Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
1 / 8
An dauko wannan littafi daga shafin https://taskarnovels.com.ng ku ziyarci shafin na https://taskarnovels.com.ng domin samun kayatattun littatafan hausa kama daga kan na yake yake dana soyayya Marubuci ko marubuciya zasu iya turo mana da littatafansu mu dora masu a shafinmu kyauta don masoyansu su rika Downloading a online, Sannan marubuta zasu iya turo mana da tarihin rahuwarsu da tarihin rubutunsu, dama sharhin littatafansu don masoyansu su gani kuma su karu da hakan Domin turo mana da littafi ko tarihin rayuwar marubuci ko marubuciya sai ayi mana magana ta whatssap da wannan nambar +2348140419490 A lura dakyau - kyauta muke saka littafi a shafinmu bama amsan ko sisin marubuci, duk wanda ya amshi kudinku da sunanmu babu ruwanmu, Alura dakyau - manazarta bama tura littafi ta private ku dena binmu private kuna neman mu tura maku littafi, duk mai bukatar littafi yaje website namu Alura da kyau - Littatfanmu suna fitowa cikin manhajoji uku ne PDF,TXT da DOC amman munfi amfani da PDF da TXT masu amfani da wayar android ko tablet ko computer zai fi kyau ku riga dauko PDF da DOC Masu amfani da kananan wayoyi java ko mara java TXT zakuna zaba don shine daidai wayarku This hausa novel was uploaded and downloaded from https://taskarnovels.com.ng You can download more hausa novels there Also you can send us your novel to upload it in our website for your fans to download it online It is free we do not charge for uploading novel Also if you are an Author be it online or Non online you can send us your biography including your book summary,commentary and others via this number +2348140419490 its free we do not charge for our services Note that - we do not charge for our services we uploaded novels and posted biography free, any person that collect your money in our name is your fault do not blame us Note that - pls readers stop calling us and be asking us to send you a novels we are not sending novels through whatssap or private our novels is public at any day, any time you can visits our site and download it Note that - our ebooks came as PDF,TXT or DOC format but the popular format are PDF or TXT, those with android or tablet or pc we suggest you to download PDF or DOC those with java phone or non-java phone we recommend you to download TXT This Novel is downloaded from https://taskarnovels.com.ng to download more hausa novels visits our site at www.taskarnovels.com.ng For feedback and support Facebook : https://facebook.com/taskarnovels Twitter : https://twitter.com/taskarnovels Telegram : https://t.me/taskarnovels Hakkin Mallaka(M): Hafsat C. Sodangi Shekarar Bugu a: 2009 GODIYA Godiya ta har kullum ga Ubangijinmu Allahu take, masanin abin da yake boye da wanda yake bayyane. Mai kowa, mai koma1 masanin yau da gobe, gwani mai hikima cikin dukkan aiyukan shi, wanda ya yi wa dan adam baiwar da ya bambanta shi da sauran dabbobi ta hanyar yin furuci ya kuma sanar da shi abin da bai sani ba. Tsira da amincin Allah ya tabbata ga Annabin karshe Manzon da ya kawowa duniya shiriya. Annabin Raharna Muhammad (S.A.W.) da Aiayycnsa da Sahabbansa da wadanda suka bi ma tafarkinsa na gaskiya har zuwa