Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
5 / 6
gidan ganin kursum, amma sai dai yasha zama a parlour bata fitowa, idan yagaji ya tafi…. Zee kuwa basu da aiki ita da meerah sai clubbing da shaye shaye, takan yi kwana biu bata kwana gida ba, ta fita harkan yazid ko sun hadu bata kulashi, dukda sonshi na nan daram azuciyar ta, har dakin kursum take shiga tayi ta janta da hira kaman gaske. Baba Shehu na nan da kudirin sa, burinsa ya kawar da Sumy,amma ya rasa yazeyi. Gimbiya hafsatu ko yaushe tana main house abaje a parlour bata da aiki sai tsegumi, kowa haushin ta yake ji agidan, tunda taga Baba Shehu take shishige mai, ita adole tasamu mijin aure, shi ko kallon bata ishe shi ba….. Bayan sati biyu Umma ce taxo gidan tayi knocking kofa, gimbiya dake kallon TV taja tsaki ta tashi taje budewa, ta bude suka gaisa da umma, umma tace amma ke bakuwa ce koh? gimbiya ta Kare mata kallo tace wata sabon gani hajiya maryam ai bazan taba mantawa da fuskan kiba, umma ta kwalalo ido waje tace ina kika sannni nikam bansan kiba……gimbiya ta kece da dariya tace Ai dole kimanta ni, 18 years ago kika kawo min kursum tana jaririya kokin mata ne? Umma ta bata rai tace banganeki bane, me kikeyi a gidan nan ? Tace zama nazoyi mana Ai Sumy daliba tace, umma tace toh yanxu babu komai tsakani na dake, tunda kursum ta rasu, karki kara gani na kice kin sanni, gimbiya tace haba hajiya miya yayi zafi haka, ki bari muyi zumunci mana,” tayi banza da ita ta wuce sama dakin hajiya. Gimbiya tace lailai matan nan,aiko saina juyo xancen da zakuyi, sadaf taje bakin kofan dakin ta kasa kunne… Hajiya tace ashe zaki zo, na dauka kokin mata dani, umma tayi dariya tace yanxu ma agurguje nazo Alhaji na gari Shiyasa kika jini shuru ,ya karfin jiki ? Hajia tace da sauki sosai, Ina son dinki kwana biu baizo ba…….umma tace indai yazid ne anjima kina iya ganin shi, ta duba agogo, nizan wuce office sai munyi waya,”tayi sallama da hajiya ta fice. Gimbiya dake labe ta bar wajan da sauri, aranta tace oh kakkyawan yaron nan dake zuwa wajan kursum ashe danta ne, ta kwalalo ido waje, idan umma ce uwarsa kenan yazid da kursum are siblings basu sani ba, ta koma bakin kofan ta tura ahankali tashi ga dakin, hajiya na zaune kan gado tana kallan pictures din daddy tana sharar kwalla, bata ankara ba sai ganin gimbiya tayi gabanta, arazane tace miya shigo dake nan, gimbiya data cika da mamaki tace keda kike makauniya hw cms kike kallon picxx, hajiya duk ta kideme,da sauri tadau glass dinta ta maida, munafuka fice min daki kafin insa ayi waje dake, “tayi shewa tace ai ina fita xan tara kowa a parlour ingaya masu Karya kike 4 d past 18yrs, kina gani kuru kuru,” afusace hajiya tace Fadi price din da kikeso in baki kiyi shuru da bakinki, gimbiya tace banason kudi idan kikamin abu biyu toh ur secret is safe wit me, tace mai kikeso ? Na farko inaso indawo main house da xama nagaji da zama part din masu aiki, na biyu kisa Shehu ya aure ni, ” hajiya taja tsaki, na yadda dana farkon, amma na biyu I don’t tink zai yuyu, bazan ma kanina auran dole ba,balle ke yar bariki wace tayi aure wajan shida ta kasa zama, gimbiya data gama kulewa tace toh naji ,xan baki time kisan yadda kikai ya aure ni, ta fice afusace kalaman hajiya sun bata haushi. Agajiye ta dawo daga office tayi sallan magrib ta fada gado, ta dauki wayanta taga 10 missed calls da sauri ta tashi zaune ganin number