Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
2 / 5
da guri ya lafa,Dr Abdul yace”Baba ka same ni, a office d’ina. Biyosa yayi, suka nufi office d’insa. Sai da Dr ya zauna, yace”Baba ka zauna, magana zamuyi da kai. Malam ya zauna, ya na fiskantan Dr, gurin shiru kusan, na minti biyu, kafin Dr ya nisa yace”Baba ina son in tan bayeka ne game da Khadija.miye alakarta da wannan matar? Kusan yawanci lokuta, in kun kawo Khadija ba ta da lafiya, matan nan sai ta mata abun da zai kunta ta. anya kuwa mahaifiyarta ce?. Malam ya nisa yace”gaskiya ba mahaifiyarta bane, Khadija yar riko ne a hannu mu, nan Malam ya kwashe tarihin Khadi, ya basa a takai ce, ba Dr Abdul ba, ni kaina Rash na tausaya mata.wayar sane tayi haske alamar kira ya yanke, d’agawa yayi, ya ga duration wajan awa d’aya da rabi, sai alokacin ya manta, bai kashe wayar ba. Dr Umar da ke jin, duk abun da ya faru da Khadi, tare da tarihin rayuwan ta, take yaji yana son tai maka mata. Ta bashi tausayi, da ace yana 9ja da ya san abunyi, kwanciya yayi, a lafiyayen gadon sa, fiskansa yana kalon silin, cike da tunani kala-kala, har bacci ya d’aukesa. Dr Abdul ya nisa yace”gsky Baba ya kamata ka d’au mataki, don yarinyan nan, tana yawan aiki da ruwa, ga wahala ya mata yawa. Malam yace”nagode in Allah ya yarda, zan d’au mataki, sallama ya masa ya koma, gunsu Khadi da har a lokacin, kuka takeyi sosai, ko da ya iso, ya kalleta cike da tausayawa, yace”Khadeejatu~Kubrah!, ki kara hak’uri akan na da, nasan ki mai biyyace, duk da Gwaggo tana cutar da ke, kuma kina hak’uri, ki ‘kara akan na da, kinji ‘yar albarka, kai ta d’aga masa alamar eh!. Sanna tace”Baba ka maida Beeba gida, tunda Gwaggi bata son zamanta anan. Murmushi yayi, yace”Beeba ba inda zata koma, har sai an sallame ki, Beeba ‘yatace nafi, Gwaggon ku iko akanta. Nan ya ta gaya mata kalamai masu dad’i, har ta mance da muwarta, dariya suke yi, ita da Beeban ta. Gwaggo ko da ta koma gida, taringa masifa da zage-zage, har Malam ya dawo bata daina ba, har tana cewa”kasake ni mana, tunda yarinyan ta lashe kurwanka, d’aki ya shiga, ya kyaleta ta gama sababinta. Kwanan su Khadi biyar, a cikin Asibiti aka sallame su, tun a hanya take far gaban, dawowa gida, don bata san dame, Gwaggo zata tareta ba. Dr Umar kuwa tunda yaji labarin,Khadi yaji yana son tai maka mata, yarinyan ta bashi tausayi. Wayarsa ya d’auka ya kira Dr Abdul bayan sun gaisa yace”ya aikin dai? Daga ban garen Abdul yace”Alhamdulilah! Aiki ba dad’i. hira sukayi sosai, Dr Abdul yake tambayar Dr Umar yaushe zaka kare course d’in nan?. Ajiyar zuciya yayi, kafin yace”saura wata shida mu gama, nima na damu in dawo 9ja, nayi missing abubuwa da yawa. Cikin zolaya Dr Abdul yace” harda Baby Sakina ko?. Mtss yayi d’an tsaki yace” ana ta kai, waya ke ta kaya. wannan mayyar yarinya, maras kamun kan, ina zan kaita?. Ae saninta ya fi nawa. Yauwa ranan wacece naji ana hayaniya akanta?. Rannan muna waya da kai, kamar a Ward d’in mata ne, sai da Dr Abdul ya d’anyi tunani kafin yace”ok! Khadijat ne, nan ya kwashe, labarinta ya basa. Dr Umar ba karamin tausaya mata yayi ba. Ya