sa Jafar ya ce, "Kin yi shiru My Moon."
Maimuna ta ce, "Gaskiya tsoro nake ji, kada tsautsayi ya sa Nazir ya dawo bai same ni a gida ba. Ka san akwai matsala tun da ba barina fita yake ba, ni dai ina ganin mu cigaba da yin video call hakan zai fi." Ba don ya so ba ya narke mata ya ce.
"To ya na iya baby? Amma dai gaskiya ki rage mini kayan jikinki, na fi son na ganki sosai bari ni ma ki ga."
Jafar yana gama maganar ya jingine wayar a gefe, ya zame ragowar ƙananan kayansa. Ita ma Maimuna babu kunya, ta zame rigar jikinta. Ya rage daga ita sai rigar mama, can saman gadonta ta haye sannan ta ɗauki wayar ta ce. "Baby ka gama kuwa."
Ido suka haɗa ta cikin wayar, Jafar ya ji wani irin abu ya tsarga masa. Bakinsa yana rawa saboda shauƙi ya ce, "Mooooonnn." Yanayin yadda ya kira sunanta ya sa ta sauke ajiyar zuciya tana lumshe ido, sai ta buɗe su tana ƙura wa faffaɗan ƙirjinsa mai cike da yalwataccan gashi da kallo.
'Haƙiƙa dole Maman Nana ta dinga ɓarin zancan a kanka, tabbas! Jafar ba irin ragowar sauran mazaje ba ne.'
Maimuna ta raya a ranta, tana shirin yin magana Jafar ya ce.
"Baby wai dama haka Allah ya zuba miki sura? A gaskiya Nazir ba ƙaramin dace ya yi ba."
Maimuna ta shagwaɓe murya ta ce, "Nazir ne ya yi dace ko Maman Nana? Allah Ya sani ba zan ɓoye maka ba Baby J. Wallahi za a daɗe ba a samu ingarman namiji kamarka ba."
Kalaman Maimuna suka sake kashe masa jiki, ya kwantar da murya cikin shauƙi ya ce.
"Ina ma yanzu haka a tare muke, da na shayar da ke romon soyayyar da ba ki taɓa sharɓa ba. Ina kewarki Moon, ina ƙaunarki komai ina ji a kanki Habibtee."
Maimuna ta saki murmushin jan hankali, suna cikin haka Jafar ya nemi Maimuna da ta cire rigar da ta rage mata, kamar ba za ta iya ba sai sheɗan ya sake ingiza ta. A hankali ta cire komai na jikinta, suka shiga musayar munanan kalaman batsa. Suna nuna wa junansu duka sassan jikinsu, Daga Jafar har Maimuna ba ƙaramin gigicewa suka yi da ganin surar junan ba. A haka har Jafar ya yi galaba a kanta, ta amsa masa gayyatar da ya dinga yi mata magiya. Maimuna ta amsa masa da cewar za ta shiga wurinsa washegari idan Nazir ya tafi kasuwa, tun da yaranta suna makaranta. Ya so ta shiga a ranar amma ta nuna masa yamma ta yi, yaranta za su iya dawowa daga makaranta. Daga ƙarshe suka yi sallama cike da kewar juna.
MAMAN NANA
Tun bayan da ta fita daga gida take tafe tana hawayen baƙinciki, ta biya ta makarantar su Nana ta ɗauke su suka wuce gidansu, yaran sai tambayarta suke yi ta ce musu ba ta da lafiya. Lokacin da ta je gida mahaifinta ya fita kasuwa, ta sanar wa mahafiyarta duk abin da ya faru. Ko kaɗan ba su ji daɗin abin da Jafar ya yi ba, amma ita ma sun yi mata faɗa sosai kuma suka ba ta rashin gaskiya.
Daddare bayan mahaifinta ya dawo, mahaifiyarta take sanar da shi abinda ya faru. Kiran Maman Nana ya yi, ta tunkari ɗakin gabanta yana faɗuwa.
"Amma ban taɓa sanin ba ki da hankali ba sai yau Sumayya, an faɗa miki miji wasa ne da za ki cakumi wuyansa a kan yana waya da budurwa."
Mahaifinta ya rufe ta da faɗa bayan ta zauna.
"Baba marina ya yi fa a kan na ce mata 'yar iska, kuma don wulaƙanci a ɗakina yake waya da ita."
