Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
Sumayya, wallahi idan kika kuma faɗar mummunar kalma a kanta sai na yi miki abin da ya fi haka." Maman Nana ta ji kamar ya watsa mata ruwan zafi, zuciya a ƙeƙashe ta ce. "Na faɗa 'yar iska karuwa don Allah ka kashe ni a wurin nan." Kamar wancan karon haka ya sake tsinke ta da mari, sai dai a wannan karon tagwayen mari Maman Nana ta samu. Wayarsa ya ɗauka, da yake dama ya yi wanka sai kawai ya shiga ɗaki ya saka kayansa ya fice daga gidan. A wurin Maman Nana ta durƙushe tana kuka kamar ranta zai fita, sai da ta yi mai isarta sannan ta sauya kaya. Ta ɗauki Abdul da yake bacci ta goya shi ta fito daga gidan, duk wanda ya ganta kallo ɗaya zai yi mata ya fahimci ba ta cikin nutsuwarta. Gidan Maimuna ta shiga ta same ta zaune a falo, Maimuna tana jin shigarta ta saki murmushin ƙeta saboda duk abin da suka yi a kan kunnenta, tunda wayar ba mutuwa ta yi ba a lokacin da ta yi wurgi da wayar Jafar. Amma a fili tana ganin Maman Nana ta dafe ƙirji ta ce, "Lafiya kuwa Maman Nana? Me ya samu fuskarki ta kumbure haka?" Da yake har lokacin da ɗacin abin a ranta, sai Maman Nana ta rushe da kuka mai cin zuciya. 'Na rantse da Allah kuka ma yanzu kika fara, mu je zuwa wai mahaukaci ya hau kura." Maimuna ta faɗa a ranta, amma a fili cikin ruɗewa ta ce. "Maman Nana ki yi magana don Allah, kin ɗaga mini hankali. Daga gida ne aka kira ki wani abu ya faru, ko Abban Nana ne?" Maman Nana ta girgiza kai, Sai Maimuna ta sauke ajiyar zuciya ta ce. "To mene ne? Don Allah ki yi mini magana, wannan kukan da gani dai ba na lafiya ba ne." "Wai yau ni Jafar ya mara saboda wata maman Asiya, Jafar ya zama wani iri wallahi asiri aka yi masa, don Jafar ɗina ba ya cikin hayyacinsa." Maman Nana ta yi maganar cikin kuka. "Innalillahi wa inna'ilahir raji'un! Kada ki ce mini tun yarinyar da muka yi magana da ke kwanaki? Ai kin ga sakacinki Maman Nana, tun wancan karon na ce ki ɗauki mataki amma kika tsaya sanya. Yanzu ai ga shi kina gani ƙarfi da yaji yarinya ƙarama ta shanye shi." Cikin ƙaguwa da neman mafita ta ce, "Yanzu mene ne abin yi Maman Asiya?" Shiru Maimuna ta yi kamar mai yin nazari, sai ta ɗago da sauri ta ce. "Gidanku sun san abin da ya faru?" Girgiza kai Maman Nana ta yi, sai Maimuna ta ce. "Yanzu abin da za ki yi kai tsaye ki wuce gida, ki sanar da iyayenki a san halin da ake ciki. Saboda wallahi matuƙar ba a ɗauki mataki ba abin ƙara gaba zai yi, kin san aka ce idan namiji ya ji daɗin dukanka ya samu wuri kenan. Kar ma ki faɗa masa za ki tafi, ki bari sai dai ya dawo kawai ya ga ba kya nan. Idan aka yi muku sulhu daga baya sai ku daidaita ki dawo, amma ina mai tabbatar miki da sai kin tashi tsaye." Shawarar Maimuna ba ƙaramin kwanciya ta yi a zuciyar Maman Nana ba, haka ta dinga ba ta shawarwari daga ƙarshe suka yi sallama ta fita. Da yake makarantar su Nana a bakin titi take, sai ta da ɗebi kayansu sannan ta wuce ta makarantar ta ɗauke su suka wuce gidansu da ke unguwa uku. Tun bayan da Maman Nana ta yi wa Maimuna sallama da ta ji fitarta daga gida, ta kira Jafar ta kwashe ƙarya da makirci ta faɗa masa. Don har cewa ta yi Maman Nana tana ta zaginsa kuma ta ce ta tafi gidansu kenan, domin ta gama zaman aure da shi. Maganar da ta fi tsaye masa