kuma kudiri aniyar, duk randa ya ganta cikin damuwa sai ya tai maka mata, duk da bai san ya kamani ta yake ba. 9:12] ﻡﺩﺮﻛ ﻟﻠﻪﺍﺪﺒﻋ ﺓﺪﻴﺷﺭ PM, 9/14/2016] Rash Kardam: YA’YA DA DUKIYA BA’A K’ETARSU NA ©RASHEEDAH .A. KARDAM. Pg-46~50 Suna isowa gida, Beeba ta ba wa mai Napep kud’insa, ta d’auko su bargo, da pillow, suka nufi k’ofar shiga gidan. Khadi ta tsaya, Beebah ta juyo ta kali Khadi, Tace”lafiya naga kin tsaya?. Nan take idon Khadi ya kawo ruwan hawaye, tafara magana, cikin muryan kuka,”Beebah ina tsoron shiga cikin gida, don Gwaggo zata iya dukana, kinga Baba baya nan, Beeba ta kalleta cike da tausayawa, Tace”Addah muyi addu’a in Allah ya yarda bazata yi mana komai ba. Kalamai masu dad’i, da ‘kwantar da hankali, tayita fad’a ma Khadi, kafin ta yarda sukayi addu’a, tare da shiga gidan. Assalamu’alaikum! Gwaggo dake d’aki, tanata sababi, taji kamar muryan Beeba da sauri ta fito, har tana tuntube, tana fitowa taga su Khadi, wani uwar ashar ta narka mata, da kalon yau zaki sani. ‘Daki ta koma, ta d’auko wata zu’ke’kiyar bulalan ta, Gwaggo tace” yau sai na rama, marin da kikasa Malam yamin, kuma wahala yanzu kika fara, Mayya kawai, sam tsabar bala’i, bata lura da qofar window, dake bud’e ba, jikake Garamm Gwaggo ta gwaru da window, sai da ta fadi a kasa. Nan take, ta saki ‘kara, oh ni Rash nace”su Gwaggo ko d’an dauriya babu. Ihu take kamar qaramar yarinya, Khadi da gudu, ta iso gunta fiskanta, d’auke da hawaye, sannu take ma Gwaggo, cikin tausayawa. Gwaggo da ‘kyar, ta iya yin shiru, tana d’agowa kuwa, bakin ya kumbura sundum, ko danaga bakin, bansan likacin da nasaki dariya ba. Gwaggo d’aki tayi, ko magana bata iyayi, sabida bakinta, paracetamol ta sha, don ta ji sanyi ajikinta. Khadi kam d’aki ta shiga, ta takure gu d’aya. Tana cike da tunani, mai tasa Gwaggo ta tsane ta haka?. To mai iyayenta sukayi ma Gwaggo ta ke tsanar su haka, har ya shafeta?. Duk wayannan tambayan bata da amsansu, haka ta hak’ura, dan bata da amsan tambayanta. Gwaggo tunda baki ya d’anyi sau’ki, ta soma gana ma Khadi azaba, na yau daban, na gobe daban, wani saran da ta samu, in Malam nanan, bata cika gallaza mata ba, amma in Malam ya fita, Khadi sai ta gwammace kid’a da karatu. Khadi ta yanke shawaran samun Malam, Tace”Baba ina son, in fara zuwa gurin, koyan d’inki, yafi zaman da nakeyi. Malam ba k’aramin dad’i yaji ba, kuma hakan zai ragemata, yawan damuwa, sati guda ya nima mata, tafara zuwa, amma sai dai yana nesa da unguwansu. Gwaggo tayi bala’i ba ‘kadan ba, gani bata da mafita yasa ta hak’ura, tafara tunanin, sabon hanyan da zata, gallaza ma Khadi. Kwanaki sun tafi,Yau saura sati d’aya, Dr Umar ya kammala course d’insa, suna yawan waya da Dr Abdul. Khadi tana zuwa gurin k’oyan d’inkinta, gata da hazaka da basira, yanzu har ta fara had’a kayan yara, zata yanka da kanta ta had’a. Ganin haka yasa Malam ya sayo mata, keken d’inkin hanu, dontana, yan facin da sanda na mutane, tana samun biyar goma. Masu karatu karkuso kuga Gwaggo ranan, kamar zatayi hauka, dan bak’in ciki da takaici, Khadi kam kule kanta, tayi a d’aki, don Gwaggo tace yau ko