ranar karshe, wato ranar Alkiyama. Godiya mai dinbin yawa ga makaranta littattafaina a ko'ira suke na gode da irin kulawar ku, Allah ya bar zumunci, amin. Na gode. Ta ku: Hafsat Cindo Sodangi 2 DAGA LITTAFIN SODANGI Uwar Miji Naga Ta Kaina Waiyo Duniya Tabbataccin Al'amari Yi wa Wani Rabon Kwado Cikar Alkawari Abu Na ku Mata Masu Duniya Nufin Allah Kifi Na Ganin ka.. Da Kamar Wuya Shamaki Daga Kin Gaskiya Hattara Duk Daya Mata da Kicin Din su. Littafin Sodangi ba sa nufin yi da wani ko habaici ga kowa, an yi su ne kawai don nishadaintarwa, da fadakarwa. Ana neman afuwa ga duk wanda ya ga wani sashi na su ya yi daida danabin da ya shafe shi, ba da shi ake yi a, an dai yi dacen hakan ne kawai. Na gode: Ta ku: Hajiya Hafsat C. Sodangi. 3 GAISUWAR SADA ZUMUNCI GARE KU: Shamsiya Ibrahim Funtua Katsina State Hauwa'u Bashir Ikara Fatima Sulaiman A Zaria Habiba Ibrahim Alabura Sulamatu Isa Kasim Amina Muhammad Maiduguri Ummce "Yar Mtan Azare Sakina Baba Diddi Jalingo Mrs Abdullah Modibbo Yagana Kacallah Kaltuma a Ali Yaskari Primary School Alairo Auwalu Azarc Sa'adatu Sa'ee Katsina Hadiza U. Audi Hindatu Usaini Gombe Dukkan ku ina yi muku fatan alheri na gode da.kulawar ku a rubutuna. SADAUKARWA Sadaukarwar littafin ta mahaifina ne Alhaji Chindo Sodangi da Hajiya Fatima C. Sodangi Ubangijinmu ya saka da mafificin sakamako bisa renon da kuka yi mini. 4 TUKUICI Tukuici na ka ne Baban su Yunus mijina, Alhaji Yunusa Abdullahi Dabai. Baban su Maryma, Aisha Yunusa da Abdulmajeed. Na gode da kulawarka a gareni. JINJINA Jinjinar ta ki.ce amarya ba kya laifi. Hajiya Khadija C. Sodangi Mrs. Alhaji Nasir Idris Kiru. Ubangiji ya ba ku zaman lafiya da fahimtar juna. Amin Summa Amin. 5 WACE CE NI? Cikin kwalliya na ke sosai, idan na ce kwalliya kuwa to ina nufin irin ta 'yan matan zamani, gwanayen yin kwalliyar ta burgewa, masu kuma abin yin kwalliyar. Tun ina yar karamata kwarai mutanen da suka sanni suka san ni din gwanace kwarai wajen tsara kwalliya ta yi kyau, to balle kuma yanzu da na zama cikakkiyar budurwa. Taku daidai nake yi cikin nutsuwar da ke kara bayyanar da gwanintar iya tafiyata. Lokacin da na shigo cikin fence house' din mu, wurin da Baba ya killace don kiwon dawakan shi. Kayataccen wuri ne sosai da aka katange shi da farin katako. Harabar shi kuma aka mamaye shi da koriyar ciyawar lawn ta yi kore shar babu komai a wurin illa skable din daure dawakai, sai ko ginin katako da Baba ya yi ya kawata shi da kayan alatu, don hutawa a cikin shi. Ina shiga wurin na hango Yaya Almu can nesa sanye ikin fararen icaya, yana rike da sprinkler a hannunshi. yana fesawa 'yan shukokin da ke wurin ruwa, saboda kasancewar mu cikin lokacin raai. Can wurin shi na nufa ina tafiyata a hankali 6 don haka lokaci mai tsawo na dauka kafin in isa wurin shi, saboda kasancewarwurin mai girma ne sosai. "Sannu da aiki." Yaya Almu ya juya a hankali ya kalleni cikin nutsuwa kafin ya maida kanshi ga kallon agogon da ke daure a hannunshi. Ya sake dago ido ya dube ni. "Ke kam kin yi sa'a komai na ki a makare kike yin shi dubi lokaci sai yanzu kika fito?" Na dan ja baya kadan saboda irin kallon da yake yi mini. A hankali cikin sanyin murya na ce mishi. "Yanzun ma fa fitowa kawai na