a rai da Maimuna ta ce wai Maman Nana tana kuka tana cewa, ta yi dana sanin haɗa zuri'a da shi, domin shi ba miji kuma uba nagari ba ne. Da irin waɗannan miyagun huɗubar, Maimuna ta samu yin galaba a kan Jafar. Har shi ma ya hau dokin zuciya da cewar ba zai taɓa nemanta ba, kuma ba zai je biko ba tun da ba shi ya ce ta tafi ba. Ya kuma ci alwashin ko a ranar ta nemi takardar saki, a shirye yake da ya miƙa mata kayarta. A ranar tun yamma ya dawo gida saboda ya san Maman Nana ba ta nan, kuma har cikin zuciyarsa da zai samu yadda yake so kuma da babu 'yan gulma tsaf zai ce Maimuna ta zagayo su sha soyayya. Amma da yake ya san akwai matan maƙota da suke kai kawo, sai ya haƙura da buƙatarsa. Ya shiga ɗaki ya rage kayan jikinsa sannan ya jira Maimuna a waya, ya ce ta kunna data za su yi magana. Ita ma da yake ta gama girki ta kuma sheƙa wankan ƙananan kaya, sai wayar ta shi ta zo mata a daidai. Ta whatsapp ya kira ta video call, ta ɗauka a kunyace tana sunne kai ƙasa. "Wai wai wai, wannan wankan duk ni aka yi wa? A gaskiya baby za ki hargitsa ni." Sai kuma Jafar ya shagwaɓe murya ya ce, "Don Allah idan babu damuwa ki zagayo mana Moon. Wallahi babu wanda zai gane, domin a cike nake da ƙishirwarki."Maimuna ta yi shiru tana nazari, domin ita kanta wannan lokacin ta jima tana buri da fata. Tun da dare ya yi bayan ta kwantar da yaran ta yi shiru tana ƙare musu kallo, Na'ima da Fatima ne ta yi musu shimfiɗa daga ƙasan katifa. Hidaya da Humaira kuma ta yi musu shimfiɗa a kan katifa, tana nan zaune Kabir ya shiga ɗakin bakinsa ɗauke da sallama. Amsa masa ta yi ta mayar da kanta gefe, saboda haka kawai haushin Kabir take ji. Shi kansa shiru ya yi ganin yanayin kwanciyar da suka yi, sai kuma jikinsa ya yi sanyi tausayinsu ya kama shi. Kayan abincinsa ta ajiye a gabansa, ba tare da ta ce masa uffan ba. Shi kansa ya fahimci fushi take da shi, sai ya ɗan saki fuska ya ce. "Haba Fauzina yanzu wannan fuskar da kika haɗe duk saboda za ki zauna da mahaifiyata ne, zaman nan fa ba na dindindin ba ne. Don Allah ki daina ɓata ranki ba na so." Fauziya da dama ciki take da shi ta ce. "Ni ba ina fushi da zaman da zan yi tare da mahaifiyarka ba ne Abban Na'ima, domin Inna tamkar mahaifiyata haka na ɗauke ta. Kawai yanayin zaman ne bai yi mini ba, dubi a inda yaran nan suka kwanta. A gaskiya sam babu tsari wallahi, don girman Allah ka bari mu koma gidannmu idan ya so ko a hankali sai ka ƙarasa." Kabir ya ɗan yi jim ya ce, "Ummu banat kin san dai muna da maƙiya, waɗanda suke son ganin cigabanmu, wallahi ba na son na koma a ga gidana ko fulasta babu. Kin san idan aka ce shago ba naka ba ne sai haƙuri, Oga ba wata kyakkaywar sallama yake mana ba. Kin ga Allah Ya taimaki Sani da yake shi kekensa ya kai shagon, shi yake cin gashin kansa. Sai dai ɗan kuɗin da yake bayarwa duk shekara, wanda Oga yake cikawa ya biya kuɗin shago. Ni ma kin ga da ina da keken kaina rufin asirin da zan samu sai ya fi haka." Shiru Fauziya ta yi, ta kallo keken ɗinkinta da ke waje. Ta tuna ba wani ɗinki take samu ba, mafi yawa sai ɗan gyare-gyare da mata suke kawo mata. A yadda take jinta kamar kwance cikin ƙaya, babban burinta bai wuce ta ga sun tashi daga wannan gidan ba. Don haka ba ta yi dogon tunani da nazari ba ta ce. "Indai