ita ko Khadi. Fanz kumin hak’uri, na rashin jina, k’wana biyu, bama samun wuta ne. ﺓﺪﻴﺷﺭ 9:12] ﻡﺩﺮﻛ ﻟﻠﻪﺍﺪﺒﻋ PM, 9/14/2016] Rash Kardam: YA’YA DA DUKIYA BA’A K’ETARSU NA ©RASHEEDAH .A. KARDAM. Pg-51~55. Gwaggo tun da taga Khadi, tana d’an samu a d’inki, hankalinta ya tashi, Gwaggo ta kudiri aniyar sai ta b’ata keken d’inkin. Beeba ko murna ganin Addah ta, tasoma iya d’inki yanzu zata bar kai d’inki, ana wulakanta ta, Gwaggo ko kulum sai ta zagi Beeba, akan yanda take, nuna zakewar ta ga Khadi. Haka rayuwa tayi ta tafiya, Khadi na cikin kunci da matsin Gwaggo, hak’uri takeyi da ita, kulum sai taci kuka, yanda Gwaggo ke zagin iyayenta.Yanzu har ta kai, yan’unguwa sunsan, Khadi yar riko ne a hannusu. In Gwaggo taga Malam baya gida ta hana Khadi zuwa gun d’inki, in makwabta sun kawo faci, Gwaggo ta korasu, ta hana su shiga cikin gidan. Khadi kusan sati bataje, gun koyar d’inki ba. Malam baya samun zaman gida, sabga sun masa yawa, gashi yau tafiya ta kamasa zuwa Jigawa, tunda asuba yatafi. Zaije ya sayar da Gona’nsa dake garin, don fara sayyan auren Khadi. Da wuri ta tashi tayi wanke- wanke’nta gama, ko karyawa batayiba ta d’au hijab da nikaf d’inta, ta fito cikin sand’a, takalmanta a hannu ta rike dan Gwaggi kartajita, cikin sand’ a ta fita, a qofar gida ta sanya hijab dinta. Sauri- sauri ta fara tafiya sai da tayi nisa ta duba jakanta, taga naira d’ari ya rage mata, Gwaggo duk ta amshe sauran kud’in. Mai Napep ta tsara, ta masa k’watancen gurin, Yace”tabada naira d’ari, nan tafara “rok’ansa ragi, da kyar ya yarda zai kaita a naira Saba’in. Ta shiga suka d’au hanya, ko da taje sai da mai koyamusu d’inki, ta mata fad’an rashin zuwanta, hak’uri ta bata.nan suka fara aiki har sai da karfe hudu suka tashi, din yau sun samu K’wangilan dinka uniform d’in wani school. Dr Umar ne ke waya, yana sanar da Mum d’insa zai da wo 9ja, girki na musamman Ummin sa ta masa, ko da jirginsu ta iso, driver ne da kanwarsa Iham sukaje d’auko sa. A hanya suke hira da ilham, yana tambayar ta, yan’uwa da abokan arziki, har suka iso gida, tun daga nesa nake hango securitys a qofar gidan, tabbas ko ba’a fad’amin ba, Umar d’an wani babban attajiri ne, ko mai mulki, don masu karatu, bazan iya tsara muku kyan gidan ba. Tundaga gate masu aiki, ke masa sannu da dawowa, har ya isa cikin wani falo, niko Rash ganin irin kyan gidan nace”bazan bari a bani labarin cikin gidan ba, da hanzari na sanya kaina cikin falo, yasalam masu karatu hmm wai in bakayi bamu guri, karkuso kuga cikin falon, sannu a hankali, nafara bin falon da kalo, komai na golden da brown ne, ko dana d’aga kaina wasu koyaye ne tamkar zinari, sai haskawa sukeyi a cikin falo. Gefe na samu na rab’e don yanda sanyin A.C ke bugani, ga wani sassayan kamshin da ke tashi, wata yar datijuwa ce, ta fito d’auke da fara’a, afuskan ta ta iso cikin falon, tana cewa”ur welcome my son. Cikin girmamawa yaje yayi hugging d’inta, yana fad’i” i miss u too my lovely mum. Kanshi ta shafa, tare da rike hannusa, my Son “muje ka watsa ruwa sai kazo ka ci abinci ka huta. Mikewa yayi ya nufi side d’insa, komai a canza