Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
ko sha. Da makilin ya soma cin karo, gasu nan kala kala, ko wanne da kudinsa manne a jiki. Sai ya dauki mai tsadar ciki, ya sai brush da sabulun dettol na wanka. Sannan ya koma gurin kayan sha. Ya rasa wanne irin drink take sha. A qarshe sai ya dauki maltina a nasa tunanin kowa yanasha. Ya sai katan din ruwan gora guda biyu, sai kayan tea na manyan gwangwani. Suga na kwali. Ya sai flask din ruwan zafi. Daya fito wajen gurin ne kuma ya isa gurin masu saida kayan marmari, ya sayi Apple, lemon zaqi, sai kankana da abarba. Dan acha6a yace, gsky malam za fa kaimin qarin kudi. Ismail yace, babu komai, Allah dai ya kaimu lfy. Da kaya niqi-niqi ya hau samansu, gabansa har faduwa yake yi daya tunkaro asibiti. Haka dai ya nufi dakinsu, tunaninsa a wane hali zai samu mimin aciki? Don yasan zaiyi wuya in bata farka ba. Ya tura qofar cikin sallama, k idanunsa suna kan gadon. Yaya Amina ta amsa Sallamar tana kishingide a dayan gadon. Yace sannu yaya na barki ko? Ta sauko tana tana fadin, banyi zatonka a wannan lokacin ba, ko har kunje zariyan? Ya nufi gadon mimi yana cewa, mun bari sai gobe, sbd yau yamma tayi. Bata farka bane? Yaya Amina ta iso gaba gadon. Tace, ta farka, ko ido bata bude ba, kuka kawai take yi. Don nima nishin kukan ta yasa nasan ta farka. Tsaki yaja cikin damuwa yace, nidai Allah ya sani wannan kukan yana damuna. Yasa yatsansa ya debe mata gashin kanta daya watso kusa da idonta, ya maida mata shi bayan kunnenta. Ya tsura ma fuskarta ido, wadda tayi jajur don kuka. Idanunta kuwa sun kumbura sunyi luhu-luhu. Ya dora tafin hannunsa akan goshinta. A fusace ta bude idanunta, qwayoyin idon sunyi jajur. Ta zuba masa harara, sannan ta girgiza kanta, alamun ya cire mata hannunsa daga goshinta. Yace bakisan in dafa miki goshi ne? To na cire. Amma ynxun ki tashi kici wani abu. Ya rusuna ya soma ciro abubuwan daya siyo daga cikin ledar. Yaya Amina tace, Yauwa yanada kyau ta wanke baki kuwa, ga makilin da brush. Amma ka manta baka siyo roba ‘yar mai fadi ba, da FO sbd fitsari, don kaga tana varcin nan duk ta fitsare kayan jikinta da na kwanciyr. Gashi Kaje gida amma baka dauko mata kayan sawa ba. Ismail yace, fitsari kuma? Ya dago ya kalli mimi, fitsarin lfy? Sabon kuka mimi ta saka. Domin farkawar da tayi taji ta sharkaf cikin fitsari ya tada mata hankali. Wai ita mimi ce haka? Mimin daddy mai shanawa. Sam bata son ta bude ido ta kalli asibitin bare malam Ismail, wanda ta tsana fiye da kowa. Ta tuna lokacin da tayi wani zazza6in mura, waje suka fita, can England aka duba lafiyarta. Tunda ta taso, duk bayan wata uku dad yake kaita a duba lafiyarta a qasar Misra. Amma yau gata a wani qazamin asibiti kwance cikin fitsari. Ina ma dai mutuwa tazo ta dauke ta. Da ma da sukayi hadarinnan itama ta mutu da yafi mata wannan Rayuwar. Ismail yace, ba zaki yi magana a saki ba mimi? Yaya Amina tace, haba Ismail, Kalli yadda take mana qafafu a sagale taya za’a sata tayi fitsari? Yace hakane. To ynxun sai dai ta dinga yi a kwance? Yaya Amina tace, dole a samu robar fitsari, amma