amma ya akayi ciwon ciki yake kara maka Aneeta bata kulaka ne?"
hawaye ya cika mishi ido ya taɓe baki zai fara kuka ya kaseem yace "karka sake kamin kuka anan"
shiru yayi, yace "to me amfaninta? kayi s** da ita?"
shiru yayi, shima ya kaseem yayi shiru da alama koda yayi to ba sosai bane sabida gashi har yanzu yana ciwon cikin da yafi ma na baya, ganin yana hawaye ya fara lallaɓashi yace "don't cry Allah zai baka sauki kaji?"
a hankali ya jijjiga kai, jingina kai ya kaseem yayi da jikin gadon yayi shiru yana tunani, meyasa Aneeta zatayi haka? yadda ya yadda da ita yayi expecting idan hameed ya aureta zata kula dashi amma sai yaga kamar hameed ɗin ma yana lalacewa ne ya zama wani kala kamar akwai abinda yake damunshi, ɗaura kanshi yayi a cinyar ya kaseem ɗin yayi shiru yana kallon saman ɗakin hawaye yana wanke mishi fuska, ya kaseem yace "ya Allah ka ragewa kanina wannan wahalan, ya Allah yasha wahala sosai banaso ya kara shan wahalan da yasha a baya, hanunshi yasa a kanshi yana shafa gashinshi da suka hargitse, shiru yayi, sai kuma can ya kara fara jujjuya kai yana rike maranshi, ya kaseem yace "sorry bari nayi maka allura"
fita yayi yazo da allura, mishi yayi yana rungume da ya kaseem har ya fara bacci sabida alluran me karfi yayi mishi, shiru yayi yana kallon innocent face nashi, bai taɓa ganin mutumin da yasha wahala a rayuwarshi kamar hameed ba, tun yana yaro yake shan wahala har yanzu bai samu nutsuwa ba, tun daga kan zeenat daya aura basu taɓa kwana ɗaya cikin kwanciyan hankali ba har zuwa yanzu da yake ganin rashin dacewa da auren Aneeta da yayi, cikin sanɗa ta turo kofan ta shigo, turus ta tsaya ganin ya kaseem ne zaune akan gadon ga hameed rungume dashi yana bacci da alama da kyar yayi baccin duba da zufan dake goshinshi, jikinta ne ya fara rawa tana sanye da bakin riga silk tasa hulan net, kanta ta sunkuyar kawai ya sauke kan hameed daga jikinshi ya kwantar dashi, kallonta yayi sama da kasa baice mata komai ba kawai ya fita daga ɗakin, taɓe baki tayi bayan ya fita sannan tazo ta hau gadon ta kwanta.
ya kaseem safa da marwa ya fara a ɗakin a ranshi yace "anya bamuyi kuskure ba?"
sai kuma ya zauna ya dafa kanshi, kullum baya bacci tunani baya bari yayi bacci idan yayi bacci to saide ɓarawon bacci ne ya saceshi, ga ɓatan meenat da yaga ya dami sultan duk ya zama wani iri kullum yana nemanta babu dare babu rana ga damuwan da yake gani da rashin kwanciyan hankali ƙarara a tare da hameed, wannan damuwan kaɗai sun isa su hanashi bacci.
washe gari duk suna breakfast babu me yiwa juna magana, Aneeta ce ta fito tayi bala'in kyau cikin atamfa fited gown ya matukar kama jikinta ta ɗaura bakin After dress a sama, takalmi me tsini tasa sannan ta rike karamin jaka ta sauko ta kallesu duka bata gaida kowa ba ta zauna akan kujera itama ta fara cin abinci, kallo ɗaya ya kaseem yayi mata ya ɗauke kai, har suka gama breakfast ta tashi cikin yauki tana tafiya, ya kaseem yace "ai da tun farko kin nuna halinki da zamufi jin daɗin zama dake sabida babu wanda zaizo yayi tunanin akuya ce aka lulluɓe da fatar kura"
murmushi tayi sannan ta ciro bakin glasses a jakanta tasa, juyowa tayi tana kallonshi tace "ya kaseem duk gidannan akuyoyi ne aka lulluɓe da fatar kura so banga laifi ba dan surukur gidan ta zama akuya da fatar kura"
zaiyi magana hameed ya rike hanunshi ya girgiza mishi kai alaman please yayi shiru.
