ya kallesa yace"kai ko wani irin abu ka ke samu a garin nan da ka zabi irin wannan Rayuwar Alhalin kai dan gata ne?
Sadiq mirmishi kawai ya yi masa bai ce komai ba, Sadiq ya je ya sauke Farali kafin su gama makaranta shi da Innani Umra kam ya sha zuwa tun yana matashinsa.
Shekaran da suka dawo ne Innani ta fara fama da matsalan idon da yasa aka kaita asibitin ido Makka na larabawa da ke kano. Aka yanka mata gilashi Tunda ganin nata ya koma sai hankali sannan ga tsufa ammh bazata bar Halinta ba.
A rayuwar Abba in da ace yau ba Sadiq da Tuni lamarinsa ya wuce Tunanin mai karatu abunda ya zama Dole kawai ya ke yi. Ko zakka baya Fitarwa sai tasowan Sadiq yasa duk Shekara sai an fitar da Zakka sannan kuma yasa yana taimaka ma su Baba Sammani da kudi duk Damina suna yin Noma domin ci da iyalansa sannan in zasu tafi sai an cika booth da kayan abinci.
Gidan Innani da ta gada Tun iyayenta Abba ya gyara nan suke sauka in sun zo garin ,Sadaka ko akai akai Sadiq kan saka Abba na yi, ko a masallaci yaji ana neman taimako zai ce Abba zamu ba da namu taimakon Abba bashi da mgana sai dai yace zamu taimaka musu magajin gida.
Shiyasa yadda Mutane ke ganin kima da Girman Magajin gida wlh Alhaji Sulaiman ba shi da wannan kimar.
Kannenshi Mata su Hassu dalilin Sadiq su kan sazo gidan su da iyalansa su yi kwanaki sai dai zasu sha Mgana da Habaici bakin Innani ta yi ta fadin Sulaimanu ba mai kudi ba ne Rufin asirin Allah ne.
Wayar Sadiq ko da yaushe cikin kiransa yan'uwa suke yi, Alhaji Sulaiman kuwa wani sai ya jima bai kirashi ba Ammh Sadiq sha yanzu ne kuma mganin yanzu.
Da ka kira shi ka gayamasa matsalan ka shikenan.
Ko'ina ka je addu'a ce da Fatan alheri ga Alhaji da iyalansa Sanadin Sadiq Magajin gida.
*Littafin TSAKA MAI WUYA paid book ne, iya Book 1 ne free Pay N500 For BOOK 2,3. Regular group or VIP GROUP N1000. Via 0552179550 Jamila Umar gt bank.*
*Shedar biya ta wad'anan lambobin 09069067488 or 08032773332.*
*SPECIAL GROUPS Follow@Jamilaumarjanafty On AREWABOOKS mutanen mu na Niger za su Tuntubi Kausar Aglan nissa +22796562223 Nagode*
*Janafty*
*TSAKA MAI WUYA.*
*Wattpad:Jamilaumar315*
*Mallakar:Janafty*
*Arewabook:Jamilaumarjanafty*
*11*
*Zariya*
Laraba.
Abubuwa biyu ne suka min tsaye a kahon raina a kwanaki nan.
Na farko yau kwanaki biyar cur mutumin da ke siyan Danwaken Sannan kuma ya kuma bar min chanjin naira na gugan naira har Dari biyu ya daina zuwa.
ina lissafe tun Alhamis da ya aiko aka siya masa bai kara dawowa ba har ga shi yau talata. Tun safe na ke duban hanya ammh shuru har su datti na kira na tambaye su sukace suma sun daina ganinsa yana zuwa. Acikin raina na ke ta faman wasi wasin to lafiya?
Wata zuciyar kuma ta kwab'eni da cewa"Hasiya kada zak'ewar ki ta cika yawa fa."
Nima sai daga baya naga na zak'en gaskiya mutumin da ban taba sani ba me yasa zan damu kaina Saboda shi? Sai wata zuciyar tace min ko ban san shi ba Cinikayar ya had'amu kuma sanin Mu'malace ka yi cigiyar abokin Cinikaryar ka.
Tun Safe da na zauna kujeran saka Danwake a tsakar gida na ke ta faman duba kofar gida da naga yaro ya shigo sai na Dauka shine, ammh kuma rashin ganin yar kular da ya saba aikowa ke sakarmin da gwiwa.
Maganar gaskiya ina cikin zullumi Ajiyar rai na sauke lokacin da Goma ta gota na gama Saka Danwake gabadaya har ya kare iya wanda zan ci kad'ai na rage.
Shi kuma abu na biyun da ke damuna Salisu ne! Ya na yawan Fad'omin a rai a kwanaki nan jiya har mafarkin sa nayi. Wai mun had'u na gaishe shi ya ki amsawa naga Musabahu a wajen da ya ce masa"Salisu Hasiya ce fa ke gaisheka ka yi kamar baka ji ba."
Kai tsaye naji muryan Salisu na Fad'in"Bazan amsa mata ba Musbahu koma miye faru. Bai kamata na kwanta Jiya Hasiya taki gaisheni ba."
Daganan na farka ina ta faman zufa. Tun daga lokacin zullumi na ya karu akan na baya. A bakin Mamam boy nake jin sun koma asibiti an kara Dubashi an ce sai karfen jikinsa ya shekara za'a cire masa.
Maman boy Idon gari ce ka rasa ina take samun wasu labaran, ko da ya ke Gantali ce da ita ba inda kafarta baya shiga da mijinta ya fita itama ta ke saka kafa ta fita kusfa kusfa a samaru nan anguwar Tsamiya Da'i da'i kun gidaje ne Maman boy ba ta shiga ba. shiyasa akwai labaran gidajen mutane da dama abakinta.
