Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
3 / 5
zoba, d’inki ma, tabar zuwa sabida bala’in Gwaggo, wai sai Malam ya saka su duka, don su Beeba su samu suma mai saya musu kaya. Malam ko yace”bata isa ba, tayi k’ad’an ta gindaya mishi sharad’i yabi. Tunda tun farko, Khadi ne tafara cewa tana so, dan haka ba zaisasu ba. Zaban tayar musu da hankali yasa Khadi ta samu Malam tace” Baba bana jin dad’i zan d’an huta da zuwa aiki, kafin wata sati, Tukun ya hak’ura. Dr Umar ko, bai da tunani da yawuce na Khadijat, so ya kemata, wanda shi kanshi, bazai iya auna shi, a mizani ba. Masu karatu zamu so musan, WAYE DR UMAR? Umar Adam Naira, shine cikaken sunansa, d’a, d’aya tilo girin Adam Naira. Adam naira haifafen d’an Kano ne, nan yayi karatunsa, har ya girma, ya Auri maransa Maryama, sun dade da aure, Allah bai basu haihuwa ba, sai daga baya Allah ya azurta su da haihuwan Umar, wanda yaci sunan Baban Mum d’insa, bayan shekaru da yawa, ta haifi Ilham, wacce itace auta, a yamzu haka. Alhaji Adam Naira yarike muk’amai, na gwamnati da dama. Wanda yanzu haka shine gwamnan Kano State mai ci. Ya kasance mutum ne mai kwatanta gaskiya da adalci, hakan yasa al’uman garin Kano ta Dabo suke sonsa. Tunda Umar ya taso, shi bamai son yawan, hayaniya bane, sannan bai kula yan’mata,sai wata yarinya, Sakina da ta makalemasa, sam bata cikin tsarinsa, don bata da kamun kai, yar’gidan, matai makin governor ne, gata da rashin kunya, shiyasa basa shiri. Yanzuma saukin da yasamu, ya dawo yasamu sun fita waje, ita da Mum d’inta. Iyayensa burinsu shine, yayi aure amma baya kula yan’mata. Tun randa ya had’u da Khadi, tunda yasanar da Mum d’insa, da murna ta, tasanar da His Excellency. Yayi farinciki ba kad’an ba. Yace” yana dawowa zasu samu iyayen yarinyan, ayi magana a sanya rana.wanna shine labarin Umar a takaice. Dr Umar zaune yau, sai tunanin Khadijat, da ya damesa. Key mutarsa ya d’auka, yana fitowa securitys, suka fara gaidasa, da gudu suka bud’e masa, k’ofar motan yashiga, gida ya nufa yayi wanka, dun zuwa gun Khadi. Yayi kyau sosai, ya shiga mota shi kad’ai batare da security’s ba, ya nufi gidan. Khadi ko tunda ta tashi, tashi tana son yin wanka, kayan da Dr Umar ya kawo mata. ta d’auko wani less, mai kyau purple da duwatsu farare a jiki. Tayi kwaliya sosai, ta kuma yi kyau. Kasancewan yanayi gari, da sanyi, gun sai yayi, bada yanayi mai kayatarwa. Gwaggo ta shiga makwabta, sai zuba take musu. Yaro ne yashigo”wai ana salama, da Khadijat inji Umar. Tace”kace ina zuwa. Yana fita ta d’auko hijab d’inta fari tasa, bakaramin kyau tayi ba. Cikin nutsuwa ta fito, tunda Umar ya hangota, zuciyar sa sai harbawa, ido ya k’ura mata. Gwaggo da tafito daga, gidan su abula, ganin Umar acikin k’atuwar mota, nan zuciyarta ya fara tafarfasa. Yau mai zanyi ma Khadi na huce?. Wata zuciya tace”kawai ki d’auko wuka ki burma mata. Mtss a’a za’a kamani, can shaidan ya tuna mata, kawai ki shek’a mata ruwan sanyi, tunda bata so. Da sauri ta koma gidan Abula, tace”dan Allah samin ruwan a fridge d’inki. Sam Abula bata kawo komai ba, ta iba mata, a karami roban plastic. Da sauri tayi gida, ta k’ara dana randa, kamar wata mahauk’aciya ta fito. Dr Umar ya shagala, da kalon Khadi, itako tana wasa, da yan’yatsun hannuta. Sai jin shaaa… sukayi, take idon Khadi ya kafe, numfashinta ya d’auke, ta tafi luuuuu zata fad’i kasa. Da sauri Dr Umar ya fito, yana kiran sunanta, tareta yayi ta fad’i a hannusa yana jijigata, amma sam bata ko motsi. 