Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
me za a hada maki na 7m Mayraah da zaki amsar masa kudade haka?" Mayraah ta marairaice tace "Wallahi nace masa yayi yawa amma yaki ji na Ammi, kuma wai banda boxes da Abaya and jewelries a kudin" Ammi dai ta kasa cewa komai, Mayraah dai sai kallonta take, can Ammi tace "To shikenan, Allah Ubangiji ya sanya alkhairi, shi kuma Allah ya kara masa budi" Mayraah ta sunkuyar da kanta, Ammi tace "Je ki canza kayanki mu je kitchen mu nema ma Abbanku abinda zai ci anjima, tun dazu nake nan nake nazarin abinda zan girka" Mayraah tace "To" Har ta mike zata wuce sama zuwa dakinta Badiyya ta fado mata, can ta juya a hankali ta kalli Ammi tace "Aunty Badiyya na sama ne?" Ammi tace "Aa wai taje amso littafinta a gidan kawarta" Mayraah dai bata ce komai ba ta wuce sama zuwa dakinta, tana bude kofar dakin ta dinga bin ko ina da kallo, ji tayi kamar tayi kuka, what is all this plss? kaya can, kaya nan, everywhere so littered with clothes kamar warce tayi sati a dakin, ta karasa ciki, within few minutes ta hada wasu abubuwanta da tasan zata bukata ta fice daga dakin ta tafi dakin yaya Maheer ta ajiyesu sannan ta cire Hijab dinta ta linke ta canza kayanta ta fita daga dakin ta dawo parlor... Sai kusan karfe shidda suka gama girkin Ammi ta fito parlor, Mayraah kuma ta hau gyara ko ina na kitchen din, Ammi na zaune parlor Maheer ya shigo gidan, bayan ya gaida Ammi ya wuce sama, Ba a wani dau lokaci ba ya dawo downstairs yana kallon Ammi yace "Ina Mimi?" Ammi tace "Tana kitchen" Ya nufi kitchen din, Mayraah na ganinsa tace "Yaya sannu da dawowa" Ya kulle kofar kitchen din yace "Me kayanki yake yi a dakina?" Mayraah ta marairaice tace "Yaya Aunty Badiyya ce ta dawo gidan nan, and she's already scattering everywhere in my room" Maheer yace "Yaushe ta zo?" Mayraah tace "Dazu" Yace "Shine kika cika min daki da kayanki? Me yasa baki kai dakin Usman ba?" Ta zaro ido tace "Kana son yayi min fling dinsu idan ya dawo?" Juyawa Maheer yayi ya fita daga kitchen din Mayraah ta ci gaba da abinda take. Ammi na zaune parlon Abba bayan ya gama cin abinci wajajen karfe tara, tana kallonsa tace "Yallabai dama nace sai ka dawo zan sanar maka, Badiyya ta dawo gidan nan da zama yanzu" Abba yace "To maa sha Allah, ai haka ake so, Allah yasa ta zauna wannan karan" Ammi tace "Ameen, sannan kuma kaga biki na ta karatowa ban ga kace a fara shirye shiryen komai ba" Abba yace "Wannan ai ba damuwa bane, a rana daya za a siya furnitures da duk wani abu da za a kai mata, so ko ana saura kwana biyu bikin ne za a iya yin wannan ko?" Ammi tace "Haka ne" Abba yace "Abinci kuma zuwa next week, za a kawo buhunhunan shinkafa da flour da su mangyada, taliya, manja da dai sauransu, duk a ajiye a store" Ammi tace "Toh Allah ya kara budi Yallabai" Yace "Ameen, akwai kudin saniya da raguna uku da na bada shekaranjiya, Usman kuma yace min zai siya lemo da ruwa da za a bukata na taro" Ammi tace "To maa sha Allah" Abba ya jawo wani envelope ya bude ya ciro wasu takardu ya mika ma Ammi ta amsa tana kallonsa tace "Na menene wannan din?" Yace "Wani Plaza aka min tallansa 2 weeks ago, to akwai wani business da nayi an samu kudi Alhamdulillah shine na yanke shawaran siyan wajen da sunan Mayraah, ki ajiye mata takardun gun yan uwansu" Ammi ta sauke idonta bata ce komai ba ta mayar da takardun cikin envelope din ta mike ta nufi Bedroom dinsa, Abba ya bi ta da kallo yace "Next one da sunanki za a siya, then Umar" murmushi kawai tayi ta shiga