tafiya a mota, yayin da yake kara gudu .
Cikin kankanin lokaci suka isa gidan, Umar kamar yadda tun tuni ya saba ya fada cikin gidan yana sallama.
Sannan bayan Nasir ya aje mota , shima ya shigo .
Zama sukai a falon , lokaci guda kuma suna hada ido da juna .
Umar ya yi saurin kauda kai gefe, wanda yayi daidai da fitowar Mama daga dakinta.
"Auu kun dawo ke nan , Umar sannunku da zuwa."
Umar ya amsa da .
"Sannu Mama da gida."
"To bari a kawo muku abinci ai kunsha rana ."
Ta shige da nufin kawo musu
Ajiyar zuciya Yaya Nasir ya sauke me zafi, kamar me shirin fara magana , amman ya yi shiru.
"Nasir me zai hana ka dau hutu , kaje kaduna dangin Mama ai zaka huta ko."
Umar ya yi maganar kamar mejin tsoron Nasir.
"Ni yanzu babu wani hutu da zan je , anan ma ina hutawa ne ."
Lokacin Mama ta gama aje musu abincin sannan ta samu guri ta zauna.
"Mama ina Laila ne, tunda na shigo banji motsinta ba ."
Uncle ya tambaya
Mama ta kalli kofar dakin Laila kana ta ce .
"Tana can tana shiryawa , ko ka manta yau Usman zai zo ya kaita gidansu."
Da sauri Nasir ya mike tsaye, shima Umar yayi saurin mikewa.
"Lafiya kuwa, kaji min yara ."?
Mama ke nan
Umar ya yi murmurshin yake tare da komawa ya zauna.
Lokacin Laila ta shigo sanye da babban dogon hijabi ,
"Yau kika ce Usman zai zo Laila."?
Ta kalli Nasir da fad'in.
"Eh Uncle yama taho."
Ya koma ya zauna kamar wanda aka cirewa laka.
Ba tare da Laila ta dubi hakan ba ta fara cewa.
"Uncle dina dan Allah ina neman alfarma a gunka , dan Allah."
Ta karasa maganar tana durkusawa
"Tashi -tashi , hau kujera ki zauna.kin fi karfin haka lailata, ke rayuwa ta ce kuma babu abin da zaki nema ki rasa."
.
Ta mike ta zauna, Mama ta ce .
"Iko sai Allah, shakuwar Laila da Nasir."
Ba tare da Laila ta sake jiran komai ba ta ce .
"Uncle dan Allah ka dubi rayuwar Batula, ka share mata hawaye, ta nuna ka matsayin wanda zata aura, Uncle dan Allah ka aurota ta zamto matarka, tana cikin wani hali."
Idanunta cike da ruwa ta karasa maganar
Mama taja dogon numfashi, Umar kam lokaci guda ya rasa tunanin sa , domin ganin Nasir ya tsaya yayi jimmm yake tunanin irin amsar dazai bayar
Murmurshi mai cike da karfin hali Umar ya yi .
"Sannan ya ce .
"Masha Allah."
Nasir ya kalleshi
Wayar Laila ce ta fara ringin
Babu ko shakka Usman ne , hakan yasa ta mike cikin mutuwar jiki, Mama ta tashi ta nufi dakinta
Ganin Laila ta fita ne , yasa Umar fad'in.
"Dan Allah Nasir ka nutsu, kasan abin da zakana fade, ni wallahi idan ka bude baki zakai magana ba karamin tsoro nake ji ba , karkaji yadda zuciya ta ke zafi, gaskiya wannan ba Nasir din dana sani ba ne."
"Umar kanajin abin da Laila tace kuwa, Batula fa, bayan ba wanda nake son rayuwa da ita sai Laila, gaskiya lokaci yayi da ya kamata kowa ya sani."
Tsakiyar kan Umar ya sara , sakamakon jin maimaicin wannan zancen
"Shin dan Allah Nasir ina ilminka, dole ne na kaika wajen malam ya sake tabbatar maka babu aure a tsakaninku, haba Nasir."
Cikin kasa-kasa da murya ya yi maganar
Lokacin Laila da Usman suka shigo nan Usman ya gaidasu
Nasir ya mike tsaye tare da fad'in.
"Tare zamu tafi, kaima Umar idan zaka je ka taho, zan kai Laila gidan , ni banma san dalilin da yasa wani sai taje gidan ku ba ."
Ya yi tsaki ya dau mukullin motarsa ya fita .
Aiko haka aka tafi, motar Usman a gaba sannan Uncle da Laila a tasu motar
Haka suka isa gidan wannan shahararren mutum me kudi.
Tabbas Uncle sun ga karamci sosai, haka kowa na gidan suka gaisa da Laila cikin farin ciki.
Sai dai babban tashin hankalin da Alaji Sani Shanshani ya sami kanshi Laila ita ce yarinyar da ya ke ta neman ko yar gidan waye, domin tunda Allah yasa ya ganta kwanaki hankalinsa ya kasa kwanciya , tabbas son Laila yake bada wasa ba , sai dai kaf a cikin su babu wanda ya kula da irin yadda mahaifin Usman wato Alaji Sani hankalinsa ya tashi, bayan yaga Usman dansa ita ce yarinyar da yake burin aura.
Tabbas zamu ga yadda za ai da wannan MAHAUKACIN so.
A wannan tsakiyar daren Alaji Muktar ya tashi yana ta rusa kuka .
Haka har ya tashi matarshi Hajjiya ma'anatu.
"Lafiya lafiya kuwa Alaji."?