hakan zai sa ka yi ka ƙarasa mana, ga kekena nan ka ɗauka Abban Nana. Babban fatana Ubangiji ya rufa mana asiri." Tana gama magana Kabir ya rungumo ta jikinsa, sai ya shiga sakar mata kiss a duk ilahirin jikinta. Cikin wata irin murya ya ce, "I love you my Fauzee." Fauziya ta saki murmushi ta ce, "I love you too Abi." Gani ta yi Kabir yana yunƙurin wuce gona da iri, don haka ta janye shi daga jikinta ta ce, "Ga abincinka fa." Kafaɗa ya maƙale mata yana bin ta da wani irin kallo ya ce. "Idan da ke abinci da komai ba ne." Tana shirin sake yin magana Kabir ya janyo ta jikinsa, ya shiga yawo da hannuwansa a cikin jikinta. "Wallahi kunya nake ji, magana ta Allah ba zan iya wani abu a cikin ɗakin nan ba. Don gani nake kamar Inna tana jin duk abin da muke yi, tun da kaga ɗakinmu a jikin ɗakinta yake. Kuma ka dubi kusancin kwaniya da muka yi da yaran nan." Kabir ya zame hannun rigarta ƙasa, ya ɗora kanta a saman cinyarsa cikin wata irin murya ya ce. "Babu abin da za ta ji, don haka kada ma ki..." "Kabiru! Kai Kabiru ashe kana ciki?" Maganar Inna da bakaɗa labulen ɗakin da ta yi ne ya sa maganar da Kabir yake yi ta maƙale, cikin tsananin jin kunya Fauziya ta tashi tana jan rigarta sama. Inna ta saki baki haɗe da riƙe baki ta ce. "Dole na ji ku shiru a ɗaki mana, ku dai wallahi an yi jarababbun yara. Don masifa tun a farkon dare? Ko tara fa ba ta yi ba, shi ne za ki saka yaro a ɗaki ki ƙadandane kamar alkaki." Shi kansa kunya Kabir ya ji, ya ɗan sosa kai ya ce. "Amma Inna ai da kin yi sallama kafin ki shigo." "Ba zan yi ba, na ce ba zan yi shashashan banza da wofi. Ina ganin jarabar su Sadiya da duk asuba za ka ji su suna karafniya da ruwa kamar kifaye, ashe nasu shafar mai ne tun da ga ku; ku tun garin bai nausa ba. To idan ka gama shinshine-shinshinen sai ka zo ka same ni a ɗaki." Inna ta ƙarasa maganar tana sakin tsaki sannan ta wuce ɗakinta. Bayin Allah na kusa kammala free pages, masu son littafin za su biya kuɗin karatu 500 ta Acc Aisha Adam 3090957579 Firstbank sai shaidar biya ta wannan lambar 07062062624 Ummou Aslam Bint Adam🌚 07062062624 [19/02, 17:43] Ameera Adam: *NAUSHIN WUTA* ©®AMEERA ADAM *FIRST CLASS WRITER'S ASSO...* GARGAƊI: Ban amince a sarrafa mini littafi da kowacce siga, ba tare da izinina ba. Yin hakan yana iya kai wa ga matakin Hukuma, don haka a kiyaye. SADAUKARWA Tun daga farko har ƙarshe, na sadaukar da wannan littafin ga duk mahaifiyar da ta kasance uwa; ko mai burin zama uwa a nan gaba. Allah Ya saka wa iyayenmu maza da mata da gidan Aljanna Amin. SHAFI NA SHA ƊAYA GIDAN INNA Wani irin ɓacin rai ne ya lulluɓe zuciyar Fauziya, rai a ɓace ta miƙe tsaye tana ɓalle maɓallin rigarta. Shi kansa Kabir bai ji daɗi ba, cikin tausasa harshe ya ce. "Don Allah ki yi haƙuri Fauziya." Fuska babu walwala ta ce, "Babu damuwa." Ya ɗan leƙa fuskarta ya ga har lokacin babu alamar fara'a, duk sai ya ji babu baɗi. "Kin san iyaye wani abin sai ana haƙuri da su." Ya furta a sanyaye. "To ni me na ce Kabir? Ka je idan ka gama sai ka ci abincin." Fauziya ta furta bayan ta zura doguwar rigar bacci, can gefen katifa ta koma ta kwanta. Kamar Kabir zai yi mata magaba sai kuma ya fasa ya nufi ɗakin Inna. A bakin gado ya samu Inna da alama ta gama cika, ya zauna a ƙasa ya