dakin. Wajajen karfe goma Mayraah ta shigo dakin Ya Maheer, yana zaune yana danna waya, ya bi ta da ido yace "Baki kwanta ba?" Tace "Ni fa a nan zan kwanta yaya, tayi occupy din ko ina" Yace "To ke tsoronta kike ji je da baza ki ce mata ta gyara zaki kwanta ba" Mayraah tace "Aa dama ni ba dakin zan kwana ba ai" Yace "You are disturbing me Mayraah ki tafi dakin Usman mana" Ta kallesa ta marairaice tace "To kai kaje ka kwanta mana he won't say anything, amma idan ni ce zai min masifa kai ma ka sani" Maheer bai sake ce mata komai ba ya ci gaba da danna wayarsa, ta lallaba ta kwanta karshen gadon kafin ya canza mind ya koreta, tana kwanciya babu ɓata lokaci bacci ya dauketa, Maheer ya dau wayarsa ya koma dakin Usman ya ci gaba da abinda yake, wajen karfe daya yaji yana jin yunwa, har ya kwanta yaji bazai iya jure yunwar ba ya tashi ya sauko downstairs, kunna fitilar parlon yayi ga mamakinsa ya ga Ammi zaune, ya nufeta da sauri yace "Ammi baki kwanta ba?" Ammi tayi saurin goge hawayen idonta wanda tuni Maheer ya gani, ya zauna yana facing dinta da damuwa yace "Ammi are you okay? Me yake faruwa ne" Ammi ta kirkiro murmushi tace "Sallah nayi shine na dawo nan na zauna" Yace "No, kuka fa kike Ammi" Ammi tace "Kukan rashin mahaifina da 'yar uwata sannan kanina, hakan har ya zame min jiki kai ma ka sani Maheer" Maheer ya kwantar da murya yace "Ammi addu'a kawai zaki dinga bin su da shi ba kukan nan ba, don Allah ki daina haka kar ki je wani ciwon ya shige ki" Ammi ta gyada masa kai tace "In sha Allah Maheer" Yace "Ki tashi kije ki kwanta" Tace "Kai me ka sakko yi" Yace "Abinci zan ci" Ammi tace "In ko baka daina cin abincin tsakar dare ba zaka ajiye tumbi ne" Yayi murmushi yana shafa cikinsa yace "Yau ne fa kawai Ammi, kuma kaɗan zan ci, bari ma in zubo ki ga" Daga haka ya mike ya tafi kitchen, ba a dau lokaci ba ya fito rike da plate din abinci, yana ci suna hira da Ammi a parlon, har ya gama, tare suka koma sama ganin ya nufi dakin Usman tace "Can zaka kwanta?" Yace "To tayi hijacking min dakin" yana fadin haka ya shige dakin Usman ya kulle, Ammi ta bude kofar dakin nasa a hankali ta kunna wuta tana kallonta, tana kwance tana bacci, Ammi ta karasa cikin dakin ta lulluba mata bargo a hankali sannan ta juya ta kashe wutan dakin ta fita ta tafi nata dakin. 07087865788✍🏻 WhatsApp only, no phone call ... [5/29, 6:36 PM] Khaleesat Haiydar💖: 💖💖 *MAYRAAH*💖💖 By _Khaleesat Haiydar_📚✍🏻 5...... Washegari sai kusan karfe goma Mayraah tayi realizing basu yi waya da Dr Musharraf ba tun bayan da ya dawo da ita jiya, ta karasa wanke wanken da take yi a kitchen ta fito, Sabira ce kadai parlon tana goge goge, Mayraah ta wuce sama ta shiga dakin Maheer, tun karfe takwas ya fita aiki, yana fita kuma ta gyara masa dakin ta wanke bandaki, wayarta ta dauka ta zauna gefen gado tayi dialing number Dr Musharraf, har ya katse ba ayi responding ba, da har zata sake dialing kawai kuma ta fasa, ta daga kai jin an bude kofar dakin, Ammi ce ta shigo, Ammi ta karaso tana kallonta tace "Meye da dakin naki da kika yi hijira daga can yanzu?" Mayraah ta ɗan yi murmushi tace "Aa ba komai, kawai ina son Aunty Badiyya ta zama comfortable ne shi yasa" Ammi tace "To bana son haka, kuma kar in sake ganin haka, ki tattara yanzun nan ki koma dakin ki, kar ki sake cewa zaki kwana dakin Maheer saboda Badiyya na dakinki, as far as tana gidan nan to daki daya za ku zauna" a hankali Mayraah tace "Toh" Ammi tace "In ke tayi ma haka zaki ji dadi? Saboda ita ki ki zaman dakinki