mu nemi Shawarar likitan. Ismail yace, to zan sameshi. Amma ynxun ya kk ganin za’ayi gurin cire mata kayan? Ko inje in fara dauko mata wasu in dawo? Yaya Amina tace, to kayi sauri don inason inje gida sbd abincin dare. Insha Allahu yanxun zan dawo. Duk akwatunanta ya chaje su tsaf, babu riga da zani, mafi yawa daga cikin kayanta ‘yan kanti ne, riga da wando, sai dogayen riguna. Na atamfan ma daga doguwar riga sai riga da siket. Tsaki yayi, cikin haushi ya bude qaramar Jakarta, wadda ta dauko zata gudu da ita. A ciki yaga Jakarta wadda ta zuba kudadenta data debo sbd guduwar su. Ya ciro jakar yaje ya daga can qasan katifarsa ya sata cikin tsohuwar malum-malum. Ya daga ledar tsakar daki, ta qasan katifar ya saka, sannan ya maida katifar. Yayi hakane sbd tsoron 6arayi, tunda shi ba wai yana kwana a gidan bane, kar a zo a bude dakin. Ya dawo ya bude akwatin da yaga kayanta na ciki. Aciki ya ciro siket da dan kanfenta, sai best. Baisan meyasa ya zuba ma rigar mamanta ido ba, qila kyau tayi masa, amma duk da haka bai dauka ba. Qamshin turarenta kayan sukeyi, sai ya dauki ‘yan shirt guda uku, tunda babu zannuwa. Yace zaibi ta bakin kasuwa ya sai turmin zani ya tsaga su gida uku. Ya dauki bargon rufarsa da zanin gado, sannan ya nufi kasuwa, daga can ya wuce asibitin. Yauma ya hangi innar su Zainabu acan baya gurin wanki. Yauma haka ya hau sama yana tambayar kansa wai wa take jinya? Ya samu yaya Amina da taimakon nurse din dake aiki a wannan lokacin suna cire mata kaya. Ido hudu sukayi da ita, lokacin daya shiga an cire mata riga. Cak ya tsaya, domin idanunsa sun kalli abinda bai ta6a gani a fili ba Runtse idanunsa da yayi, sunzo daidai da ihun data yi. Yaya Amina tace, “mun yi miki fami ko? ” Malam Ismail ku rufemin jikina. Tun farfadowarta, sai ynxun tayi magana. Ismail ya ajiye kayan hannunsa a gurin. Idanunsa a Runtse ya juya. Sannan ya bude idanun. Abin daya gani suna yi masa gizo. Ya fita kan benci, ya zauna tare da tura hular kansa baya. Sannan yasa hannunsa ya shafe fuskarsa. Wani yanayi ya samu kansa a ciki, wanda ba zai iya tantance shi ba. Wata zuciyar tace, ba fa haramun ka gani ba, duk ka rude haka, matar kace. A cikin dakin kuwa, yaya Amina ce ta zo ta dauki kayan da uwanta ya ajiye taje kan daya gadon ta zazzage su tana dubawa tare da cewa, shikenan tunda ya fita sai kiyi haquri. Nurse tace, wane haquri, ba kunce mijinta bane? Yayan tace ai bata ta re bane shiyasa. Nurse tace, to kuwa kina da aiki. Mimi dai sai kukanta takeyi, saboda baqin cikin qirjinta da malam Ismail ya gani, har suka gama kintsa ta bata daina kuka ba, sunce zasu sa mata robar fitsari, tace ita dai bata so, Nurse din ce taba yaya Amina Shawarar su sai mata pampers na manya. Shi sai dai kawai a cire a yar, ayi mata tsaki, yaya Amina tayi mata brush, taqi cin komai, sai ruwan data sha kusan rabin gora. Baiji fitowar nurse din ba, sai dai muryarta yaji tana cewa, kana zaune anan ne? Ya kalleta, kun gama? Tace eh, ya ce na gode. Tace ba komai, sai kaje kayi lallashi, don shagwa6ar matarnan taka tayi yawa. Hannu yasa ya shafa fuskarsa tare da yin guntun murmushi. Ta wuce gurin aamansu shi kam ya kasa shiga dakin.