bai kara magana ba ita kuma ta fita domin zuwa school, Ammi murmushin da yafi kuka ciwo tayi sultan kuma ya sunkuyar da kai ya rasa yadda zaiyi abin yana damunshi gaba ɗaya ya zama shiru shiru.
ya kaseem labcoat nashi yasa ya fita a gidan ranshi a ɓace, sai dare ta dawo gidan, suna falo tace "sannunku"
ya kaseem yace "daga ina kike?"
tace "ya kaseem a ganina yarima hameed ne kaɗai yakeda iko akaina shine zai iya tambayata daga ina nake, to amma ba komai daga school nake"
zaiyi magana sultan yace "dan Allah yaya kada mu kara wani tashin hankalin akan wanda muke ciki a gidannan"
shiru yayi amma fa zuwa yanzu ranshi ya gama tafasa wallahi da yasan haka halin Aneeta da babu abinda zaisa ya taimaka mata harma tazo gidan bale ta samu fuskan auren hameed, banda ƙaddara ma ai tasan hameed ba sa'anta bane, hameed ya fita komai harma da kyau babu abinda bai fita dashi ba, amma tayi sa'a hameed yana sonta da wallahi saiya koreta, tashi yayi yabar wajen ranshi yana soyuwa.
murmushi tayi lokacin data buɗe kofa taga hameed zaune akan kujera yayi shiru abin duniya duk ya isheshi haka takeson ganinshi cikin damuwa abin yana bata nishaɗi, kallonta yayi yaga tana mishi murmushi, shima murmushin yayi mata, a hankali tayi wurgi da jakan cikin gajiya ta cire after dress ɗin shima ta wurgar, zuwa tayi inda yake ta zauna akan cinyarshi, rungume kanshi tayi a hankali tasa hanunshi a waist nata, riketa yayi sosai yana jin sonta har cikin ranshi, a kunnenshi tayi magana cikin wani kasalallen murya tace "am sorry my prince"
shiru yayi, a hankali ta haɗa bakinta da nashi, kissing nashi ta fara ta rufe ido, cikin damuwa da kewan da yake ciki ya fara mayar mata, Allah sarki jikinshi har rawa yake sabida Allah ya yishi da matukar needing, zuge zip ɗinta yayi yayi kasa da rigan, hanunshi yasa a chest nata ya fara wasa dashi, lumshe ido tayi cikin wani irin murya tace "Ahhh"
ji yayi gaba ɗaya yana neman zaucewa, fuskanshi ya ɗaura a chest nata, shafa kanshi ta fara tana kara matsowa sosai ta yadda bom bom ɗinta zai haɗu da jkinshi, saida ta tabbatar ta gama fitar dashi hayyacinshi kafin ta fara zamewa a hankali, riketa yayi sosai yana ji yau idan ta matsa a wajenshi babu abinda zai hanashi suma, cikin sanyi tasa hanu akan nashi ta rabashi da jikinta, idanunshi da suka tsume yake kallonta dasu a hankali ta sauka daga jikinshi ta shiga bedroom, rufewa tayi harda makulli sannan ta jingina bayanta da kofan tana maida numfashi idonta a rufe.
hameed sauka kasa yayi ya kwanta ya fara kuka, ya rasa yadda ma zai fara yi da kanshi.
wayanshi dake gefe ya kalla ya janyo ya turawa ya kaseem text (_yaya zan mutu_)
daga nan yayi jifa da wayan yana kuka sosai.
ya kaseem sai safa da marwa yake ya kasa zama sai tunanin mafita yake, wannan aneetan wani hali takeso ta fara nunawa koma yace ta nuna, dunƙule hanu yayi ya fesar da iskan bakinshi karan shigowan text da yaji yayi saurin ɗauka yana dubawa, da sauri ya fita a ɗakin, ko sallama baiyi ba ya buɗe kofansu ya shiga, gani yayi yana birgima a kasa, da gudu ya karaso ya ɗagashi, kwanciya yayi akan sofa, idonshi yayi jajur kamar yadda bakinshi ya koma red, daga idonshi kaɗai zaka san me yake damunshi, dafa kai yayi yace "hasbunallah yarima ina Aneetan?"