yi, amma ko karyawa ban yi ba." Da sauri ya ce, "Eh ai yana da kyau. Haka din yana da kyau, sanyin jikin ki ya rinka ja miki dalilin rashin karyawa a gida, tun da ke ba ki san ki tashi da wuri ki yi abin da ya daçe ki yi ba, akan komai sai kin makara je ki sai kin dawo." Na yi maza na kauce daga wurin feshin da yake shirin jika ni, na ce mishi, "Ai zuwa na yi da in ce ko za ka sauke nine?" Ya ci gaba da aikin shi yana tambayata, "Ina su Junaidu?" Na ce, "Ai.babu. kowa a gidan duk sun tafi." 7 Bai bata lokaci ba ya kashe sprinkler din ya Diyo bayana ya wuce ni ban iya yin komai akan lokaci ba, in mutum yana da abin yi ai ba zai yiwu ya iya hakurin jirana ba, in dai shi ma ba zama mai latti irina zai yi ba. Kan in fito waje tuni ya tayar da motar da na wuce a gindin bishiyar da ke bakin get din shiga fence house din Toyota Camry 2008 model, fara sol hakan nan kayayyakin da ke cikinta. Ina zama a cikin motar ya hau kan hanya har lokaci bai daina mitar da yake yi ba. Jaddada mini muhimmancin yin abu akan iokaci yake yi. "Kin san ma ma anar iokaci kuwa?" Ya dan waiwayo ya kalleni. Ban kalle shi ba, balle in tanka mishi. "Yana da kyau a ce mutum yana kiyaye muhimmancin okacin shi, ya rinka amfani da shi yanada ya dac ya rimka barin shi yana tafiya a aka kawai ba, ba tare da ya yi wani abin da ya amfanu a cikin shi ba. Ki yi kokari kina amfani da lokacin ki a yarda ya dace, sannan kar ki yarda ki saba da yin latti a kan komai ko kuma yawan sab6a alkawura." Na yi kokari na bude bakina na ce mishi, To Yaya afuwan na gode." Gaskiya ne Yaya Almu yana daya daga cikin 8 mutanen da suke kiyaye lokutansu, suke amfani da su a yanda ya dace. Kullum ka shiga dakin shi matukar ya gama komai na wunin ranar yana shirin kwanciya, to za ka same shi ne yana rubuta abubuwan da zai yi a wuni mai biye daga karfe kaza zuwa kaza, zan yi abu kaza da kaza, ko kuma za ni wuri kaza da kaza. Zai yi kuma wuya kwarai a ce bai yi hakan ba. Ma'abocin yawan istigifari da yawan salatin Annabin Rahama (S.A.W.). a kowanne lokaci ko da kuwa wani aiki yake yi in dai ba magana da wani yake yi ba. In ma maganar yake yi yana gama ta za ka ji ya koma kan abin da ya saba yi. Wani irin mutum da hira ba ta dame shi ba, ya kan yi magana nc kawai a lokacin da hakan ya zama mishi dole, don ko ni ce na saki baki ina ta surutu ya rinka kallon kenan. Sau da yawa kuma idan na gaya mishi wata magana zuba mini ido yake yi cikin nazari sai in na ce mishi Yaya Almu ba ka yarda da ni ba ne? Sai ya dan motsa kafada tare da tabe baki ya ce, ba zan iya fadin hakan ba, tun da ban saba kama ki da laifin yin karya ba, sai dai kina da alamomin hakan, don kuwa surutu ya yi miki yawa. Shi mutum kuwa in ba ki sani ba an hore shi ne da fadin alkhairi ko kuma ya kama bakin shi ya yi shiru, amma ba ya yi ta sakin magana ratata-ratata ba. 9 Har muka iso hukumar zabe inda aka toro ni zaman sanin makamar aiki, saboda kasancewata daliba mai karatun diploma a Federal Poly garin mu. Yaya Almu bai daina yi mini nasiha akan mubimmancin lokaci ba, ta hanyar kawo mini ayoyi da hadisi da suka jaddada muhimmancin lokacin, ni kam kullum cikin mamakin Yaya Almu nake, musamman in ji shi yana karatun alkur'ani mai girma ko