Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
9 / 11
ta ƙara barin reception ta nufi wurin A&E ta tsaya. Tana cikin tsayuwar Dr. Ya fito. Ganin ɗazu ya ganta tare da Ammi yasa ya nufe ta. “Baby ina mamar taku?” “tana can reception” kallon ta yayi yace ta ƙura Maman su. Da sauri ammi ta biyo bayan Badi'a suka taho. Ganin irin tashin hankalin da Maman nasu ta shiga yasa Dr. Yin murmushi. “Yauwah Hajiya ke ce kika kawo wannan yarinyar ko?” “e...eeeh nice ta farka ne?” “eh ta farka ammah bata cikin hayyacin ta, so yanzu za'a sauya mata ɗaki sai a bata abinci taci” “tooh shikenan” Bayan an sauya wa Zahrah ɗaki zuwa medical ward Ammi da Badi'a suka wuce. So da yake amenity suka kai ta ya sa duk su biyun suka shiga. Lumshe idanuwan ta suke yayin da fuskar ta tayi pale, sai kamannin ta da Mamah ya ƙara bayyana. Ƙarasawa wajen ta suka yi suna ambaton sunan ta. MU HAƊU GOBE DON JIN YADDA ZATA KAYA ______________★★★_______________ Typing 📲 🏡𝙱𝙰𝙱𝙱𝙰𝙽 𝙶𝙸𝙳𝙰🏡 (𝔗𝔥𝔢 𝔟𝔦𝔤 𝔥𝔬𝔲𝔰𝔢🏠) ★TAKUN FARKO★ [Labari/Rubutawa] 🄳🄸🄰🄼🄾🄽🄳 🄻🄰🄳🅈 𝔒𝔲𝔪 ℨ𝔞𝔦𝔫𝔞𝔟🖊️ ﷽ PROLOGUE 𝕻𝕬𝕲𝕰 1️⃣6️⃣ Dedicated to Aunty fateemah (oum sa'eem) SHARE AND COMMENT PLEASE _______________★★★_________ A hankali Zahrah ke buɗe idanuwan ta yayin da suka buɗe ras sun sauƙa kan Ammi da Badi'a. Juya idon tayi don gane a wani wuri take, ganin I.V line maƙale hannun ta ga kuma ruwan da ke zuba a hankali yasa ta fahimci a asibiti take. Ammah me ya kawo ta? A hankali ta fara tuna last scene nata ta shiga duba Mamah gidan Ammi kuma bata ganta ba daga nan ta manta yadda take. Katse mata tunani Ammi tayi ta hanyar zuba cips and fried egg da ta soyo mata a plate. Kujera ta na ta zauna yayin da ta miƙawa Badi'a plate ɗin wacce fuskar ta ke ɗauke da murmushi. A hankali Ammi ta ɗago Zahrah bayan ta zaunar da ita da kyau ta amso plate ɗin hannun Badi'a ta fara feeding Zahrah, bata Musa ba ta buɗe baki ta naɗi child ɗin tas. Bayan ta kammala ci Ammi ta dama mata tea Mai kauri ta Sha, daga nan nurse da ke duty ta shigo, ganin IV fluid ɗin ya ƙare yasa ta zare mata shi kada jini ya zuba. Daga nan ta turo doctor. Dr. Yayi farin ciki sosai ganin ta ji sauƙi har ya jata da zance. Tuni ta ware kamar babu abun da ke damun ta. Da zai fita ya kira Ammi zuwa office ɗin shi, a nan ta sanar da ita abun da ke damun Zahrah “ba komai ke damun ta ba sai anxiety Wanda yayi sanadiyar faɗawar ta shock ammah abun bai yi nisa ba Alhamdulillah, sai dai yarinyar taki na buƙatar kulawa ta musamman in ba haka ba akwai matsala. So yanzu na rubuta drugs sai ku bi pharmacy ku amsa. Don Allah Hajiya a kula da ita kuma a nuna mata soyayya” Daga nan Ammi tayi mishi godia ta koma ward ɗin cike da fargaban ina Maman Zahrah ta je yau kuma, sannan menene dalilin faɗuwar Zahrah. Basu ɓata wani lokaci ba aka yi discharge nasu, bayan shawarwarin da nurse ɗin da ke duty ta Basu. A gajiye suka wuce gidan Ammi. Ɗakin