Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

fara.
"Mene ne kuma haka." Abdul ya
tambaya cikin fushi.
"Mai da wukar ango na amarya
ba laifina bane ni dan aike ne."
"Aiken me wane ne ya aiko ka."
Nasir Jakal ya kanne ido daya ya
ce cikin rada.
"Tare muke da Bose." Abdul ya
dafe kirjinsa cikin fargaba. "Kai
da wasa ka ke." Nasir Jakal ya
fashe da dariya. "Don ubanka ni
abokin wasanka ne,, wallahi tare
muke da ita. Kuma wallahi ta
sami labarin aurenka." Abdul ya
sake dafe kirji a karo na biyu.
"Yanzu tana ina tana waje ne?".
Jakal ya girgiza kansa. Sannan ya
nuna kofar dakin da bakinsa. A
lokacin ne to suka ji motsin tafiya
kwas! Kwas!!.
Kamshin turarenta ne ya fara
sallama sannan sai Bose ta shigo.
Doguwa ce farar Bayarabiya.
Tana da kyawu irin nata, da
kuma aji irin nata. Ita ce yarinyar
da Abdul ya fi shakuwa da ita a
duk cikin yan matansa na bariki,
wadanda in har ma lissafin
gaskiya za ayi bana dokin rano
ba, to sun doshi goma sha biyu
Bose ta dubi Abdul sannan Abdul
ya dubi Bose. Ya yi murmushin
karfin hali ya ce.
"Bose manyan gari."
"Haba Abdul, ina ni ina manyan
gari, ai sai ku masu aure da
tsakar rana, na ji an ce za ka yi
aure gobe, koma a fada mana,
shi ne na zo da kaina mu yi
sallama."
Ta bata fuska tana duban Abdul.
"Haba Bose, ai dan zan yi aure ba
wai yana nufin mun rabu da ke
ba ne..."
"Yi min shiru, munafiki, kana jin
zan iya daukar tatsuniyar da kake
rerawa shashashan abokan ka,
wai auren rama wulakanci za ka
yi, ai ba zai yiwu ba da ba ka
sonta da ba za ka aure ta ba...".
"Haba Bose ke wallahi..." Ta katse
shi "Ka ga daga yau kada na kara
ganin (Your ungly face) a cikin
(Rose Mary Club) ba ni ba kai,
muddin kuna tare da matar nan
to mun yi hannun riga." Bose ta
juya cikin fushi ta bar dakin tana
sassarfa.
Abdul ya dubi Jakal ya ce. "Manta
da ita, sai na gama da wannan
karamar yar iskar Rabi'atu,
sannan zan koma ta kanta." Shi
kansa bai gaskata abin da yake
fadi ba.*****
.
Abdul ya karawa motar wuta ya
nufo garejin a guje bai tashi
tsayawa ba sai da ya zo daf da
garejin motar sannan ya taka
birki ku!!!. Kura ta tashi sama.
Wasu daga cikin dattijai
makwabtansa da ke hutawa a
kofar gidajensu, suka dubi motar
cikin kunan rai suka yi tofin Ala
tsine.
"Kai Allah ya shiryi wannan yaro,
lallai duniya na rudinsa." Wani
dan tankwararren tsoho mai
kamar baka ne ke fadi. Tun sa'ar
da Abdul ya tare a sabon
gidanshi da matarsa Rabi'atu,
mutanen layin suka daina
kwanciyar dare, domin fargabar
kada wata rana Abdul ya shawo
giya ya bi ta kansu cikin tukin
ganganci. Da zarar an jiyo sautin
injin motar Abdul za ka ga kowa
na kokarin janye kananan yara
daga kan hanya, domin sun san
Abdul kan iya banke yaro, ku yi
magana kuma ya nuna maka
iyakarku.
Watanni shida kenan yau da
daurin auren Abdul da Rabi'atu.