inna sadiya, ta buga ringing daya Inna ta dauka, jin kukan hanifa yasa kursum ta gigice, tace Inna miya sameta ? Kukan mi take? Inna tace wlh zazzabi ke damunta tun jiya munje asibiti amma ba sauki har yanxu shiyasa ma nake kiranki,” hankali tashe kursum tace inna dare yayi balle inzo, Ki cigaba da lallashin ta, gobe da sassafe zanzo in dauke ta, Inna tace toh sai kinzo, sukayi sallama. Tunani take yadda zata dawo da hanifa gidan, bata da wani mafita ,da sauri ta tashi ta sauka kasa, suna kan dinning suna cin abinci ,zee sai wani bata rai take ganin gimbiya zaune dasu tana wurga loma, ta kalli baba Shehu tace waimi matar nan keyi anan ? Hajiya tayi caraf tace ke bana son rashin kunya, kici abinci……..kursum ta karaso ta zauna tace baba xan tafi bauchi gobe, ya kalleta lafiya dai ko ? Tace eh, inaso kasamo mun driver dazai kaini kasan ban kware sosai ba, “zee tace sister y not inkai ki, baba Shehu ya watsa mata harara, bazaki kaita ba, ya kalleta kursum yace karki damu zan shirya miki driver dazai kaiki gobe wajan 8am, tace toh nagode baba, hajiya ni xanyi tafiya gobe xanma doctor malik magana ya turo nurse dazata na baki maganin ki, ” hajiya taja ta tsaki tace shekara zakiyi kenan ? tace a’a agoben xan dawo xanyi dare dai, tace to asauka kalau ta mike ta wuce Daki, Baba shehu ma ya tashi ya fishi, zee data gama kulewa tayi wurgi da glass cup din dake hannuta ta fice daga gidan…..gimbiya ta kalli kursum, amma zainab dinnan is crazy koh ? yauwa mi zaikai ki bauchi? kursum tace hmm hanifa xan dauko bata da lafiya,” gimbiya tace tashin hankali idan kika dauko ta mi zaki cewa masu gidan, yarki zakice ko wa? Tayi banza da ita ta tashi ta wuce…. Wajan karfe dayan dare, tana parlour tana kallon TV, taji motsi kaman ana saukowa kasa, da sauri ta kashe wutan ta labe bayan kujera, taji yana waya “yace bala kajira ni bakin gate gani nan zuwa ya fice waje, gimbiya dake labe tace shehu wazai gani a darannan, sadaf ta bishi ahankali har waje, baba shehu yace bala nasan zaka iya aikin shiyasa na samoka, gobe karfe 8am zakazo ka kaita bauchi, bala yace angama duk yadda kace haka zaai, “yace yauwa ashe ka gane, kasheta zakayi idan kunyi nisa ka jefar da gawar ta yadda babu Wanda zai gani, sannan kai kuma ka bace kabar gari, ya fiddo makudan kudi Ya damka mai, bala ya karba yace angama, sai nazo goben, sukayi sallama ya koma ciki da sauri. Gimbiya dake labe tana jinsu saida ta girgiza, mamaki kawai take kowa da hidden agenda dinshi a gidan, hajiya mai karyan maganta, zee d crazy gal, ga umma da yar’ta amma bata saniba, shehu da nashi makircin, kursum dake using identity din dead Sumy, ta tabbata yazid yana da nashi unknw secret din, Wat a mysterious family. Tayi kwafa ta koma ciki, tunani kawai take yadda zatayi saving kursum in 7hours, cox idan ta bari aka kasheta barin gidan nan yakamata dole. *Xarah Bukar* *Dedicated to Bady social* ~luv u all~ [08/09 12:20 am] Xarah bukar : KURSUM by ~ Xarah Bukar Page Tun 7am ta shirya tama hajiya sallama “ta fito haraban gidan jiran driver. “Gimbiya sai kai komo take a daki tun bayan sallan asubah, ta leka waje ta hango kursum tsaye bakin mota tana jiran bala,” can dabara ta fado mata, da sauri ta fice ta shiga dakin baba shehu ahankali, da alama yana toilet, sadaf ta karasa bakin gadon ta dau wayarshi ta ta binciko contact din bala driver,” ta tura mai msg “` “change of plans kazo by 