masa na d’akin, wanka ya shiga, bayan ya fito ne ya nufi falo, nan ya cika cikinsa da abinci kala- kala, yana kammalawa kenan ya nufo falo, wani daga cikin security d’in yazo, yace”Oga kana tare da bako Dr Abdul, ya kalesa cikin girmamawa, Yace” barshi ya shigo ae ba bako bane shi d’an gida ne. Dr Abdul ne ya shigo, sai da ya gaida Ummin su Dr Umar, tukuna suka nufi side d’in sa, hira sukayi sosai kafin ya masa sallama, akan zasu had’u, sai da ya rakosa, har jikin motarsa yashiga sai da, Dr Abdul ya bar gidan, kafin ya koma cikin gida. Amin afuwa, har yanzu wuta bai tsaya ba, shiyasa kuke jina shiru. 9:12] ﻡﺩﺮﻛ ﻟﻠﻪﺍﺪﺒﻋ ﺓﺪﻴﺷﺭ PM, 9/14/2016] Rash Kardam: YA’YA DA DUKIYA BA’A K’ETARSU NA ©RASHEEDAH .A. KARDAM. Pg-56~60. Yau kwanan Dr Umar 8 da dawowa, har ya koma bakin aikinsa, tun safe yake jin son yawo zai zaga gari, kuma bai son security ko d’aya yabisa, don shi daman bai cika fita da security’s ba, don Dad ke matsa masa baya son yana yawo haka, ko driver yana bari yana jansa, yana tashi a office karfe 3:30pm, gida ya nufa yayi wanka, yau sai ya tsinci kansa da son sanya jamfa, nan ya ciro wata shadda dark blue amata aiki, da surkin farin zare da blue, hularsa ma blue ce da surkin fari, ya d’auko ta kalminsa ya tare da agogo, tsayawa yayi a madubi, yana kare ma kansa kalo, gaskiya ya hadu ko ni Rash dana kalesa, sai da kirjina ya bada dumm, Umar mutum ne mai kyau ga kamala ga k’warjini, fari ne tass, yana da dogon hacci tare da karamin baki, kai in ka kallesa sai karasa da wani yare zaka danganta shi, India ne ko balarabe, ko Fulani. Tunda ya sauk’o falo falo, umma ta ga d’anta, sai murmushi take zubawa, tace”Baba na sai ina haka?. “Wananan wankan fa?. “Ko nayi surkace?. Don raboka da saka manyan kaya ka dade. Cike da murmushi ya kalli Umma, Yace” Ummana duk wannan tambayar ni kad’ai, bata surka Umma da saura tukun, zan dai zaga cikin gari ne. Cike da kulawa tace”Allah yasa futanka a samomin surka mai hankali da tarbiya, yar mutunci, cikin jin dad’i ya amsa da Ameen. Tace”Son Allah tsare a dawo lafiya, ka kuma tafi a hankali, to ya amsa ya fita, tun a harabar gidan ma’aikata ke masa sannu kud’i ya ciro a aljuhunsa wanda bai san nawa bane ya basu, ya shiga motarsa ya ja. Khadi tafe take, tana tunani yau ta kad’e, in cikin zuciyar ta tace” yau gashi malam baya nan, nikam na banu, bansan wani irin duka zata min ba. Hala yau kamma, k’wananane ya kare, nan tafara “Ya Allah ka yafe min, kasa na cika da imani, wasu hawaye ke bin fuskarta. Tafiya take sam bata san inda take nufa ba. Tsaban zance zuci, har ta hau kan titi, jama’ a dake hanyar sai kalonta suke, wasu na tausaya mata, gashi fuskanta da nikaf, jama’a na ta mata magana sam bata sani ba, bata ma san sunanyi ba,”wai kunu a wani gida”. Dr Umar na tafe a cikin motarsa, ya kuna qira’ar Ahmad Sulaiman, yana tafe cikin nutsuwa, ya wuce ran about baban gwari kenan ya d’auki hanya. Sam bai hangi yarinya ba, sai da yazo kusa ya ganta. Sai tafiya take a tsakiyar titi ga mutane sai kalota suke horn yayeyi da k’arfi, amma sam bata ji, gashi ya d’au gudu sosai, wani wawan burki