ce. "Gani Inna." "Kai ma ashe sakarai ne Kabiru ban sani ba? Don Allah kai ba ka ji kunyar kanka ba, a ce tun farkon dare ka naniƙe 'yar mutane a ɗaki? Kai Allah dai ya sawaƙe da wannan jaraba ta 'yan zamani." Shiru Kabir ya yi, sai ya ji kunya duk ta kama shi. Inna ta taɓe baki ta ce, "To dama kuɗinka na wurina nake son na ranta, idan ba amfani za ka yi da su ba. Na ji an ce barkono ya sauko a ƙauye zan saro na dinga ƙulla wa yaran nan." Da sauri Kabir ya ɗago ya ce, "A'a Inna, dama na ce ki adana mini su ne saboda ban samu ciko ba. Amma zaman da muka yi da Fauziya, yanzu ta ba ni keken ɗinkinta, idan na sayar da shi sai na haɗa kuɗin suka cike dubu ɗari. Idan ya so sai a tura su Yaya su kai kuɗin, don Allah Inna kada ki taɓa ko sisi, wallahi yayan yarinyar nan ne ya ba ni sati biyu. Idan ban tura ba zai iya aura mata wani." Inna ta wara hannu ta ce, "Ai ka ga matar rufin asiri, wallahi da Sadiya ce sisi ba za ta ba shi ba. To idan an kai kuɗin auren wai a ina za ka saka ta, ban da abin ka ai da bari ka yi ka kammala gidanka tukunna. Ka ga lokacin hidima ta yi maka sauki, don ma kai Allah Ya haɗa ƙashin arzikinka da na matarka" Tagumi Kabir ya zuba da hannuwa biyu ya ce, "Wallahi ni ma haka na so Inna, to yayanta ya matsa ne. Haka ta kira ni tana kuka wai zai aura mata wani ɗan uwansu idan ba ta fitar da miji ba." A gwasale Inna ta ce, "To dama mene ne ribar yawan zancen idan ba aure za a yi ba? Ai gara a yi wacce za a yi a wuce wurin." Kabir ya tashi daga wurin da yake zaune, ya hau kan gado gefen Inna ya riƙo hannunta, sannan ya yi ƙasa da murya ya ce. "Amma wata alfarma nake nema a wurinki Inna, don girman Allah ki cewa su Yaya kada su faɗa wa matansu. Don ina gudun kada Fauziya ta ji labari, da so samu ne ma har sai bikin ya matso tukunna." "Idan ta ji uwarka ce da za ta hana ka aure? Ko kuma ƙanwar uwarka ce ita?" Kabir ya miƙe tsaye cikin tsoron kada Fauziya ta ji ya ce, "Don Allah Inna ki yi shiru kada ta ji, kin san fa yadda aka yi wurin sayen filin gidan can da kuma ginin. Wallahi idan ta sani tana iya cewa Surayya ba za ta zauna a gidan ba, tun da haɗa su nake son yi.." "Mtsswww." Inna ta ja dogon tsaki ta cigaba da cewa, "Amma dai wallahi an yi lusarin namiji, shashasha da bai san ciwon kansa ba. Saboda ta sayar da firjinta ta ba ka ka sayi ƙofofi, sai ta hana ka yin aure? Wai me ya sa kake son zama sakarai hotiho ne Kabiru? Kai ne fa miji ba ita ba, wai dama haka ka lalace a wurin yarinyar nan ban sani ba?" Kabir ya saka hannu yana kare bakinsa alamar Inna ta yi shiru, ya sake kwantar da murya ya ce. "Ba fa kuɗin firji nake nufi ba, wannan ai na ƙarshe-ƙarshe ne da ta ba ni. Kin manta na ce miki kuɗin gadon wurin mahaifiyarta ne, ta ba ni muka haɗa da kuɗin wurina muka sayi filin, to a ginin ma akwai kuɗaɗen da ta ara mini sai daga baya ne ta ba ni na firji." Jin kalaman Kabir ya sa Inna ta taɓe baki ta ce, "To sai me? Kai dai an riga da an shanye ka wallahi." Kabir da ya lura Inna ta ɗauki zafi kuma tana iya tsula wa kwaɓarsa ruwa, sai ya shiga rarrashinta. Sannan ya nuna mata da ta gargaɗi 'yan'uwansa a kan maganar auren, har ya samu ya shawo kanta. A lokacin da ya koma ɗaki Fauziya tuni ta yi bacci saboda gajiyar aikin da ta sha, cikin sanɗa ya sake jan