9:12] ﻡﺩﺮﻛ ﻪﻠﻠﺗﺪﺒﻋ ﺓﺪﻴﺷﺭ PM, 9/14/2016] Rash Kardam: YA’YA DA DUKIYA BA’A K’ETARSU NA ©RASHEEDAH .A. KARDAM. Pg-81~85. Malam sun isa Asibiti, direct office d’in Dr Abdul sukaje, Don tambayansa, ko nan aka kawo Khadija, don shi har yanzu, bai san a ina, Dr Umar yake aiki ba. Duk da yasan dai, shi likita ne, suna zuwa suka tarar da Dr Abdul a office, cikin yanayi damuwa Malam”ya gaidashi, ya tambayes ya aiki?. Alhamdulilah!, Malam yace”Dr dan Allah, ko nan asibitin, aka kawo Khadi?. Dr Abdul ya amsa masa da eh!. Barin rakaku d’akin da take. Sai da sukayi tafiya mai d’an nisa kad’an, kafin suka shiga, wani Ward mai kyau, kana shiga, falo zakagani babba, sai gurin da likitoci ke zama, gefe kum d’akin hutun likitoci ne. Sai d’akuna da suke jere, gwanin birgewa, gurin tsab da shi, kamar ba’a cikin asibiti ba. Kowani d’aki gado d’ayane a ciki, sai yar loka da ke gefe, Malam suka tura, qofar d’akin da sallamansu. Dr Umar ne zaune ya zabga tagumin gaban Khadi, sam bai masan sun shigoba, suka sake mai-maita sallama, amma shiru, Dr Abdul ne ya isa gunsa da sauri ya dafasa, yace”my friend, cikin razana ya d’ago, sai a lokacin yaga Malam, duk kunya ta rufesa. Mik’ewa yayi da sauri, yana musu, sannu da zuwa. Kalo d’aya Malam yayi ma Khadi, yaji wani mugun tausayinta, ya kamasa, tambayan kamsa yayi anya bayi da laifi, shima acikin cutar da Khadi, da Gwaggo takeyi?. Idonsa ne ya ciko da kwala, bakin gadon yaje, ya rike hannuta, cikin muryan damuwa, Yace”Khadijatu kiyafr min, duk nine silan saki, cikin wannan damuwar. Tabbas Hauwa watarana sai tayi nadama, mai d’umbin yawa, Allah ya miki Albarka, ya Allah kajikan Adamu. Duk wanda suke gurin saida jikinsu yayi sanyi, Beeba kam kuka takeyi sosai. Malam ya juya ya kali, Dr Umar yace”Umaru na rasa, da wani irin, kalma zan gode maka. Tabbas ka taimaki Khadijatu iya taimako, Allah ya bamu, abunda zamu saka maka dashi.Allah ya maku Albarka Cikin zuciyan Dr Umar yace”abida zaumin kad’ai kubani Khadijat, don zuciyata, takamu da azaban sonta. Gwaggo da ke gida, sai fatan take, “Allah yasa adawo, da gawan Khadi. Na tsani ganinta, kamar mayya, komai zakamata bata zuciya. Mtsss ina da daga nan, tashiga uwa duniya, in huta da fitinaniyan, yarinyannan. Ko da taji Beebah tabi Malam, sun tafi asibiti, bakaramin haushi tajiba. Tunanin kalan, rashin mutuncin da zan masu. Kwanan su Khadi, biyu a Asibiti, Dr Umar shi ke d’awainiya da su. Kulum yana hanyan Asibiti, yana tashi daga aiki bayan ya duba Khadi, shagon waya ya zarce, yasaya mata, iPhone 7, wayar ta had’u. Gida yanufa, yana zuwa, yayi wanka, ya fito dining, Iham ce tazo tazauna a gefensa, tana masa surutu, can idonta ya kyalo waya maroon, tace”bros wannan fa?. Tare da kai hannuta ta d’auka, “bros wayan tayi kyau, bai kaleta ba Yace”na Khadiyat ne, ihu tasa tare da cewa”wooow wayan tayi kyau. Barin samata number, nan harda WhatsApp, ta bud’e mata. Sai da yagama tukun ya amshi wayan yafita. 