10am”“` tana turawa tayi deleting ta kashe wayan ta ajiye ta fice da sauri, ta sauke ajiyan zuciya, atleast zata samu tym din samu mafita. “Yana fitowa ya shirya da sauri yadau wayoyin sa ya fice, ” kursum dake tsaya ta karaso ta gaida shi, baba kasan 8am zan wuce, gashi 7.45 har yanxu baizo ba, “yace karki damu bala baya wasa da aikin sa zaizo Yanxun nan, ” toh baba Allah yasa karya bata min tym, sukayi sallama baba shehu ya wuce office, aranshi sai murna yake , yarinya zaman ki yazo karshe a duniya. “Sai leke take ta window ta rasa mafita, ta sauko sum sum ta karasa wajan kursum dake tsaye rai abace, “tace anya bazaki hakura da tafiyan ba naga har 9 yayi driver bai iso ba, ” kursum ta kalleta tace haba gimbiya kinsan hanifa amana tace dole in dauko ta, gashi layin baba shehu off bansan yadda xanyi ba, “gimbiya tayi shuru tama rasa me zatace, fatan ta kawai kar bala yazo dan 30mins ya rage goma ta cika… “Hankali kwance yake driving har ya iso gidan, ya kudiri niyya yau saiya ganta koda zata makale adaki, kusan 3weeks kenan yana bibiyanta…. Suna tsaye yashigo, dukta daburce ganin shi, zata koma ciki da gudu gimbiya ta riketa tsam, Ai babu guduwa da zakiyi in har kinason ganin hanif dole ki rokeshi ya kaiki, kursum ta bata rai banason haka, bakisan banaso in hadu dashi ba, gimbiya tayi shewa, tace ahab ai nasan kina sonshi kina kaiwa kasuwa, taja ta har wajan shi ta bude motan ta turata ciki, ” yazid dake kokarin fitowa daga motan saida ya tsorata,Sam bai lura dasu ba sai ganin gimbiya yayi ta turo ta…. “ya tamke fuska, miya haka ? zaki ji mata ciwo ne ? Ta washe baki tace ai nasan wajan ta kazo, sai ka kaita Inda zata, ta kalli kursum da tayi kicin kicin fuska a murtuke, sai ki gayamai inda zaki ta rufe motan ta koma ciki…… “Yaja mota suka kama hanya, ya kalle ta yayi murmushi, my witch ina zan kaiki ? Kaman tayi banza dashi, sai kuma tace ” bauchi zaka kaini… “Ya kalleta, hop all is well. tayi banza dashi Ya cigaba da sharara gudu, can yace miya sa kike guduna ? “Banason ganin ka ne” Ya murmusa yace Y “i hate yhu” Kinsan I hate lies, nasan u Luv me” I dunno y kike cewa u hate me, gashi ni am deeply inluv wit u kina bani tough time….. “Tace hmmm I don’t biliv, infact I don’t trust yhu. Am serious, u can trust me yace mata. Tayi murmushi, last tym da muka hadu baka karasa min labarin yarinyar nan da kuka hadu a bauchi ba, kace ka manta sunanta, kasan inda take yanxu ??? ” ya sauke ajiyan zuciya, matata CE just 4 a nyt, na aureta da kwana daya nasake ta, wat tace “kana nufin u wia once married n divorced ?? ” eh, dat was d biggest mistake da nayi arayuwata, koda na saketa na tafi nakara komawa in dawo da ita, amma it waz 2 late aka cemin ta sake aure tabar nigeria.. Kursum dake sharar kwalla a boye, aranta tana mamaki waya cemai Sumy ta sake aure, ta nisa tace eyya iyayen ta suka gayama ta sake aure kenan ? “Yace a’a, bata da kowa agarin ma, wani jamilu dana tura naiman aurenta a makarantar su shina turo ya bincikomin ita, koda yaje director din tace mai ai tayi aure bata kasar…. ” ya kalli kursum dake zubda hawaye, ya ciro hankie dinshi ya mika ta, kukan mi kike, “ta karba tace it a pity, umma tasan da faruwar haka ? Yace e tasani na gayama ta komai, tare ma muka so zuwa naiman yarinyar, amma she was so busy, ” I hop duk inda take yanxu zata yafemun. “tace am sure ta yafemaka. Kinsan tane, hw are u sure she