\Yaya Amina ta fito, cikin jin nauyi ya kalleta. “tafiya zakiyi? “Tace, eh, kaga yamma tayi, ga girki. Ummi ba girki ta iyaba. Nasan dai zata share min gd tsaf, har ma ta hana su Saddam yimin wasa a cikin daki. In ba ayi sa’a ba sai yayi ta dukanta. Ismail yace, ai rigimar sako da sako na gurin saddam da Ummi, kamar masu ganin hanjin juna. Tayi dariya. Haka suke, amma in daya baiga daya ba, ayi ta damuna, mama ina take, ko ina yake? Ismail yace, haka suke fa. Cikin zaulaya yace to kisa abbansu saddam ya qaro aure mana. Kin ga kin huta, baki da tunanin yin wani girki. Tace oho, sakamakona kenan nayi maka jinyar mata? Cikin dariya yace, yaya laifi ne? Tace, ban sani ba, ni kaga tafiya ta, sai anjima. Yace yaya ki vari sai gobe mana. Tunda ma da kayan tea, sai in sha ruwan zafi. Tace shikenan sai goben. Yace, zaki zo da wuri ne, sbd inason zamuje zariyar nan. Tace, zanzo dai kamar qarfe goma. Yace, Allah ya kaimu. Har gurin matattakalar ya rakata sannan ya dawo. Tsaye yayi a bakin qofa yana tunanin yadda zai shiga dakin. Daga bisani yayi ta maza, ya tura qofar tare da yin sallama. Tana zaune akan gadon, an cire mata qafafun daga sagalewar da akayi musu. Sannan an dago gadonta, gurin kwanciyr, ta yadda zata iya kishingida. Ya kasa kallon fuskarta. Yace, meyasa bakici komai ba? Ya isa gurin fridge ya bude, ya ciro gwangwanin maltina. Kisha maltina mana? Tsakin da ta ja shine yasa shi kallon fuskarta. Harara take ta zabga masa da jajayen idanunta. Ya sauke idanunsa, yasan kan abin da ya kalla dazu ne. Sannan ya sake kallon fuskarta. “kiyi haquri, dazun bansan ana shiryaki bane. Kuma ni banga komai ba ma. Bata dai tanka shi ba. Yace, kisha maltina ko kadan ne kinji? Tace, ni bana sha. Yace to fadamin kk so kici? Ta soma kuka. Yace, kinga matsalarki. An ce miki kuka yana maganin matsala ne? Wannan kukan sai dai ya qara miki ciwon. Tace, ni da zan mutu sai nafi murna. Rayuwata ba tada amfani. Yace sbd me? Tace, khalil ya mutu. Shine kawai ya ragemin a duniya. Ismail yayi murmushin takaici. Ko zaki bishi ne? Ta Kalli Ismael a fusace, ai da ace inada izinin tashi, to da tuni na fada ta wannan windon. Ismail yace, in kuma Allah baiga dama ba, kk karye, kuma yaqi daukan ranki, kizo kiyi ta jinya ba. Wai shin ma in tambayeki, da kk ta burin mutuwa, me kk tanada na ibada ko na alheri, wanda zaki kare kanki, ko kuma ince wanda zaki amsa tambayoyi a gaban Allah? Mimi ta sunkuyar da kai. Yace, inaso kisan wani abu, fushin iyaye ba qaramin bala’i bane. Dakin mutu a hadarinnan, kin tafi da fushin iyaye a gudun da kk yi, kinsan illar dake cikin guduwar ‘ya mace kuwa? Koda yake kece zaki bada labari tunda gaki a gadon asibiti. Sannan gudunki na farko ma nasan kin hadu da wani qalubalen, sai dai in ba zaki fada ba. Ta daga masa hannunta mai lafiyar, ni bance maka kaimin wa’azi ba. Da zama da kai a matsayin miji, gara min mutuwa. Yace sbd me? Tace ni ban son ka, na tsane ka. Ismail baya varin bashin magana. Don haka yace, ashe duk daya muke. Nima