kamar ba er uwarki ba, naga dai ko cacan baki bai taɓa hada ku ba balle kice, to me ya janyo wannan abu haka? In kinyi hakuri duka duka ma kwana nawa ya rage maki a dakin Mayraah" Mayraah ta sunkuyar da kanta cikin sanyin murya tace "Kiyi hakuri Ammi" Ammi tace "Ki tashi ki koma dakin ki" Daga haka ta juya ta bar dakin, Mayraah ta bi ta da kallo. A hankali Mayraah ta bude kofar dakinta ta shiga ciki da sallama, Badiyya dake shiryawa bata ko amsa sallaman nata ba balle ta kalli inda take sai ma wani tsuke fuska da tayi, Mayraah ta karasa cikin dakin ta ajiye wayarta gefen gado sannan ta shiga bandaki rike da shower gel dinta da towel, Badiyya ta bi ta da kallon gefen ido har ta kulle kofar bandakin, Badiyya ta wani taɓe baki ta ci gaba da shafa cream dinta, ko minti biyar Mayraah bata yi a bandaki ba wayarta da ta ajiye gefen gado ya fara vibrate, Badiyya ta juya tana kallon wayar, da sauri ta dauka tana kallon number jikin screen din don da Emoji aka yi saving maimakon suna, wayarta ta jawo tayi snapping screen din sannan ta mayar da wayar inda yake ta ajiye da sauri, babu bata lokaci ta haddace number sa tayi snapping ta shiga True caller don ganin number waye, Musharraf Abdallah taga ya fito, wanda sai da gabanta ya fadi ganin sunansa kadai, a sanyaye ta ajiye wayarta ta karasa shafe shafenta ta mike ta dau kayanta ta saka ta koma gefen gado ta zauna, tayi nisa cikin tunanin da take bayan kusan minti ashirin taji fitowar Mayraah daga bandaki, mikewa Badiyya tayi ta figi wayarta ta fita daga dakin, Mayraah ta bi ta da ido, ganin bata kulle mata kofar ba ta karasa ta kulle kofarta. Musharraf ya shigo parlorn Maminsa ya zauna opposite dinta yana kallonta yace "Gani Mami" Mami tace "Why ain't u picking ur brother's call?" Yana karasa buttoning din t-shirt dinsa yace "Bana kusa da wayan" Mami tace "To ka kirasa za ku yi magana" Musharraf yace "Ohk" daga haka ya mike, Mami tace "Ina kuma za ka? koma ka zauna ka kirasa yanzu, don nasan ba kiransa zaka yi ba" Musharraf ya kalleta yace "Mami sauri fa nake, ba ni nace maki zan kirasa ba" Mami tace "Musharraf" Komawa yayi ya zauna ya jinginar da kansa da kujera, Mami tace "Kira sa yanzu" Musharraf ya hade rai yace "Mami shi fa gayen nan baya taɓa kiran mutum haka kawai, i know there is definitely something annoying that he wants to say to me" Mami tace "Why don't u respect the fact that he is ur elder brother Musharraf?" Musharraf bai ce mata komai ba ya dau wayarsa yayi dialing number brother din nasa wanda ko saving dinsa ma bai yi a wayarsa ba, yana fara ring ya sa handsfree, Mami dai sai kallonsa take, sai da ya kusa katsewa aka daga from the other side, Musharraf yace "Good morning" Yayan nasa yace "Baka ganin kirana ne?" Musharraf yace "Eh yanzu naga kiran" Daga daya bangaren brothern nasa da ake kira da Daddy yace "Akwai personal discussion da nake son mu yi akan auren nan da zaka yi" Musharraf ya ɗan yi jim, sai kuma yace "Ina ji" Daddy yace "Ok, amma da farko ina son sanin ko kana da issue da Farrah ne?" Musharraf yace "Wacece haka?" Ita dai Mami kallonsa kawai take, Daddy yace "Farrah ce baka sani ba?" Musharraf yace "Oh, me yasa ka min wannan tambayar?" Daddy yace "At the first place.... Why did u decide to date somewhere else ga er uwarka that has all qualities also" Musharraf bai san sanda ya mike tsaye ba yace "Is that so? Since ni ban yi ba ai kai zaka iya yi a madadina it's still not too late, look yaya ni dama nasan there is nothing good da zaka kirani ka