da yata kane yasa dawo cikin hayyacinta, damar motan, ta gabanta ya tazo, suman tsaye tayi, dan tsaban razana ita bata fadi ba ita bata motsaba. Da sauri ya fito cikin motar, yana zuwa kusa da ita, yaga bata motsa ba ga idonta sun kafe, cikin dakiyar zuciya yave” ke lafiyarki klau kuwa kika hau kan titi?. Me kike tunani haka? Luuu yaga ta tafi zata fad’i cikin zafin nama ya tareta, ta sauka a jikinsa. Jijigata yayi yaga bata motsi, cikin sauri ya fincike nikaf dinta, sam bai ga fuskanta ba, juyaa yayi, ya kali wanda suka taru a gun, wasu na masa kalon mamaki, wani d’an tsoho yagani yace”Baba pls kazo ka taimaka min dan Allah. kamata sukayi, suka dawo da ita gefen titi, da sauri Dr Umar yaje da gudu ya bud’e motarsa, ya d’auko goran ruwa, yazo ya yayya fa mata, sai a lokacin ya kali fuskan, kasa d’auke idonsa yayi, yana furta”Sarki ya tabbbata ga ubangijin sammai da kassai, lalle ubangiji yayi hallita a gurin. a hankali tasoma bud’e idonta, tarass ta sauke su akan, Dr Umar da ya zuba mata na mujiya, ya kasa d’auke kansa ga fiskanta. ﺓﺪﻴﺷﺭ 9:12] ﻡﺩﺮﻛ ﻟﻠﻪﺍﺪﺒﻋ PM, 9/14/2016] Rash Kardam: YA’YA DA DUKIYA BA’A K’ETARSU NA ©RASHEEDAH .A. KARDAM. Pg-66~70. Gwaggo cikin hayaniya da masifa, Tace”mai yasa baka tura, Beebah ko Rabee’atu, sai Khadi, to sai dai na k’ona kayan. Malam kasa magana yayi, tsaban takaicin dake damunsa, wannan wace irin fitinaniyar macece?. Gwaggo ta d’ibi kayan, tayi hanyan kitchen dasu, Malam na ganin haka ya bita, kafin ya isa, har ta fara sawa a wuta, kwacewa yayi tare da zaro na wutan, wani gyalens mai kyau, da sauri ya taka, da takalmin sa, wutar ta mutu. Wani gumun kalo ya mata, duk iskancinta sai da ta shiga taitayinta, ta fito a kitchen, koda tazo dai-dai gun Khadi shureta tayi da kafa, sai da Khadi ta fad’i, ta Beeba ne ta d’aga ta, rana mata sannu, Malam yace”Hauwa mai yasa baki da tausayi ne?. Kina tuna kema zaki mutu kuwa?. Ki sani fa duk inda, iyayen Khadeeja sukaje, kema zakije, kuma Allah baya kyaleki bane, kuma nima ba wai fa tsoronki nake ji ba, ina d’aga miki k’afa ne. Hauwa kisani ‘YA’YA DA DABBA, DA DUKIYA, BA’A K’ETAR SU, bakisan wacce irin baiwa Allah yayi ma Khadija ba, bakisana wani irin taimako, zata miki a rayuwan ki nan gaba. Gwaggo ta kali Malam cikin kalon da ban d’au maganar ka da muhimmanci ba, tace” ehehehe Khadi ne zata taimaken, ahir ahir, Allah ya tsare gatari da saran k’ota, ni da Khadi badai muzauna inwa d’aya ba. Malam ya kaleta yace”Hauwa da badun Allah bayason saki ba, to da yau tabbas sai kin bar gidana, kuma kinci albarkacin Khadi da ‘YA’AYAN da kika haifa. Koda Malam ya ambaci saki, sai da k’irjin Gwaggo bada sautin damm! damm!.. Amma cikin k’arfin hali, dake shaid’an ya mata kururuwa, tace”sai me in ka sakeni?.daman wani abu nake samu a gidanka, in banda gayyan tsiya. Malam ya d’aga hannu yace”Ya Allah kana jina, kana ganin abunda ke faruwa, Ya Allah ka azurta Khadi da abunda zata taimaki Hauwa’u. Yana dasa aya, Gwaggo tace” ba amin ba har abada, sai dai ku da wannan mayyan, talashe zuciyarku. Fuuuu Gwaggo takama hannu Rabee, tajuya ta kali Beebah, kee da ta