nuna mishi kofan ɗakin dake rufe yayi, a fusace ya tashi zaije ya rike hanunshi alama yayi mishi na yaya please, komawa yayi ya zauna, ganin yana kuka shima yaji kamar zaiyi kukan yace "yarima ya zanyi? da wanne zanji yarima? da wanne zanji?"
sai kuma yayi shiru, ganin haka hameed ya ɗan rage kukan.
tausayinshi yasa ya rike hanunshi yace "tashi muje ɗakina"
tashi yayi a hankali yake tafiya yana mishi sannu har sukaje ɗakin, ya mishi allura sannan yace "kwanta"
kwanciya yayi babu jimawa bacci ya ɗaukeshi, waya ya kira da sauri aka ɗaga yace "Alameen ya kake?"
ya amsa da "ina lafiya ya kaseem ya abokina?"
yace "gashi nan kamar yadda ka sanshi, kana gari?"
yace "gobe zan dawo dai"
yace "idan ka dawo ka rinƙa zuwa kuna fita da hameed"
faɗa mishi duk abinda ke faruwa yayi dama basa ɓoyewa Alameen komai sabida good friend na hameed ne, yayi shiru sai kuma yace "wai ya kaseem har yanzu komai bai daidaita bane?"
cikin gajiya shima yace "saima kara lalacewa da komai yake yi, please nasan yadda kuke aminta da hameed ya dawo kamar da ya rinƙa zuwa gidanku kaima ka rinƙa fita dashi may be ya ɗan samu sauƙin rayuwarshi may be ya rabu da depression, yanzu so nake ma ya rabu da wannan shegiyar Aneetan da naji na fara tsananta sabida abinda take mishi kuma naga kamar yana sonta sosai"
yace "ba komai ya kaseem gobe ina dawowa zanzo"
yace "yawwa Alameen Allah maka albarka"
yace "Ameen"
zama yayi a gefen hameed ɗin yace "ɗan albarka Allah ya baka ikon cinye jarabawa"
shiru yayi yana tunanin meenat wacce har yau babu labarinta kullum sai mai martaba yayi zancenta sun kasa mantawa da ita.
washe gari kamar yadda Alameen ya yiwa kaseem alkwari sai gashi ya shigo, duk sukayi murnan ganinshi cikin jin daɗin ganinsu shima yace "ina abokina?"
sultan yace "dama ai mun san shi kazo wajenshi ba muba ya Alameen"
dariya yayi, Alameen kyakkyawa ne sosai amma shi chocolate ne saide kalanshi me bala'in kyau ne, yace "wai ina yake?"
Aneeta data fito yanzu daga ɗaki sanye da simple riga da wando tace "waye yake tambayan mijina?"
murmushi yayi mata yace "nine amininshi sunana Alameen"
kallo ɗaya ta mishi ta watsar, jikinshi yayi sanyi yace "yana ciki?"
kaseem daya fito yanzu daga ɗaki yanasa uniform yace "meyasa zaka tambayi wanda basuda hakki a kanshi? ƴan gidansu zaka tambaya ba bare ba"
yayi maganan yana kallon Aneeta, murmushi Alameen yayi yace "ya kaseem banga meenat tawa ba ina take?"
yace "meenat ta ɓata"
yace "innalillahi yaushe?"
faɗa mishi komai yayi sannan yace "ka kwantar da hankalinka zamu samu meenat insha Allah kuma kamar yadda akayi maka alkwari kaine zaka aureta meenat ba zata auri kowa ba sai kai.
yace "amma ya kaseem meyasa baku faɗamin ba?"
yace "sabida nasan zaka iya barin komai da kakeyi a kasar waje ka dawo nigeria domin neman meenat sabida nasan yadda kake sonta da mukayi hakuri ba gashi ka dawo ba? kuma tare da kai zamu fara nemanta"
yace "insha Allah sai inda karfina ya kare sannan duk wanda yake da sa hanu saina wulaƙanta rayuwarshi"
ya kaseem yace "kaje ciki hameed yana ɗakina"
da sauri ya shiga ciki domin ganin abokinshi.