Allah mai yadda ya so, wata daya
kacal kawai da yin auren, sai
Allah ya dawo da babban yayan
su Abdul, Sagiru wanda ke karatu
a kasar Amurka, ko da yake ya
dade da gama karatun har ma ya
fara aiki a can. Tun sa'ar da ya
bar gida ya tafi karatu Amurka,
bai taba zuwa, gida ko da da
hutu ba, sai wannan karon. Yau
kusan shekaru tara kenan, tun
Abdul yana matashi. Zuwan
yayan Abdul daga Amurka ba
karamin alheri ya zamewa Abdul
ba. Domin kuwa yayan Abdul ya
je kasar Amurka da kafar dama,
inda ya dawo da makudan masu
gidan rana. Da zuwansa ya
sayawa Abdul sabon gida ya sai
masa mota (Honda), sannan ya
bashi kudi ya ce da Abdul ga su
nan na ka ne, ko ka juya su ko ka
kashe kai kaso, in kuma ka so ma
kana iya kashe su baki daya idan
sun kare ka dawo na kara ma.
Sagir ya fi Abdul ma lalacewa
nesa ba kusa ba.
Yau kusan watanni shida kenan
Abdul yana fantamawarsa yadda
ya so. Idan ya ga dama sai ya yi
kwana biyu bai zo gida ba. Satin
farko na Auren sa, shi ne kawai
Rabi'atu za ta iya lissafawa a
cikin ranakun farin cikinsu na
aure, to amma a kwana na
takwas. Da yin auren ma Abdul
bai kwana a gida ba. A lokacin da
aka daura Auren Abdul da
Rabi'atu, da kwana biyu sai
mahaifin Abdul wanda tsohon
dan sanda ne, mai murabus, ya
kira su shi da Rabi'atu ya ce yana
son magana da su. Abdul da
Rabi'atu suka zauna gaban sa
kansu a sunkuye suna sauraron
Dattijon. Insifecto S.B. Rabi'u,
wanda shine sunan mahaifin
Abdul, ya muskuta a kan kujerar
da yake zaune sanna ya ce da
su.......ACI BULUS - 04
.
Kansu a sunkuye suna sauraron
Dattijon. Insifecto S.B. Rabi'u,
wanda shine sunan mahaifin
Abdul, ya muskuta a kan kujerar
da yake zaune sanna ya ce da su.
"Abdul na gode wa Allah da ya
shirya min kai, tunda gashi duk
da surutun da mutane ke yi a
akanka, wai ka ki aure kana
yawon iskanci, hakan bai hana
ka ba yau ka zabarwa kanka
mata."
Ya dan yi shiru sannan ya dubi
Abdul ya ce "Ba kuma ka aureta
ba, wallahi idan ka sake ka
wulakantata tamu ce da kai na
san halinka, Allah sa na ji labarin
ka yi mata wani abu." Sannan ya
dubi Rabi'a ya ce "Yarinya ki bi
mijinki sau da kafa domin
Aljannarki tana karkashin
sawunsa, kada ki bata masa idan
kuma shi ya sake ya bata miki to
ki zo ki sanar da ni zan yi miki
maganinsa. Ku tashi ku tafi Allah
ya yi muku Albarka." Rabi'atu ta
ce ameen. Abdul bai ce komai ba,
domin ya san kamar ya saba ma
abinda babansa ya gama wa'azi
yanzu ne. Duk wannan ya faru ne
watanni shida da suka wuce.
Abdul ya tura kofar motar da
karfi garam! Ya rufe sannan ya
shiga cikin gidan cikin sauri tun
daga tsakar gida ya fara kwalla
mata kira. "Rabi'atu!!. Ina kike ne,
wanne irin iskancin banza ne
kuma haka kika bar famfo yana
ta zuba shi kadai, ko kin dauka
kyauta (RECA) suke bamu ruwan
ba biya muke ba."
Rabi'atu ta muskuta daga kan
gadon ta tashi da kyar cikin
kunan rai. Tun sa'ar da ta ji karar
takun birkin motar Abdul
gabanta ke faduwa domin ta san
masifa ta dawo, kullum aikin
kenan zagi na safe da ban na
rana da ban, yau wata biyar
kenan abin da ke kona mata rai a
yau shi ne, tun da Abdul zai fita
da safe ta ce da shi ba ta da lafiya
tana son ya kaita asibiti. Yanzu
zan dawo. Abdul ya ce da ita bai
dawo din ba sai yanzu waje
karfe biyar na yamma. Bayan
kuma ya san juna biyu ne da ita.
Cikin ya kai wajen wata uku a
yanzu.
Rabi'atu ta tashi da kyar ta leko
ta tagar benen ta dubi Abdul ya
yi tsaye a tsakar gidan yana ta
masifa.