Mahaifinta ya girgiza kai ya ce, "Idan ya yi waya a ɗakinki Sumayya, tambarin wayar ne zai fito a goshinki? Tun da kin faɗa da baki bai ji ba me ya sa ba za ki bar masa ɗakin ba? Kin san maza kowa da irin halinsa ai, wani har ya gama neman aurensa mace ba za ta sani ba. Wani kuma a gabanta zai yi komai, to yanzu da kika yi hakan me ya rage shi?"
Maman Nana ta saka kuka, Baba ta nuna ta da yatsa ya ce.
"Daga yau kada na sake jin kin aikata wannan ɗanyan aikin Summaya, idan kin ji yana wayarsa ki bar masa ɗakin ko ki kama aikin gabanki. Kuma ko da wasa kada na sake jin ki kira budurwarsa da 'yar iska, ke ba a auren aka aure ki? Namiji ai mijin mace huɗu ne, bayan ita ma yana ikon neman guda biyu ya aura."
Cikin shasshekar kuka ta ce, "Baba ba za ka gane ba, Jafar duk ya canza mini kamar ba shi ba. Yanzu fa ko abinci bai cika ci ba, ga shi gas ɗin da nake aiki ya ɗauke sai buhun gawayi ya dire mini. Da na yi masa magana har gori ya yi mini, wai su Umma ma da itace suke amfani."
"Ƙarya ya yi? Ai ba ƙarya ba ne, ko ɗazu ma da shi kika ga na yi girki ai. Yaran yanzu ba ku ajiye komai ba sai baƙin kishin tsiya."
Mahaifiyarta ta yi maganar cikin faɗa.
"Tun da har yana ciyar da ke yana tufatar da ke, duk abin da ya kawo miki matuƙar ba guba ba ne sai ki karɓa, da hannu bibbiyu ki yi godiya ki sarrafa shi. Haba Sumayyan Baba ina ganin ki kamar mai wayo ashe ba haka ba ne, don Allah ki kiyaye gaba. Shi kuma zan kira shi ya zo na yi masa faɗa don a sharuɗɗan aure babu dukan mace a ciki."
Baba ya ƙarasa maganar cikin tattausan lafazi, sai ya ciro wayarsa ya latsa lambar Jafar ya ji ta a kashe. Ya mayar da kallonsa wurin Sumayya ya ce.
"Na kira mijinki wayarsa a kashe, yanzu dai dare ya yi babu damar ki tafi. Amma idan Allah Ya kai mu gobe da safe, ki shirya yaranki ki koma ɗakinki za mu yi magana da Jafarun."
Maman Nana ta gyaɗa masa kai, Mahaifi da mahaifiyarta sun jima suna yi mata nasiha sannan ta tashi ta koma ɗaki.
In Shaa Allah gobe za mu gama free pages, masu son littafin za su biya kuɗin karatu 500 ta Acc Aisha Adam 3090957579 Firstbank sai shaidar biya ta wannan lambar 07062062624
Idan kun ba ni haɗin kai zan yi ƙoƙari na kammala shi kafin Azumi🥹 idan kuma na ga kun wankacalar da ni, sai na bari zuwa bayan Sallah idan muna da yawancin kwana.🥸
Ummou Aslam Bint Adam🌚
07062062624
[20/02, 19:45] Ameera Adam: *NAUSHIN WUTA*
©®AMEERA ADAM
*FIRST CLASS WRITER'S ASSO...*
GARGAƊI: Ban amince a sarrafa mini littafi da kowacce siga, ba tare da izinina ba. Yin hakan yana iya kai wa ga matakin Hukuma, don haka a kiyaye.
SADAUKARWA
Tun daga farko har ƙarshe, na sadaukar da wannan littafin ga duk mahaifiyar da ta kasance uwa; ko mai burin zama uwa a nan gaba. Allah Ya saka wa iyayenmu maza da mata da gidan Aljanna Amin.