Badi'ah Ammi ta raka Zahrah, ta haɗa mata ruwa mai zafi ta sata tayi wanka. Bayan ta shiga wanka ta turo Badi'a wurin ta sannan ta koma gidan ko mamah ta dawo sai dai shaaaaam kamar yadda taga ɗakin Mamah yanzu haka yake. A sukwane ta dawo gidan lokacin Zahrah tayi wankan ta ta saka light gown na Badi'a. Ita dai Zahrah baki ƙimmm bata ce komai ba tunda suka shigo gidan, ganin haka yasa Ammi ta bar ta zuwa safiya suji meh yasa ta faɗi. “daughter ki kwanta ki huta, sai da safe.” Kaɗa kai Zahrah tayi daga nan suka kwanta ita da Badi'a. Ɓangaren Ammi da Abba abun ya ɗaure musu kai. Abba tun bayan Ammi ta sanar da shi mamahn Zahrah fah Bata nan shima ya shiga halin mamaki. Daga ƙarshe suka yanke shawarar neman ta gobe bayan sun ji damuwar Zahrah ɗin. ★★★★★★★ “gaskiya ƙawata aikin boka Bulebule kamar yankan wuƙa yake” Tafawa suka yi ita da Asabe kafin Asabe tace “ke dai ki bari yanzu bani labarin abun da ke faruwa manah, shegiyar ta mutu ne” Kallon ta baba amarya tayi kafin tace “ke har kin manta boka Bulebule baya kisa ne?,” “ooooh haka fah” ta faɗa tana riƙe baki alamun ta tuna Baba amarya ta Kamo hannun Asabe ta riƙe sannan tace “ina baki labari, ban san yaushe shegiyar matar ta fita ba ammah dai zancen da nake miki an rasa ta....wataƙila yanzu kam ta riga ta kama bolar zama” Ta faɗa suna sheƙewa da dariyar shaƙiyyanci. “baki da dama ƙawa ta, toh ita ƴar tata fah?” Ɗan zare ido tayi sannan tayi fari “ohoooh Ni ban sani ba, ammah na sani babu makawa aikin boka ya yi ina jira ta dawo ta sane ni nan” Girkin da take yi ta ƙarasa ta zuba musu shi duka a tray, suna ci suna magana kamar wasu mahaukata. Bayan sun cinye suka ji gaba da hirarrakin su. Baba amarya ta dubi Asabe ta ce “ƙawa ta yaushe ya dace na ɗauko Bibalo ne daga ƙauye don yanzu kam ita ma nan zata dawo NBmu zauna mu mulki ɗiyar shegiyar tare” Dariya Asabe tayi tace “ƙwarai ya kamata ki ɗauko mana Bibalo gashi kuma ba zata fi sa'ar ƴar kishiyar taki ba” Jin kishiya yasa Baba amarya makawa Asabe harara. Da yake duk ƴan duniya ne tuni Asabe ta harbo jirgin ƙawar tata sannan tace “Kaji uwar kishi, kin zo kin samu mata da ƴa gidan su ammah ke kike kishi ba ma ita ba” “yo ai dole nayi kishi da ita, da ace irin banzayen nan ne ma tooooh, ammah baki ga matar ba ga kyau ga kamala ni wallahi bata yi min kama da ƴar talakawa daga gani ƴar babban gida ce” “ai kuwa na lura da hakan, ammah ko ma ƴar jibgegen gida ne ba babban gida ba yanzu kam ai kin wulaƙanta ta ta zama kashi” Tafawa suka yi suna dariya kafin Baba amarya tace “yanzu dai gobe ki raka ni ƙauye mu ɗauko Bibalo mudawo nan saboda ina son mu gasawa shegiyar aljanar yarinyar nan aya a hannu, ta yadda zata daina rasar kunyar da ta zama mata jiki” “Ai Ni ƴar nan tun ranar tariyar ki na ƙullace ta saboda abun da tayi ga kuma shegen kyau har ta so ta fi uwar fa” Bana amarya ta ce “hmm ke dai ki bari kawai, zamu