"Au har ma leke na kike yi. Kin ma
mai da ni abin kallo kenan, za ki
sakko ne ko kuwa sai na hawo
na turo ki da ke da koton cikinki
na banza mai kamar kwarya."
Rabi'atu ta bude kofar dakin
numfashinta sama-sama, sannan
ta rike kafar benen ta ci gaba da
gangarowa kasa a hankali.
"Idan kin ga dama sai ki kai min
ruwan wanka." Abdul ya ce da ita
a fusace lokacin da ta sauko
daga kan benen. Rabi'atu ta rike
kafar benen. Sannan ta dafe dan
matashin juna biyunta ta cije
baki ta ce.
"Haba Abdul, kai yanzu ko
tausayina ba ka ji tuna fa tunda
safe nace da kai bani da lafiya
amma ka share ni ka yi tafiyarka
yawo sai yanzu ka ga dama ka
dawo."
"To idan na zauna aikin me zan yi
miki, rashin lafiyar ki ba ta shafe
ni ba ke ta shafa, in kin ga dama
ki tafi asibitin ke kadai in kuma
ba ki ga dama ba zauna ke ta
shafa, babu abin da zai sa na
dora ki gaban motata, da ciki
tirtsi kamar kwarya sama-sama
bai yiyuwa."
Ya dan yi shiru yana dubanta
duban wulakanci yana kada dan
mukullin da ke hannunsa.
"Za ki kai min ruwan wankan ko
kuwa."
Hawaye ya fara kwararowa a kan
kumatun Rabi'atu. "Yanzu Abdul
ka san cewa da shawa fa a
bandakin nan, amma kuma dan
wulakanci da rashin Imani ka ce
wai sai na kai maka ruwan
wanka."
"Kin ga ba na son rashin kunya,
kada kuma ki zage ni in ba so ki
ke yanzun nan ba na tumurmusa
ki ke da tulelen cikinki. In ba za ki
kai min ba kawai ki ce ba za ki
kai min ba. Kai wallahi na auro
jaraba ni na rasa masifar ma da
ta sa ni ma auro ki Rabi'atu."
.
Rabi'atu ta fashe da kuka cikin
takaici ta kifa kanta a kan kafar
benen, yanzu hannayenta na rike
da kofar benen.
.
Abdul ya nufi inda take ya turar
da ita sannan ya bi kan
matattakala ya haye saman
benen, ba a dade ba ya sauko
daga kan benen daure da tawul
iya kirjinsa ya shiga bandakin.
Mintuna bakwai ya gama
wankan ya sauya kaya sannan ya
sauko daga kan benen yana
takawa daidai. Har yanzu
Rabi'atu na dafe da kafar benen
tana kuka.
"Ki tabbata kafin na dawo kin
dafa abinci, in kuma ba haka ba
sai na lahira ya fi ki jin dadi, kina
ji ko!". Ya buga mata tsawa. Ba ta
dago koda kan ta ba, ballan tana
ta dube shi, Abdul ya matso inda
take cikin fushi sannan ya hada
da dankwalin kanta da gashin
kanta ya rike sannan ya fizgota,
ta ci karo da kirjinsa, Rabi'at ta
kwalla kara saboda azaba.
"Wayyo Allah! Don Allah ka sake
ni Abdul zaka ji min rauni...za ka
ji min rauni Abdul don Allah ka
bari."
"Ai gara in ji miki raunin, tun da
na yi miki magana kin share ni
kina ji ko!". Ya sake buga mata
tsawa.
"I... Ina ji dan Allah ka sake ni
Abdul dan Allah." Abdul ya
hankadata gaba ta fadi a kan
tafukan hannayenta tana kuka.
Abdul ya fice yana murmushin jin
dadin ya fara ramawa. Sannan ya
shiga motar ya tada ita ya taka ta
da gudu ya nufi kan titin da zai
kai shi (Rose Mary Club) shin ko
Bose kuwa tana nan ya tambayi
kansa.
Rabi'atu ta tashi cikin tsananin
azaba ta daddafa kafar benen ta
koma dakinta. Ta fada kan gado
ta fara kuka. Ta yi kuka ta yi kuka
har hawaye ya kare a idanunta,
sannan sai ta lumshe idanunta ta
Dulmiya cikin kogin tunanin
mutum daya a rayuwarta, wanda
ko a da, kuma har a yanzu shi ne
kawai ta taba kauna. "IMRAN".