ƙafa ya fice daga ɗakin sai ya nufi hanyar fita. A bayan layinsu ya tsaya ya zaro wayarsa ya latsa lambar Surayya, bugu ɗaya wayar ta yi ya ji ta ɗauka muryarta da alamun bacci. "Baaabyyy." Jin yanayin muryarta ya sa jin wani irin yanayi, ya kwantar da murya yana raɓewa a jikin bango ya ce. "Baby wannan muryar tana azabtar da ni." Surry ta saki murmushin ƙeta ta ce, "Kamar yadda taka take hargitsa ni ba." "Albishirinki zumata." Cikin sauri Suryy ta ce, "Goro My." "In Shaa Allahu a satin nan su Yaya za su kawo kuɗin aurena gidanku." Farinciki kwance a saman harshenta ta ce, "Don Allah da gaske?" "Zan yi miki wasa ne?" Kamar tana gabansa ta girgiza masa kai, Kabir ya cigaba da cewa. "Ina tunanin har da rana za a saka, kafin nan da shekara guda In Shaa Allahu na gama haɗa lefe." Surry ta sake kanne murya ta ce, "Na ji daɗi sosai sadaukina, ina ƙaunarka masoyi." Shi ma Kabir ya kwantar da murya ya ce, "Na yi kewar komai naki." "Surayya da komai mallakinka ce Kbna." Wata sabuwar soyayyarta ce ta sake mamaye shi, ya gyara tsayuwarsa haɗe da sakarwa wayar kiss kamar yana tare da Surayyan. Sun jima suna musayar daɗaɗan kalamai, sai da dare yayi sosai sannan suka yi sallama Kabir ya koma gida. Yanayin da Surayya ta jefa shi a ciki ne ya sa bayan ya gama cin abinci, ya lallaɓe jikin Fauziya domin ya rage zafi. Duk da ya so a ce Surayya ce a maƙale a gefensa, amma a haka ya samu da ƙyar Fauziya ta ba shi haɗin kai. Domin gani take ko yaya suka yi motsi Inna za ta iya gane halin da suke ciki. Washegari tun da farar safiya ta fara jiyo hayaniyar Sadiya da mijinta, tun suna yin faɗan da cacar baki a cikin ɗaki har suka fito tsakar gida. Kamar Fauziya ta danne kada ta fita, sai ta ji kamar dukanta Sadiya Yaya Nura yake yi. "Wallahi ba zan taɓa yafe maka ba, Allah sai ya saka mana." "Kada ki yafe mana, ai wallahi na yi nadamar aurenki." Cikin kuka ta ji Sadiya ta ce, "Ni zan faɗi haka don wallahi na gama zama da kai har abada." Da sauri ta fita tsakar gidan tana faɗin, "Subhanallah me yake faruwa haka?" Wurin Sadiya ta ƙarasa da ke yashe a ƙasa tana kuka, a daidai lokacin Yaya Nura ya fito yana faɗin. "Ki tarkata komatsanki ki koma can baƙin garinku, na ƙarashe ragowar igiyar aurenki a kaina. Na saki, yau zan yi bacci da saleɓa." Sadiya ta fisge hannunta daga jikin Fauziya ta ce, "Sai me? Ai wallahi da wannan ƙaddararran auren na ka gara na ƙarasa rayuwata a haka." A wannan lokacin Kabir ya fito daga banɗaki ya ce, "Haba Yaya, a gaskiya abin da ka yi sam bai dace ba. Aunty Sadiya ba ta cancanci haka daga wurinka ba, ga duka ga saki abin ya yi yawa." "Ɓarauniyar za ka ce na cigaba da zama da ita? Me ake da mace ɓarauniya ana zaune ƙalau, ni wallahi da na san haka zuri'arsu take ta ɓarayi; wallahi da ban auro ta ba. Haka kawai ta zo ta gurɓata mini zuri'a da mugun hali." Inna da tun farko take ɗaki tana sauraronsu, sai a lokacin ta leƙo ta ce. "Ai wallahi ya yi mini daidai, saboda Allah Sadiya duk ta raina yaron nan. Miji wasa ne? Abin ya kai har da sata, yara gasu nan su uku ne Allah ya raya su." Mamaki ne ƙarara ya lulluɓe Fauziya, don son zuciyar Inna a bayyane yake ƙarara. Duk wanda ya ga Sadiya ya ga halin da take ciki ya san ba ta jin daɗin gidan aure. Cikin tsantsar tsana Sadiya