ci uban ta ne ai” Haka suka yi ta hirar su daga ƙarshe Asabe ta koma gidan mata da yake dama can ita a can take da zama. ★★★★★★ Asuba nayi Zahrah ta tashi a hankali tayi alwala tayi sallah bayan tayi ta tayar da Badi'a ma tayi. Bayan sun yi sallah suka yi wanka saboda yau zasu koma makaranta bayan sun dawo daga Jos. Basu shirya ba sai around 6:30am suka nufi kitchen don taya Ammi aiki sai dai Ammi ta kora Zahrah kan ta huta ai bata da lafiya ita kam. Da wuri suka yi breakfast ganin akwai sauran lokaci mai ɗan yawa yasa Ammi tace “zahrah” a hankali ta ɗago da kanta ta mayar da hankalin ta kan Ammi “jiya MEH ya same ki bayan jin zo nan kika faɗi??” Bata ɓoyewa Ammi komai ba daga baccin su da tashin ta daga bacci har zuwa rasa Mamah da tayi. Rarrashin ta Ammi tayi tace mata kada ta damu Mamah za ta dawo coz Abba ya sa a nemo ta. Cike da farin ciki tayi a Ammi godiya sannan suka wuce school. Har suka dawo babu wani labari da aka samu akan Mamah, hakan ya ƙara sanya Zahrah cikin halin damuwa duk da cewa Ammi da Badi'a har da Abba na ƙoƙarin kwantar wa Zahrah hankalin ta. A haka suka wuce islamiyya bayan sun dawo ammah Mamah shiru Babu it's Babu labarin ta. ★★★★★★ Kwanaki uku kenan da ɓatan Mamah ammah shiru babu labari, duk wani radiostation da aka sanar babu wani ci GABA. Gashi har TV stations an sanar harda picture ammah babu ko tari balle wani ya ganta. Yau da safe Zahrah ta cewa Ammi zata je gida ta ɗauko wasu kayan ta. Tana fita Kai tsaye gida ta shiga, bata tsaya ko Ina ba ta ahiga ɗakin Mamah, cike da damuwa da ƙunci Zahrah ke kallon ɗakin Tana hawaye. Ɗauko wanna bag din da Mamah ta Bata a daren da zata ɓata tayi tana manna shi a ƙirjin ta. Wani sanyi take ji tamkar Mamah tayi hugging. “Allah sarki Mamah na, Ina matuƙar ƙaunar ki, Ina Kika tafi haka Kika bar ɗiyar ki ɗaya? Don Allah Mamah ki samu ki dawo kada ki bar ni Ni kadai a nan” Tsagaitawa tayi da maganar sannan ta ci gaba tamkar Mamah take gani “aah Mamah nafi so ko zan je gidan ku wurin su Hajjaty da Kika bani labari muje tare da ke tunda ke ce dolem su” Haka zahatah tayi ta surutai wasa wasa sai da ta kwashe awa guda a wurin. Motsin da ta ji ne yasa ta miƙe ta waiwayo ko zata ga mamah ammah wayam, hakan yasa ta ɗauki bag din tare da haɗa wasu kayayyakin ta ta wuce gidan Ammi. Baba AMARYA dake tsaye bakin ƙofar ɗakin ta ta Kama kunkumi sai wani jijjiga take tamkar wacce ta ke jiran abokiyar faɗa ta kawo mata dambe. Ashe tun shigar zahrah da taji motsi ta leƙo ganin shegiyar yarinyar da take jiran dawowar ta yasa ta tsaya Tana jiran ganin ko zata fito tace zata taho. ______________★★★_______________ Typing 📲 🏡𝙱𝙰𝙱𝙱𝙰𝙽 𝙶𝙸𝙳𝙰🏡 (𝔗𝔥𝔢 𝔟𝔦𝔤 𝔥𝔬𝔲𝔰𝔢🏠) ★TAKUN FARKO★ [Labari/Rubutawa] 🄳🄸🄰🄼🄾🄽🄳 🄻🄰🄳🅈 𝔒𝔲𝔪 ℨ𝔞𝔦𝔫𝔞𝔟🖊️ ﷽ PROLOGUE 𝕻𝕬𝕲𝕰 1️⃣7️⃣ Dedicated to mah sister saddeeqah. Much love dear SHARE AND COMMENT PLEASE _______________★★★_________ Fitowar Zahrah