SHAFI NA SHA BIYU
GIDANSU MAIMUNA
Ganin irin miyagun ɗabi'un da Maimuna ta ɓullo wa Nazir, ya sa shi tattara ta gabaɗaya ya yi watsi da ita. Dama can ba ya dawowa gida da wuri, don haka ko da ya kai dare idan ya ci abinci hakan ba ya hana shi ya sake fita. Har mamakin Maimuna yake, saboda gabaɗaya halayenta sun sauya. Maimunan da ya sani a baya ko kara ya ajiye ba ta isa ta ƙetare ba, duk da taurin zuciya irin nata sai da ta kai ta kawo ya sa ta yi laushi, ta yadda ko musu ba ta isa ta yi masa ba. Amma a yanzu Maimuna ta yi masa rainin da ko ƙannensa ba su yi masa ba, ya hana ta shiga mutane ya hana ta hulɗa da maƙota. Ya hana ta riƙe babbar waya, ya hana ta shige cikin danginta sosai. Ya hana ta cigaba da karatu duk don kada ta saba da shiga jama mata su zuga masa ita. Amma sai ga shi a rana tsaka tana shuka masa rashin mutumci son ranta, don a yanzu ba ta shakkun idan ya faɗi magana ta mayar masa. Dalilin haka ne ya sa ya tsiri zuwa majalisar gaban gidansa, da yake wasu maƙonsu suna zama shi ma ya bi sahunsu.
A ɓangaren Maimuna kuwa hakan ba ƙaramin daɗi yake yi mata ba, saboda tana jin fitarsa take yin zaraf ta ɗauko wayarta ta kunna data su fara shan soyayya ita da Jafar. Maimuna bayan whatsapp har sabon Acc na facebook ta buɗe, amma ba da sunanta na ainahi ba sai kawai ta rubuta 'Matar Mai Rabo' ta cigaba da fantamawa tana harkokin gabanta.
Zaman Nazir a majalisar kenan, ya samu maƙocinsa Adam yana nuna wa ɗayan maƙocin wani rubutu da ya ga an yi posting ya ce.
"Ni ban san me matan aure suka ɗauki aure ba, bini-bini za ka ga rubutu ace wai a bata shawara ga halin da take ciki. Don Allah dubi wannan, wai mijinta ya hana ta cigaba da karatu bayan an yi yarjejeniya a ba ta shawara."
Lawan ya saki tsaki ya ce, "Sakarcin fa, ai mata wasu a cikinsu mahaukata ne. Na tabbata a nan wasu za su zuge ta har ta kashe auren."
Haruna ya ce, "A'a ba lalle ba, ka san wasu matan suna jin nauyin tambayar 'yan'uwansu neman mafita. Sai suka zaɓi a ɓoye sunansu tun da ba wani ne zai gane su ba."
"Kai wannan fa ba magana ba ce, shi ya sa tun matata tana budurwa na ce mata ban yarda da wannan hawa soshiyal midiyar ba."
Adam ya faɗa cikin ɓacin rai. Jin haka ya sa Nazir ya yi zaraf ya ce, "Ai wallahi tun farko shi ya sa na datse duk wata alaƙa da za ta sa a hurewa iyalina kunne, ba sai ta fita ko tana hawa soshiyal midiyar kanta zai sake wayewa ba? Don lalacewa kwanaki haka na ji ana maganar wata matar aure tana soyayya da wani matashi. Shi ma kuma a onlayin ɗin suka haɗu." Haruna ya yi dariya ya ce, "Wallahi ina faɗa muku mace fa kariyar Ubangiji ce, wallahi duk kaffa-kaffarka idan mace ta so ninke ka a baibai wallahi ba za ka taɓa ganewa ba. Kai tsanani fa ba shi ne ba, ka yi ƙoƙari iya iyawarka a kan kula da iyalinka. Kada ka saki gidanka sakaka, kuma kada ka tsananta. Sauran sai ka bar wa Allah, shi zai tsare maka su."
Ya ƙarasa maganar yana miƙewa, sai sauran ma suka miƙe. Nazir ya kaɗe rigarsa ya ce.
"Ai wallahi wannan zance ne, kai dai kawai kowa ya ji da gidansa. Amma ka saki mace take walwalawa ai ka riga da ka daɓa wa kanka wuƙa, musamman ma ace ka bar ta tana aiki ko sana'a kuɗi yana juya mata. To kuwa sai abin da ka gani, don matan auren yanzu wallahi mafi yawa sun gama lalacewa."
"A'a gaskiya Alhaji Nazir, waɗannan zantukanma bai kamata mu dinga danganta su da iyalanmu ba, Allah Ya nesanta mana su da dukkan wani abin ƙi."
Adam ya furta, sannan suka yi wa junansu sallama.
Gida Nazir ya nufa sai kuma tunanin Maimuna ya faɗo masa, don haƙurinsa yana gab da ƙarewa. Tun da ta yi watsi da shi, a duk lokacin da ya neme ta sai kawo masa wani uzurin.
Maimuna tana kwance ta ji motsin shigowar Nazir, da sauri ta ɗauki wayar ta ɓoye ta koma ta kwanta. Haka kawai ya ji kamar ba bacci take yi ba, don haka ya zauna agefenta yana bubbuga hannunta.