gaya min, and sorry to say bana son kowa ya kara sa bakinsa a lamarin aurena, not even you! Hatta su Aunty Halima babu ruwansu da matar da zan aura, i am not a kid da za ayi min zabin matar aure... Kai idan ka tashi auren sai ka auri Farrah ai ka ma fi ni saninta" Yana gama fadin haka ya katse wayar, Mami kam buda baki tayi tana kallonsa da mugun mamaki, ya juya ya fice daga parlon, Dama ita she is not in support of cewar sai ya auri cousin dinsa kamar yanda dangin ubansa suka dage, beside she is not even interested da wannan hadin da suke ta dagewa a kai, Allah kadai yasan me suka kira Daddyn suka tsara masa shine ya kirata da batun ita kuma tace ba ruwanta ya kira ɗan uwan nasa sun fi kusa, to dai ga yanda kiran ya karke a gabanta, Wayarta ne ya fara ring ta dauka ganin Daddy ke kiranta ta daga ta kai kunne, Daddy yace "Mami daga wannan moment din na cire baki a kan duk wani issue da yayi concerning Musharraf, he can go an do whatever he wish, sannan wllh bazan zo daurin auren ba ma, kudi da na kai masa gidansu yarinyar ma nayi da na sani, kawai na bata lokaci na shigo kano akan yaron da ya bi ya raina kowa...." Mami tace "Wani magana kenan kake yi Daddy, kana da kamarsa a duniya ne? Ni fa ban ga lafinsa ba, he is not a kid da za ace lallai lallai sai an zabar masa warce zai aura, kuma ai gaskiya ya fada kawai choice of words dinsa ne are wrong, a gabana ya kiraka ai, meye za su dage sai ya auri Farrah?" Daddy yace "of course nasan zaki yi supporting dinsa ne ai Mami, to sai yaje ya auri yarinyar da zai aura, amma ni kam bazan zo daurin aurensa ba tunda har ni yayi ma rashin kunya a waya" Mami ta tabe baki tace "Yana da wani ɗan uwan da ya wuceka ne da zaka ce baza ka zo daurin aurensa ba? Ni don Allah sai anjima kar ku ɓata min rai kai da shi" Daga haka ta katse wayar ta mike ta tafi wajen Musharraf, yana kokarin fitowa daga dakinsa tace "Ina za ka?" Ya ɗan kalleta yace "Zan fita ne" Mami tace "Musharraf shi yayan naka ka gaggaya ma magana babu kunya a gabana?" Musharraf yace "Mami ke baki ji maganan da yake min bane, he just love controlling me alhalin naji kunce da shekara biyu kawai ya girmeni, nasan ai bashi da girlfriend to don me bazai yi dating farrah ba su yi aure" Mami ta kamo hannunsa tace "I know they are wrong but ba haka ya kamata kayi approaching maganar da yayi maka ba, yayi deserving some respect from u, for peace kawai kamata yayi kace masa u are not interested shikenan" Musharraf yace "Mami ni fa as far as u are not against my marriage to babu wanda ya isa ya hanani abinda nake so, tun daga kan Daddy har su kawu da su Aunty Halima, nobody" Mami ta sauke ajiyar zuciya tace "Yanzu ya batun lefen jiya baka ce min komai ba" Yace "I decided to give her the money su siya kayan" Mami tace "Nawa ka bata?" Yace "7M" Mami tace "Why not make it 10m?" Yace "Zan kara mata" Mami tace "To ka dai ce mata banda Abaya da akwati ko?" Yace "Yeah" Badiyya na zaune dakin Haseenah tana goge hawayen da yaki tsaya mata cikin rawan murya tace "Haka kawai kun sa in koma gidan ni ban ga amfanin komawata ba yau kwana biyu kenan, tun da naje dama ta tattara ta koma dakin Maheer, ba wani information da nake samu banda numbersa da nayi snapping dazu da ya kirata tana bandaki, kuma kinga ai tun dazu muke kira baya shiga saboda settings dinsa da ya saka idan baya da numberka bazaka samesa" Haseenah tace "Kilan Private line dinsa ne, amma babu ta yanda likita zai sa wayarsa a wannan setting din, definitely yana da wani layin da kowa