has 4given me ? ” nayi guessing ne kawai tace mai….aranta mamakin hali gimbiya take, wato ita tayi karyan cewa sumy tayi aure tabar kasar, wat a cruel woman, aiko tana komawa zata fadi gaskia, inyaso daga ita har gimbayan sabar gidan. “Ta dau wayanta ta kira inna, suka gaisa, ya jikin hanifa ” Inna tace da sauki sosai yanxu bacci ma take, inna nima Ina hanya, tace toh kursum Allah ya kawoki lapia, sai kinzo, sukayi sallama. “Ya kalleta yace wace ce Hanifa ???? Ta fuske tace ya’ta CE, Wat yaja birki da karfi, kina da aure dama ? tace banda shi asali ma ban taba yiba, amma inada Ya’ yar shekara daya, dauko ta xanyi bata da lapia, ” yayi shuru bai ce komai ba, yasan dai she is decent ,hw cms take da Ya’ ba aure, Afusace ya tada mota ya dunga sharara gudu kaman xai tashi sama, ni phatee mai dauko rahoto saida na tsorata, wanga sheka gudu kaman ba gobe:oops::oops: Tana baje a parlour (as usual) tana taunar cingam kaman wata yar gidan mangwaro, zee dake kan dinning tana cin abinci ta ja tsaki tace tsohuwar banza haka zaki kare munafuka, “gimbiya ta nuna ta da yatse, ni kike zagi ? Zee tace kwarai kuwa mayya, ta tashi afusace ta kama zee tana duka, ihu take bazan kara ba ki kyaleni, ba mafita ta dankara mata cizo ba shiri gimbiya ta sake ta, da gudu tabar wajen. ” gimbiya tayi kwafa, shegian yarinya nakusa zama uwarki, ubanki ya shigo hannu na dole ya aureni ko yanaso ko baya so *Xarah Bukar* *Dedicated to Bady social* ~luv u all~ KURSUM by ~ Xarah bukar page Babu wanda yace uffan har suka iso garin bauchi, direct gidan inna sadiya suka zarce, “yayi parking yace karki dade cox bana nyt driving, ” baza ka shigo ku gaisa da inna ba? no need, jux hurry up ki fito mu wuce, xan shiga masallaci Toh kawai tace ta shige gidan. Inna na tsakar gida tana wanki taji sallaman ta, ta amsa tace amma dai kinyi saurin isowa “Kursum tace eh wlh inna ya kuke? lapia lau, taja ta suka shiga daki, hanifa na kwance tana Bacci, yanxu kam xaxxabin ya sauka sosai, saidai bata son cin abinci inji inna ” kursum ta nisa tace ai rashin cin abincin nata nada muna, ina isa gida zan kaita asibiti, “inna tace barin kawo maki naci da sha Kidai barshi wlh, muda muke sauri sallah kadai xanyi in wuce, inna tace irin sauri haka, bara na zubo maki ruwa a buta. “Bayan tayi sallah, sukayi sallama da inna tare da bata makudan kudi ta kula da kanta, tadau hanifa suka fice, inna sai zuba godiya ake. “tsaye yake bakin mota yana waya da umma ” son kace tana da ya’ marar lapia ? Haka dai tace min. Okay don’t bother asking her anytn, irinsu nasan situation dinsu, kuna isowa kano ka kaita asibiti, xanzo insa meku “Yace toh. Hey ka gama wayan can we go ya juyo yaganta zaune cikin mota, wen kika fito ko motsin kin ban jiba ” nayi kusan 10mins anan ai, “yayi murmushi ya shiga mota, ya kalli hanifa dake bacci jinkinta yace ur baby is cute tnx kawai tace, suka Kama hanya Baba shehu zaune a office, ya kalli agogo yasan by diz tym she is already dead, wayashi ya dauka zai kira bala driver, yay mamaki matuka gannin wayan nashi kashe, yasan dai baya kashe waya, da sauri ya kunne ya kira bala, bugu daya ya dauka ” ina fatan dai ka cika aiki? Bala yace wana aiki kuma, naje gidan around 10 wata Mata tacemin ai kace anfasa tafiyan sai gobe, nayi kokarin kiran ka layin kashe “ya tamke fuska, kaida nacema 8am maiya kawo ka 10, kuma wace tacema anfasa tafiyan? bala yace ka turomin