yana kawo hadisi da maganganun manyan malaman addini. Sai in ce oh oh! Ko yaushe ya samu damar yin karatun addini haka? Oho. Tun da ni dai na san Yaya Almu ne bayan na yi wayo shekarun kuruciyar shi gaba daya a London ya yi su. can Baba ya kai shi karatu tun sa'ad da ya gama primary school dinshi, bai kuma dawo gida ba sai da ya kammala karatun shi. Yaya Almu wanane da muke uba daya. Mutane da yawa suna yabon shi, saboda tsayuwar shi da kuma kulawar shi kan al'amari na. Ni kuwa nake kallon abin da yake mini din a matsayin takura, ko kuma ma in ce yan ubanci irin na dan uba, don kuwa kafin dawowar shi gida cin karena nake yi babu babbaka, in ci duniya, kuma da tsincke. Shi ne ya dawo ya takura mini ya hanani rawar gaban hantsi, ya tasani a gaba da yawan 10 fadi da yawan tsawa da yawan zare ido, da yawan fadin ke nutsu. Ga barazanar duka a kowanne lokaci, saboda ni wai ya je ya sayi wata sharbebiyar dorina, irin ta Baba maigadin gidan mu da yake fito da ita kowanne lokaci ya sharbaneta da mai ya shanyata ta sha rana kafin ya daukcta ya je ya rataye ta a dakin shi wai don ranar da ya bugeni da ita, in ji jiki. Yaya Almu ne ya dawo ya same ni ina tsakiyar zuba shagwabata ya katse mini hakan cikin kasa da makonni biyu.kacal da dawowar shi. Kasancewar shi mutum daya tal da Ummana ba ta daga ido ta kalli abin da ya yi mini, balle tambaye shi dalilin yin hakan ya bashi cikakkiyar dama ta shiga ahrkokin rayuwata ya takura su, kafin dawowar na shi ni din shagwababbiyar yarinya ce takin kárawa, gashi dai ni kadai ce yar da Ummana ta haife, ni kadai ce kuma ya maçe a wurin baba. Gani kuma da sunan mahaifiyar shi, kowa a gidan mu gudun bacin raina yake yi, don kuwa ya san bacin ran nawa yana nufin bacin ran Umma, don kuwa a fili take fada ba ta boye ba da 6atawa Adawiyya rai gara ita a zo inda take a bata mata. Wannan dalili ya sa kowa yake kaffa-kaffa da ni, saboda an san abin da bacin ran Umma yake nufi a gidan nan. Yau na zama zagin baba, 11 ba komai ba ne a wurina hakan nan in na ga dama ina iya warware yanyatsuna in wanke fuskar na gaba da ni da mari, yin hakan ba wani abu ba ne in an kai kara a wurin Umma hakuri take bayarwa ta ce kuruciya ce. Wata rana ko da kudi aka ce ta yin hakan ba za ta yi ba, don ta yi hankali. Hakan nan da wayona na san Umma tana goyani ta kuma ba ni abinci a baki. Ina cikin wannan sha'anin ne ya dawo ya same ni bai kuma yi kwana goma sha hudu a gidan ba sai da ya dauke ni daga gidan ya kai. ni makarantar secondary yan mata ta kwana dama kuma ya zo ya same ni ne ina J.S.S 1, ya kuma yi hakan ne ba tare da ya shawarci kowa ba, bai kuma sanar da makarantar da ya kai nin ba, balle a samu damar kai mini ziyara. Yana kai ni mamakarantar nan nan tsinci kaina cikin wata irin matsananciyar rayuwar da ban taba mafarkin ana yin irin ta ba. Ni da na saba tashi daga barcina Baba Talatu, ko Umma wata cikin su ne za ta yi mini brush ta yi mini wanka, ta dauro mini alwala, sannan in fita in zo in yi sallah, a shafa mini mai a taya ni n sanya uniform dina, a kawo mini abin karyawana in karya, direban da yake kai yaran gidan nmu makaranta ya y1 ta zirga-zirgar neman in fito in ban ga dama ba in ce ni ban gama ba, umma ta ce 12 mishi kai