"Maimuna! Maimuna."
A yatsine ta tashi tana faɗin, "Ya aka yi?"
Mamaita kalaman ya yi yana jin ɓacin rai, ya ɗan haɗe fuska ya ce.
"Ki tashi mu yi magana."
"Ni bacci nake yi sai da safe ma yi maganar."
A ɗan tsawace ya ce, "Ki tashi na ce, yanzu nake son mu yi maganar." A hankali ta tashi yana sakin guntun tsaki.
"Me ya sa kike ƙaurace mini, me ya sa duka kika canza kin raina niMaimu kada ki bari ki kai ni bango."
Murmushi ta saki cikin halin ko inkula ta ce, "Wane kalar ɓacin ranka ne bn sani ba Nazir? Ai sai dai ka faɗa wa wata macen idan ka sake aure."
Idanunsa suka kaɗa jawur saboda ɓacin rai, ya matso kusa da ita ya damƙi hannunta yana faɗin.
"Uban waye yake zuga ki da yake hure miki kunne har kika raina ni?"
Ido cikin ido ta kalle shi ta ce, "Sai ka fara sanar da ni wanda ya zuga ka har ka tauye ni, ka kuma dakushe burikana saboda zalinci ka ƙuntata mini ta hanyar tsauwalawa. Sannan ni kuma na sanar da kai wanda ya zuga ni."
Shiru ya yi yana kallonta kamar a ranar ya taɓa ganinta, cikin rashin damuwa ta ce.
"Idan kuma ba ka da abin magana sai na yi kwanciyata."
"Ni kike faɗa wa haka Maimuna."
Nazir ya tambaye ta a zafafe, sai kuwa ta mayar masa da martani cikin sauri kamar tana jira.
"Na faɗa maka Nazir, na fa jima ina tara ka a zuciyata. Wlalahi-wallahi daraja ɗaya kake ci a wurin, wato mahaifina. Da ace mahaifina ba ya raye, wallahi da na jima da datse alaƙar auratayyata da kai."
Tas! Ta ji ya sauke mata mari a fuska, zuciyarsa tana suya ya nuna ta da yatse.
"Duk rashin mutumcin da kike tunƙaho da shi, wallahi daidai nake na sauke miki su. Kin san wane ne ni sarai, ba zan ɗauki wannan iskancin ba." Maimuna ta dafe kumatu tana bin sa da kallon tsana, har zai fita ta ce.
"Allah Ya isa ban yafe maka ba, kuma wallahi indai ni ce ba zan taɓa komawa yadda nake a baya ba."
Nazir bai kula ta ba ya fita, kai tsaye cikin store ɗin ta ya shiga. Ya ɗauko wani ƙaramin mukulli ya rufe shi, sannan ya ɗauke ƙaramar wayar Maimuna da ke falo ya koma ɗakin.
Duk abin da yake yi tana jin sa, don ba sabon abu ba ne idan sun yi faɗa ya rife store ɗinta na kayan abinci. Sai dai kullum idan zai fita ya ɗebo mata wanda za ta dafa. Fulo ta ga ya ɗauka ya tafi falo, ta taɓe baki tana nuna ko a jikinta. Don ta sake ɓa ta masa rai sai ta furta.
"Ko a jikina, wai an tsikari kakkaura."
Ta gyara kwanciyarta, tana ayyana irin abin da za ta yi wa Nazir don ta huce takaicin marin da ya yi mata.
GIDAN INNA
Tun bayan fitar Sadiya gidan Inna ya kacame da iface-ifacen kukan yaranta, Inna ban da kyara da hantararsu ba abin da take yi. Fauziya ce ta janyo su ta rarrashe su, da ƙyar Zainabu ta ta yi shiru. Zazzaɓi ne ya rufe Fauziya, saboda duk cikin matan 'yan'uwan Kabiru Sadiya ce ta hannun damanta, suna ba wa junansu shawara musamman da ya kasance Sadiya ba ta da kowa a garin. Sai su rufe su binne ba tare da wani ya ji labari ba, domin dama Kabir da Yaya Nura sune masu ƙaramin ƙarfi. Gudun raini ne ya sa su Fauziya suka kama kansu, don haka ma ya sa matan su Yaya Tasi'u ko gidansu ba sa zuwa.