_Jiddah Ce...✍️_
08144818849
[20/08, 2:11 am] Shuraihu Usman: 🌸🌸🌸🌸🌸
*ƘADDARA TA*
🌸🌸🌸🌸🌸
Na
*Jiddah S Mapi*
*Chapter 12*
~Yau ake ɗaura auren meenat da hamma najeeb, banda murna da farin ciki babu abinda Asmeeta take yi, itama meenat ɗin murna take yi sunyi wanka me kyau duk da babu mutane dayawa amma sun ɗan zo har aka ɗaura aure, tunda aka ɗaura aure ya dawo gida ya cire kayan jikinshi daya taƙura mishi, kayanshi na zuwa jeji yasa sannan ya ɗau takobi zai fita, meenat wacce ta ɓata rai tana kallonshi tace "to ina zakaje?"
sajenshi me kyau ya shafa, sannan ya zuba mata kyawawan idanunshi da suke ɗaukan hankalinta kamat idanun turawa cikin idon brown ne, lips nashi na kasa ya tsotsa dama wannan ya zame mishi jiki yace "zanje bazan jima ba zan dawo"
kamar zatayi kuka tace "yau fa akayi aurenmu amma shine zaka fita?"
yace "kiyi hakuri ba zan jima ba zan dawo"
tace "gaskiya babu inda zakaje"
tsawan daya daka mata yasa tayi shiru tana kallonshi a tsorace
yace "ni sa'anki ne? ko kin manta ni yayanki ne kike min wannan maganan nace miki ba zan jima ba"
matsa mishi tayi ya wuce, ɗakinsu taje Asmeeta ta kalleta tayi shiru sabida tasan idan tayi magana hamma yana dawowa zata faɗa mishi daga karshe taci ɗan banzan duka shiyasa take kame bakinta yanzu ta daina ɓarin zance domin meenat tana mugun son hamma najeeb kamar ranta, ta harareta tace "wa kike kallo?"
kama baki tayi tace "ni ban kalleki ba kuma bance komai ba, ki barni da dukan da nakesha ma ya isheni"
tace "ni ɗin ya daina duka na ne?"
tsit tayi, duk rashin kunyar Asmeeta idan taji hamma najeeb to shiru takeyi dan tasan dakuwa take a hanunshi, mimi tace "Adda na miki kitso?"
tace "ban son kitso taho muje yawo na siya miki mangoro kinji ɗiyata?"
cikin jin daɗi tayi tsalle tayi kyau da kwalliyan da Asmee tayi mata, durkusawa tayi ta ɗale bayanta zasu fita meenat tace "ku jirani zan biku"
Asmeeta tace "ki tabbatar idan yaya ya dawo ba zakice tare muka fita ba"
tace "naji"
fita sukayi kamar ranan yauma dare suka dawo, cikin sanɗa meenat ce ta fara shigowa hamdala tayi ganin baya nan tace "ku shigo baya cikin gida"
Asmee dake goye da mimi wacce tayi bacci tsaban gajiya ta shigo ta kwantar da ita a ɗaki kafin ta fito tace "da alama yau hamma ba zai dawo da wuri ba, kai amma fa na iya rawa kinga kuɗin da ake watsamin a filin wasa?"
meenat tace "kin iya rawa sosai, ai nima yau nayi rawa ba kaɗan ba"
fitowa yayi daga ɗakin ya kallesu, Asmeeta da gudu ta juya zata shiga ɗaki meenat ta bita yace "ku tsaya"
tsayawa sukayi meenat tace "dan girman Allah kada ka dakemu mun tuba kuma Asmee ce tace muje"
dafa kirji tayi manyan idanunta ta zuba mata tace "ni kuma ameena? a tashi mimi zata faɗi waye yace zai je"
yace "kuzo magana zamuyi"
sun kasa yadda dashi da kyar suka zauna, gani sukayi ya zauna yayi shiru, Asmee cikin mutuwan jiki tace "hamma kana lafiya?"