mimi bana sonki. Sam bakya cikin tsarin macen da nake so. A ra’ayina inason mace mai kyau, mai son addini, kuma maijin maganar mahaifanta. Kalamansa sunyi wa mimi zafi. Har ta kasa cewa komai, sai kai data sunkuyar ta soma kuka. yasa hannu ya daga fuskarta. Karki damu in kin samu sauqi, zamu san yaya za’ayi ,ta goce kanta da qarfi, kar hannunka ya sake ta6a ni. Yace, nifa damuwa ta kici wani abu, tace bazan ci ba, ni ka barni, ya koma bakin dayan gadon ya zauna. Ya soma shan maltina tare da cewa. Na barki. Har bayan isha’i tana kukan maganganun da Ismail ya danqara mata, lokacin kuma likita yazo. Bayan sun gaisa, ya tambayi jikin nata. Ismail yace, jikin da sauqi, amma taqi taci komai. Likitan ya kalleta, khadija! Ta dago ta dubeshi. Yace me zakici? Cikin wata murya mai ban tausayi tace, ba komai. Ismail ya ta6e baki, barta likita, cikinta ne zai fada mata. Sai kuma maganar pampers, dazun wata nurse ta ba yayata Shawarar mu sa mata pampers sbd fitsari, tunda taqi a sa mata roba. Likitan ya kalleta, ki bari mana a sa miki robar fitsari? Tace doctor bana so. Ta sunkuyar da kai tana tuna zuwansu katsina, ita da hajiya. Ta matsa wai sai an kai ziyara asibiti da gdn marayu. Daddy baiso zuwa ba yace zai bada abinda za’a kai, amma hajiya ta cije tace dashi za’aje. Aka tafi harda ita, a wani asibiti ne taga marasa lfy an daura musu ledar fitsari. Ta tambaya menene wannan? Aka ce mata ledar fitsari ce, saida tayi rashin lfy sanadin ganin marasa lafiyan. Sannan ace za’a sa mata. Shikenan ka sai mata pampers din, amma amma dai zaku sha kudi, in kuma zaka dinga sata a toilet din da kanka, da sai yafi muku. Da sauri mimi ta daga kai, Allah ya tsareni, ko hannuna karka sake ta6a min. Ba mijinki bane? Ko pampers din waye zaisa miki in ba shi ba? Duk wahalar da yake miki, yana kashe kudi akanki shine zaki dinga yi masa haka? Mimi tasoma kuka,”Ni bana son yasake tabani,na tsaneshi”. Kuma ai kudina ya dauka yakemin magani.Ai bashida kudin dazai kashemin. “Likita kar ka damu da ita,nima inayi mata ne don Allah,da Lima tausayin halin da take ciki,amma rashin mutunci halintane ko tayi min bazae dameni back.Ita ikirarinta bata sona,nima kuma bnga abinso a gurinta ba”. Likitan yayi murmushi ,don ya fahimci Isma’il yana maganar ne don son cusa haushi ga marar lafiyar. Yace “khadija wae bakya son shi?” Tace “eh”. Saboda me? Tanuna isma’il da yatsanta,”saboda abubuwa da yawa. Ina zargin sa da shiga cikin rayuwata. Kuma ya taemaka gurin shigata wannan halin. Isma’il yazaro ido yana kallonta,a zuciarsa yace”sharri zatayi min?” Likitan yaja kujera, yazauna tare da tattara hankalinsa gareta. Sanar dani hujjoinki,kila inada taemakon dazanyi miki. Tasoma kula “Ranar wata asabar nasoma jin lavarinsa a wurin kannaina. Sunaji dashi a matsayin malaminsu. Ranar farko Dana dora idanuana a Kansa,ranar ya raena min wayau,tare dafada min maganganu na wulaqanci. Abinda baa taba yi min ba a rayuwa ta. Sannan shi ne mutum na farko da banyi nasarar rama abinda yaemin ba, duk da cewa yayi min abin da baa taba yimin ba. Sannan shine mutum na farko