Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
da farin ciki" da sassafe washegari ya je ofishinsa dake birnin tarayya" sai yayi wasu muhimman baki a motoci sanye da bakaken kot" Sai bayan da mutanen suka cika ofishin ne kamar kwari" sannan ya fahimci rundunar hana barna ne da babakere akan dukiyar kasa" shugaban tafiyar ya kalli Alhaji Elbashir yace dashi "Munzo ne domin kayi mana bayanin yadda ka salwantar da Dala miliyan hamsin daga sashinka" sannan kuma an tsinci gawarwakin abokan aikinka an gina wani rami a cikin wani rafi a kano an binne su" muna so kayi mana bayani akan abinda ka sani Alhaji Elbashir yaji kamar duniya ce ta ruguzo masa domin dai yasan cewar tashi tazo karshe . ======>******************<====== . Kwana uku cur" Rambo yana tafiya a cikin kusurgumin daji" idan dare yayi" sai ya haye bishiya ya rungumo akwatin kudinshi yayi shiru yana tunanin hanyar da zaibi ya gudu yabar kasar dasu" yana jin tsoron fitowa cikin gari domin kuwa yayi tsammanin tuni an baza jami'an tsaro domin su gano inda ya shiga" Wani lokacin yakan yi ta wuce tsaunuka da lardin da fulani ke zaune jefi-jefi" ya gwammace yaci gaba da rayuwarshi a daji" komai dadewa idan kura ta lafa yasan cewar zai fito sarari zai ci gajiyar miliyoyin kudinshi" wannan wani lamari ne dake bukatar juriya da hankuri" Rambo ya kware a wannan fannin tun awani zama da yayi na wata takwas a gidan yari. A dare na uku Rambo yana saman wata katuwar tsamiya" yayi lamo a cikin duhu sai kace aljani yana rungume da akwatin kudin" yana sauraron kukan kwari da tsuntsaye" farin wata ya haske ko ina a cikin dajin ba gida gaba ba gida baya" Rambo yana matukar jin yunwa mai tsanani" domin kuwa rabon ya sami wani abu yasa a cikinshi tun kwana biyu da suka wuce a lokacin da yasami wata gwandar daji ya tsinka yasha" tun lokacin har aka kwana biyu Rambo bai sake samun wani abu naci a duk yawon da yake yi a cikin dajin ba To amma kuma da Rambo yaji yunwa ta tsananta mishi sai ya fara tunanin saukowa ya fita cikin dajin ya zagaya me yiwuwa ko tsada ya samu" to amma kuma da yayi tunanin barin ringimemen akwatin kudin a saman bishiya" sai yaji baya bukatar saukowa daga kan bishiyar" yafi so duk inda zai shiga yana nan tare da akwatin miliyoyin kudin shi sune mabudin jin dadin rayuwarshi da yake so yayi nan da wani dan lokacin idan ya koma kasar turai" Rambo yana nan kwance akan wani reshe sai yaji motsin wani abu a kusa da gindin bishiyar ya taho yana keta kayoyi da ganyen gauda dake warwatse ako ina a cikin dajin" sannan kuma yaji wani gurnani" da nishi mai karfi ya cika ko ina awajen" Rambo yayi saurin gyara zama a tsorace ya duka da kanshi ya kalli kasan bishiyar" domin ganin abinda ke motsi" yaji gabanshi ya fadi" hantar cikinshi ta motsa wata shirgegiyar kura ce" tana tafiya dakyar" tana zaro harshe tana lashe bakinta Rambo yayi lamo a cikin bishiyar ya daina numfashi " sai kace bashi da rai domin kuwa yasha jin ana bada labarin kuraye tun yana yaro" Ya dade yana jin cewar in har kura ta jiyo warin mutum ko daga ina take saita biyo warin tazo ta cimmashi" Rambo yasan cewar warinshi ta jjiwo daga nesa shiyasa take ta zagaye zagaye a gindin tsamiyar tana gurnani tana tona ganyaye da kafafuwanta domin taci sa'ar ganin inda mutum yake ta sami abinda zata ci ta kaiwa jariran 'ya'yanta ragowa Rambo yana