yayi daidai da matsowar Baba amarya bakin ɗakin Mamah. Babu zato babu tsammani ta fara zubowa Zahrah uban Bala'i “yanzu ke dan uban ki ina kuka gudu ke da shegiyar uwar taki...” Bata kai ga gama faɗa ba Zahrah ta kai mata duka jin ta zagi missing mamahn ta. Baba amarya ta jawo Zahrah har sai da bag ɗin da ta ɗauko ya faɗi.... “don ubanki da shegiyar uwar ki Ni nafi ƙarfin ki har Ni zaki kaiwa bugu don ubanki, toh wallahi yau sai naga wanda ya tsaya miki a gidan nan...bari kiji babu inda zaki ƙara fita don uwarki shegiyar yarinyar mai siffar mayu” Tana shirin kai mata bugu da bulalar da ta zaro daga bayan ta kwatsam Badi'a ta shigo don kiran Zahrah. Ganin Aminiyar ta hannun shegiyar babar ta yasa ta fita da sauri ta sanar da Ammi. Da sauri ammi ta biyo ta suka dawo lokacin kuwa Baba amarya ta jibgi rabon ta. Ganin mata ƴar gayu da yarinyar da ke shigo da abinci kwanaki yasa ta tsayar da dukan tana cilla Zahrah gefe wacce ta faɗi ƙasa. Kallon tuhuma Ammi ta maka mata sannan tace “meh tayi miki kika duka ta?” Daga haka ta ƙarasa ta ɗago Zahrah dake yashe. “badia riƙe ta ku koma gida” Caraf baba AMARYA tace “gidan uban wa?” “gidan da za'a kula da ita” Daga haka Ammi ta ɗauki bags ɗin Zahrah ta bi bayan su. Cike da takaici suka koma gida Ammi ta sa Zahrah ta ƙara wanka, Badi'a kuma ta wuce school. Tunda Badi'a ta fita Zahrah bata furta uffan ba don yanzu mugun shakkar Baba amarya take yi. Kafin Badi'a ta dawo zahrah ta ɓoye bag ɗin da Mamah ta bata. Bayan sun yi lunch Ammi take sanar da Abba abun da ya faru ɗazu. “lallai matar nan ba ƙaramar muguwa bace, toh menene damuwar ta da yarinyar da ba kulata ma take yi ba? “nimah abun ya ɗaure mun kai gaskiya, shiyasa nace ya kamata a samo wa Zahrah mafita tunda yanzu ba wata lafiya isasshiya gare ta ba” “worry not dear, zan san abun yi, idan ma magana zanyi wa baban nata sai ya bar min ita a nan su zauna har zuwa lokacin da za'a samu mamar tata.” Suna cikin zancen suka ji ana wani mahaukacin knocking da ake yi kamar za'a ɓalla gaye. Da Abba ya fita yana isa bakin gate ɗin bayan ya buɗe kawun Zahrah ne kamar wani mahaukaci. Ƙure shi da ido Abba yayi kafin yace “lafiya kake buga min ƙofa kamar wani mahaukaci” “yoh ai dole na haukace bayan ka sace min yarinya toh wallahi ka fito da ita ko na ƙona gida” ya faɗa a hasale yana nuna wa Abba gallon na petrol dake hannun shi. “toh ka ƙona ka gani, wallahi sai na sa an ɗaure ka har ka bar duniya a prison zaka zauna” Jin abun da Abba ya faɗa yasa Baba rusuna yace “shikenan bazan ƙona ba ammah ka bani yarinya ta na wuce” “aah babu inda Zahrah zata je a nan zata ci gaba da zama zuwa a samu mahaifiyar ta” Ba tare da Kawu ya damu da jin sai an samu mamar ta ba yace shi bai yadda ba. Wasa wasa haka suka yi ta ɓata lokaci daga ƙarshe Abba ya ce zata koma ammah da sharaɗin zai kula da ita. Kawu ya amince saboda shi yanzu damuwar