ke samunsa" Badiyya ta jinginar da kanta jikin gado tana shessheka tace "Wllh na gaji Haseenah, wasa wasa fa yau saura wata daya bikin" Haseenah ta sauke ajiyar zuciya tace "Ni zaki gaya ma sauran kwana nawa bayan rana daya ne da nawa da Maheer, ai ko nima an cuceni wannan damuwar da aka sa ki, banda haka da yanzu ai har dake zamu yi ta shirye shiryen bikina, amma ace ana ta abu ba ke" Badiyya dai bata ce komai ba sai hawaye take, Haseenah tayi kasa da murya tace "Toh kece da gaddamar tsiya, Nan nan Zaliha ta kawo mana shawara shekaranjiya kince ba haka ba, wannan kadai ne fa option dinmu yanzu Badiyya" Badiyya tace "Ke ni fa bazan dau kudina in kai ma wani kato wai Malami ba, wa enda na kai a baya wani result din na gani? Duk karyace da cin kudin jama'a in gaya maki, da zan gaya maki nawa Malamai suka ci kudina a shekaru na talatin da biyu a duniya wllh sai kinyi mamaki, ke bari kiji tun ina 22 years nake bin Malamai amma har yau ban ga out come ba, don haka wannan karan ma bazan yi asaran kudina ba, bayan samari haka na dinga ba malamai kudi akan in hada common degree din nan amma dubi sau nawa ana Withdrawing dina from this university to another, ta dalilin wannan Dr Musharraf din ne na gano ashe ina da ilimi rashin maida hankali ne kawai, ai abun akwai mamaki ace wai ni Badiyya ke final year a Nursing Science, alhalin Microbiology ma na kasa shekarun baya" Haseenah tayi wani murmushi tana girgiza kai tace "Uhumm Badiyya kenan, wllh baki dai samu na kwarai bane kawai" Badiyya ta zaro mata ido tace "Ke na fa ce maki duk karya ce Haseenah, haka nan ake cewa ba a samu na kwarai ba amma ni nayi harka da Malamai sun fi 50 kuma idan gaskiya ce ace a cikin mutum hamsin babu na kwarai ko daya? Aa wllh ba da kudina ba wannan karan" Haseenah dai tayi shiruu, Badiyya ta kalleta tace "Ko ke kinsan wani Malami ne?" Da sauri Haseenah ta zaro ido tace "Ah haba dai, wane ni??? ina nake zuwa da zan san Malamai, kuma su waye kawayen nawa banda ku? Ban san kowa ba wllh, kawai shawara na kawo amma ni ba malamin da na sani" Badiyya na goge idonta tace "Shikenan nasan abinda zan yi" Haseenah tace "Me za ki yi?" Badiyya ta mike ta dau handbag dinta tace "Ke dai kawai ki zuba ido" Haseenah tace "Toh Allah Ubangiji ya sa a dace, yanzu yaushe zaku fara final exams din ku?" Badiyya ta nufi kofa tace "Wa ke ta wani final exams" Haseenah tace "Aa Badiyya kar fa kije kiyi 2-0 gwara ki samu ki kammala degree din nan naki successfully, shekara biyar fa ba wasa ba" Badiyya ta hade rai ta juyo tana kallonta tace "Ai sai dai Mayraah tayi 2-0 babu degreen babu miji, tunda har ta shiga gonata... Wallahi in dai ina numfashi i can go to any extent na ganin auren nan ya lalace, kuma lalacewar auren zai yi distablizing dinta har sai ta kasa final exams" Tana gama fadin haka ta fice daga dakin tayi banging kofar, Haseenah dai ta taɓe baki, haka kawai tace mata ga malamin da ke mata aiki har ya karkato da hankalin Maheer gareta wataran abu ya hadasu ta tona mata asiri a familynsu ta shiga uku, waye bai san Badiyya da tonan silili idan abu ya hadaku ba.... Sai bayan Magrib Badiyya ta shigo gida, Ammi na zaune parlor tare da Maheer, ta gaida Ammi, sannan Maheer ma ta gaishesa ciki ciki, zata wuce yace "Zo nan" tsayawa tayi, sai kuma ta juyo tana kallonsa, yace "In taso in sameki ne?" Dawowa tayi ta zauna saman kujera bata ce masa komai ba, yace "Daga ina kike?" Ta daure fuska tace "Daga gidansu Haseenah nake muna shirye shirye" Maheer yace "This should be