je ka in ta gama za a kawo ta wata ra a kai ni, wata ran kuwa in ce ba za ni ba, in hau gado in yi kwanciyata da uniform din a jikina ina kallon finafinan yara. Shi ne wai Yaya Almu ya dauko ni ya zo ya jefar da ni a wannan fankaceciyar makarantar da kowa ta kan shi take yi. Wuni nake yi ina kukan bakin ciki da rashin sanin abin yi, tun ina bai wa yara tausayi su taru suna ba ni hakuri sai suka koma cewa ai sai ki y1 ta yi har sarkin kuka ya zo ya same ki, da yake kin ga wata wacce ba daga gida ta fito ta zo nan ba da za ki tasa mu a gaba da kuka kowanne lokaci in ba ki sani ba mu gaya miki muma duk iyaye ne da mu suna son mu kuma suka kawo mu, bake kadai ce mai iyaye ba. Da. abu ya kai matuka ma suna ganin bawaye sun soma zubowa daga idanuna za su watse su ba ni wuri, Suna fadin maiya in ba ki daina kukan nan ba sai mamanki da babanki sun mutu kya yi kukan mai dalili. Wannan kalma ta su ita ce ta yi matukar razanani ta yi dalilin da na daina kuka, na koma zaman bakin ciki da damuwa da kunci da yunwa. Ina cikin wannan halin ne har ranar ziyara ta zo Yaya Almu ya kawo mini ziyara yana sanye da faraen kaya kaftani da wandonsu, sun yi matukar 13 kar6ar shi. Rike hannuna ya yi ya jani ya kai ni cikin motar da ya zo a cikinta wacce take ta kan shi saboda ta dace da samun ma'abocin tsabta. Tasa ni a gaba ya yi yana yi mini kalamai, saboda irin kukan da na rinka yi mishi. "Hakuri kawai za ki yi R abi, ya zame mini dole ne kawai in yi miki hakan, saboda ba zai yiwu in barki ki girma cikin yanayin da na same ki ba, in na yi miki hakan ban yi wa kainaa adalci ba, ke ma kuma ban yi miki ba. Hakan nan ban yi wa Baba ba, ke din kina bukatar zama jaruma ne, saboda al'amuran da ke gabanki ki zama wacce wadansu za su dogara da ke, don tsayuwar su ba wacce ba za ta iya dogaro da kanta ba, komai sai an yi mata. Ki zama wacce ta san darajar dan adam da girman shi, ba wacce take taka shi a.duk lokacin da ta ga dama ba. Wannan dalili ne kawai ya sa na rabaki da gida, don haka ki yi hakuri ki saki ranki, ki kwantar da hankalinki, ki koyi mu'amallah da mutanen da kika samu kan ki a cikin su, don ki ji dadin rayuwa tare da su." Har ya yi maganganun shi ya gama ban tanka mishi ba, ban kuma dainan kukan da nake yin ba. "Ina kawayenki?" Ya tambaye ni yana kallona cikin nutsuwa 14 duk da bai furta ba, tsananin ramar da ya gani a tare da ni ya ba shi tsoro da tausayi. "Ki yi kawaye 'yan guda biyu ko uku za su taimake ki ki fita daga cikin damuwa mai yawa kin ji?" Ban amsa mishi ba, ya ci gaba da magana. "Ki maida hankalin ki akan karatunki, ki shiga duk harkokin da ake yi a makaranta za ki ji dadi yanzu mu je in kai miki kayayyakin amfanin da na zo miki da su." Ban tankaba, ban kuma musa mishi ba. Shake bayan but din shi ya yi da kayayyakin amfani gaba daya aka jide su aka shirya mini su a lokata da lokar yarinyar nan da ke kusa da ni Asabe Aliyu, duk yaran da muke daki daya kuma sai da ya ba su sabulai da omo da kayan tea, sannan ya kama hanya ya tafi ya bar ni ina ta faman kukan takaici wanda in ban da tsananin tsoron shi da nake ji da rike shi na yi na ce mishi ya kai ni kawai wurin Ummana. A haka na yi zaman makaranta, tun ban iya hidimominta ba har na koya kullum