dana taba kae qaran shi wurin daddyna bae amshi korafina ba. Tundaga ranar asabar din daya dira gidanmu Abuja,van qara samun kwanciar hankali ba.A qarshe shine daddy ya daura min aure dashi a ranar asabar kuma. Kalli wannan abin doctor,ta yaya zan yafemasa wannan zunubin? Salis yayi qoqarin danne dariyar da ke qoqarin kufce masa,sannan cikin zolaya yacee “gaskia yayi babban zunubi”. Ismail kam dariyarsa yayi harda qwalla.sannan yace, “Mimi kenan ,kiyi haquri,don nifa haka nake, duk inda nashiga sae nayi nasara akan duk mae ja dani, saboda na dogara ga Allah.kinsan duk Wanda ya mika lamuransa ga Allah,to fa Allah ya Isar masa.kinci sa’a ma wannan guntun labarin naki agaban likita kika fada,ba agaban alqali ba, da sae ya daureki.Domin babu abinda ya hada labarin nan da halin dakike ciki.ni na hanaki bin umurnin mahaefinki? Ni nace miki ki gudu? To, in baki sani ba kisani,bijirewa mahaifinki da kuma gudun dakikayi kika bar iyayenki sune silar shigarki wannan Hamlin. Likita have, wai-wai-wai kin gudu ne dama? Ta sunkuyar da kai, hawaye ne kawai ke zuba. Lallai kinyi babban laifi. Ko dani ba alqali bane. Kamar yadda Ismael yace, amma na yarda gudunki ne ya jawo miki wannan halin da kk tsinci kanki a ciki. Ta soma tuna yadda suka auna arziki a gudun farko. Ashe gargadi ne suka tsallake. Na biyu kuwa shine masoyinta ya mutu, ita kuma gashi ta kakkarye, Burinta in ta warke ta sake guduwa inda iyayenta da danginta ba zasu ta6a jin labarinta ba. To kenan mezai faru in ta sake guduwa? Duk zatonta a zuciya takai qarshen maganarta. Ashe a fili ne. Sai kurum taji yace, in kk sake guduwa na uku, qila qafafunki da hannayenki su gutsire, ki koma gundulmi, kinga kenan sai bara. “Bara? ” ta zaro ido. Likita cikin son firgita ta yace, “bara kuwa” sabon kuka ta dora, tare da cewa, ” Allah ya dauki raina in huta. ” Ismail yace kinata burin mutuwa, an fada miki sauqi zaki samu in kin mutu a haka? Na tambayeki guzurin da kkyi na zuwa lahira, amma baki ban amsa ba. Kk yarda kk mutu a haka, ai kwanciyr kabari ma kawai ya isheki. Ta Runtse ido cikin tsoro, tana tunanin kalmar likita. Wai tayi bara, Nan ta tuna wani English novel data karanta yadda Yarinyar cikin labarin ‘yar sarauta, sakamakon son zuciya, ta qare da gutsurarrun qafafu kuma a gidan yari. A firgice ta dago ta Kalli likitan, sai taga ya yagi kwalin magani ya ciro biro a gaban aljihunsa ya soma rubutu. Ya gama, sannan ya miqa ma Ismael tare da cewa, duba ka gani, kasan wannan magani? Ismail ya kar6a tare da cewa to, Ya soma karantawa kamar haka. “Ismail inason ka sauke duk abinda ke ranka game da Yarinyar nan. Ynxun na san bata san tunanin da zatayi ba. Amma ni da kai in mun hadu zamu saita mata tunanin ta. Ismail ya dago kai, ya kalli likitan sannan ya kada kai, na san shi. Likita yace, to kasai mata shi a hada cikin magungunan. Ba damuwa, inji Ismail. Likitan ya sake kusantar gadon mimin, “yanxun, menene tunanin ki a gaba, ko ince burinki? Inason in taimakeki ne matuqa. Mimi cikin kuka tace, banda wani sauran tunani, tunda malam ya dage wai mutuwa ma ba hutu bace a