shi bai wuce ta koma ba don tsoron Baba amarya yake kamar mutuwa shiyasa tana cewa ya nemo ta ya zo nan ɗin. Bayan ta sha kukan ta Ammi tayi mata nasiha daga haka ta wuce. Tunda Zahrah ta koma Baba amarya ta saka ta gaba da faɗa har da duka, daga ƙarshe yace ita zata ke yin aikin gida gabaɗaya. Tsananin shakkar ta ya hana Zahrah cewa komai. Bayan tayi girki baba AMARYA tace ai babu rabon ta a abincin. Haka daren Zahrah bata ci abinci ba. Sassafiya ta tashi saboda ta yi ayyukan da aka gindaya mata cizon bata don makara. Tana gama shara tayi wanke wanke ta ɗaura musu girki, abun da bata yi kullum Mamah ke girka musu ammah yau ita zata girkawa maƙiyar mahaifiyar ta. Sai around 7:25am Baba amarya ta fito daga ɗaki tana hammah alamun ko salla bata yi ba. Ido ta ƙurawa Zahrah dake gaban wuta tana izawa. Yayin da zuciyar ta ke ƙara saƙa mata irin izayar da zata yi wa Zahrah, ba zata taɓa bari ta ji daɗi ba wallahi. “ke don ubanki baki iya gaisuwa bane?” Zahrah da bata san da fitowar Baba amarya ba ta sunkuyar da kanta ƙasa “ina kwana” Harara ta maka mata kafin tayi tsaki “yo da ban kwana ba zaki ganni ne shegiya kawai mayya” Ita dai Zahrah baki ya mutu bata ce komai ba, sai da Baba amarya ta kewaya taga Zahrah ta gama komai yasa takaici ya cika ta cikin ranta tace “zaki ci ubanki ne, aikin zan ƙara yawan sa” Taliya leda ɗaya baba amarya ta Bata bayan ta dafa ta soya manja da yaji ammah baiwar Allahn nan ta hana Zahrah. Ba tare da ta damu ba ta shirya a gaggauce sai dai lokacin already Badi'a ta wuce, Ammi sai da ta tambaye Zahrah ko taci abinci tace A'ah. Kai kawai ta gyaɗa taje ta haɗa mata basket ɗin ta sannan ta kaita school da kan ta bayan ƙorafin da ta shigar kan makarar Zahrah. Daga nan ta wuce. Zahrah kenan, gaba ɗaya bata jin daɗin rayuwar fatan ta Allah ya ɗauke ta ta huta ita ma, ina Mamah ta gudu ta bar ta ita bata sani ba gashi yanzu ta dawo ƙarƙashin kulawar Kawu, mutumin da tafi tsana, mutumin da sanadin shi ta tsani maza with the exception of Yaya Ishaq ɗin ta da Abba. Bayan an tashi suna komawa Zahrah ta shige gida abun ta, tana shiga babu wata wata ta cire uniform tayi wanka, daga nan ta zo bakin ƙofar Baba amarya, ɗan rusunawa tayi saboda hango ta baje kan katifa da tayi. “ina wuni Baba amarya” Ai bata amsa ba ita kuwa Zahrah tayi tunanin ko bacci take yasa zata juya, bata ankara ba taji sauƙar dorinar Baba AMARYA a jikin ta. “don ubanki shegiya mayya Gara na kashe ki na huta, gidan uban wa kika tafi ɗazun” Cikin Muryar kuka da azabtuwa Zahrah tace “makaranta naje kuma ai na gama aikin safe” Ɗan dakatawa tayi tana bin Zahrah da matsiyacin kallo kafin tace “toh kafiku uban karatu, kin fi ƙarfin tambaya ta to ba zaki ƙara zuwa makarantar ba” Lafazin ta na ƙarshe yasa Zahrah ba shiri ta kamo ƙafafuwan ta tana kuka “don Allah Baba AMARYA kar kiyi min iyaka da makaranta, zanyi miki duk abun da