9:12] ﻡﺩﺮﻛ ﻟﻠﻪﺍﺪﺒﻋ ﺓﺪﻴﺷﺭ PM, 9/14/2016] Rash Kardam: YA’YA DA DUKIYA BA’A K’ETARSU NA ©RASHEEDAH .A. KARDAM. Pg-86~90. Sai da yayi musu, sayya mai yawa, ya nufi Asibiti. Ko da ya shiga, sai da ya biya office dinsa, ya ajiye wasu files, kafin ya nufi ,d’akin da su, Khadi suke. Da sallama ya shiga, suka amsa masa. Beebah ne “ta gaida shi, cikin girmamawa ya amsa, “ya tambayeta ya mai jiki?. “Ba shi amsa da sauki Alhamdulilah!. Fita tayi ta basu guri, ya kali Khadi da ke kwance, “ta gaida shi, cikin muryan, marasa lafiya, “ya amsa mata, tare da tambayan ya jikinta?. ta bashi amsa da sauki. Ido ya zuba mata, har saida tasoma jin kunya, ajiyar zuciya ya sauke, ya kara lumshe idonsa, a hankali ya bud’esu, cikin wani salo, da karya murya, ya kira sunan Khadeejat!!!. Duk da rashin lafiyan da take fama dashi, sai da taji, jikinta yamata, wani iri,”Na’am ta amsa masa cikin siririyan muryanta. Ya kaleta, yace”Khadeejat!. Na kasa hak’uri akanki, Khadeejat!. Ki taimaki zuciyata, da take fama da azaban sonki, My Khady tun randa, na fara d’aura idona a kanki, nakamu da qaunar ki, ki taimaka in samu gurbi, a cikin zuciyarki. Duk maganan, da yakeyi Khadi, bata ce komai ba. Sai lumshe idonta datayi, kamar mai jin bacci, cikin kasa-kasa da murya, harda d’an sauk’owa daga kujera, Yace”pls Khadeejat ki taimaki rayuwata. Tabbas nasan ina aure ki, a matsayin mata, kuma uwar ‘YA’YA NA, nasan zasuyi alfahari dake, a matsayi uwa ta gari. Khadeejat!. Ki sani duk wani abunda akeso, mace ta gari ta had’a, kin had’a. Khadeey na!! I’m deeply in ur love,pla don’t let me go!! You d joy of my lyf, pls n pls Khadeey!!, ki samamin matsuguni, a zuciyarki, ko k’ad’an ne. Ganin shiru batace komai ba, Yace”Khadeetaul~Kubrah, in kin amince pls ko murmushi, kimin in samu sanyi, a zuciyata. Ganin shiru yasa yanayinsa ya canza, duk da idonta na rufe, tana iya ganinsa, amma shi bai lura, da hakan ba. “Wani lallausan murmushi ta saki, tare da rufe fuskanta. Ganin haka, ya sauke ajiyar zuciya, yayi godiya ma Allah. Juya masa baya tayi, duk yanzu kunyansa, ta soma ji, ya dad’e yana mata hira, ganin tana jin kunyarsa, ya ajiye mata waya tare da mikewa, Yace”yau k’anwata kunya na takeji, amma badamuwa, wataran zanyi maganin kunyan nan. “Ga wannan d’an ajima zamuyi waya, ya fita abunsa, a waje yayi sallama da Beebah. Ko da tashi go d’aki, lokacin Khadi ta mike, sai murmushi take zubawa, Beebah tace”Addah lafiya naganki cikin wannan fara’a?, cikin zumud’i ta labarta ma Beebah, itama tayi murna sosai,nan suka bud’e, kayan da yakawo musu, yasha addu’a kam, suna bud’e na waya, kalo ya koma kansa, sun yaba da kyan, wayan sosai. Sai can dare taji wayar na k’ara, ko da tad’aga wayar kasa d’aukan kiran, duk sun rasa ma ya’akeyi, Beebata tayi nata basiran ama ina! Har wayan ta yanke, sai can dai Khadi tace”tsaya inaga wannan, ruwan ganyen ne amsa kira, do d’azu jan ya katse ne. Tana jan ruwan ganyen, ta tafara jin magana. Assalamu’alaikum! Wa’alaikumusalamu! Ta