kallonta ta saman bishiyar" tana ta neme-neme" gabanshi sai faduwa yake yi" amma kuma akwatin kudinshi yana nan a kankame a kirjin shi. Bayan wani lokaci sai kurar ta hakura ta koma" Rambo ya hangota a cikin hasken farin watan cikin ciyawa" da ganyaye tana tafiya" bayan tayi nisa ta bace" ya daina hangenta" sai ya kama reshikan tsamiyar ya sauko" domin ya gudu yabar dajin" ya sami labarin idan har kura ta kwallafa ranta akan abinda take so" to koda ace tafiya tayi" ba hakura tayi ba zata sake dawowa. Rambo ya diro daga saman bishiyar" ya yanki wani bangare na dajin ya fara cin gudu" nauyin akwatin kudin dake kankame a hannunshi ya sashi yin zufa" amma kuma bai tsaya ba sai dai lokaci-lokaci yakan sa hannunshi ya share zufar dake a fuskarshi" Rambo yayi nisa yana cin gudu" wani lokaci yakan fada cikin kananan ramukan da ganyaye suka lullube" bayan wani lokaci sai ya fito ya sake maida hankali domin tserewa mafadaciyar kurar da ta bashi tsoro Bai san iyakar awoyin da yayi yana gudu a cikin daji ba" ya dai tsinci kanshi ne a bakin wani kauye da motoci ke bi suna wucewa wacce ta ratsa ta cikin wani karamin labi da fulani kebi suna wucewa da shanun su. Rambo ya tsaya a jikin wata karamar bishiya mai yawan reshuka" bayan wani lokaci yana nan tsaye yana mayar da numfashi sai ya yanke shawarar sake hayewa saman bishiyar ya boye kudin shi. Rambo ya hau saman bishiyar tare da akwatin kudin ya makale a jikinshi" ya dora akwatin akan wani reshe ya kwantar dashi sannan ya fara shawarar fita neman abinci.......RALIYA-18 . Rambo yahau saman bishiyar ya boye kudin a makale a jikinshi" ya dora akwatin akan wani reshe ya kwantar dashi" sannan ya fara shawarar fita neman abinci" domin kuwa a halin yanzu ya fahimci idan har bai nemi abinci ba" to in ba sa'a ba nan da wani lokaci bazai iya tafiya ba Rambo ya sauko daga bishiyar yabar akwatin kudin shi a sama" sannan ya fara waige-waige domin ya samu wani abu a cikin kayan itatuwa da zai tsinka yaci" to amma kuma duk bishiyoyin dake wajen babu wanda ke da wani abinci da za'a tsinka" yawanci daga tsofaffin kukoki" sai gamji da kuma gawo" sai kuma dorawa da kadanya birjik ko ina Rambo ya yanke shawarar shiga cikin dajin domin samun abinci" ya fara tafiya kenan saiya tsaya ya waigo ya daga kanshi sama" ya tabbatar akwatin kudinshi suna nan ba abinda ya samesu Rambo yaci gaba da tafiya yana yi yana waigawa" domin kuwa ba'a son ranshi zai rabu da wannan akwati mai miliyoyin kudi ba" to amma kuma ai yunwa ta kare komai da zarar ya nemi abinci yaci" zai dawo cikin hanzari yahau sama ya kwanta tare da akwatinshi kafin gari ya waye Rambo yana cikin tafiya sai yaci karo da wata doguwar giginya" wacce 'ya'yanta suka nuna jawur dasu a sama" har guda biyu sun fado kasa Rambo yayi hanzarin daukar giginya daya yaji ta nuna" nan da nan ya share wuri ya zauna agindin itaciyar giginyar" ya fasa kwallo daya dake hannunshi" ya fara sha bai dade ba azaune yaji tunaninshi ya koma can wata duniya" yakamata ace a yanzu haka yana kasar turai" tare da fararen 'yan matan turawa kyawawa Amma yanzu cikin rashin sa'a gashi a daji cikin dare" yana neman abinci zaici to amma kuma da zarar Rambo ya tuno irin miliyoyin kudin da suka jefashi cikin wannan wahalar sai yaji sun cancanta su sashi kwana a daji Rambo ya kammala shanye giginyar ya kishingida