Abincin kari Fauziya ta haɗa gabaɗaya har yaran Sadiya, bayan ta gama ta zuba wa yaran. Suka fara ci, sai dai ta lura har lokacin sun gagara sakin jikinsu.
Kabir kafin ya tafi sai da ya kira Mai adaidaita sahu ya fita da keken ɗinkin Fauziya, kai tsaye shagonsu ya wuce da shi. Ya yi sa'a Ogansu yana nan, yana ganinsa ya washe baki ya ce.
"Allah Ya taimaki Oga"
Oga ya faɗaɗa fara'arsa ya ce, "Kb namu."
Janyo keken ɗinki ya fara yi har ya samu ya shigar da shi cikin shagon, sai ya ce, "Oga ya ka ga keken? Ay na faɗa maka sabo ne bai ji jiki ba."
Tasowa ya yi daga mazauninsa ya sake leƙa keken ya ce, "Gaskiya ne kuma na ga butterfly ne. A ajiye shi a gefe, zan sa a yi masa service sai ku cigaba da amfani da shi."
Kabir ya matsar da keken ciki, sai kuma ya saki murmushi ya ce.
"To Oga cittar fa?"
"Idan za ka tafi an jima ka yi mini magana, zan ba ka rabin, rabin kuɗin kuma sai zuwa nan da rana ita uku."
Ba haka Kabir ya so ba, ya so ace duka kuɗin ya samu. Amma duk da haka ya san idan ya karɓi kuɗin, za su cika a haɗa a kai gidansu Surayya.
Tun daga wannan ranar zaman Fauziya da Inna ya fara ɗaukan sabon salo, sai dai Fauziya tana bakin ƙoƙarinta don ganin wani abu bai haɗo su ba. Duk safiya idan ta yi abinci tana bakin ƙoƙarinta, don ta ga ta ba wa su Zainabu abinci ko yaya ne duk da ciyarwarsu ta koma hannun Inna kacokam.
Kwana biyu da tafiyar Sadiya, har gida Yaya Tas'u ya zo ya ƙarewa Yaya Nura faɗa a kan sakin da ya yi wa Sadiya. Don wani lokacin idan suka yi faɗa tana zuwa ta kai ƙararsa wurinsa, shi kuma sai ya je ya yi masa faɗa. Idan aka yi haka sai Sadiya ta samu sassaucin rashin mutumcinsa, bayan kwana biyu kuma ya ɗora daga inda ya tsaya.
Duk aikin da Sadiya take yi wa Inno sannu a hankali ya dinga dawowa kan Fauziya, lokaci ɗaya ta yi wani irin duhu ga rashin hutu daga wannan sai wannan. Murmurewar jegon da ta yi duk sai ta zuge, a ɓangare ɗaya ga tunanin halin da gininsu yake ciki. Saboda halayen Kabir sun dawo mata sababbi, don tana yi masa magana yake rufe ta da faɗa. Idan Inna ta jiyo sai ta ƙarasa bakin ƙofa ita ma ta cigaba da tofa albarkacin bakinta.
Babban abin da ya fi ɗaga mata hankali, bai wuce yadda ta lura da take-taken Inna tana son fara ɗora wa su Na'ima talla ba. Duk da ba ta fito ta faɗa ba, amma ta lura da yanayin shaguɓen da take yi. Hakan ne ya sa ta shiga takura wa Kabir a kan ya saka su a makaranta, amma sai dai ya ce mata ba shi da kuɗi. Kuma ta rasa wurin da yake zuwa, a kullum ya dawo gida da wuri haka zai buga wankan ƙananan kaya ko manya ya fice daga gidan. Wani lokacin ma sai ta yi bacci yake dawowa, saboda gajiya ta sa ana yin sallar Isha'i take yin bacci.
Watarana suna zaune bayan magriba yana tsaka da shiri ta ce.
"Abban Na'ima!"
"Ina jin ki."
Ya amsa mata yana saka belt ɗin wandonsa.
"Wai kasuwar ɗinkin ce yanzu ba a samu ko yaya? Zaman yaran nan babu makaranta baya zai mayar da su, don Allah ko Islamiya ce ka saka su."
Sai da ya ƙarasa komai sannan ya ce, "Islamiyyar ma ai ba kyauta ake zuwa ba, ki bari idan na samu kuɗi zan saka su. Kin san dai yadda abubuwa suke ƙara tsada."