Ta masa tambayar tana share idanunta na bacci .
Cikin wannan kukan ya fara cewa.
"Tabbas Allah abin tsoro ne Ma'anatu, yanzu bani da komai sai tarin dukiya kawai, bani da farin ciki bani da sukuni , haka Allah ya yi wa Hajjiya rasuwa tana shirin ganar dani hanya me kyau, na zama butuulu abin gudu abin kyama, rayuwa ta babu wani kyau a cikinta."
Ya sake rushewa da sabon kuka
Duk sai tausayinshi ya kama Hajjiya, karon farko data fara ganin kukan sa .
Kafin ta ce dashi komai ya cigaba da cewa.
"Allah ya jikanki uwata, Allah ya jikanki Hajjiya, kullum gobe na kike son ta gyaru, gashi yanzu na girma, tsufa ya fara cimmin Hajjiya innalillahi wa inna'laihir raji un 😭."
"Tabbas lokaci ya yi da zan gyara kuskure na, ya Allah na tuba , ya Allah na tuba ."
Ya kwanta kafar Hajjiya Ma'anatu yana sake rangada kukanshi
Farkawar Fatima ke nan , ta tashi da niyyar yin sallar darenta kamar kullum yadda ta saba ,
Haske ta kunna cikin dakin tana kallon Fa'iza dake ta sharbar bacci .
Murmurshi Fatima tai tana cewa.
"Bari na yo alwaala kema tashin ki zan Fa'iza."
Ta karasa maganar yayin da kanta yayi wata sarawa
Hakan yasa ta koma bakin gadon ta zauna,tana dafa kanta ,
Ta bata wajen minti biyar sannan ta mike tsaye tare da shiga bandakinta dake cikin daki
Babu bata lokaci ta dauro alwala, sannan ta shinfida sallaya ,
Kana ta nufi bakin gado tana lissafin baza ta iya wannan sallar a tsaye ba
"Fa'iza."
Fatima ta fada da niyyar tashin Fa'iza a bacci .
Kafin ta sake bude baki ta kira sunan Fa'iza , taji muryar Fa'iza ba tare data farkaba tana cewa.
"Shi ke nan Abdallah, son ka ne kaddarata, amman kafi dacewa da Fatima, babu yadda zan yi ."
Cikin tashin hankali Fateema ta durkusa gaban Fa'iza dake bacci
Bisa idanunta ta ga hawaye jeri-jeri .
Ajiyar zuciya mai zafi Fatima ta sauke tare da fad'in.
"Abdallah kuma."🤔
To masu karatu alhamdulillah Masha Allah nan na kawo karshen free page na wannan labarin nawa mai suna MAHAUKACIN SO.
Ga masu son jin yadda kowanne sashi na wannan littafi zai kasance kofa a bude take Koda yaushe
masu bukatar cigaba da karanta wannan labarin, suna iya biyan kudinsu ta wannan hanyar 👇
7040805269 opay Fatima Abdullahi Ismail
Shaidar biya 07040805269
300 naira only 🙏
An dauko wannan littafi daga shafin https://taskarnovels.com.ng ku ziyarci shafin na https://taskarnovels.com.ng domin samun kayatattun littatafan hausa kama daga kan na yake yake dana soyayya
Marubuci ko marubuciya zasu iya turo mana da littatafansu mu dora masu a shafinmu kyauta don masoyansu su rika Downloading a online,
Sannan marubuta zasu iya turo mana da tarihin rahuwarsu da tarihin rubutunsu, dama sharhin littatafansu don masoyansu su gani kuma su karu da hakan
Domin turo mana da littafi ko tarihin rayuwar marubuci ko marubuciya sai ayi mana magana ta whatssap da wannan nambar +2348140419490
A lura dakyau - kyauta muke saka littafi a shafinmu bama amsan ko sisin marubuci, duk wanda ya amshi kudinku da sunanmu babu ruwanmu,
Alura dakyau - manazarta bama tura littafi ta private ku dena binmu private kuna neman mu tura maku littafi, duk mai bukatar littafi yaje website namu
Alura da kyau - Littatfanmu suna fitowa cikin manhajoji uku ne PDF,TXT da DOC amman munfi amfani da PDF da TXT masu amfani da wayar android ko tablet ko computer zai fi kyau ku riga dauko PDF da DOC
Masu amfani da kananan wayoyi java ko mara java TXT zakuna zaba don shine daidai wayarku
This hausa novel was uploaded and downloaded from https://taskarnovels.com.ng
You can download more hausa novels there
Also you can send us your novel to upload it in our website for your fans to download it online
It is free we do not charge for uploading novel
Also if you are an Author be it online or Non online you can send us your biography including your book summary,commentary and others via this number +2348140419490 its free we do not charge for our services
Note that - we do not charge for our services we uploaded novels and posted biography free, any person that collect your money in our name is your fault do not blame us
Note that - pls readers stop calling us and be asking us to send you a novels we are not sending novels through whatssap or private our novels is public at any day, any time you can visits our site and download it
Note that - our ebooks came as PDF,TXT or DOC format but the popular format are PDF or TXT, those with android or tablet or pc we suggest you to download PDF or DOC
those with java phone or non-java phone we recommend you to download TXT
This Novel is downloaded from https://taskarnovels.com.ng
to download more hausa novels visits our site at www.taskarnovels.com.ng
For feedback and support
Facebook : https://facebook.com/taskarnovels
Twitter : https://twitter.com/taskarnovels
Telegram : https://t.me/taskarnovels