amsa, sai tayi shiru, ” Khadeejat ya jikin?. “Da sauki Alhamdulilah!. Hira ya rinka janta dashi, har sai da yaji, kamar bacci na son d’aukanta, ya kyaleta. Kwanan Khadi 7 aka sallameta, tayi fress kamar batayi rashin lafiya ba, suna dawo gida, suka samu Gwaggo bata nan, suka shiga, harda Dr Umar ganin irin yanayi, d’akin da Khadi take kwana, ransa ba dad’i ya kira waya, ba’a fi minti talatin ba, sai ga mota da sabuwar Katifa, irin manyan nan, da filo da bargo, aka gyara d’akin fess, ya musu sallama ya tafi, ko da Malam ya dawo yayi godiya, ana haka sai ga Gwaggo. Yau kam ta cika kamar zatayi hakuka, don ba haka taso ba, taso a fitar da kayan amma Malam ya hana. Rayuwa sai tafiya yakeyi, soyayya tsakanin Khadi da Dr Umar sai abunda ya karu, kulum suna gaisawa da Ilham, harta sata a group d’in novel ta yi kawaye yanzu. Duk inda kake da jama’a, baka rasa yan gulma, acikin mukaraban, Dr Umar ansamu wanda ya sanar da Sakeenat, Dr Umar yana neman wata yarinya, yanzu haka ana kan shirin magana Aure, nan take hankalinta ya tashi, bashi ta biyo jirgi yau ta tazo 9ja. 9:12] ﻡﺩﺮﻛ ﻟﻠﻪﺍﺪﺒﻋ ﺓﺪﻴﺷﺭ PM, 9/14/2016] Rash Kardam: YA’YA DA DUKIYA BA’A K’ETARSU NA ©RASHEEDAH .A. KARDAM. Pg-91~95. Karfe shidan yamma, jirgin su ya sauka, acikun garin Abuja. Bata bata lokaci ba, ta sake shiga jirgin Kano, ko da ta iso, anyi sallah magriba, ana shirin yin isha’i, taso yau taje taga yar gidan uban waye, Dr Umar ke sonta, kuma da me tafita da shi, da har zai aureta, tabbas yarinyan sai ta raina kanta, washe gari da had’a security dinta, wankan kece raini tayi, ta kira kawarta, Zulaihat tace”Zuly ki shirya kizo, zaki rakani, wani karamin unguwa, wai shi Dakata. Cike da tsokana Zuly tace”kawas mai zaki dakata acan, nan Sakeenat, ta sanar mata da komai, Zuly tace”ban minti kad’an ina zuwa ko ku biyo ku d’auken. Haka akayi, suka dauketa, cike da rashin mutunci a fuskokinsu. Khadi ko wanka tayi, sabi da tasan yau weekend, Ya Umar d’inta zaizo, tayi kyau kamar wata amarya. Suna tsakar gida suna tad’i’ ita da Beebah kasancewan, Gwaggo ta tafi gidan kawarta, shiyasa suka sami freedom yau. Tun daga nesa suke jin, wi wi wi wi, kukan jiniya alamar, wani babab yazo unguwan, har sai da aka zo qofar gidansu, tukun kukan ya tsaya, cikin mamaki suna jira suji maisu shigowa, Khadi tace”Beeba kardai police ne suka zo gidannan?. To wayayi laifi?. Tana wannan tunani ko taga masu bakaken kaya, suna shigowa cikin gidan, nan take hanjin cikinta ya kad’a. Sai da suka shigo, sun tsatsaya musu, wasu yan mata ne biyu, su ka danno kai cikin gidan, kalo d’aya zaka musu ka gane, sun san bariki, idonsu abud’e yake, ga fiskansu ta sha man bleaching. Cikin isa da taunar chewing gum, ta iso gaban su, sai da suka musu kalon, sama da kasa, kafi ta juya, ta kare ma gidan kalo. A tare suka kwashe da dariya, Zuly tace”kai yayan talakawa, a cikin ku waye Khadi ko Khadija, shiru ba wanda ya bada amsa. Cikin zafin rai suka sake magana, da kyar, Khadi tace” gani nice Khadi. Sai da suka kaleta sama da kasa, sai da gaban Sakeenat ya bmfad’i don sai yanzu ta lura da Khadi, tabbas yarinyan ta had’u, dole Dr Umar ya