the last day da zaki fita ki kai magariba a waje, nan ba gidan Hajja bane da kike fita sanda kike so ki dawo sanda kika ga dama, sannan gidan nan ba a fita anyhow without control we are not animal, this should be ur first and last warning" Tuni ta kauda kai zuciyarta na tafarfasa, tabdijam banda su Haseenah da Zaliha da suka ja mata a ina wannan mutumin zai ganta ya dinga yanka mata warning haka kamar er cikinsa, duka duka da shekara nawa ya girmeta?? Ita dai Ammi bata ce komai ba, Lokaci daya ta mike fuuu ta wuce sama, Ammi na kallon Maheer tace "Allah ya shirya mana ita" Maheer yace "Allah abunta har da iskanci saboda taga babu me ce mata komai, gashi Hajja ta gama lalatata, su kansu dangin babanta are not helping matters at all, da anyi magana sai kuce marainiya" Mayraah na zaune tana karatu a daki Badiyya ta shigo ko sallama babu, Mayraah na kallonta tace "Sannu da zuwa" Wani mugun kallo Badiyya ta watsa mata, daga nan ta hau tube kaya tana diresu kan gado, Mayraah dai ta ci gaba da karatun da take, Badiyyah na shiga bandaki Mayraah ta mike ta bar dakin, a stairs suka hadu da Maheer ta bi sa zuwa dakinsa kamar zata yi kuka tace "Yaya don Allah ka tayani yi ma Ammi magana ko downstairs ne in koma, wllh i can't stay in the same room with Badiyya, ko na mata magana bata kulani, and ta riga tayi occupying ko ina a dakin, ni tsoronta ma nake baxan iya kwana daki daya da ita ba, Ammi kuma tace dole sae na tsaya a dakin" Maheer yace "Leave Ammi alone, ki shigo nan kiyi duk abinda za kiyi, in few weeks time zaki bar mata gidan ita da Ammin ai" Yana fadin haka ya shiga bandaki, Mayraah ta karasa a hankali ta zauna gefen gado. Karfe bakwai na safe Mayraah ta fito daga dakin Maheer kafin Ammi tayi noticing a nan ta kwana, dakinta ta nufa da sauri ta buda kofar dakin a hankali ta shiga, bbu kowa cikin dakin tasan probably tana banɗaki, Mayraah ta fiddo kayan da zata sa yau don karfe tara take da lectures, zaunawa tayi tana jiran fitowar Badiyya amma shiru, ta kalli agogo ganin she is been sitting for 30min ta kalli kofar bandakin, ita dai bata ji an buda ruwa ko kuma dai wani alama da zai nuna mutum na bandakin ba, tana ta zaune bayan wani minti goman ta mike tana bin dakin da kallo, to ko dai bata bandakin ne, Boxes din Badiyyah uku ne ranan da ta zo gidan, yanzu kuma maimakon uku Mayraah sai taga biyu kawai babu na tsakiya, kallon gaban mirror tayi da sauri taga babu wasu turarruka da kayan shafe shafen Badiyya, nan ta lura hatta Charger dinta da power bank dake bedside drawer babu su, kofar bandakin ta nufa ta ɗan tura kafin ta leka ciki taga wayam, fita tayi daga dakin ta tafi dakin Usman don can Maheer ya kwana, knocking tayi sai da ya amsa sannan ta bude ta shiga, ta samesa kwance, ta karasa kusa da shi da sauri tace "Yaya Aunty Badiyyah fa bata gidan nan" Maheer yace "How?" Mayraah tace "Wallahi kuwa, yanzu naje dakin nama yi zaton tana bathroom ina ra jiranta sai daga baya nayi noticing babu jakanta daya a dakin" Maheer yace "To me zanyi kika zo kika tasheni" Mayraah tace "To ko gidan Hajja ta koma?" Maheer yace "Da ya fi mata dai" yana fadin haka ya gyara kwanciyarsa ya juya mata baya, Mayraah ta ɗan turo baki, can tace "Zan je in gaya ma Ammi" bai ce mata komai ba, hakan yasa ta mike ta fita daga dakin, Hankali tashe Ammi ta nufi dakin Mayraah bayan Mayraah taje ta sanar mata Badiyyah bata gidan, Ita dai Mayraah na tsaye bakin kofar dakin nata tana kallon Ammi dake bin ko ina na dakin da kallo har da

Chapter 5 of 14