lashe maki zuciya, saikiyi ta makale mata, suka shiga d’aki. Malam ya kama hannu Khadi, da Beeba ya kaisu d’akunsa, albarka ya samusu, ya musu nasiha, tare da k’ara bama Khadi hak’uri. Tace” Baba ba komai, ae Gwaggo uwatace, ita na bud’i ido na gani, ita na santa, kuma ina mata fatan Allah yasa ta gane Ameen ya amsa. Dr Umar kuwa, yana komawa gida, ya tarar da Mum d’insa, suna hira da Ilham, shima zama yayi, tare dacewa washh, Mum tace” daga ina haka Son?. Gyara zama yayi, ya kali Mum yace”daga gidansu Khadeejat nake. Kafin Mum tayi magana Ilham tace”bros nikam ina son gani Aunty Khadejat d’inana. Kulum sai labarinta mukeji, fuskansa cike da murmushi, yace”zaki ganta har sai kin gaji da ganinta ma. Mum tace” Alhamdulilah! Allah ya nunan ranan da Babana ya samu wacce yake so, sai fatan Allah ya kaumu lokacin biki, cike da zumu d’i ya amsa da Ameen. Dr Umar yace” Mum baki ga yarinyan bane, gata da hankali, kuma inkinji rayuwanta abun tausayi, nan ya basu labarin had’uwansu, da irin wahalan, su Mum da ilham sun tausaya mata. Ilham tayi karaf tace” bros to ina wacce katab’a ban lbr ta, itama wacce Khaji a agun Dr Abdul?. Ummm itakam har yanzu ba labarinta. Mikewa zai haura sama, yakali Mum yace”yau she Dad zai dawo daga Dubai d’in?. Umma tace” umm sai next week. Ok! Allah ya kaimu. 9:12] ﻡﺩﺮﻛ ﻟﻠﻪﺍﺪﺒﻋ ﺓﺪﻴﺷﺭ PM, 9/14/2016] Rash Kardam: YA’YA DA DUKIYA BA’A K’ETARSU NA ©RASHEEDAH .A. KARDAM. Pg-61~65. Sai da ta dad’e kafin, ta d’an tashi, sannu suke mata, bata iya amsawa ba, sai da ta huta sosai, Dr Umar ya kaleta, cike da tausaya, Yace”yan’mata mai yake damunki haka?. Da har kike irin wannan tunanin?. Kasacewa komai tayi, sai da yamata fad’a sosai, Yace” ki tashi mukauki gida, sai a lokacin ta zaro ido, kai ta girgiza musu alamar a’a, bayanda basuyi ba, amma fir taki, daga k’arshe Dr Umar ya tsara mata Napep, nan ta bada kwatance gidansu, sai da tashiga Napep sun d’au hanyan, Dr Umar ma motarsa yashiga, har yayi hanyan gida, komai tuna ya juya kan motarsa zuwa Dakata, gudu yakeyi sosai, cikin sa’a ya hango Napep d’insu, a baya ya rinka binsu har suka kai k’ofar gida. Mai Napep ya tafi, ta tsaya a k’ofar gida, tana tunani shiga, gashi yamma tayi sosai, ga yunwan da takeji, da kyar ta iya shiga gidan. Ganin ta nufi cikin gidan ya fito daga motarsa yazo dai-dai zauren. Assalamu’alaikum ta fad’a cike da tsoro, kara shiga ciki tayi ganin Gwaggo bata kusa, da sauri Gwaggo ta fito,”kee karuwa yar’iska ina kika fito?. Cikin fargaba da zaro ido, Khadi tace” wallahi Gwaggo gun d’inki naje. “Karya kike dan ubakiki, dukanta Gwaggo tayitayi kamar ta samu jaka. Dr Umar tun daga, nesa ke jin murtan ta tana ihu, sai leke yaykeyi, zuciyarsa na tafarfasa, ganin Gwaggo ta d’auko muciya, Beeba da ke gefe sai kuka takeyi, tana bama Gwaggo hak’uri, Dr Umar dake cikin zaure, ganin Gwaggo, ta d’aga muciya zata kwada mata, bai san lokacin da ya shiga gidan ba, rike muciyar. Gwaggo cikin fushi, d’ago tana masa kalon raini, daga kai waye ne?. K’ok’arin fincike muciyar takeyi, Malam da ya dawo daga tafiya, yaji da sauri ya k’araso cikin gidan, ganin