Nasan ko giyan wake na sha ban isa na dauki Siraran kafafuwana zuwa gidan Salisu da sunan gaishe shi ba. na tabbata Sahura sai ta kasheni kamar yadda ta kudurta in kuma ban mutu ba to tabbas zan samu manyan Rauninka da zan jima cikin Doguwar suma. tuna haka kad'ai kan kwabar da Niyyata ko Amma na kasa gayamata zuciyata duk da ta ganni suku suku da ta tambayeni sai na ce mata ban jin dad'i da Safen ne.
Amma na da wani irin hali ko ya ya na ke cikin damuwa ta sani sai da ta kalleni cikin Nazarina kafin ta kad'a kai tana fadin"Ko ulcer d'in ki ce zata tashi?
Kai tsaye nace mata"In ma itace ina da Sauran magunguna na ruwa da na kwayar sai na sha."
Kai tsaye itama tace min"In bazaki Jefa Danwaken nan ba a hakura yau Hasiya."
Ban bari ma na ja mganar da ita ba. Taga na mike na fara had'a kayan yin Danwaken sai ba ta kara mgana ba Ammh ta jima ta na kallona ta kuma san tabbas wani abu na Damuna to ta ina ma zatayi Tunanin bazan damu ba. Damuwa a gareni ta zama Tilas ko domin yadda na zama abun gudu da kyama wajen jama'a.
Ramatu na ke son gani ko zan gayamata cikina ta ba ni shawara, Shiyasa ina gama wanke wanken kayan da na bata, bayan na kai Daki na zo na saka ruwan zafi a rushin da na rage na leka Dakin Maman Boy nace ta aramin wayarta zan kira Ramatu.
Kai tsaye tace min"Gaskiya ba kudi acikin wayar"
Cikin mamaki nace mata"Ba kud'i? Ba shekaranjiya na saka Dari da zan kira Adda Fati ba? Kuma ba mu jima mu na mgana ba. Na dai san ban isa cinye wannan Darin ba."
Cikin tabe baki tace"To ni dai bansani ba, ban kira kowa da shi ba."
Ban kara mgana ba Na karb'i wayar na juya ban ko tsaya duba kudin wayar ba na leka kofar gida na kira Salihi na Dauki Naira dari da goma cikin cinikin Danwake na ce ya ruga ya siyomin Katin Mtn ya yi Sauri.
Sanin Halin Salihi da aikensa da sai ka mamta da shi ya ke dawowa yasa na koma Daki na fara kanta shi zan gyara Amma na saman gadonta barci ya kwasheta itama duk sai a hankali kwanaki nan da zazzabi ta ke kwana.
Har sai da na gama na share daki na wanke bayi saboda bazan iya shigarsa haka batare da na wanke ba. Na juye ruwa na yi wanka na fito na sauya kaya sannan Salihi ya dawo, Allah ya taimakeni ma ya kawomin katin lafiya.
Ina gama Loda katin na kira Ramatu daman na Haddace lambarta bayan ta Dauka mun gaisa da tambayan su Amma da Noor nace"Ke ina son ganinki kina gida gobe..?
Da zumud'i tace"To ni kuma ai goben nake shirin zuwa miki Yini ni da Noor. Gidan Inna zan kwana da Sassafe tahowa kawai zan yi"
Cikin jin dad'i nace"To shikenan ma sai kin zo d'in. Ki gaida inna Talatu"
Kai tsaye tace"Zata ji nima ki gaidamin da Amma da Habi auta."
Daganan muka yi sallama. Jin tace zata zo sai naji dadi a raina.
Ban koma na zauna ba sai da na Mayar ma Maman boy wayarta sannan na dawo na saka Danwake da manja da maggi naci.
Ganin Amma nata barci yasa na kwashe yan kayanta da suka yi datti na Daureye mata da nawa na aikin Danwake. Kayan ba su da yawa tunda wanchan Sati Habi ita tayi mana wankin kayan duka ranar Sati tunda ba makaranta.
Su datti na bama goma goma suka Debemin ruwa a waje. Ina mamakin yadda matan gidanmu ba su damu da sanya yaransu a makaranta ba sai dai su bar su su yi ta gararamba a gari ba arabi ba boko. Na taba yin musu mgana Maman Salihi tace min da na abinci za su ji ko da na kudin makarantarsu daganan sai na Rufe bakina. Duk da sai ayi abu Dari ban saka bakina ba yanzu sai kiji gori na tashi ni da ke da ababen gori gasusan kaca kaca.
Kwanakin nan ma da na ga Kaltume na jin Haushina daga ni har Amma bata kulamu kawai saboda mijinta na son Danwake na,ya kan siya ya ci kafin ya fita sai ta fara adawa da ni kai Tsaye kuma ta same ni ta min mgana cewa bata son na kara saida ma Mijinta Danwaken mu in tace bata so kawai a barshi kada rayuka su baci.
Amma na jin haka tace a barshi kawai saboda Kaltume ba ta tsoron Tijara Tundaga ranar ban kara saida masa ba ko ya aiko zan ce gabadaya an siye shi ba bu. Daganan na samu lafiya,ammh har alokacin bata daina min gani gani ba ita a tunaninta kada Mijinta yace ya na sona na saka ta uku ni kam a raina nace ta ya ya zai ce ya na sona? Shi kan shi ai baya so ya shiga cikin ukun ba.
*****
Washegari saboda zuwan Ramatu sai ban kwab'a danwake da yawa ba. Tunda tace min sabon gari ta kwana kenan zata iso nan da wuri, shiyasa tun safe na tashi na fara aikin Habiba ta taimakamin da wura gawayi ni har ta sakamin tukunyar Farko.
Daga baya na amsheta
All Chapters
Font Size
16px
Background
Progress
Chapter 12 Chapter of 24