ɗago kai yayi ya kalleta sannan ya girgiza kai, cikin sonshi da tausayinshi tace "hamma me yake damunka?"
yace "Asmeeta"
tace "na'am hamma"
"tunda iyayenmu suka haifemu muke fama da talauci da rashin jin daɗin rayuwa, kin san duk duniya babu wacce nake so sai ke, bayan ke kuma sai mimi sai kuma Allah ya kawo mana Ameena cikin rayuwarmu wacce nake jinta har cikin raina, Asmeeta duk da mutanen kauyen nan suna ganin kin kai aure amma ni karamar yarinya nake ganinki hakan yasa ban damu kiyi aure ba, kullum addu'ata Allah ya baki rayuwa me kyau wanda zakiyi farin ciki saboda kin taso cikin maraici babu uwa babu uba nine uwa kuma nine uba a wajenki"
tace "hamma soyayyan daka nunamin ko mama da baba sai haka"
yace "Albishir nakeso nayi muku"
da sauri tace "na me?"
ya nuna musu wani dutse dake hanunshi yana yalƙi sosai, tace "me wannan hamma najeeb?"
yace "wannan shine asalin gold, na samu a cikin ruwa yau da naje wanke takobina, nasan kuɗin gold wanda bai kai wannan bama zai iya ciremu a talauci bale wanda na samo dayawa"
tashi yayi ya shiga ɗaki, fitowa yayi dasu dayawa a bakin leda yace "wannan sune arzikin da Allah ya bani a yau bayan aurena da Ameena"
rufe baki asmeeta tayi tana kallonshi with surprise, bakinta yana rawa tace "hamma gold?"
ya bata a hanunta yace "tabbas Allah ya karɓi addu'ar mu zakuyi rayuwa cikin farin ciki, zamu bar wannan kauyen zamu koma birni muyi rayuwa me ɗauke da gata, dama alƙawari nake miki tun kina karama cewar zan kula dake kamar sarauniya yanzu tare da matata Ameenah zan kula daku tamkar ƴaƴan sarki"
tashi tayi ta rungumeshi tana murna, Ameena hawayen farin ciki ta share tace "Alhmdllh dama banada buri kamar naga yana cikin farin ciki gashi yau yana dariya"
ido kawai ta zuba mishi yadda dariya yake bala'in yi mishi kyau.
hanu ya buɗe mata tazo itama ta rungumesu, yace "gobe zan tafi birni da asuba zan tafi ba lalle ya zama kun tashi a bacci ba, zanje na siyar may be na kwana may be na dawo da wuri, zanja kunnenku musamman ke Asmeeta na sanki da taurin kai da rashin jin magana, ku kula da gidannan ku kula da mimi kunji?"
duk suka amsa da "to hamma"
sakinsu yayi yace "shine maganan dana kiraku muyi"
murmushi akan face nasu suka koma ɗaki, yana kwance a ɗaki yayi shiru yanata juye juye tunanin yadda zai gyara rayuwarsu yake, sallama yayi, da mamaki ya amsa jin muryan meenat, shigowa tayi ya kalleta ta cikin haske kaɗan na fitila yace "Ameena kece?"
tana tsaye ta gyaɗa kai a hankali, yace "me kikazo yi?"
tana turo karamin bakinta tace "Asmeeta ce tace min idan anyi aure ɗaki ɗaya ake kwana da miji shine nazo"
dariya yayi kaɗan sannan yace "to ki karaso"
a hankali ta karaso ta zauna a gefenshi, ba zato taji ya janyota jikinshi, rungumeta yayi cikin sanyin murya yace "ina sanki sosai"
wani sanyi taji a ranta jin kalman daya faɗa, ta jima tanason jin wannan kalman daga bakinshi, a hankali tace "nima ina sanka"
yace "kar kice nima kice ina sanka"
tace "ina sanka"
a hankali ya juyo da face nata yana kallonta, lumshe ido yayi yace "kimin alkwari duk inda naje ba zaki taɓa mantawa dani ba"
murmushi tayi tace "ba zan taɓa mantawa da kai ba har karshen rayuwata"
a hankali ya kara mannata da jikinshi, ji tayi ya fara yawo da hanunshi a bayanta yadda take jin sonshi batajin zata iya hanashi yin komai da ita.
a hankali ya matso da lips nashi ya ɗaura akan nata, kiss ya fara mata ta rufe ido, a hankali yake sauke numfashi me wuyan fasara, kashe fitilan yayi sannan a kunnenta yace "kiyi hakuri zakiji zafi kaɗan"
rufe ido tayi tace "idan kaine ko mutuwa zanyi ban damu ba"
wani irin sonta ya mamaye zuciyarshi, a hankali yake bi da ita, duk da taji zafi amma ta daure saida zafin yayi yawa kafin ta buɗe baki zata fara kuka cikin lallashi yana hana kanshi rasa control yace "yi hakuri"
a daren saida ya tabbatar ya maidata nashi kafin ya fara bata hakuri, sai kuma yayi shiru yana jin saukan numfashinta a faffaɗan kirjinshi.