abunda ke faruwa yace”Hauwa mai kikeyi haka?. Nan fa tafara ba Malam labarin karya da gaskiya, ta d’aura dacewa”Khadi karuwa ce yar’iska, da sauri Malam ya dafe kansa, don harcikin zuciyan sa, yaji kalman ta dake shi. Cikin kunan rai, Dr Umar yace”wannan sharri ne wlh, nan ya kwashe abunda ya faru ya fad’a musu. Gwaggo nan ta tire, “sam ni banyarda ba, shine ya d’auketa suke iskanci tare, Malam ya mata kwalon uku saura kwata, hak’uri ya fara ba Dr Umar, tare da masa godia. Dr Umar yayi musu salma ya nufi gida, cike da jimamin rayuwan Khadi. Tun daga wannan ranan, Dr Umar yasamu gurin zuwa, gidan gun Malam susha hira sosai, wani lokaci Malam ya turo Khadi su gaisa, sam bainuna musu ko shi waye ba, kuma bai taba sayan wani abu ya basu ba. A hankali shak’uwa ta shiga tsakaninta da Dr Umar. Kamar kulum Dr Umar, yayi wanka cikin manyan kaya, yayi kyau sosai, sai da ya biya ta, Sahad store yayi sayya, kaya ya had’a ma Khadi, less da atamfa da shadda d’inkaku, da su takalma da jaka. A hankali yake tafiya, har ya shigo unguwan, cikin sa’a ya samu Malam na gida, sai da suka gaisa, ya bud’e boot din motarsa, buhun shinkafa biyu, na tuwo dana dafawa, sai taliya carton biyar da makaroni, harda su maggi star. Malam dake gefe, ya tsaya yana kalon ikon Allah. Sai da aka gama shigarwa, Yace”Umar mai yasa kayi irin wannan d’awainiyar, kai ya sunkuyar, Malam ae ba komai, kai mahaifi ne ae. Godiya yayi masa sosai, dai-dai lokacin, Khadi tafito Gwaggo ta aike ta, tazo wuce musu, ta gaida Dr Umar ya amsa cikin kulawa zata wuce, Yace”tsaya ki amshi sak’onki, don ina sauri yau, wasu manyan ledoji ya miko mata, Malam Yace” Umar d’awainiyan yayi yawa, bakomai Baba sauri nake, sai na dawo, godiya yayi masa Dr Umar yaja motarsa ya bar gidan, Khadi ne tafara shiga cikin gidan da laida, Malam na biye da ita. Gwaggo tana ganin laida a hannu Khadi, da sauri taso zata amsa, ganin Malam tace”yau samuwa mukayi haka?. Malam yace”eh! Wallahi wanda ya taimaka ma Khadi ne yayi mana alkairi, Gwaggo ta dafe k’irji lokacin ta zazzage kayan ciki, nan fa ta tsorata, “ae wallahi abunda bazai yuwuba kenan, wannan k’arya ne. Malam daman funa furci ka kula shine ka tsiri kai Khadi koyar d’inki, don kana son ta had’u, da wanda ya kawo kayan, mai yasa baka tura Beebah ko Raee’atu ba?. Sai Khadi, nan tafara tonan silili ma Khadi, cikin takaici Malam ke kalonta. 9:12] ﻡﺩﺮﻛ ﻟﻠﻪﺍﺪﺒﻋ ﺓﺪﻴﺷﺭ PM, 9/14/2016] Rash Kardam: YA’YA DA DUKIYA BA’A K’ETARSU NA ©RASHEEDAH .A. KARDAM. Pg-76~80. Da sauri ya tareta, ta fad’a hannusa, sunanta yakira, Khadijat! Khadijat Khadijat… Pls ki tashi, kar ki tafi ki barni lokacin dana ke bukatarki, kene farin cikina. Pls Khadijat, yana jijigata, amma sam ko motsi batayi, Dr Umar ya fita a hayyacinsa, sai sam batu yakeyi, Gwaggo ko wani ruwan sanyi, tasake d’ebowa bata tsaya, wata-wata ba, ta k’wara ma Dr Umar. Duk da na da lafiya sai da ya razana, ajiyar zuciya ya sauke, nan take ya dawo cikin hayyacinsa, hannu sa ya kala, da sauri ya d’auketa, cikin mota ya sanya ta. Da gudu yabar unguwan. Asibitin Murtala ya wuce, yana zuwa ya d’auketa a