msg inxo by 10am, ni bansan matar ba, amma daganin ta yar gari ce. Afusace ya tsinke call din ya dauki car keys dinshi yayi waje, yasan babu tantama gimbiya ce ta ruguza mai plans dinshi, amma hw cms tasan komai, lailai ko sai ya koya mata hankali. Tana zaune kan dinning ta hada varieties of abinci sai wurga loma take, ya banko kofa ya shigo, saida ta tsorata ta mike tsaya, shehu lapia ? Ko sauraron ta bai yiba, ya cafko wuyan ta ya shake, bana hanaki shiga tsabga taba ” gimbiya dake kakarin shedewa tace kashe ni zakayi kenan kaman yadda ka tura akasheta, ” ba shiri ya tsake ta ya wurga mata harara, bangane me kike nufi ba tayi shewa, shehu karka raina min yawo, ta fito da wayatan ta kunna mai zancen su da tayi recording, “yayi tsuru tsuru, toh mai zakiyi dashi? “ta kece da dariya, police station zan kai yanxu kuwa, ” haba hafsatu mi yayi zafi haka kiyi hakuri mana….ta balla mai harara, aurena ko prison sai ka zabi daya “Ya kwalalo ido waje, are u trying to blackmail me. za tayi magana hajiya ta sauko, lafiya nake jin hayaniya? gimbiya tayi caraf tace ba komai dama zancen auran mu muke da shehu, ta kalle shi koh shehu ? ” yayi banza da ita ya wuce abunshi. Ta kalli hajiya,nagama part dina sai ki san yadda zakiyi ayi auran cikin sati daya, “hajiya ta balla mata harara, matsiya ciya ai dama nasan zuwanki ba alheri bane, ” ta washe baki, karfa ki zageni kinsan nasan komai, “takaici duk ya isheta tama rasa mizata ce. Karfe takwas na dare suka iso kano, suka wuce asibiti, ” Dr aesherh dangusau ce on duty, da sauri ta tarbesu sanin tasan dazuwan su, suna zaune a office dinta ta gama duba hanifa ta kalle su, babyn ba wani serious sickness take ba, dou rashin appetite ke hana ta cin abinci, ta dau pen da paper, “ta mata prescribing paracetamol syrup na pain relieve, da Oral rehydration salt na restoring body fluid & electrolytes lost due to dehydration, idan tasha zataji dama sosai tace ” ta mika mai paper ya karba tace baby dinnan sam bata kama da mamanta, kamar ku da ita yayi yawa, “nan gaban kursum ya buga, sai yanxu ta kara tabbatar wa da kaman yayi yawa” shiko yazid ko acikin shi, dan baiga kaman komai ba. Suka fito zuwa pharmacy sukayi kicibis da umma ta shigo, “kursum tayi murmushi ta gaida ta aladabce, ta amsa da fara’arta ta amshi hanifa, ” yazid yace umma barin barku anan inje amso magani, tace OK. Taja ta suka samu guri suka zauna, ta kalle kursum tace sumy kinsan na dauke ki tamkar nina haifeki, “yazid ya gayamin komai yanxu gayamin waye uban hanifa ? tayi narai narai da ido, aranta tace danki ne ubanta……..afili tarasa mi zatace kawai ta fashe da kuka, ” jikin umma yayi sanyi matuka, kar kiyi kuka kinji, am sure kina da kamun kai, saidai ko u are a victim of rape.. “kursum tayi shuru batace komai ba illa sharar kwalla da take, “umma tace kirki damu haka Allah ya kaddara, so if u nid any1 to talk to kina iya xuwa kisame ni, kinji ? ” toh umma nagode sosai da kulawarki, aranta tace da umma ce mahaifiyar ta da nayi sa’ar uwa.” ya dawo rike da maganin, ya amshi hanifa yace muje koh suka mike zasu wuce umma taja shi gefe, my son plz karka ce xaka rabu sumy, yanxu yakamta mu taimake ta, kasan yan gidansu ba sonta suke ba, ‘karki damu umma no matter wat ina tare da ita, I will 4ever luv her till eternity. tayi murmushi, tnx my son, tayi sallama da kursum ta wuce gida. shima yaja mota suka bar asibiti. tana