makance a sonta. Daurewa tayi, ta fara yi ma Khadi, “concrete warning, duk randa naji ance kin kula Umar sai na muki rashin mutunci, sai nasa an d’aureki, tabbas duk halin naka-naka ne, mai rashin kunya ma wataran yana da rana. Beebah da Khadi kasa magana sukayi, Rabee’at dake bacci a d’aki, hayanayi ya fitar da ita, jin yanda, aketa zaginsu, dana iyayensu ta karaso da gudu, ta kalisu Sakeenat, ta sama da kasa, ta nuna su da yatsa, tace”banza mai fiskan biri, kin wani sha bleaching, waye ke?. Da har zakina zagin iyayena, nan Rabee’at tashiga sauke musu, kwandon rashin kunya. Dr Umar yayi wankan sa ya nufo, gidan su Khadi, tun da ya shigo unguwan ya fara ganin motoci, har ya iso qofar gidansu Khadi, nan yaga security, gidan gwamnati, da sauri ya fito daga mota, ya kira wani body guard, tambayesa mai ya faru, nan yake basa bayani, Sakeenat ne a ciki, da sauri ya shiga gidan, dai-dai likacin da, Sakeena ta harzuk’o zata mari Rabee’at da sauri Khadi, ta shiga tsakanin su, sai jikayi tasss!!, karan saukan mari a fiskan Khadi, kafin ta motsa, sai nasojin wasu karan tass!! Tasss!! Tass!! Gar sau uku, Dr Umar ya mari Sakeenat. Ya juya ya kali security d’in, da sauri suka bar cikin gidan. Cikin fushi ya kali Sakeenat, Yace” kee waya baki izinin zuwa gidan nan?. Duk randa na k’ara, ganin k’afarki sai kinji ajikinki, ki kuma sani Khadeejat ta miki nisa, itace uwar ‘YA’YA Na, ita nakeso, itace rayuwa, farinciki na, in part rayuwata bazatayi dai-dai ba in ita, banza sakarya, ko ana soyayyan dole ne?. Nace bana sonki bana sonki, ba kuma zan soki ba. Cikin b’acin rai yazo, rik’o hannu Khadi yace”My wife kiyi hak’uri dan Allah, hannu yasa, ya share mata hawayenta. Ya rike hannuta, ya Sakeenat da bakin ciki ya isheta, kaman ta shid’e a gurin. Yace”kee Sakeenat! Kinga wannan ta fi minke komai, itace mahad’an rayuwa ta, tafiki kamun kai, da nutsuwa, in kin…… Da gudu ta bar cikin gidan tana kuka, wi-wi da hawaye. Tabbas yau taja ma kanta raini agaban, wayanda take takasu son ranta, yau Umar ya mata haka?. Tana fita mota tashiga, Zuly ma ta biyota, rake suka bar unguwan. 9:12] ﻡﺩﺮﻛ ﻟﻠﻪﺍﺪﺒﻋ ﺓﺪﻴﺷﺭ PM, 9/14/2016] Rash Kardam: YA’YA DA DUKIYA BA’A K’ETARSU NA ©RASHEEDAH .A. KARDAM. Pg-96~100. Tana fita suka nufi gida, da gudu ta shige d’akinta, kuka ta rinka rusa sosai, Hajiyarta ne ta shigo, tace”Zuly mai ya sami k’awarki ne?. Zuly tafara bama labarin komai. Hajiya tanisa tace”Zulaihat ba ki ba ma kawarki, shawara mai kyau, tunda Umar baya sonta, sai ta hak’ura, ko ana son dolene, kusani a ko da yaushe mace, ita ke jan kimarta, nikam bazan goyi bayan k’arya ba. Kunutsu kusan mekukeyi kun fa girma fa, ae ko irin shigan da kukeyi, wazai so ku?. Inayi fad’a Abban su Sakeenah, yace nacika takura masu, ga irinta nan, nima ina goyon bayan Umar, matsawan ba canzawa kukayi ba. Kukan Sakeenat ya karu, sai buga k’afa takeyi, tana cewa”Hajiya ni baki sona, tunda bakison abunda nake so, “tsawa ta daka mata, ke bana son aakarcin banza da wofi fa, sai da tamusu ba dad’i, tukun ta bar d’akin. Dr Umar kuwa lallashin Khadi yayitayi, Gwaggo ne ta shigo da sallamarta, tun daga waje an fata