ji yake kamar su dawwama a haka, karo na farko daya fara jin farin ciki da kaunar mace a ranshi ji yayi Ameena ta zame mishi komai a rayuwa idan ya rasata da Asmee zai iya rasa rayuwarshi.
bacci ne ya ɗaukeshi. washe gari ya fara ɗaukanta da asuba ya kaita banɗaki ruwan zafi ya dafa sannan yazo yayi mata wanka, sai ciza baki take cikin azaba yace "sannu kinji?"
alwala yayi mata sannan ya fito da ita, kwantar da ita yayi a ɗakinshi yace tayi salla, salla tayi shima yayi salla sannan ya shirya yace "kiyi hakuri nayi ɓarna kuma zan tafi na miki alkawari zan dawo duk inda naje kina raina kuma zan dawo bada jimawa ba zan baki rayuwa me kyau zakiyi rayuwa kamar ƴar sarki"
a hankali ta shafa kanshi tace "Allah baka sa'a amma ka dawo da wuri"
yace "insha Allah"
yace "kimin murmushi to"
a hankali tayi murmushi yace "yawwa matata abin alfaharita"
tashi yayi ya ɗau jakan da gold ɗin yake ciki yace "na tafi"
tace "Allah tsare hanya"
a hankali yace "Ameen"
fita yayi ya shiga ɗakinsu Asmeeta baccinta da takeyi kamar wacce ta mutu shi takeyi yasan ko za'a kwana ana tashinta ba zata buɗe ido ba, tsaki kaɗan yaja yace "Allah shiryamin ke asmeeta Allah yasa ki girma kisan fari da baki"
kallon mimi yayi yace "Allah yasa kada kibi halinta"
murmushi yayi yace "na barku lafiya"
fita yayi daga gidan.
saida gari yayi haske sosai kafin Asmeeta ta fara buɗe ido, tashi tayi da sauri ta kame tulin gashinta daya barbazu ta tashi da sauri tace "Allah sa hamma najeeb bai tafi ba"
ɗakin ta buɗe taga meenat ce kaɗai kwance tana bacci, da sauri ta fara tashinta, cikin gajiya meenat ta buɗe ido, kallonta asmee tayi cikin wauta da rashin sanin komai tace "kinzo sai bacci kike ina hamma najeeb?"
tana hamma tace "ya tafi"
shiru tayi bataji daɗi ba taso suyi sallama kafin ya tafi, cikin kwantar da hankali meenat tace "kiyi hakuri zai dawo ko yau ko gobe ba zai wuce jibi ko gata ba"
tace "to wanne zan ɗauka? yau? gobe? jibi? gata?"
tace "zai dawo Asmee karki damu kinji?"
tace "to Allah yasa ya dawo mana da kuɗi dayawa dako kullum sai mun siya abu me daɗi munci"
dariya tayi kaɗan sai kuma ta rufe ido zata koma bacci tace "bakida lafiya ne?"
gyaɗa kai tayi, tace "Ayya sannu kinji?"
shiru tayi bacci har yayi gaba da ita, fita asmee tayi ta fara salla sannan tazo ta fara girki ta gama ta kawo musu sukaci meenat ta kara komawa baccin.
Aneeta ce tsaye a cikin school ta kasa zaune ta kasa tsaye hanunta goye a baya kawarta billy wacce suka alaka sosai tazo ta dafata tace "haba Aneeta meyasa kike wannan damuwan?"
ta kalleta sannan ta cire glasses black na idonta tace "meyasa nake damuwa kuma billy? kin san ni ƴar sarki ce ban taso cikin wahala ba, na taso cikin jin daɗi da kwanciyar hankali yau ace bayan tashin hankali da nake ciki wai ina ɗauke da ciki? ciki nefa dani billy cikin yarima hameed"
billy tace "common Anee ai yarima yana son yara sosai kema kin faɗa me zaisa ki damu to?"