kike so amma kada ki zama shamaki tsakanina da....” Wani banzan bugu Baba AMARYA ta kaiwa Zahrah tare da tura ta gefe, tuni ta faɗi ƙasa tana kuka, har ta wuce ɗaki ta dawo gaban Zahrah tace “shegiya mayya kuma tashi yanzu ki girka min abinci duk kin bar Ni da yunwa” Babu yadda ta iya ta tashi da ƙyar ta kaɗe ƙasar jikin ta sannan ta fara ƙoƙarin haɗa wuta. Bayan ta gama kamar da safe Baba AMARYA bata bata abincin ba, hakan yasa ta koma ta kwanta kan gadon Mamah tana kuka. “haba Mamah, MEH yasa? MEH yasa? MEH yasa zaki bar Zahrahn ki a wurin mugwagen nan?, Gashi yanzu ko makaranta an dakatar da Ni ammah wallahi ko meh zata yi sai naje” cikin zuciyar ta ta faɗi hakan daga nan ta miƙe tunawa da kayan abincin su da ba sosai suka yi amfani da shi ba coz tun da aka fara kawo abinci daga gidan Ammi Mamah ta daina girki sosai. Cikin ranta tace “Allah sarki yaya Ishaq ɗi na mai tausayi na! Kaima ka tafi kaƙi dawowa balle na ganka na faɗa maka halin Baba AMARYA da hukuncin da ta yanke game da karatu na!” Goge hawayen da ya zubo mata tayi ta wuce ta zaro ledar taliya ɗaya, a hankali ta fito ta girka ta, thank God baba AMARYA bata fito ba har ta gama ta tattare komai. Sai a lokacin ta samu ta juye abincin a cooler ta ɗiba taci da mai da yajin da ya rage musu. Wanka ta ƙara yi tayi shirin islamiyya duk da cewa lokacin ta ya wuce, ta ƙara fiye da hour guda. Still Bata tambaye Baba AMARYA ba ta kama hanyar ta ta fita. Gidan Ammi da ta shiga ta tarar Badi'a kwance babu lafiya. Bata jima ba ta miƙe ta wuce islamiyya. Bayan ta dawo gida ta wuce kai tsaye, sabon Bala'i ko kaya bata cire ba ta jiyomuryar Baba AMARYA. Bata san ita da waye ba ammah taji ana cewa “sai ta dawo zata ci ubanta, ban san ina ta tafi ba shegiya wata ƙila wurin maza ta tafi kin san ƴaƴan yanzu haka suke. Yarinya ƙarama sai kiga ta san bin maza balle wannan da jikin ta ya kai na wata ƴar shekara 18yrs.” Bata ji me ɗayar ta ce ba Baba AMARYA ta cafke “bar shegiya tunda na wulaƙanta uwar ta har ta bar gidan saura ita, shegiya mai fuskar aljanu.” Duk da cewa Zahrah ba babba bace ammah ai ta sanbata kula maza ita dai, kuma kenan Baba AMARYA ce ta kora Mamah?, Lallai kuwa zan sanar da Abba ya taimaka wajen nemo ta kuma a nema mata haƙƙin ta wurin baba AMARYA. Ganin babu inda tunanin zai kai ta yasa ta fito don ta lallaɓa ta je gidan Ammi kwatsam suka haɗa ido da Baba AMARYA ta rako baƙuwar ta. Cike da fargaba ta juya zata koma ɗaki sai dai bata kai ga ƙarara shiga ɗakin ba baƙuwar ta dakatar da ita. “ke mai siffar Mayu baki iya gaisuwa bane ko Saudatu baki koya mata ba” A sanyaye ta juyo tace “ina wuni” Ko amsa wa batayi ba suka wuce abun su, sai can Baba AMARYA ta dawo. “ke mayyatu fito” A guje Zahrah ta fito tace gani Jawo ta Baba AMARYA tayi ta ɗurma mata dundu ta ja ta....har sai da suka je wajen bulalar ta ta janyo ta rinƙa tsulawa zahrah har sai