domin ya dan huta" kafin ya koma inda ya boye akwatin akan bishiya" yana nan har barci ya dan fara surashi" ba'a dade ba" ba zato ba tsammani sai yaji wasu abubuwa dake kama da wukake su kimanin ashirin sun hadu wuri guda sun kwashe naman cinyarshi a lokaci daya kamar yadda yaro ke yago tsokar biredi" idan yana jin yunwa Rambo ya tashi a gigice yakai hannu a fusace" yaji ya mari fuskar wani abu cukus! Mai laima laima" dago kanshi keda wuya yana kara sai ya hada idanu da katuwar kurar dake tsaye a kanshi tana tauna naman dake bakinta" farin wata ya haske ko ina a jikinta" tana tauna naman suna kallon-kallo ita da Rambo Gama taunar keda wuya sai ta sake matsowa da sauri wajen Rambo tana gurnani" Rambo ya fasa kururuwa iyakar karfinshi sannan ya sake matsawa baya a tsorace ya duba cinyarshi yaga farin kashi a fili yana kyalli a cikin hasken farin watan babu tsoka Rambo ya dafe kafarshi yaja jikinshi ya matsa jikin itaciyar giginyar" domin yabar inda kurar Take A lokacin ne ta rugo a guje ta haureshi da kafarta na hagu" sannan ta tattakeshi da ragowar kafafuwanta" ta sake tirmisa katon bakinta a kwankwasonshi" ta sake samun nasarar debo katuwar tsokar nama" Rambo ya fashe da kuka yana kururuwa" kurar ta sake tsayawa tana taunar naman dake bakinta" tana kallon Rambo dake burari da jajayen idanuwansa" bayan ta kammala sai ta sake matsawa inda yake a kwance baya iya tashi" tayi tsalle ta sake dirmisa bakinta a jikinshi" ta jawo fatar kirjinshi yana kallo" fatar ta biyota nan da nan kurar ya tattake fatar ta tsinkata" taci gaba da taunawa" ko ina a jikin Rambo yayi face-face da jini" Abu na karshe da yaji kafin ranshi ya fita" shine bakin kurar dake kokarin karya dokin wuyanshi" har zuwa lokacin da Rambo ya mutu hankalinshi yana kan akwatin kudinshi da ya boye a saman bishiya Da ace yasan kurar zata sake biyoshi da bai sauko daga saman bishiyar ya bar akwatin kudinshi ba. Kafin safiya tayi" kurar ta gayyato jariran 'ya'yanta suka karashe dan abinda taci ta rage na ragowar jikin Rambo . =====>**********************<===== . Lokacin daurin auren Rufa'i da masoyiyarsa Raliya yazo A ranar daurin auren matasan karkara sunyi wasanni iri iri da kuma raye-raye" da bikin ya tashi ne abokan Rufa'i suka rakashi dakin amaryarshi Raliya" Duk wanda ya kalli wadannan ma'aurata biyu yasan cewar suna cikin farin ciki" domin kuwa Allah ya cika masu burinsu Haka Rufa'i da matarshi Raliya" suka ci gaba da rayuwarsu a kauyen Danmarke" wani lokaci idan suna cikin nishado haka kawai sai su tuno rigimar da akayi a kauyensu na misayar akwati a mota duk da yake cewar abin tsoro ne" yakan ba Raliya dariya" Tasancewar wannan al'amari ya zama tarihi bazai sake faruwa ba" Abinda Rufa'i da matarshi Raliya basu sani ba shine akwatin da ake ta rigima a kanshi har Yanzu yana nan a raye a saman wata bishiya tun watanni uku da suka wuce . A safiyar wata lahadi ne an tashi da lullumi da kuma sanyi muku-muku" wata tsohuwar mota mai ruwan toka kirar (HONDA ACCORD) ta keto ta cikin kauyen tungar malam tana burari kamar an tayar da injin nika motar tazo daidai wurin da wasu mutane ke zaune sun zagaye wutar dake ci suna shan dumi" tare da wata budurwa dake sayar da koko da siga" kwatsam! Sai motar ta fada cikin wani karamin rami" inda wata kwata kebi tana wucewa motar ta yunkura kamar zata haye