Saboda takaici ba ta tanka masa ba, ya gama shiryawa yana fesa turare, a daidai lokacin wayarsa ta kawo haske da yake a silent take. Da sauri ya ɗauke wayar ya saka a aljihu har zai fita Fauziya ta ce, "Abban Na'ima ni fa ban gane wannan shige da ficen nan da kake yi ba. Ina za ka je ne da daren nan?"
"Haifata kika yi da za ki tsare ni da tambaya, ina ruwanki da wurin da za ni? Kin san dai yanzu na daina shaye-shaye ballanta ki kafa mini zargi."
Sai kawai ya saka kai ya fice daga ɗakin, shiru Fauziya ta yi tana nazari.
"Tabbas ruwa ba ya tsami banza, wallahi akwai abin da Abban Na'ima yake ƙullawa." Ta faɗa a sanyaye, tana jin nadamar ba shi kekenta. Saboda ta san da ko da kuɗin gyaran da take yi ne za ta iya samu ta biya musu kuɗin makaranta, a nan take tunani ya faɗo mata a kan ta fara yin wankau tun da yanzu Sadiya ba ta nan. Sai kuma ta ga sam ba za ta iya wankau ba, don wani lokacin ko wankin yaranta ta yi wuni take bayanta yana ciwo. Sai kuma dabara ta faɗo mata a kan ta fara yin kitso, da wannan shawarar ta bar wa zuciyarta a kan idan gari ya waye za ta shiga maƙota duk ta faɗa musu.
Kabir yana fita daga gidan ya ciro wayarsa ya latsa lambar Surayya yana faɗin, "Na fito fa baby."
Surayya ta akashe murya ta ce, "Tun ɗazu fa nake ciki da muradin son ganinka gwarzona."
Amsa mata ya yi sannan ya kashe wayar. Adaidaita sahu ya tara kai tsaye ya wuce unguwarsu Surry, waya ya ciro ya kira ta sannan ta fito. Kamar kullum idan za su yi zance a soron gidan suke yi, hakan ce ta sa yanzu ma ta shimfiɗa musu dadduma a soro.
Rungumo Surayya ya yi, ita kuma ta kamo bakinsa ta fara sakar masa kiss. Nan take Kabir ya fara birkice mata, ya shiga kai hannunsa cikin sassan jikinta. Jingina suka yi da bango, ita ma Surry ta fara sarrafa shi da hannunta tamkar ƙwararriyar matar aure.
"Baby na gaji fa!"
Kabir ya furta cikin wani irin yanayi.
"Kamar yau ne fa, ba yanzu saura wata goma ba. Ni fa ba don 'yan gidanmu ba, da ko ba lefe tsaf za a sha biki. Don tun lokacin da aka tsayar da rana na so a saka wata shida."
Janye kansa ya yi daga cikin ƙirjinta ya ɗago yana kai hannunsa ciki jikinta sannan ya ce, "Amma kafin lokacin me ya sa ba za ki ɗan dinga rage mini zafi ba dear?"
Surry don ta zolaye shi sai ta ce, "Ba kana da mata ba, ya kake abu kamar wanda bai taɓa aure ba."
"Mtswww."
Ta ji Kabir ya ja dogon tsaki sannan ya ce, "Ana maganar matan da suka cika cikakkun mata, kina sako mini zancan waccan abar. Don Allah ki taimaka mu dinga zuwa gidan can kina yi mini dabaru." Wani irin daɗi Surry ta ji, saboda ta jima da fahimtar matarsa ba komai ba ce a wurinsa. Ta sake maƙale shi ta ce.
"Shi kenan my love, zan yi ƙoƙari na dinga yi wa su Yaya dabarar fita, kasan tun da aka saka ranarmu yake saka mini ido sosai."
Sake haɗe bakinsu Kabir ya yi sai da suka ji alamar motsin za a fito, da sauri ya sake ta yana sauke numfashi, Surry ta wayance da cewa.
"Hasko nan mu ga ko can azurfar taka ta yi."
Wayarsa ya zaro ya fara haska mata, kamar masu neman azurfar gaske. Suna cikin haka Yaya Umar ya yi musu sallama ya fita daga gidan. Ya so sake yamutsa Surry ta nuna masa ya yi haƙuri za ta dinga zuwa can gidan, saboda tana tsoron kada yayanta ya sake dawowa ya kama su.
Cike da kewar Surry Kabir ya fito daga soron gidan, yana fitowa babu jimawa ya zaro wayarsa. Misscall ɗin Farha ya gani har sau uku, ya latsa layin nata yana karawa a kunne ya ce.
"Ina fatan sarauniya ba ta yi fushi da ni da."
"Idan