Ta kira sunansa a hankali, a
tunaninta kiran sunan nasa na
iya sanyaya mata zuciya.****
.
Hannayensa na cikin aljihunsa,
sanye da bakin tabarau, karan
sigari (Rothmans) na cin wuta a
makale tsakanin fatar bakinsa. A
haka Abdul ya shiga (Rose Mary
Club) kusan duk wani matashin
birni mai ji da yan kudi bashi da
wani wajen shakatawa da ya
wuce (Rose Mary). Tun sa'ar da
ya shiga (Club) din yake hange-
hange ko zai hango Bose, amma
ko keyarta. Yau (Club) din ya cika
tab, duk kusan teburan da ke
cikin (Club) din dauke suke da
Jama'a, da yawa daga cikinsu
suna kora ruwan bagaja.
Abdul bai kula da su ba, domin
muddin zai zauna a gurin to dole
ne shi ma ya dan kora, tunda shi
ma yanzu ya dawo ruwa, kudi
sun dawo da shi. Abdul ya juya
ya dubi bayansa, inda ya ji
hayaniyar dariyar mutane, wani
tsohon Bayerabe ne ya sha giya
ya ke ta shirme.
Tsohon Bayeraben ya ja da baya
taga taga kamar zai fadi sannan
ya zazzaro idanu ya ce.
"Can I see the light...". Mutanen da
ke zaune kusa da teburin da
Bayeraben ya ke suka fashe da
dariya, sannan tsohon Bayeraben
ya sake ja da baya ya ce.
"I Can .... See...the light". Aka sake
fashewa da dariya. Wasu karti su
uku masu mummunar fuska
kamar an sassakota daga itacen
marke suka shigo (Club) din
kamar an jefo su, sannan suka
cakumi tsohon suka yi waje da
shi.
A daidai lokacin ne to Abdul ya
hango Bose ita kadai zaune acan
kuryar Club din. Abin mamaki
kuma shi ne ita kadai ce zaune a
kan teburin, kwalbar coke da
kuma kwalbar giya biyu a
gabanta. Abdul ya nufi gurin
yana murmushi.
Bose ta yi sauri ta mike tsaye
lokacin da ta hango Abdul ya
nufo ta.
"Kada ka zo min nan wallahi kada
ka maso inda na ke ba ruwa na
da kai."
"Ni kuwa halina da ke ke nan
wallahi baki jin lallashi, yanzu
Bose haka za mu yi da ke, ki tuna
fa yau zuwana gurin nan goma
sha daya ban ganki ba, amma
duk da haka yanzu ma bayan na
ganki za ki kore ni, haba Bose,
Sisiliya ba ta fada miki ba ne na
zazzo nemanki."
"Ina ruwa na ina ma sau dubu ka
zo nan kai ta shafa. Ka share
kawai malam ka ji ko Bose ta yi
maka nisa ga ra ma ka bar gurin
nan tun wuri kada saurayina ya
ganni da kai ya saye ka."
Ki shi ya tokare kirjin Abdul da
kyar ya ke numfashi.
"Haba Bose yanzu haka za mu yi
da ke, ki tuna fa irin rayuwar
da...". Ta katse shi.
"Abdul, ka yi min shiru bana son
jin muryarka, ka kuma ishe ni da
surutu, ya kamata ka kyale ni
haka na sha iska, ka nace min
ka nace min kamar (Chewing
gum). Ka koma mana can gurin
matar ka wacce ka ke so ni mene
kuma na nemana, wato sai da ka
gama soyayyarka da matarka,
sannan ka dawo gurin banza
Bose wacce ka raina. To koma
can gurin matar ka da ka dawone
KACI BULUS ?
To Allah ya kiyaye.
Abdul ya rasa abinda ke yi masa
dadi, hakika yana masifar son
Bose, ba zai iya rabuwa da ita ba.
"Sai an jima"....ACI BULUS - 05
.
Allah ya kiyaye.
Abdul ya rasa abinda ke yi masa
dadi, hakika yana masifar son
Bose, ba zai iya rabuwa da ita ba.
.
"Sai an jima". Bose ta ce da shi.
Sannan ta juya ta fara tafiya.