rahoto, shiyasa take fara’a, tana ganin Umar, tace” eehehe duniya yau taimin dad’i, in dai a kanka ne, da Khadi naso da dukan tsiya suka mata, ka wani shigo mana gida d’an iska, wato karuwanka ne suka kasa hak’uri suka biyo ka nan?. Ran Umar in yayi dubu ya baci, don ba abuda yatsana kaman a danganta shi da mazinaci. Gwaggo ta zagesu tass shida Khadi, tayi d’aki, Beebah ko sai basu hak’uri takeyi, Khadi kam kuka takeyi, kafansa yaja jiki ba kwari ya bar gidan. Malam ya na dawowa ya samu labari, yajima yana tunani daga k’arshe, yace anya kuwa bazan dakatar, da Umar da zuwa gidan nan ba?. Haka ya ta sake- sake, har ya tsayar da amsa ma kansa. Bayan kwana biyu Umar yazo, tun a waje suka gaisa da Malam, nan ya fara ba ma Malam hak’uri, Malam yace”ba komai ya wuce, amma inaga ka hak’ura da zuwa kawai, tunda daman ba wata alaka bace a tsakanin ka da Khadeejat, cikin firgici ya d’ago, yanaso yayi magana ya kasa, Malam yajima yana zargin Umar na son Khadi, amma bai furta ba, shiyasa yayi hakan don ya tabbatar. Don zan bada dama ga mai sonta ya turo magabatan sa, ayi magar Aurenta kawai. Inaga hakan shine zai zame mata hutu, Umar duk ya rud’e, yakasa magana jiki ba kwari, yabar unguwan, gudu yakeyi Allah ne ya kaisa gida lafiya, yana zuwa ya tarar da Mum a falo, gunta ya nufa, ya kwantar da kansa, a kan cinyanta, sai ga hawaye. Cikin sanyin murya yace”Mum zan rasata, Mum ki taimaka min, pls dan Allah!. Cikin rashin fahimta Mum tace”wacece zaka rasata?. Ajiyar zuciya ya sauke, Yace”Mun Khadeejat ce, Mum tace”kamar yaya zaka rasata?. Nan ya kwashe labari, ya fad’a ma Mum komai. Tab lallae Sakeenat bata kyauta ba, amma ko da Dad d’inaka bai dawo ba zamuyi waya dole asan abinyi. A yan kwanakin nan duk Dr Umar ya rame, hakan yasa Mum, ta sanar da Dad d’insu, ko da sukayi magana dashi, yace”bazai samu daman dawuwa, a satin ba don haka zai sa mataimakinsa, yaje da kansa, Mum tace” ni a’a ban yarda ba, kasan Alhaji Bashir baya da sauki, akan yara , kawai inaga zamu nimi wani yaje, kuma kaga yanda yakeson Sakeenat, komai zai iya yi. Dad yace”shikenan duk yanda kukayi, Mum ta sanar da Umar komai yayi murna, sanna yace”shi yanaga a tura Baba Liman, don yana da halin dattaku. Haka ko akayi, Baba Liman yaje neman auren Khadi ma Umar, basu wani samu Matsala Baban Khadi ba ya amince. Nan suka zuba kayan mun gani anaso, da kud’in gaisuwa dubu 2k, Malam yaki karba yace sunyi yawa, amma Baba Liman ya dage sai da ya karba. Da murna yashiga gida, a zuciyar shi, yana mai cewa tabbas Khadijansa zata huta, don da alama Umar d’an manyan mutanene, kuma zai riketa da AMANA. da murna ya shiga gun Gwaggo, cikin zak’uwa takaleshi “Malam lafiya naga sai farin ciki kakeyi?. Hmm kedai bari kawai, ina cikin farin ciki, mik’omata su gidan goro da catoons d’in minti yayi, tare da d’aura mata damin kud’i akai, ido ta zaro su waje, “Malam wayan nan kud’in fa da kayan fa?. Cikin murmushi yace”na Khadijat ne, kud’in aurenta. Jakar uba! Ina bazai yuba, ina na Beeba ko Rabee’atu?. To ba a gidan nan za’ayi wannan abun ba, sai dai ko inda Beeba ne. Malam yayi dariya yace”Hauwa kenan wai meysa ba kya