hannu, Emergency yayi da ita. Kasancewar shi duty safe ke dashi, Dr Abdul ke duty kwana. Da sauri ya d’aga waya ya kirashi, “Dr Abdul dan Allah kazo Emergency, Khadija tace bata da lafiya, kazo ka taimka min, muryansa kaman zaiyi kuka, duk ya rud’a Dr Abdul, don bai kuma taba jin, Dr Umar cikin wannan, yanayin ba. Dr Abdul yace”Friend wacece Khadija?.cikin fushi yace”Malam in zakazo to in bazaka zo nakira, DR James, kashe wayan yayi, yafara kiran Dr Jame kenan, Dr Abdul ya turo qofar ya shigo. Da sauri yayi kanta, yana ganin Khadi ce, mamaki ya cikasa, tambayoyi yafara yi makansa,” daman Umar yasan Khadi ne?. “To mai yasa yarinka min tambayoyi akanta?. “Ta ya’akayi tazama Khadijansa?. Maganan Dr Umar ne ya dawo da shi, daga dogon tunanin daya shiga. Dr Umar Yace”kai Malam, lafiya kake mata, irin wan kalon?. Da sauri yazo ya kareta, cikin kishi da jin haushi, yake maganan. Dr Abdul bai cemasa uffan ba, cikin hanzari yasoma dubata, daman yariga yasan matsalanta, cikin ikon Allah, ansamu numfashin ta, ya dawo dai-dai. Sai dai bata farka ba, sun mata aluran baci, don ta samu hutu. Special room aka kaita, don hutawa ita kad’aine a d’akin. Dr Umar ya zauna, a bakin gadon ya zuba mata ido, ko kyaftawa ba yayi. Ji yake kaman ya k’arba mata ciwon, Dr Abdul ne ya shigo, yace”Ya mai jiki?. Da sauki ya bashi amsa. “Allah ya k’ara sauki. “In ka gama kasameni a office d’ina. Ok! Dr Abdul ya fita, office d’insa ya koma, ya zauna cike da tambayoyi, a fuskansa. Dr Umar sai daya kai, kusan kamar 1hrs, kafin ya kira nurse, yace”ta kulamasa, da patient d’insa. Da sallama ya shiga office d’in Dr Abdul, bayan ya zauna ne, Dr Abdul Yace”friend ina kasamu Khadi?. Ko dama ka santa tun- tuni, Dr Umar yace” kai ka santa ne?. Dr Abdul ya d’aga masa kai alamar eh!. Ajiyan zuciya Dr Umar yayi, nan ya kwashe labari, tunga randa ya fara ganinta, har yanzu, dayake fama da azaban sonta. Sai da Dr Abdul ya jijina kai, yace”Allah mai iko, to ae itace Khadijan, da ranan kaji ana case akanta. Cikin mamaki Dr Umar yace” mai kace ne ban fahimta ba. Nan Dr Abdul yabashi labarinta, iya yanda ya sani. Umar ya tausaya mata ba kad’an ba, wani Sonta da Qaunarta, suka k’ara shigansa. Cikin tsokana Dr Abdul yace” friend amma gaskiya, ka cika kishi, kawai don ina mata kalon sani, amma kawani tare, dariya Dr Umar yamasa, tare da kai masa dukan wasa. Malam dawowansa, daga kasuwa kenan, aka basa labarin, abunda ya faru bai iya shiga gidan ba, ya juya zai tafi kenan, yaga Beeba ta fito, duk ta rud’e hijab ma bai- bai tasa. Da sauri ta bisa, Napep ya tsara musu, suka nufi Asibitin Murtala. Zuciyan Malam sai tafasa yakeyi, yana tunanin wani kalan hukunci, zai yanke ma Gwaggo. Don abuntan yayi yawa,”to wai mai Khadi ta tsare mata a rayuwanta ne?. Da takeson ganin bayanta, tabbas zai Aura da Khadi, don ta huta da bala’in Gwaggo. ﻟﻠﻪﺍﺪﺒﻋ ﺓﺪﻴﺷﺭ 9:12] ﻡﺩﺮﻛ PM, 9/14/2016] Rash Kardam: YA’YA DA DUKIYA BA’A K’ETARSU NA ©RASHEEDAH .A. KARDAM. Pg-71~75. Khadi kulum tana cikin k’unci, Gwaggo ta sata a gaba, baran in taga, Malam ya fita kasuwa. Gashi Dr Umar ya kwana biyu bai

Chapter 2 of 5