Sannan ne to Abdul ya kula da
cewa ashe duk Club din an yi
shiru su ake sauraro. Kafin ya
farga Bose ta yi tafiyarta, tana
rangwada kamar reshen bishiya
Acan wani bangare na (Club) din
wani dan giya ya fashe da dariya
sannan ya ce.
"Allah ya tsinewa marar zuciya,
ina ma ni ta yiwa." Abdul ya ji shi
amma bai ce komai ba, sai kawai
ya zauna kan teburin da Bose ta
bari, ya sa giyar a gaba ya yi ta
sha sai da ya yi tatul sannan ya
kifa kansa a kan teburin cikin
takaici.
karfe biyu na dare Bose ta dawo
(Club) din, Babu kowa sai Abdul
shi kadai, sai kuma mai kula da
(Club) din. Bose ta kama kafadar
Abdul sannan ta ja shi zuwa
dakinta da kyar yana tangadi. A
dakin nata ya kwana a ranar.
Da safe bayan ya wartsake, ta
kawo masa karin kummalo,
bayan ya gama sai Bose ta ce da
shi.
"Abdul kana sona?".
"Haba Bose, ai kema kin san ina
sonki".
"To, indai gaskiya ne, kana sona
ka jira ni, yau da yamma zan zo
gidanka mu yi soyayyar mu a
gaban matarka, idan ka yi haka
to, ka nuna min lallai kana
kaunata". Abdul ya dubeta cikin
zumudi, sannan ya ce. "Ai
wannan mai sauki ne."
"Ai ba shike nan ba." Abdul ya
dube ta ya ce "Sai me kuma?".
Bose ta dafa kafadarsa, sannan
ta rungume shi ta ce.
"Abdul ina son bayan haka kuma
ka saki matarka saki uku, sai mu
koma kamar yadda mu ke a da,
za ka iya?".
"Wannan mai sauki ne Bose
domin abin da na ke niyya
kenan." Bose ta yi ajiyar zuciya
sannan ta dada da cewa. "Ina
son sai ka zane ta ciki da baya
kafin ka sake ta". Abdul ya gyada
kai, cikin amincewa. Bose ta dada
kankame shi tana cewa. "Bani da
wanda ya fi ka Abdul."
.
KASHI NA HUDU (4) SHAFI NA (30)
_____________________________
Hasken ranar da ya yi wa kansa
hanya ta tsakanin labulen tagar
dakin shi ya fara dumama
fuskarta, sannan kuma sautin.
Kararrawar agogon ta fara ruri
karfe takwas na safe. Rabi'atu ta
yi mika a hankali gami da salati
ga shugaban talikai sannan ta
bude idanunta.
Ta zuro kafafunta a hankali daga
kan gadon, sannan ta gangaro
daga kan benen zuwa tsakar
gidan ta shiga bayan gida. Bayan
yan mintuna ta dawo ta sa
madubi a gaba tana kallon
fuskarta. Abin da ta gani a jikin
madubin ba karamin razanata ya
yi ba kyakkaywar fuskar doguwa
ma'abociyar annuri da tattausan
Murmushi wacce a kullum
Rabi'atu kan yi alfahari da ita,
duk ta yamutse ta yi duhu,
idanunta duk sun koma cikin
loko. Rabi'atu ta yi sauri ta daina
kallon madubin jikinta na bari. Ba
zata iya jure ganin kamanninta
ajikin madubin ba. Ta juyo a
hankali ta fada kan gadon a
rigingine sannan ta dafe dan
matashin juna biyunta ta fara
kuka cikin boyayyiyar murya, ba
ta damu ba da ta yi yan shafe-
shafen da mata suka saba yi idan
sun fito daga wanka ba, domin a
yau ba za ta iya ganin
kamanninta jikin madubi ba.
Tunanin Imran ya sake fado
mata, tunanin ranar da ya zo
gidansu ana sauran kwana daya
kacal a daura mata aure.
"Yanzu Rabi'atu shike nan mun
rabu kenan duk soyayyarmu ta
tashi a banza?".
"Gaskiya...Imran...sai dai hakuri ka
je ka nemi wata, Allah ya hada ka
da wadda ta fi ni amma ni kam
na yi maka nisa, sai dai ka
rungumi kaddara domin gobe
war haka an daura aurena da
Abdul."