gareni. Da farko na daura aniyar dana warke zan gudu, in nesanta kaina da mahaifana, yadda baza su sake samun labari na ba. Inason su manta sun haifi ‘ya irina. Kai in mutu ma yadda zan nesanta dasu gaba daya. Amma ynxun kunce haka. Likita kai ka taimakeni ka nesanta ni dasu mana. Doctor salis yace, “yi shiru daina kuka, in miki abinda kk so, ta tsagaita saidai ajiyar zuciya da takeyi. Yace, na tabbata in kin kwantar da hankalinki, Ismail dinnan zai nesanta ki dasu, kamar yadda kk so domin shi mijink… “Ta katse likitan da cewa, bana buqatar yaci gaba da zama mijina. Doctor salis yace, dukda haka zai iya, zaka iya ko? Ya kalli Ismail. Yace zan iya matsawar zatayi min alqawari guda daya, sannan zata kwantar da hankalinta tare da bani hadin kai, to zan nesanta ta da mahaifanta, sannan ba aanci gaba da zama mijin nata ba, in ta buqaci hakan. Tace, menene tabbacin, zaka bar gari dani ko qasar? Ya ce, kina cikin garin katsina amma ba dole ku hadu ba, ko susan inda kk. Ta danyi shiru, sannan tace, fadi alqawarin inji. Yace, zaki dauki alqawarin cewa, ba zaki gudu ba, duk wuya, duk runtsi. In kinyi haka, ni kuwa zan 6oyeki, tare da yi miki duk abinda kk so, iyakar iyawa ta. Haka kuma in bakya buqatar inci gaba da zama mijinki, sai in koma wanki. Likita yace, bakida wani za6i sama da wannan. Kuma asirinki rufe. Tace, in kuma hajiya ta kirashi fa ko Alhaji don jin inda nake? Yace daga yau zan kwafe duk numbers din dake wayata banda nasu, sai in baki sim din ki karya, ki zubar. Tace, to in akazo gidanku fa? Ai kafin mubar asibiti zan nemi haya a wata unguwa daban, kuma ko ‘yan gidanmu ba zasu sani ba. Dama basu san gidanmu ba. Dama Hamisu direba ne kawai ya sani. Tayi shiru, domin qaramar kwanyarta ta yarda da abinda akace. Ta kalli Ismail, kenan daga ynxun kai ba mijina bane? Ismail yace, a’a wannan shine zai zama a qarshe, ko yaya kace likita? Likitan yace, wannan hakane. Ta girgiza kai, tare da dan yatsina fuska, sbd dan radadin da ciwonta keyi mata. Tace ban fahimta ba. Likita yace, kinsan za’a bi abin daki-daki ne. Farko dai zamu fara ta lafiyarki. Zanso ki bada hadin kai gurin ganin anyi jinyar ki cikin sauqi. Ki dinga cin abincinki, kina shan magani har a sallameki. Kinga wannan ne farko. Sai mu koma kan abu na biyu, bayan an. Sallameki ki zauna dashi tamkar ‘yar uwa, kiyi haquri da duk abinda ya samo ya baki na abinci, ko na sutura, ki kuma nutsu, babu batun guduwa, don kamar yadda yace, zai zamar miki wa. Ko ince kun riga da kun zama daya ma, domin jininsa ne aka zuba miki yake hade da naki. Ta dago ido ta Kalli Ismael, sannan ta Kalli hannunta mai lafiyar. Ta runtse tafin hannunta tana kallon tsintsiyar hannunta, kamar mai kallon jinin yana haduwa. Likitan shiru yayi, daya ga tayi hakan, don yasan zantukan nasa sun shigeta sosai. Ta katsewa likitan tunani da cewa, Doctor in nayi haka fa? Ina nufin sai menene a gaba? Yace, sai batun raba auren ku dashi. Ismail yace, kuma in kin samu wanda kk so, ba zai hana muyi miki aure dashi ba. Da sauri ta Kalli Ismael. “Ni bazan qara soyayya ba. Nayi ta na gama, don na