zaune a parlour nurse ta shigo tace hajiya lokacin shan magani yayi, “ta yatsine fuska ke nifa karki takura ni da magani, da safe ma nasha. nurse tace kiyi hakuri, aiki na in kula da lafiyar ki, idan baki sha ba abakin aiki na, zee dake kallon tv taja tsaki ta mike, kun cika min kunne da surutu, “hajiya tace baa dole saiki tafi daki kiyi kallo. “turo wan kofan ne yasata tsayawa chak, ganin su tare ga kursum rike da yarinya, ta bata rai, ku kuma da ga ina adaran nan ? ko kallanta basuyi ba suka karasa wajan hajiya suka gaida ta, “ta amsa ayatsine ganinsu da yar yarinya da bazata wuce 1year ba, aranta tace Allah kadai yasan ina suka samota, “tayi gyaran murya, ina jin motsin yara, yazid kazo da baby ne ?? “kursum tayi caraf tace eh ya’ta dama ita naje dauko wa a bauchi. Daga zee har hajiya sai da suka tsorata, lokaci guda suka ce badai shegiya bace. tayi banza dasu, yazid yace ba shegiya bace zee data gama kulewa tace kaine ubanta kenan “yace bani bane amma daga yau nazama ubanta. hajiya tace zainab kiramin gimbiya in ji daga bakinta, dan bazan yadda da shegia agidan nan ba…… Dam gaban kursum ya buga, Allah yasa kar gimbiya ta kufsa mata…. *Xarah Bukar* *Dedicated to Bady Social* ~luv u all~ kursum 59 to 63 Posted by XARAH ABUBAKAR on NOVEMBER 13, 2016 KURSUM by ~ Xarah Bukar Page Hankali kwance ta shigo palon, ganin kursum rike da hanifa yasa tasha jinin cikinta, aranta tace oooh family drama dinsu baya karewa. “hajiya lafia kika naima na ? Ta wurga mata harara, gayamin zakiyi ya akai sumy tayi ciki harta haihu bani da labari ? ” gimbiya ta kwashe da dariya, abu mai sauki ai ita zaki tambaya bani ba, “zee tayi caraf tace dama bakin ku daya, kun gama karuwanci ku tare ai dole ki rufa mata asiri, Hajiya ta daka mata tsawa, ke banson hauka anan, tunda sunki magana kawai tadau shegiar yar’ta ta maida ta inda ta dauko ta. “Yazid da takaici ya ishe shi yace babu inda xata , infact aurenta xanyi sai inga mai ce wa yar’mu shegia, ” daga kursum har zee saida suka girgiza jin kalaman sa Xee ta fashe ihu, baby akan karuwa zaka gujeni, toh wlh baka isaba, ke kuma kin gama iskanci a duniya shine zaki lake mai dan matsiyaciyar yarki tasamu uba ,”kursum data gama fusata ta nunata da yatsa, kince min karuwa nayi shuru, don’t u dare insult my daughter…. “zee ta yi kwafa tace na zaga din shegia, du your worst….tass din kakkyawa marin da taji a kuncin ta yasa ta mut lokaci daya, ” ya wurga mata harara, kara zakinta kiga abunda zan miki, marar hankali kawai, yaja hannun kursum suka hau sama. Zee dake hawaye ta kalli hajiya tace ki taimaka kar ya aureta yabar ni , “hajiya taja tsaki, indai zai aureta aina ji dadi, barinta gidan nan shine farin cikina, gimbiya tayi shewa, buki bidiri aure biyu zaai kenan, ” akule zee ta kalleta, ke kuma yar bariki wazai kwashe ki ? “tayi fari da ido, ashe baki da labari toh ubanki ne zai kwashe ni, aure nan da kwana uku, ” haushi da takaici ya hana ta magana, ta suri Jakarta ta fice daga gidan. Har dakinta ya shigo da ita, ta kwantar da hanifa, ta kifa kai kan gado tana zubda hawaye, “yana tsaye yana kallonta, tausayi da tsananin sonta yaci gaba da ratsa shi, ya yarfe hannuwa gami da durkusawa a gabanta, ” kukan nan naki na breaking heart dina, atleast say sumtim ko zanji dadi. “Ta dago idonta da ya sauya launi tana dubansa, ta kwantar da kai tace ya yazid I don’t deserve ur love saboda ni ba wace