Rabi'at ta fashe da kuka a kan
gadon, lokacin da ta tuna irin
yadda Imran ya fara zubar da
kwalla a gabanta saboda kauna.
Shin da Imran ta aura kuwa anya
zai yi mata haka?
Abubuwan da suka fara a
yammacin jiya suka fara dawowa
zuciyarta, ita daman tun sa'adda
Abdul ya fice daga gidan ta san
da wahala idan zai dawo ya
kwana a gidan. Ko ina yake
yanzu ta tambayi kanta. Sannan
kamar amsar tambayarta sai aka
banko kofar dakin da karfi kamar
iska ta turo ta. Rabi'atu ta yi
firgigit cikin fargaba ta tashi
zaune sannan ta yi ido biyu da
shi.
Abdul ne tsaye yana dubanta,
idanunsa jajur kamar garwashin
wuta.
"San..nu da zuwa." Ta ce da shi
cikin tsoro kirjinta na dukan uku-uku.
.
Gabanta ya fadi domin ba irin
turaren da Abdul ya saba fesawa
ba ne, kuma ko da Abdul zai sake
sabon turare to ta san zai yi
wuya ace ya sayi turaren mata,
Rabi'atu ta shaki kamshin
turaren. Tabbas turaren mata ne,
gumi ya fara sartu a kan dogon
wuyanta, sannan a hankali sai ta
nufi kofar dakin tana matsawa
kusa, kamshin turaren na kara
bugun hancinta. Lokaci guda sai
kawai Rabi'at ta ji ta daina
tsoron ko zata sami Abdul ciki,
abin da kawai take so shi ne ta
shiga dakin ta ga abinda ke
kamshin turaren. Don haka sai
kawai ta tura kofar dakin, sanan
ne to ta ji kamar an soka mata
kibiya a kirji. Rabi'at ta yi turus
tana duban doguwar arniyar da
ke kwance a kan gadonta daga
ita sai siket, gashin robar da aka
yi wa Bose kari da shi ya
warwatsu a kan matashin kan.
Bose ba ta ma san abinda ake ba.
Barcinta take cikin kwanciyar
hankali. Rabi'at ta ji wani abu ya
tokare makogwaronta, sannan ta
ji idanunta sun fara dusashewa.
Cikin fushi sai ta matsa kusa da
Bose ta sharara mata mari tas!!.
Bose ta yi firgigit cikin razana
kadan ya rage ta fado daga kan
gadon. "Abdul me nene...haka."
Sannan sai ta yi shiru lokacin da
ganinta ya dawo sosai. Bose ta
dubi Rabi'at tsaye ita ma Rabi'atu
ta dubi Bose. "Ai sai ki tashi ko,
tunda ba gadon ubanki ba ne."
Ga mamakin Rabi'at da kuma
karin haushi sai ta ga Bose ta yi
murmushi sannan ta sauko daga
kan gadon ta ce. "Sannu da zuwa
Rabi'at daman ke nake jira ki
dawo."***
.
Yan matan biyu suka dubi juna,
alamun tsana karara a
fuskokinsu. "Kin mare ni kin ji
dadi, sai dai ina son ki sani cewa
baki ci bulus ba, wallahi sai na
rama, sannan kuma na
lugwigwita cikinki, idan kika yi
wasa sai kin haife dan yanzun
nan ko da lokacin haihuwarsa
bai zo ba." Bose ce ke fada tana
zazzare idanu. "Karya ki ke yi
arniya ba kece Allah ba." Rabi'at
ta ce a tsorace, tana ja da baya.
Rabi'at ta san cewa idan ba dan
juna biyun dake jikinta ba babu
yadda Bose za ta yi da ita, to
amma a yanzu idan ta biye mata
tana iya halakata. Bose ta kaiwa
Rabi'at cafka da karfin gaske
kafin Rabi'at ta janye jikinta Bose
ta rike mata riga. Rabi'at ta kawo
mata duka, Bose ta kare sannan
ta sa hannu ta mangare Rabi'at a
fuska, sannan ta hankada ta
zuwa kofar dakin. Rabi'at ta
kwalla kara cikin tsananin ciwo,
ta fada da baya ta yi zaman yan
bori a kofar dakin kafin ta tashi
Bose ta yi tsalle ta fada a kanta.