ba ni da wani aiki in na kwanta sai na lissafin ranar hutu. Ranar da Yaya Almu ya gaya mini kenan zai kawo ni gida in sadu da Ummana ranar da zuciyata ta rinka shakkun isowarta, saboda tsaikonta da nake 15 gani. Duk ranar ziyara dai Yaya Almu bai fashin zuwa, in zai zo kuwa hatta ruwan sha kawo mini yake yi, amma duk da haka a banza ban ganin alherin shi. Kawayena dai ba su da wata hira in banda hirar kai Yayan Rabi'atu yana sonta, ji rannan ma da ya zo ya yi mata abu kaza da kaza, muma ya ba mu abu kaza da kaza. Ni kam zuba musu ido kawai na yi ina kallon su. Ana gobe za a ba mu hutu kuwa ni kam kwana na yi idona biyu ko gyangyadi ban 1ya yi ba, saboda zumudi, gar na wayewa na gama shirina ko wanka ban yi ba na tasa jakata a gabana ina zaman jiran zuwan Yaya Amu da na rinka ganin kamar ba zai iso ba. Sai wajen karfe goma sha biyu ya. iso kan nan kuwa na riga na gaji da jira wai da ya kalleni sai ya ce mini; "Na dan sarara ne ki samu ki gama kintsa kayanki: " Ban tanka mishi ba, kawai yaran ajin mu suka biyo ni da jakata suka kawo mini ita cikin motar, Yaya Almu shi kuma ya kawo kudi ya ba su. A gida rannan Ummana da Baba Talatu kuka suka yi ta yi suna fyace majina ana ba su hakuri da suka ganni. 16 "Mu je in yi miki wanka in dirje miki wannan dattin da ya zauna miki a jiki, saboda rashin wanka mai kyau." In ji Baba Talatu. Na ce mata, 'A'a zan yi wankan da kaina." Da daddare muna kwance a kan gadon Umma tana kankame da ni, tanfar so take ta maida ni cikinta ta ce; "Bari hutun nan ya zo Rarshe zan ga yanda za a yi Lamido ya ce zai maida ke wannan makarantar ja'irin yaro káwai ya je ya kai ki wata munafukar makarantar da ya ki. fadar inda take balle in rinka zuwa duba ki inda na san inda kike ai ko ban rinka zuwa ganinki kullum-kullum ba zan je kowanne sati." Ni kam tun da Umma ta ce ba za ta bari Yaya Almu ya maida ni ba, na samu kwanciyar hankalinan da nan na dan yi kyau na yi kumari kibata ta soma dawowa. Kullum ina tare da Ummana ita da kanta dai ta yarda cewar wai zaman makarantar ya canzani na zama nutsatstsiya mai son aiki na daina zagin mutane ba na ma shiga harkar su in ba sune suka tsoma ni a ciki ba, to amma kuma ta kafe kan cewar wahalar ta ta yi yawa, don haka zan dawo gida a canza mini wata wacce za a ninka ba ni cikakkiyar kulawar da ta dace da ni. Shi kam Yaya Almu harkokin shi kawai yake 17 yi, tsakanina da shi dai ina kwana ne ina gajiya? in na yi kamar ban gan shi ba, kuma shima ya yi kamar bai san da ni ba, ni kuwa ko motsin tahowar shi na ji sai in yi maza na shige dakin Ummana, don ban son ganin shi. Rannan da safe ranar wata litinin ya shigo falon Unma da safe cikin shirin fita, shigar shi ce dai a tare da shi ta fareren kaya kamar kullum, kuma ya yi kyau yana sosa kunnenshi da dan makullin motar da ke hannun shi. "Ina Rabi take Umma? Ba tare da ta yi wani tunani ba ta ce misba, Tana ciki." Ya bude bakin shi ya kirani, "Rabi zo mu je nan ki yi mini rakiya." Kullum kalmar da yake amfani da ita kenan in zai ce in yi mishi rakrya, bakan nan ya sha fita da ni don haka abim ba1 zamo mana wani sabon al'amari ba. Mun fito mun hau kan hanya muna taifya ya dan juyo kadan ya kalleni kafin ya tambayeni, Yaushe ne butun