ramin" sai kuma ta sare nan take tayi dif" ta mutu ko kawo wuta batayi Wani dogon mutum ke cikin motar tare da wata 'yar figilgilar matarshi tana sanye da atamfa dinkin zamani ta tsira dankwalinta a kusa da goshinta tana zazzare idanuwa" da ganinta ansan cewar da wahala tayi hankuri da kuma ladabi Mutumin yaci gaba da shurar motar kamar keken dinki" amma kuma ko sau daya bata kawo wuta ba" yana cikin kokarin ganin motar ta tashi ne" sai mutanen kauyen suka ji matar dake cikin motar ta fara balbalawa mijin nata masifa "Wai menene haka BALARABE ? Baka iya fita ka bude murfin injin motar domin kaga abinda ke damunta" idan ka sake har lokaci ya kure ban sami wacce zanje nema ba wallahi sai ranka ya baci" tun jiya kasan motar bata da lafiya" amma baka kaita an gyara ba sai yanzu da muka fito zaka kama wani haure hauren munafurci" Dogon mutumin ya share zufar dake fuskarshi da kuma dogon gemunshi yace da matar a fusace" Amma baki da imani ASABE saboda Allah da gangan zan lalata motar tawa" ni banfiki son muje lafiya domin inyi sauri in dawo ba" ina fa da aikin da zanyi kika matsa mani saina kaiki unguwar nan" kuma yanzu zaki kama yi mani masifa" to da wanne zanji da lalacewar motar zanji ko kuwa da masifarki Asabe? Mutanen kauyen suka mayar da hankalinsu kan mutumin da kuma matarshi wadanda suke ta misayar maganganu a cikin motar" wadanda ke shan dumi a bakin wutar" tuntuni sun bar wajen sun matso kusa da motar" sunyi mamaki da sukaji matar ta dakawa mutumin tsawa tace dashi a fusace "Ni ce kake cewa masifaffiya balarabe ?" Don kaga mun shigo cikin jama'a shine kake wannan cika bakin ko?" zamu bar nan din" zamu koma gida" saika fadamin wacce kake cewa masifaffiya" yan kwanakin nan nayi maka sakwa-sakwa naga ka fara raina ni" to wallahi zaka sha mamaki indai nice Dogon mutumin yace da ita "Idan mum bar nan don Allah kisa wuka ki yankani Asabe bana so ki barni da rai" Wani dattijo dake a zaune a cikin mutanen kauyen yana shan koko a roba" ya taso yaje inda motar ta kafe ya duba ya cewa dogon mutumin "Salamu-Alaikum malam ya akayi ne mukeji kuna ta sa-in-sa kaida iyalin naka meya faru ne?" Dogon mutumin ya waigo ya kalli tsohon yace dashi" baba wannan matar bata da mutunci" wallahi in banda rashin imani tare muka fada da ita a cikin motar ta lalace" amma zata hauni da masifa" to ni zan lalata motar da kaina?" ko ta fini son motar tawa ne? Tsohon ya dubi 'yar gajeriyar matar yaga ta zare mashi idanu" gata dai a tsayi bazata wuce rabin mijinta ba to amma kuma ko miskala zaratan bata shayin fada masa maganar da taga dama" wannan abu ya daurewa tsohon kai" yace da dogon mutumin Bari in kira yara gasu can mu turaku mu gani" idan ka fita a cikin motar watakila a samu ta tashi" Tsoho ya kwadawa wasu samari kira a cikin wadanda ke shan dumin nan da nan suka garzayo" suka matso wajen domin kuwa dama suna son zuwa kallon fadan da sukaji miji da matar sunayi a cikin motar" suna gudun kada suzo ba wani dalili ace sunje yin tsegumi ne" Tsohon da kuma samarin suka hadu a bayan motar suka fara tura motar" balarabe yana tare da matarshi Asabe a cikin motar" har mutanen kauyen suka fitar da motar daga cikin kwatar" Asabe bata sake fadan komai ba" saida balarabe ne ya fito yayi musu godiya ya basu hannu suka gaisa yana sanye da fararen kayanshi farare dinkin kaftani" dake tattare