"Sai na ci ubanki kafin Abdul din
ya zo, shi ma kuma idan ya zo
nasa shi ya kara miki." Rabi'at ta
yi yunkurin tashi sai Bose ta mai
da ita. Cikin Rabi'at ya motsa, ta ji
numfashinta ya fara yin sama-
sama. Ta sake yunkurawa, suka
mirgina zuwa wajen kofar dakin
da haka da haka har suka zo daf
da kofar bene. Bose ta sa hannu
ta shake Rabi'at. "Ina karfin naki
yake yanzu, bari na kashe ki kafin
ya zo, sai ya binne ki." Bose tace.
"Rabi'at ta san cewa idan ta sake
Bose na iya halakata, ita kuma ta
san a haka bata iya fada da Bose,
don haka sai ta ga abinda ya
dace shi ne ta yi kokarin ture
Bose daga kanta, sai ta yi kokarin
sauka daga kan benen, ta san ko
da Bose ta bita kasa, tana iya yin
ihu a cece ta. Wannan shi ya sa
Rabi'at ta tattara sauran karfinta
guri guda, da kyar ta ke
numfashi sannan ta yunkura da
karfin gaske ta jefar da Bose gefe
guda. Bose ta mike cikin
gaggawa da nufin ta sake
turmushe Rabi'at, Ashe ba ta sani
ba, kafarta a daf da matattakalar
benen na farko take. Rabi'at ta yi
kokarin tashi zaune, sannan ta
mike tsaye cikinta rungume da
hannayenta, ta nufi matattakalar
benen, sai Bose ta tsare hanyar.
"Babu hanyar gudu yarinya, yau
zaki fada musu sai na ga ta
rashin kunya." Bose tace. Rabi'at
ta yi kunan bakin wake, ta nufi
inda Bose ta tare da gudu-gudu.
A tsammaninta Bose zata kauce
ta bata hanya tunda ta san a daf
da matattakalar benen take.
Yunkurin da Rabi'at ta yi sai ya
zamo na kaddara, domin Bose
bata dauka kafafunta suna daf
da zamewa ba. Rabi'at ta bangaji
Bose da gefen jikinta. Sannan ne
to kafar Bose ta zame. Bose ta yi
kokarin rike kafar benen sai dai
kuma ta makara. Ta kwalla kara a
sa'adda ta wuntsula kasan benen
ta fado da ka a tsakar gidan. A
nan ta baje wanwar kamar
yartsanar roba. Jikin Rabi'at na
rawa ta sauko cikin fargaba ta
taba Bose a kafada. "Ki...ki tashi
mana." Tace muryarta na rawa a
tsorace, sannan ne to jini ya fara
zubowa ta bakin Bose idanunta
sun birkice. Rabi'at ta fashe da
kuka, ta yi kisan kai tabbas ta yi
kisan kai. Duk da yake ba ta taba
ko da kusantar gawa ba, to
amma ta taba ganin yadda
idanun Balaraba kanwarta suka
birkice a lokacin da Allah ya yi
mata rasuwa, Rabi'at ta sake
taba jikin Bose, sai ta ji jikinta ya
yi lagwaf-gwaf kamar jikakken
tsumma.
TABBAS TA MUTUACI BULUS - 06
.
TABBAS TA MUTU***
Rabi'at ta mike a hankali ta dubi
hannunta sai taga jini. Hanjin
cikinta ya yamutse kamar za ta yi
amai Abu na farko da ya fara
zuwa zuciyarta shi ne ta nemi
taimakon mutane Sannan sai ta
tuna Idan ta kirawo su ta ce da
su ta kashe mutum Tasha jin
labarin cewa duk wanda ya
kashe mutum kashe shi za a yi ta
sha ganin lokacin da ake harbe
yan fashi da makami a talabijin
tare da wasu masu laifin kisan
kai Babu abin da Rabi'at ta tsana
a rayuwarta irin ta buda talabijin
ta ga ana harbe barayi To kuma
yau sai gashi ita ma ta kashe
mutum yanzu ita ma kashe ta za
a yi Tsoro da fargaba suka rikita
kwakwalwarta gaba daya ta rasa
ma me za ta yi sannan sai wani
tunani ya fado mata Tunanin shi
ne ai babu wanda ya san ta
shigo gidan duk inda Abdul yake
a yanzu ta tabbata zai yi tunanin
ba zata dawo ba sai bayan
magariba to idan haka ne kuwa
abinda za ta yi shi ne ta hada yan
kayanta ta bar gidan idan Abdul
ya dawo sai ya san yadda zai yi
da ita Sai dai kuma ta sha jin
labarin kwazon yansada waje
binciken kisan kai ta sha jin
cewa zai yi wuya ka yi kisan kai
irin wannan ba tare da an gano
ka ba
Rabi'at ta fashe da kuka duk
duniyar ta yi mata kuna Ita kam
yanzu ta san rayuwarta ta zo
karshe ina amfanin auren Abdul
ta tambayi kanta yanzu mene ne
amfanin auren mutumin banza
irinsa ita kanta sai yanzu ne take
mamakin abinda ya sa ta aure
shi KADDARA ta amsawa kanta
Sannan lokaci guda sai ta ji wata
irin mummunar tsana ta shiga
zuciyarta, babu abin da ta tsana a
yanzu irin Abdul, dama shi ta
kashe, ta huce bakin cikin da ya
kulla mata, amma duk, da
haka....zan rama tace cikin kuka.