haqa rami na binne ta. Zan rayu ne ni kadai. Ismail yace, duk wannan babu matsala, matsawar zaki cika alqawarinki na qin guduwa ko ina. Ni kuma zanyi miki duk abin da kk so. Ta soma qoqarin zamewa don ta kwanta. Sai dai amma ta kasa. Likitan yace, yayanki ya taimaka miki? Tace a’a likita, bana so ya dinga kai hannunsa jikina. Likita yace, wannan babu matsala. Ya miqe ya nufi waje, nurse ya kira yace tazo ta taimaka mata. Sannan ya kira Ismail, zo mana, mu danyi wata magana. Sun jera tamkar abokai. Likitan yace, Ismail banaso ka damu da duk abinda Yarinyar nan zatayi. Ka ceci Rayuwar ta ta hanyar kyautata mata don kar tace zata sake guduwa. Kabi da ita ta hanyar da muka sata akai. Sannan kayi mata qoqarin nesanta ta da mahaifanta na wani lokaci, sbd a samu ta nutsu, ta kuma saba daku. Ismail yace, Allah yasa ta iya. Domin in kaji labarin gatan da take ciki zaka sha mamaki. Allah dai ya shige mana gaba. Doctor salis yace, Ameen. Sannan inason duk lokacin da kk buqatar taimakona a game da wannan matsalar taku, ka kira number ta, sannan ya ciro katinsa ya miqa ma Ismael, “akwai numbers dina a jiki, ko da bana nan a asibiti. Ismail yace, nagode sosai Doctor. Na’ima kuwa, yadda taga rana, haka taga dare, sbd mijinta yana samanshi tare da wata mace, wadda ba halalinsa ba. Tayi kuka ta gaji, idanunta sun kukkumbura sunyi jajur. Maimakon Na’ima ta tashi cikin darennan ta miqa kukanta ga Allah, madadin kukan da takeyi. Saidai kash ba zata iya yi ba. Tasan ma anayin hakan. Allah ka ganar damu, Ameen. Bata qara tsurewa ba saida gari ya waye kusan goma da wani abu tayi wanka ta fito. A tunaninta sun bar Gidan. Ta nufi kicin ne don tasa masu yi mata aiki su hada mata abin kari. Cak ta tsaya sakamakon ganin karuwar tare da angon nata suna hada abin da zasu karya. Batasan sadda zuciya ta kwashe ta ba, ta qarasa kicin din cikin fushi ta daqumi wuyan ‘yar best din da Jennifer ta saka, tana kuka tana cewa, “zo ki fita a gidana, shegiyar karuwa. Saukar marin da taji ne ya sata sakin Jennifer cikin sauri, ta tallabe kumatunta. Ta kalli Abbas, wanda yake cewa, kinsan dawa kk son yin fada? In baki sani ba, to tsaya in sanar dake. Sunanta Jennifer kuma itace ta musamman dina. Ko da ace mimin da nakeso ce na aura, dole ta barni da ta musamman dina, bare ke wadda baki cikin ra’ayina! Karki sake ki sake kai wannan baqin hannun naki jikinta. Sannan ya juya gurin Jennifer, wadda ta koma gefe, ta 6ata rai matuqa, ya janyo ta jikinsa. Kar ki damu da wannan ‘yar wahalar kinji ko? Banida lokacinta. Na’ima tace, cikin kukan takaici, Akan wannan zaka mareni? Yace kadan na miki na gargadi. In kin sake kuma, zaki bada bayani. Sannan ki fita anan, in mun gama, mun fita kina iya shigowa kiyi abinda zakiyi, haka Na’ima ta fita, ta koma daki, cikin nadamar auren Abbas. Bakin gado ta zauna, tare da daukar waya ta soma kiran layin momi, tare da fadin cewa, ko momy bata zo ta tafi dani ba, yau na gama Rayuwar gidannan. Momy tana dagawa, kafin Na’ima tayi magana, ta katse ta da cewa “ga daddyn ku kiyi masa sannu da jiki, kafin mu gaisa sbd Jikinsa