boye hassadanki a fili, ae ni na d’auka Khadi da Beeba da, Rabee’at, duk d’aya suke a gunki?. Allah ya sauwake, nawa-nawa ne. Kuma wannan auren bazai yuwuba, sai dai ko in zaka kawo na Beeba sai a had’a. Shikam dariya ta basa, don suk tagama fita a hayyacinta, ya d’ibi kayan ya kai d’akinsa. Khadi najinsu amma duk ta damu da taji wa Malam zai had’ata aure da shi?. Malam ne ya shigo d’akinta, ya zauna a kujera, cikin nutsuwa ya kira sunanta, ta amsa, sai da yamata nasiha, kamar yanda ya saba, tukun ya saida mata, Umar ya kawo kayan ,yagani yana so, ina fatan kin amince kina sosa?. Shiru tayi, daga yanayinta ya gane ta amince, albarka ya samata ya fita. Washe gari Dr Umar yayi wanka sa, yayi kyau sosai, sai da yabiya Sahad ya mata shooping mai yawa, tukun ya nufo gidan, yaro yasamu ya aika ta fito. Cikin nutsuwa take takawa, tana sanye da hijab ash yamata kyau, hannu tasa a aljihu yana kare mata kalo. Da sallama ta karaso bayan sun gaisa, yace”gimbiya Khadeejatu, murmushi tayi yace kali nan, tana d’ago fuska ya kashe mata ido d’aya, tare da d’aga mata gira, duk sai taji kunya ya kamata. Haka sukayi hiransu a zaure, sai dab zai tafi ya d’ebo mata, kayan saya mata, godia ta masa har zata tafi yace”tsaya barin yi surprising d’inki, murmushi tayi. Yace” pls close ur eye, ba musu ta rufe, ” miko hannuki, bata komai ba ta mika masa tana murmushi, wani zobe ya ciro sai kyali yakeyi, ya sanya mata a hannu, nan take hannuta ya d’au kyalu yana haskawa. Kiss ya kaimta a hannu, sai sukaji, la ha ila ha illalahu, uhu jama’a da sauri Gwaggo ta damke su duka. Ta kwalala jama’a ku kawon d’auki na kama yan iska yau. Ihu take kamar mahaukaciya, Khadi ko duk jikinta sai bari yakeyi, nan take hawaye ya fara zuba, Umar ko don takaici kasa motsi yayi. ﻡﺩﺮﻛ ﻟﻠﻪﺍﺪﺒﻋ ﺓﺪﻴﺷﺭ ]9:12 PM, 9/14/2016] Rash Kardam: ’YA’YA DA DUKIYA BA’A K’ETARSU NA ©RASHEEDAH .A. KARDAM. Pg-101~105. Cikin takaici ya fincike rigansa, kalon tsana yake mata, da sauri Gwaggo ta sha gabansa, yau fa sai na tona muku asiri. Wani mugun kalon da ya aika mata, yasa Gwaggo bashi hanya, Khadi da gudu tabar gun. Gwaggo ta ga kayan da Dr Umar ya kawo da rawar jiki ta d’iba tayi cikin gida. Beeba na ganin haka tace”Gwaggo mai yasa keke ma Addah Khadi haka?. Gwaggo cikin zumud’i tace”kee bari kawai ae ido da ido na kamasu suna iskanci, cil da cil ganin annabin tsohuwa. Beeba tace”kai Gwaggo gaskiya Adda Khadi bazatayi haka ba, zata taba zubar da mutuncinta ba, kuma na yarda da tarbiyan da Malam ya bamu. Cikin b’acin rai Gwaggo tace”oh to! to! Wato Malam shi ya kula da tarbiyan ku bani ba?. Beeba shiru tayi ganin Gwaggo ta d’au da zafi. Malam na dawowa Gwaggo da munafurci tazo ta fara labartawa Malam, Malam ya kaleta sama da kasa yace”tashi ki ban guri bana son gulma, a yanzu a kwai wani abunda zaki fad’an na yarda, bacin nasan irin tsanar da kikayi ma Khadija, yarinyan mai hankali, bataji ba bata gani ba, kna gallaza mata, jiki ba kwari Gwaggo ta bar d’akin. Dr Umar ko hankalisa kwance ke gudanar da aiki, yanzu Dad d’insa kad’ai ake jira a kawo sadaki, sai asaka ranar biki. Sakeenat kuwa sam Mum d’inta, taki goya mata