da wani tarihi da balarabe baya so ya rika tunoshi" tsohon ya cewa balarabe malam indai sha'anin matane sai kayi hankuri ko ina haka suke kaji Allah ya kiyaye hanya sai kun dawo Balarabe ya shiga cikin motar ya tayar da ita" saida ya amshi wuta ya tuka ya tafi tare da azababbiyar matarshe Asabe wadannan ma'aurata biyu dake a cikin motar suna tattare da dimbin tarihi mai yawa a zamanin aurensu" Allah ya hadasu suka zama miji da mata amma kuma kowa ya gansu yasan cewar ba abokan zama da juna bane Domin kuwa a kullum Asabe bata da wani aiki sai musgunawa wannan miji nata malam balarabe wanda yake kamilin mutum mai mutunci da kwarjini a wurin mutane" A dalilin ta ya shiga cikin masifu a duniya iri-iri ba iyaka" to amma kuma har yanzun Allah bai kawo karshen zamansu ba" suna nan a zaune da dadi da ba dadi..... . KUN TUNA SUWAYE WAYANNAN MATA DA MIJIN ??RALIYA - 19 . . Da dadi Ba Dadi dayawan mutanen suna rade-radin cewar wasu lokuta har dukan balarabe matar keyi ko kuma ta kulle gidan idan ya fita koda ya dawo ba zata bude mishi ya shigo ba" sai dai ya kwana a masallaci dake a kusa da gidan shi to idan ma duk wannan sharrine na masu karawa miya gishiri" abinda kowa ya sani ne Asabe bata ragawa malam balarabe kuma duk abinda tace tana so a duniya saiya nemo mata koda kuwa ace sata zaiyi Da farko farko kafin ya aureta da kamshin arziki" to amma kuma tun sanda tazo gidanshi bana shekaru kusan biyu kenan duk al'amuranshi sun tabarbare sun lalace bashi da komai a duniya yanzu in banda wannan tsohuwar mota da kuma gidanshi Ba karamin sa'a balarabe yaci Asabe ta barshi ya kara aure ba a shekarar da ta gabata" koda yake auren ba wani mai wahala bane" aure ne na rufawa juna asiri" wata yarinya ce data rabu da sana'ar bariki ko kuma da akayi korar matan banza ta rasa inda zata sa kanta sai kakarta ta daukota tazo da ita wajen malam balarabe domin yayi mata nasiha ta sami miji tayi aure" Bayan yayi mata fada ne ya jawo hankalinta data tuba" sai ta sanarwa kakarta cewa malam Balarabe take so" Da yake makwabtan juna ne da gidan balarabe dana kakar yarinyar mai suna MOMI ba'a wuce sati biyu ba aka daura auren momi ta tare gidan malam balarabe" tun daga ranar da akayi auren saida Asabe tayi kwana talatin da shida tana zazzaaga masifa a cikin gidan" sannan kuma tun lokacin da akayi auren har zuwa yanzu sai Asabe taga dama takeyin abinci a gidan" Idan ta bushi iska duk ranar da abincinta ya Zagayo sai ta rike kayan abincin ba zata yiba kuma bazata bar momi kishiyarta ta amsa tayi girkin ba Sai dai idan malam balarabe ya dawo ya iske ba'ayi komai ba a gidan sai ya nemowa amaryarshi abinda zataci a boye domin kuwa idan ya kuskura Asabe ta gani to a ranar bazai kwana a cikin gidan ba" sai dai ya kwana a masallaci Sauda yawa Asabe tasha hayewa kishiyarta momi ta nemeta da masifa na gaira ba dalili duk lokacin da irin wannan ta taso momi bata kula ta watarana haka kawai sunci abinci sun koshi" sai Asabe taje har dakin kishiyarta taci mata kwala tace da ita ta fahimci tana yi mata wani gani-gani don taga itace amarya a lokacin ne momi ta nunawa Asabe ko ita wacece" bayan ta lakadawa Asabe shegen duka a cikin dakin sai tace da ita "koda kike ganin ina yi maki shiru shiru" ni ba tsoronki nake yi ba" ina kyaleki ne Asabe saboda yanzu ba zaman banxa nakeyi ba" zaman aure nake