da Muryar ta ta dishe ta tsaya. Allah Sarki Zahrah abun tausayi. “tashi ki je kiyi girki kuma mai daɗi zaki yi saboda yau ƴata zata zo, daga nan kuma in kin gama akwai wanki na da zaki yi min kinji ko?” A hankali ta miƙa ta ɗaura musu girki har sai da ta gama Baba AMARYA tazo ta kwashe tas bata bar mata ba. Haka ta jibgo kayan ta Zahrah ta wanke. Sai 8:45pmta kammala komai daga nan ta shiga ɗakin mamah ta ci taliyar da ta dafa. Ɓigirewa tayi ta fara bacci babu tsammani taji an watsa mata ruwa. A gigice ta miƙe tsaya. Wata ƴarinya ce da bata girmi Zahrah ɗin ba, da wani ƙaton hancin ta da ƙananun idanuwan ta. “ke don buraubanki ki tashi ba ke babu bacci tunda na dawo” Kan Zahrah ɗaure take kallon Bibalo da ke zaro mata ido. A zuciye ta janyo ta ta fara dukan ta tana ramawa daga ƙarshe Zahrah ta naushe Bibalo a ciki. Cike da munafurci ta ƙwalla ƙara. Da gudu Baba AMARYA ta fito tana zuwa, ta hau Zahrah da duka. Bayan nan taja hannun Bibalo suka wuce, ita kuma Zahrah awurin bacci ya ɗauke ta. Bayan Baba AMARYA ta shiga ɗaki ita da Bibalo, ta busawa Bibalo huɗubar irin azabar da zasu ganawa Zahrah. ★★★★★★ Some month later, Zahrah ta azabtu iya azabtuwa wurin Baba AMARYA da Bibalo, sun mayar da ita jakar su, wanki girki duk ita ce abun takaici in tayi girkin ma ba za'a bata ta ci ba and gidan Ammi yanzu ba zuwa take yi ba, duk ranar da ta saka ƙafa ta je gidan kuwa har Baba AMARYA ta fahimta to kashin ta ya bushe,Kawunzu ba abun da yake yi sai da izinin Baba AMARYA. Ashe ba banza ba su Ammi suka cire damuwar Zahrah a ran su ba sai dai ashe aikin Bulebule ne da baba AMARYA ta kai mishi. Zahrah ta samu sauyi cikin rayuwar ta, duk hasken fata irin na Zahrah sai da ta disashe, ga kuma wata shegiyar rama da tayi, wuyan nan kamar mariƙar lema ƙasusuwa sun fito kamar wata skeleton, Abu ɗaya da bai sauyu ba jikin Zahrah shine tsantsan kyau da Ubangiji ya bata wanda wahala bata sa ya tafi ba. Ƴan abubuwa kuwa sai dai in zahrah ta samu shiga school ƙawaye su tarkata su bata Ana cikin haka kuwa school ya gagari Zahrah, da ƙyar ta kammala ss1 nata daga nan ita ma ta cire rabon ci gaba da karatu. Sannu sannu babu wuya a wurin Allah Zahrah ta kai shekaru goma sha biyar, ta fara menses sai dai babu wani mai kula da al'amarin ta, don ma bata manta wasu karatukan ta na islamiyya ba tana applying wurin tafiyar da rayuwar ta. duk irin ranar da ke jikin ta bai hana ainihin ƙirar jikin ta bayyana ba, tana da ƙirji ga kuma hips nata so Masha Allah kamar na wata babbar mace. TEAM ZAHRAH WAI KUNA INA NE JARUMAR KU TA ZAMA ASARA A HANNUN BIBALO DA BABA AMARYA? WHEN ZASU DAINA AZABTAR DA ITA? KO INA RAI MAMAH TAKE? TA MUTU KO TANA RAYE? All theses na a cikin littafin babban gida wanda yanzu ake dab da fara wasan IN ALLAH YA KAI MU GOBE ZAN CI GABA kunga kwana biyu bana post saboda baku yi comments ne, at least in ma

Chapter 9 of 11