baya. Hankalinta duk ya tashi, can ta tuno wata shawara, Zuly ta k’ira a waya. Tace” kqwara kina ina ne yanzu?. Zuly tace”gani a hanyan zuwa gidan ku. “Ok sai kin iso. Ta ajiye wayar tana zaman jiran zuwan Zuly. Ko da Zuly tazo bayan ta gaisa da Hajiyar Sakeenat, tashiga gun Sakeenat, bayan sun zauna Sakeena tace”kawa nifa bazan share mari da Umar ya minba gaskiya. Zuly tace”wani mataki zaki d’auka?. Sakeenat tace”na bayar a sayo min dorina hud’u masu kyau, zamuje unguwansu ba tare da securitys ba, in munga yarinyan ko mu aika tazo sai mu cazata.Zuly tace”good idea, haka zamuyi. Key motarta ta d’auka suka fita,nan idi security ya kawo mata sak’onta, ta karba suka ja mota sai Dakata. Sun dad’e a unguwan Khadi bata fito ba, can da suka gaji yaro suka tura yaro ya kirata, Khadi ko kamar bazata fito ba, amma can da yaron yasake dawowa, ta d’au hijab d’inta tace”Beeba ana kira na a waje barin duba ga wayata nan. Khadi na fitowa yaron yace”gasu can a wancan motar. Khadi tana ta raba ido, don Umar bai tab’a zuwa mata da irin motar ba. Sakeenat ko suka rike bulala kowa ne bibiyi a hannusu, sai da Khadi tazo kusa suka bud’e motar atare, suka nufota da gudu dukanta suke tak’o’ina. Khadi ihu take amma basu kyaleta ba, Beeba taji kamar muryan Khadi da gudu ta lek’o ganin ana dukanta, koma gida “Gwaggo dan Allah kizo, yaran ranan suna dukan Adda Khadi, Gwaggo tace”ha da gaske Beeba tace”eh!. Duka suka fito da gudu. Dukanta ko suke Gwaggo ta fara kukara mata, kunyi min dai-dai. Rab Beeba ya b’aci sosai, ganin ba mai ceton Khadi, gashi ba maza a gun, yasa ta tuna da Dr Umar. Da sauri ta duba call history, ta kira number, bugu biyi yad’aga, “hello hello Ya Umar kazo ga wasu na ta dukan Adda Khadi, wanda suka zo ranana. Cikin figici yace”what suwaye?. Kashe yawar yayi ya shiga mota gudu yake kamar zai tashi sama. Sakeenat ko ganin sun mata lilis, ga mutane sun soma taruwa da gudu suka shiga mota, suka bar unguwan. Dai-dai zasufita a layi motar Dr Umar yadanno kai ganin motar Sakeenat yasa yasha gabanta, ganin zai tsaresu yasa taja motar da k’arfi sai da ta buge masa glass d’in mota ta gudu. Da har zai bita sai ya tuna kowani hali Khadi take kuma?. Sai ya fasa ya kara gudu. Beeba ko ganin sun tafi dakyar wata makwabciyar su, ta taimaka mata suka shiga da Khadi gida. Karkuga fiskan Gwaggo fal farin ciki. Dr Umar na zuwa yaga mutane, da gudu yayi salama ya shiga gidan, Beeba ya fara karo da ita cikin damuwa ke tambayrta ina Khadija?. Hawaye ya k’ara zubowa “tana d’aki a kwance. Yana shiga yaga halin da take ransa ya b’aci sosai. Ya kira beeba yace” ki had’a ruwan zafi don tayi wanka, waya ya kira ba afi minti goma ba sai ga wasu ma’aikatan asibiti da kaya, da kanta yamata treatment, ya mata allura nan take bacci ya d’auketa. Yana fitowa yace”sistet Beebah barinje gida na dawo. Na mata allura ta samu bacci, in ta tashi ki kaimata ruwa ta watsa zataji dadi. Yana zuwa gida yasanar da Mum d’insa komai, cikin bacin rai takira His Excellency yana d’auka, tace” ranka shidad’e! Ya aiki?. Cikin jin dad’i His Excellency ya amsa. Nan ta sanar masa da komai, sai

Chapter 3 of 5