yi" Amma da ace a lokacin da nake zaune a gidan MAI LOMA" kafin in tuba ke kanki baki isa kizo ki tare da irin wannan rashin mutunci ba"" na zauna da masifaffun mata wadanda suka damaki suka shanyeki a wurin fitina" irinsu marigayiya SIMA kawata" irin su surayya" da kinsan zamanin da mukayi a baya da kin gane cewa ni din nan hatsabibiya ce" to amma yanzu bada bane ina so ki hada kai dani mu zauna lafiya" Allah ya bamu miji mai kwazo da hakuri me zai sa ki rika tayar mana da Hankali Asabe? Tun daga wannan ranar Asabe ta fara tsorata da momi" domin kuwa ta gano cewar hakika itama momin ba kanwar lasa bace" haka suke ta zama cikin hakuri duk kurar da Asabe ta kwaso sai ta watsa ta akan mijinsu malam balarabe momi tana kallo bata ce komai domin kuwa ita a ganinta laifin balarabe ne daya bari har matarshi tafi karfin shi. Balarabe yana da wata bakar mage wacce yake matukar so a duniya domin kuwa ita kanta magen tana da nata tarihin rayuwar" farkon haduwar balarabe da wannan magen tsoron ta yake ji" to amma daya ga cewar duk inda yaje tana nan biye dashi" sai ya dauke ta a matsayin amana tunda zuwan momi gidan take gatanta malam balarabe Amma kuma ita Asabe haka kawai sai ta hau magen da duka don balarabe yaji haushi idan abin ya dami momi sai ta cewa Asabe "Bai kamata kina zaluntar dabba ba Asabe wannan magen da kike gani a wani lokaci da ya wuce" tafi ki gatanci" wata kawata data rasu take da magen" bayan mutuwarta sai ta barwa wani gaye mai suna Sule Oska shi kuma da ya mutu gashi yanzun ta dawo hannun malam balarabe itama yanzu magen ta shiryu ne" ta baro gidan mai loma ta dawo gidan malamai bai kamata kina takura mana ba ni da ita" domin kuwa duk tarihin mu daya da ita" Wannan shine dan takaitaccen tarihin rayuwar auren malam balarabe tare da wannan mata data zame mashi karfen kafa wato Asabe ko a lokacin da yake kan tuka motar a hanyar kauyen da zai kaita" sai da ya tuno irin wadannan halaye data sha yi mashi na alatsine tun shekara da shekaru Wani lokacin sai balarabe yayi kamar zai saki matarshi Asabe" to amma da zarar ya shigo gidanshi sun hada ido" sai yaji yana masifar sonta bazai iya rabuwa da ita ba" Sannan kuma wasu lokutan koda ace ya dauki alkawarin idan ta sake sashi wani abu bazai yi ba" da zarar tazo ta tsaya gabanshi ta kalleshi ko me ta sashi sai ya tashi yaji jikinshi yana rawa ta riga ta zame mishi bala'i bazai iya rabuwa da ita ba" Balarabe da Asabe suna cikin tafiya a motar" suna wuce bukkokin masara a gonaki" da kuma giccikan dawa da aka girbe" sunzo daidai wajen wani shuri kenan" daidai wani dan karamin fako da ya zama saura ba.a noma shi ba" sai dai shanu da awaki ke shiga suna kiwo" Sai motar balarabe ta sake birkicewa" tana zillo Zuwa can saita mace" balarabe yayi ajiyar zuciya sannan yayi sauri yayi fakin a gefen hanyar cikin ciyawa" Asabe tayi tsaki iyakar karfinta" suka hada ido da mijinta balarabe" yayi saurin kawar da kanshi gefe guda" domin kuwa yasan cewar ta gama kulewa" ci gaba da kallonta ba alheri bane agareshi" ga shi kuma nan daji ne ko fada suka yi babu mai sasantasu" sai dai ta bugi na bugu ta kyaleshi" ba yadda zaiyi da ita" Asabe ta dakawa balarabe tsawa a fusace To ka tsaya zaman jiran motar ta gyara kanta ne bazaka fita ka duba aga abinda ya sameta ba? Balarabe yayi sauri ya bude kofar motar ya fita kafin ya