yayi zafi yau. Na’ima ta fahimci tayi hakane sbd ta sanar da ita tana tare da daddy. Sbd batason daddy yaji wannan matsalar. Muryar daddyn ce ta katseta da cewa, “Na’imatu. Tace, Na’am daddy ina kwana? Yace lafiya lau Na’imatu, yaya kuke da maigidan naki? Tace, lfy daddy yaya jikinka? To da sauqi kenan za’ace tunda ina gd. Amma sugar din yaqi sauka sam. Tace to Allah ya sauwaqe daddy, sai nazo duba ka. Yace a’a Na’imatu karki soma fitowa da wuri haka, in dai ba mijinki bane yace kuzo tare. Tace to daddy, Allah ya qara maka lfy. Yace Ameen. ga Momyn taku. Ta amshi wayar, sannan ta nufi fita. Alhajin yace, kizo ki bani maganin. Tace to Alhaji ina zuwa. Alhaji bashir ya kwanta shiru, yana tunanin yadda sukayi da likitansa daya fita ynxun. Bayan likitan ya auna shi ne yace, “Alhaji meyasa sugar dinka bata sauka? Alhaji yace kuma ina qoqari gurin shan magani da kuma kiyaye duk abinda aka hanani. Doctor yace, to kuwa kana tare da wata damuwa. Saboda shima sugar haka yake, kamar hawan jini 6acin rai yana tayar dashi. Alhaji yace, ni bana tare da 6acin ran komai likita. Likitan yace, to ynxu zanyi maka allurar da zata saukar da sugar din inqha Allah. Sannan kasha wannan maganin. Ya dago daya daga cikin magungunan ya nuna masa. Sannan yace, Allah ya qara sauqi. Kuma yana da kyau kadan qara samun varci. Momy Nafisa ce ta katse masa tunani da cewa, “Alhaji ga ruwan kasha maganin. Ta dauki kwalin maganin ta bude masa tare da cewa, likita fa yace, ka rage wannan tunanin. Wai tunanin me kkyi ne Alhaji? Saida ya afa sannan yace, ko na fada bakida maganinsa. Amma ni burina ynxun in dan samu sauqi inje katsina. Inason ganin sauda sosai, don tana buqatar lallashina. Na tabbata ban kyauta mata ba. Nafisa ta ta6e baki, ka 6ata mata rai, ko mimi ta 6ata mata rai? Shawarata dai a gareka Alhaji. Ka kauda kanka ga komai din lafiyar jikinka ta samu. A tunanina tunda Na’ima ta share maka Hawaye, bai dace ka tsaya tuna wata damuwa ba, wadda zata hana ciwonka sauka, “hannu ya daga mata, alamun tai shiru. Sannan yayi mata alamun cewa ta fita daga dakinsa kurum. Rigingine yayi, tare da dora qafafunsa wadanda sukeyi masa zafi tamkar ana hura musu wuta akan filon, ya kalli qafafun nasa wadanda ciwon sugar din yasa suke masa radadi, ya mai da kansa gefe, yana tuna sai zuwa yaushe kenan zai rabu da wannan ciwon? Domin kuwa damuwa agurinsa ta zama dole. Bai ta6a tunanin cewa, don ya yi wa mimi abin da yayi mata zai dameshi ba. Duk da qoqarin da yakeyi na tanqwasa kansa don fada da zuciyar sa. Mimi ce dai, har ynxun sonta a zuciyar sa bai canza ba. Harma wani sashen na zuciyar sa yana fada masa cewa, bai yi wa ‘yar tashi adalci ba, domin yasan har ynxun mahaifiyar ta kawai yake yiwa tsantsar SO. Sai yaji tamkar ya daga waya ya kirata, ko kuma ya tashi yaje gurinta. Amma in ya tuna qudirinsa, sai ya fasa, ya lallashi zuciyar sa da cewa, lokaci baiyi ba da zan nemeta. A fili yace, ynxun sauda ce babbar damuwa ta. Yakama in je inyi mata bayani, yadda zata fahimci dalilina. Ya karkata kansa, ya kalli wayoyinsa dake saman durowar

Chapter 18 of 32