tace "ya zanyi da karatuna? kuma ya zanyi na haihu na tsufa kenan?"
tace "Aneeta..."
rufe mata baki tayi tace "please billy idan zaki taimaka ki taimakamin na zubar da wannan cikin"
tace "karki damu muje yanzu ma zan kaiki wajen dr na zai zubar yau ɗinnan"
ajiyan zuciya ta sauke tace "ko kefa billy ta?"
tace "muje class zuwa anjima"
tace "da zafi ake dukan karfe mu tafi yanzu"
zatayi magana ta turata suka tafi kawai, motar billyn suka shiga direct sai wajen Dr ɗinta, da suka mishi bayani magani ya bata a wajen ta haɗiye sannan ya bata sauran yace zuwa azahar tasha cikin zai zube yau, ta amsa da godiya sannan ta bashi kuɗaɗe masu yawa, school suka koma sai kusan azahar tasha sauran ta fito daga school ɗin tana jin cikinta har ya fara ciwo, motar yarima ta gani da sauri ta karaso tana mishi murmushi shima murmushin yayi mata yayi bala'in kyau cikin ƙananan kaya, shiga tayi ya tada motan suka tafi, suna isa gida taga yasa hanu a baya ya ciro leda, mika mata yayi ta karɓa tana buɗewa, teddy ta gani da sauran kayan jarirai, gabanta ne ya faɗi tayi saurin rufewa tace "sunyi kyau sosai my prince amma basu kaika kyau ba"
ta lakaci karan hancinshi, murmushi yayi suka fito tare, tsayawa yayi yana duba flower ɗin da yaga sun karye kuma ba'a cire ba shiga ciki tayi tana amsa call ɗin daya shigo, da sauri tace "billy inaga fa cikinnan yama fara zubewa kuma banaso yarima yasan na zubar da ciki sabida inada task dayawa da ban gama ba a gidannan..."
sauke wayan tayi tana kallon fadeel da yake kallonta cike da zargi da alama yaji duk abinda ta faɗa, zata wuce ya tare hanyan, tace "ka matsa na wuce meyasa zaka taremin hanya fadeel?"
yace "Anty Aneeta meyasa kike cutar da innocent soul? meyasa kike cutar da yaya yarima bayan kin san baida niyan cutar da kowa a ranshi?"
tace "me kake nufi fadeel?"
zaiyi magana ta tureshi ta wuce binta yayi yace "naji duk abinda kike faɗa kuma wallahi saina faɗa mishi"
tafiya take har ta kusa haura stair ta juyo tace "fadeel kada ka shiga abinda bai shafeka ba"
yace "wallahi saina faɗa"
ya kaseem daya fito yanzu ya tsaya yana kallonsu, zata wuce fadeel ya rike hanunta, tace "ka sakarmin hanu fadeel"
yace "ba zan sakeki ba har sai yaya yareema yazo...."
juyi tayi ta rike hanunshi gam ta fara gangara daga stair wani irin ihu ta kwala tace "cikina ya zubar da cikin"
yarima daya shigo yanzu tsayawa yayi a razane idanunshi sunyi girma yana kallonta jini yana zuba daga kasanta, fadeel ya fara girgiza mishi kai yace "wallahi yaya yarima na rantse da Allah...."
kuka ya fara ganin yadda take rike cikinta tana ihu, take abi dake salla ya idar da wuri baima san sanda ya shigo ba, ammi ma da hijabi a jikinta da calbi ta tsaya ta kasa sakin kofan tana kallon Aneeta dake kwance tana birgima jini yana zuba, ya kaseem ya kasa gane me yake faruwa, abinda be gane ba shine itace ta faɗi da kanta ko fadeel ne ya tureta?
fadeel wand ya gama tsorata yazo da gudu zai ɗagata, marin da hameed ya ɗaukeshi dashi saida ya faɗi a gaban ya kaseem da yake zuwa wajen, ba bakin magana amma wani kallo yake mishi, nufanshi yayi zai rikeshi ya kanƙame ya kaseem yace "dan Allah ya kaseem na san fushinshi na san idan ranshi ya ɓaci ba abinda ba zai iya ba dan Allah ka tainakeni karya kasheni"
jikin Ammi ya fara rawa, Aneeta sai juyi take a kasa cikin azaba tana