bude murfin injin ne yaji Asabe taci gaba da balbala mishi azabar da ta saba" Ina amfanin mace ta auri matsiyacin miji a duniya" kawai da kuruciyar mutum duk ya lalace a banza ace kana da miji motar arziki ma bashi da ita" ni in banda ma kaddare me zan dauka awajen gayyar tsiya" Ba wani muhalli na fita kunya" ba motar arziki ba gara ma zama na a gidan Alhaji mai nasara ba" ina cikin mutumci naja wa kaina na fito" dole ne in gaggauta komawa wurin tsohon mijina mai Nasara Balarabe yana jin matarshi Asabe tana ta aikin bala'i a cikin motar yasan cewar jira takeyi ya tanka mata ta fito taci mishi mutunci" yaci gaba da gyara wayoyin injin motar baice da ita uffan ba Domin kuwa shi dama yawanci yafi mayar mata da martani idan yaga akwai mutane a kusa dasu to amma idan su biyu ne baya kulata ya riga ya saba Akwai lokutan da in aikinta ya zagayo da zarar ya dawo daga sallar isha'i ya kwanta domin ya huta" zata haushi da masifa" idan ta gama wannan sai ta fada wannan" a haka har barci yake kwasheshi tana masifa ita kadai bata sani ba Idan irin haka ta faru" sai Asabe tasa hannu ta makawa balarabe duka ya tashi barci afirgice domin kuwa bata son tana zazzagawa mutum bala'i yayi shiru ya mayar da ita mahaukaciya tafi son ko sau daya ne mutum ya dan ce da ita wani abu" to amma kuma a wannan karon ma haka akayi" Balarabe yaci gaba da gyaran motar kamar baya jinta! Da Asabe tayi iya tsiyarta" har makogwaronta ya fara zafi" saita hakura taci gaba da zama a cikin motar" zuwa can da taji zaman ya isheta" saita bude motar ta fito waje" bata cewa Balarabe komai ba" saita nufi gindin wata karamar bishiya mai yawan reshuka" wacce ke gefen labin da shanu ke wucewa" ta zauna a gindin bishiyar" tana wasi-wasi a zuciyarta" wajen wata bokarta zataje" batason tana bata lokaci idan sunyi alkawari shiyasa ta matsawa mijinta balarabe ya kawota a mota" gashi kuma motar ta lalace" tuntuni bokar keyi mata aiki akan wani hamshakin mai kudi da Asabe take satar jiki taje wurinshi idan balarabe yaje wurin aiki Wasu makudan kudi take so ta fizga a wurin attajirin" to amma kuma ta fahimci saita hada da 'yan dabarun da ta saba" na wani turare da take amsa a wurin bokarta" Kudi!!" Hakika Asabe tana neman kudi a duniya ido rufe" to amma kuma sunki taruwa" Asabe tayi ajiyar zuciya" sannan ta jingina a jikin bishiyar ta daga kanta sama" tana kallon reshikan dake kadawa suna kara sannu a hankali idan iska ta busa" A lokacin ne Asabe ta hango wani abu mai duhu-duhu a boye a can kololuwar bishiyar ganyaye sun rufeshi" Asabe ta kura idanunta a tsammaninta kukun Zuma ne da ake sawa a kira zuma ta taru" to amma kuma sai Asabe taga abin yana kyalli kamar akwati" tabbas akwati ne! Ta tabbatarwa zuciyarta" me ya kawo akwati saman bishiya" anya kuwa ba barayi bane suka yi sata suka zo suka boye a saman bishiyar?" Asabe ta kwadaya mijinta balarabe kira cikin kosawa" nan da nan ya saki gyaran motar ya hanzarta zuwa wurinta tayi saurin nuna mishi abinda ta gani a saman bishiyar Wani abu na gani kamar akwati a saman bishiyar nan gashi can duba ka gani Balarabe ya daga kai yabi yatsan Asabe matarshi kuwa inda take nuna mashi" ya hango abin baki wuluk a cikin reshuka" akwai wani dan karfe mai kyalli a jikinshi yace "tabbas wancan akwati ne" to amma meya kawo akwati nan? Asabe tace da balarabe

Chapter 7 of 11