makarantar ku zai kare?" Sai da na ji kirjina ya yi dam kafin na shiga kici-kicin kokarin tunanowa cikin fargaba da tsoro sai dai ban iya tunowa ba, saboda tun da ka ba mu hutun ban taba damuwa da son in san yaushe hutun zai kare ba, ni dai bukatata kawai ita ce in 18 ganni a gida. Tsawon lokaci ina nazari ban iya bashi amsa ba, sai shi da kan shi ne ya gaji ya ce mini, "Hutun ya kare tun shekaran jiya, don haka yanzu daukoki na yi zan maida ke makarantar kár kuma ki ce za ki yi mini kuka, don wancan karon wahalar da kika ba ni ba karama ba ce, in kika ce za ki sake yi mini haka a yanzu ba zan rinka zuwa duba ki ba." Kankame bakina na yi na rike don kar ya ji Rarar kukan da nake yi na yi ta zubar da hawaye kawai, har muka isa makaranta kuwa maganganu yake yi mini kan muhimmancin ilimi da kuma iya mu'amalla da jama'a. Muka isa makaranta ya bude bayan motar shi ya yi ta ciro jakankunan da ya riga ya yi mini.sayayya yara suka dibar mini jakankunan ni kuma na bi bayan su ina kuka. Ina shiga dakin mu yaran da na tarar a ciki suka hayayyako mini. "Kai Rabi'atu hutun ma ke da kuka ki ke dawowa? To Maman ki ta bar ki a gida mana kawai ta rinka dora miki tallan kamu." Gaba daya suka kwashe da dariya, suna fadin, 'Ai kuwa wannan za ta yi kyau da daukan tiren kamu da sassafe." To a kwana a tashi haka dai har na hakura na 19 saba da zaman makáranta, har na kwaci kaina wurin yaran da sakarcina ya sa suka rainani a farkon shiga ta makarantar a haka na kasance har na zo aji uku muka yi jarabawa na dawo gida ina Jiran fitowar sakamakona, har a wannan zaman ma Yaya Almu bai bar ni na sarara ba, samin ido ya yi ya kafa mini dokar tashi in je masallacin gidan mu da Asuba in yi sallah, bai yarda a ce mishi na yi a daki ba, in na zo másallacin ma wai sai na bari ya ganni tukunna kafin in bar masallacin in dawo daki. Ni kam cewa Umma na yi sai dai ya san yanda zai yi da ni ba dorina ba ya sa takobi ya fillce mini kai, in ga karshen kiyayya kenan da tsana. A ce tun daga nan sai na tafi har masallaci kafin in yi sallah? Umma ta zuba mini ido tanan kallona ta ce. Ba dai Babangida kike wa wadannan naganganun ba ko?" Na kara daure fuska na ce mata, Shi mana Umma ai kina kallon abubuwan da yake yi mini na 'yan ubanci, amma ba ki taba yi mishi magana ba." Ta kama baki ta Tike nuna alamar mamaki ta ce, "Babangidan ne mai nuna miki yan ubanci?" Na ce, "Eh mana." Ta gyada kai tare da cewar, "Lalle ba ki da 20 wayo." Sau biyu na san Yaya Almu ya kiranı ya jaddada mini dokar da ya kafa mini ta zuwa sallar Asuba a masallaci, bai kuma yarda in zo in tafi ba tare da na jira mun hada ido da shi ba, ni kuwa na yi ko in kula. Rannan da Umma ta zo tana tashina da Asuba ma kurma mata ihu na yi na ce, "Ni Umma ki bar ni ki daina tashina a wannan muku mukun sanyin." Ina jin Yaya Almu okacin da ya zo gaishe ta yana gaya mata har yanzu Rabi.ba ta soma zuwa sallar Asuba a masallacei ba, kamar yadda sauran yaran gidan suke zuwa? Umma ta bashi labarin sakarcin da na yi mata sanda ta zo tashina tana dariya da ta gama sai ta ce mishi ai ina ganin hakuri za ki. yi da wannan dokar sai badi war aka kan nan ta kara kwari. Bai ce mata komai ba ya sauko musu wata hirar. Washe gari

Chapter 1 of 8