Sannan ne to ta yanke
shashashar shawarar da ta dada
jefa ta cikin masifar baki daya.
Rabi'at ta lallaba a hankali ta nufi
zauren gidan ta janyo kofar ta sa
sakata, sanan ta dawo tsakar
gidan ta dubi gawar Bose yanzu
kam ta san babu tunanin kowa
ni zai shigo gidan ya kama ta
dumu-dumu da gawa. Yanzu
abinda ya rage mata shi ne ta
mai da gawar bose saman
benen. A nan ake yinta lokacin da
ta fara ciccibar Bose sai ta ji
kamar dan da ke cikinta zai fasa
ya fito saboda nauyi. Rabi'at ta
ajje gawar jikinta na rawa,
sannan ta zauna dirshan a tsakar
gidan tana mai da numfashinta, a
lokaci guda kuma tana tunanin
hanyar da za ta bi ta hau da
gawar sama, sannan ne to
dabara ta fado mata. Ta tashi da
kyar ta nufi saman benen, ta
dauko tabarma, sanan ta dawo,
ta warware tabarmar, ta kama
kafar gawar ta janyota kan
tabarmar, sannan ta nannade
gawar a ciki. Ita kanta abin na
bata mamaki irin yadda take
wasa da gawar babu tsoro ko
fargaba. Abin da ba ta sni ba, shi
ne tsananin bacin rai, da kuma
tsattsauran ra'ayin ramuwar
gaiyar da ke zuciyarta su suka
dakushe dukkan tunaninta na
hankali da kuma tsoro dan haka
take jujjuya gawar babu fargaba,
Hakika abin na da mutukar
mamaki ace mace kamarta tana
jujjuya gawa yadda ta so.
Bayan da Rabi'at ta gama
nannade gawar Bose cikin
tabarmar sai ta ruga dakin ajje
kayan girke-girke, ba a dade ba
ta dawo da doguwar igiya ta
roba fara, sannan ta sa igiyar ta
daure tsakiyar tabarmar don
kada ta warware. Sai dai kuma
tsayin gawar ya fi tsayin
tabarmar, hakan shi ya sa kan
Bose da kafafunta duk a waje
suke gangar jikin tane kawai a
tabarmar.
Rabi'at ta dan dafe cikinta yayin
da ta ji ya motsa mata, ta dan
dakata ta huta sannan sai ta
kama kafafun gawar ta fara ja,
tana hawa benen da baya a
hankali a hankali tana tafiya tana
hutawa a haka har ta kai karshen
benen.
Mintuna biyar da faruwar hakan
Rabi'at ta mai da gawar Bose kan
gadonta, ta kwantar da ita
sannan ta dora kan gawar kan
matashin kai, ta janyo mayafi ta
rufe gawar. Sannan cikin
gaggawa ta harhada yan kayan
da take jin za su yi mata amfani
ta zuba su cikin jaka. Ta dauko
jakar kudinta ta lissafa, tana da
naira dubu biyar cif-cif, sun ishe
ni na bar garin, ta ce cikin
zuciyarta, sannan ta nufi

Book Chapters
Chapter 1
Chapter 2
Chapter 3Chapter 4Chapter 5Chapter 6

Please Login or Register in order to submit comment