kake tunani bace, ” yayi murmushi, ai nasan u wia adopted, hajiya ba mom dinki, kar kiyi tunanin kozan ki’ke dan baki da asali, “ta kalleshi da mamaki, aranta tace nikam ba haka nake nufi ba, inason gayama wace ce ni amma ina tsoron karka gujeni, ” afili ta nisa tace yaya just go I need some space, ya kalleta okay I’ll but promise me u won’t cry again, “tace yes I promise “ok gud nyt ” ya sauko yama hajiya sai da safe ya fice daga gidan. gimbiya tayi murmushi mugunta, yanxu inta auri shehu tazama queen of d house, shiyasa baza ta gayawa kursum cewa yazid yayanta ne ba, gwanda ta aure shi tabar mata gidan….hmm( wa’iyazubillah gimbiya kiji tsoron Allah, dukda munsan basu hada jiniba bai kamata kice haka ba ). ************************ Tana bacci taji an daka mata duka, firgigit ta tashi tana murtsuka ido,”miye haka zaki dakeni? “Meerah tace nayi mamakin ganin kine, yaushe kika zo ? Zee ta gyara kwanciya, ke nifa jiya da daddare na shigo, tension yamin yawa datx y nazo ke kuma as usual bakya nan, Meerah ta kwalalo ido, galfrnd wana tension, gayamin miya Sameki, “humm ta nisa, ta fyade mata biri har wutsiya ” meerah tace anya cousin sis dinki ba jazz tama ya yazid ba, ta gama yawon duniya harda shegia gareta but still he is willing 2 marry her, “zee tace babu wani jazz, dama yana dason yara, ni yanxu bansan ya xanyi ba, ga p.D yace mu bashi nan da sati biu, ” meerah tace karki damu muna da hope ai nasan detective zai samo komai akanta, ita kuma gimbiya ki shareta naga alama matar ba mutunci. “aiko dai, ni bansan hw cms baba ya yadda da aurenta ba, koda yake datz his problem not mine. Abba yayi doguwa ajiyar zuciya ya kalli umma yace narasa miyasa kike son yazid ya aure yarinyan nan alhalin kuma har ciki shege tayi, ” ta bata rai, haba alhaji karka ce haka, kowa arayuwa yana da nasa laifin dan ya aureta aiba haram bane, “ya nisa yace toh shi kenan xanje wajan shehu naima mai auranta, amma kisani duk abunda ya faru nan gaba babu ruwana, ” umma tayi murmushi, babu abunda zai faru sai alheri, yace toh nidai nagama magana, yadau hulansa ya fice. Tun daga wannan ranar wata irin soyayya suke gudanarwa mai cike da kauna, wani lokaci abin yakan baiwa kursum mamaki, shin dama zuciya takan iya son abunda ta tsana da fari ,domin ko taki ko taso ayanxu tasan dan zaman da tayi da yazid takamu da sonshi, dan ba karamin kula da hanifa yake ba…… Salma ce tazo gidan, suka gaisa da samira dake rike da hanifa, “samira Ina kike samu pretty gal ? ” tayi dariya tace ai diyar Antee sumy ce, “salma data cika da mamaki tace sumy na daki ? Tace eh tana nan. ” ta shigo dakin, kursum dake zauna tana shafa mai tayi dariya, kawata yanxu nake shirin calling dinki, salma tayi yake, nima kasuwa zani shine nabiyo, yau baki je office ba, “eh kwana biu bana zuwa, dayake ya’ta bata jin dadi. Salma tace wai dagaske yar’ kice , nidai ban yadda ba, sam baku kama, ” kursum ta sauke ajiyan zuciya, ta tashi ta rufe kofan dakin da mukulli, taja hannu salma suka zauna kan gado, tace kawata yau xan gayamaki sirrin rayuwata, ta tsara mata komai tun daga ranar da mahaifiyar ta tayar da ita har izuwa yau, “ba karamin tausaya mata tai ba tace Allah yaji kan sumy, ni aganina it better ki gayawa yazid gaskia yasan cewa shine uban hanifa, ” kursum ta nisa, inason gayamai ina tsoro karya gujeni, “salma tace karki ji tsoro, ba karamin sonki yake ba am

Chapter 5 of 6