ta miƙe ta isa gaban Inna zuciya tana suya ta ce, "Ai dama 'ya'yanki ba sa laifi, amma ki sani ki bar ganin 'ya'ya maza duk gare ki. In Shaa Allahu sai kin ga sakayyar son zuciyar da kika nuna mini, shi kuma yadda ya azabtar da ni da yunwa haƙƙinmu ba zai bar shi ba. Sata kuma da ake iƙirari ko gaban malamai na je hukuncin sata ba zai hau kaina ba. Saboda abinci ya hana mu, ni kuma na shiga rumbunsa na ɗiba zan girka mana shi ne ya rufe ni da duka. Allah Ya ba ni wanda ya fi ka, domin kai ba mijin aure ba ne." Yaya Nura ya saki dariyar izgilanci ya ce, "Kina fama da gajartar ne za ki samu wanda ya fi ni, ai ni ma tsautsayi ne ya taɗe ƙafafuwana har na faɗo kanki. Ki tashi ki fice mana daga gida, kuma kada ki sake ki ɗaukar mini 'ya'ya." Tuni hawaye ya wanke Fuskar Fauziya ta ce, "Sadiya wai mene ne haka kuke yi a gaban yara ne?" Ta kalli yaran Sadiya da su Na'ima da suka yi carko-carko, wasu daga cikinsu suna hawaye. "Waɗannan mutanen da kika gani ƙarshen butulaye ne, ba su san karamci da hallaci ba Fauziya. Hakan shi ya fi mini alheri In Shaa Allahu." Sadiya tana gama magana ta miƙe ta shiga ɗaki, kayan jikinta ta sauya. Ta ɗauko wata ƙatuwar jakarta ta loda kayanta a ciki, hijabinta ta saka ta fice daga gidan. Maƙota ta dinga bi tana karɓar kuɗaɗen waukau da take bi, sannan ta ƙarasa titi ta taro Mai adaidaita sahu har ƙofar gida. Kusan a inda ta bar Fauziya a nan ta koma ta same ta, suna ganinta gabaɗaya suka yi kanta cikin sanyin jiki. Ɗaki ta shiga ta jango ƙatuwar jakartata, Salim da Zainabu suka ƙarasa suka rungume ta suna kuka. "Don Allah kada ki tafi Umma." "Umma idan kika tafi Inna dukanmu za ta yi." Suka furta cikin kuka, hawayen da Fauziya take riƙewa ne ya fara zuba. Ta saka hannu ta toshe bakinta tana kuka, Sadiya ta haɗiyi yawu mai ɗaci hawaye masu zafi suka shiga tsiyaya daga idanunta. Cikin tausasa lafazi ta riƙo hannunsu ta ce, "Zan dinga zuwa ina ganinku lokaci-lokaci, Allah Ya yi muku albarka Zainabu." "A'a mu dai ki tafi da mu." Zainabu ta faɗa tana hawaye. Da sauri Yaya Nura ya ƙarasa a fusace ya fisge hannunsu yana faɗin, "Duk wanda na ƙara jin muryarsa sai na taka wuyan yaro." Fauziya ta ƙarasa cikin kuka ta ce, "Don Allah ka bari ta yi sallama da 'ya'yanta cikin salama, wannan hawayen da ka ga suna fitarwa har abada ba za su manta da shi ba." "Da ta san tana ƙaunar yaran take ƙin yin haƙurin zaman gidan ubansu." Sadiya ta dube shi cike da tsana ta ce, "Kada ki damu Fauziya, ni uwa ce na tabbata duk daren daɗewa za su nemo ni. Hakan da ya yi ba shi zai sa su kankare ni a matsayina na mahaifiyarsu ba, ba don na san halin mugun halin gidan nan ba. Da sai na damƙa miki amanar 'ya'yana, amma na san wacece ke Fauziya da kyakkyawar zuciyarki. Ina fatan Allah ya sada mu da alheri. Fauziya ta rungume Sadiya tana hawaye, a hankali ta janye jikinta tana jan jaka har ƙofar gida. Ganin haka ya sa su Salim suka saki matsanancin kuka suna ƙwala mata kira. Sadiya ba ta waigo ba sai ma hawaye da take zubarwa, jakar ta saka a cikin adaidaita sahun. Har ta zauna a ciki tana jin ihun Zainabu da take ƙwala mata kira tana ihu, sai kawai ta kifa kanta a kan cinyoyinta ta saki gunjin kuka mai cin zuciya. GIDANSU MAIMUNA Shirun da Maimuna ta yi ya

Chapter 9 of 11