leko kansa yana murmush ya ce
"Hajiya Su'ad yammata kwana dayawa ko nemana bakya yi"
Ni dariyama yabani ko akanme zan nemesa daga gani ɗaya danai masa to in nemesa ince masa me, buɗemin kofa yayi yana faɗin
"Zomu tafi gidan dama na nufa Ma'ma ta aikeni wajan Maminki" haka kawai naji bazan iya yimasa musu ba na shuga, tare muka shuga gida da Nurein hakan na lura ba karamin daɗi yayiwa Mami ba, wasa wasa saiga shakuwa ta shuga tsakanina da Nurein harya fara bayyana min asirin zuciyarsa tun ina sharesa amma yawan nacinsa yasa na amshi soyayyar sa, kamar da wasa muka fara soyayay mai zafi harta kai ga muna batun aure.
__________Ashirye ya futo cikin da kakkiyar shaddarsa ruwan zuma kallo ɗaya zakayiwa shaddar kasan bata kananun kuɗi bace wani kyalli take da walkiyya mai ɗaukar idanu hannunsa ɗaure yakeda agogo na zallar fata baki, yakafa hular tangaran ta zauna das akan nasa kafafunsa na saye cikin tsadaddan takalmi Haf shoe baki mai matukar kyau, tunda yafuto Jakadiya take binsa tana masa kirari dariya ta bashi sosai yanda take zuzuta sa saida yadara wanda hakan yasa Umma dake zaune a falon ta ce
"Lah yau wacce rana Turaki yana dariya gaskiyya jakadiya nabaki dubu hamsin" guɗa jakadiya tayi wacce tasa Turaki ya toshe kunnansa yana murmushi ya kalli Juhaina dake zaune gefan Umma tayi tagumi tareda zubawa Turakin idanu ba karamin kyau yayi mata ba yau nan take wani abu ya tokare kirjinta, Turaki zama yayi a kusa da'ita ganin yanda ta kafesa da idanu ya ce
"Autar Umma lafiya kike kuwa irin wannan kallon kamar baki sanni ba" taɓe baki tayi tareda mikewa ta shuge ɗakinta faɗawa saman gado tayi ta fashe da kuka, tarasa yaya zatayi da soyayyar Fu'ad ta kasa son ko wanne namiji shi kaɗai takewa wani irin so, wayarta ta ɗauka ta kira lambar Khady tana kuka take cewa
"Deeja na kasa jurewa soyayyar Yah Yarima zata kashe ni yaya zanyi ina zansa kaina naji daɗi, inata kokarin ganin na manta da soyayyarsa amma yau ganinsa ya tada min tsohon mikin son sa daya jima yana addabar zuciyata, nayita nuna masa ta hanyoyi daban daban acan baya amma yakasa ganewa"
"Juhaina ya kikeso ki maida mana hannun agogo baya, ya zakiyi da Abdallah kuma wanda kika amshi soyayyarsa dan Allah ki manta da wani Ameen sauran wata" Khady ta faɗa ranta ɓace
bayanta Turaki yabi ya tsaya bakin kofa yana jiyo maganganunta da khady shuga yayi ciki ya zauna gefan gado saida ya zauna ɗin sannan ta gansa da sauri ta kashe wayan tana maida kanta saman fulo
"Tashi ki gayamin da gaske sona kike mai yasa kike sona?"
Sake ɓoye fuskarta tayi cikin fulo, ganin baza tayi magana ba yasa yamike tareda faɗin
"Shi kenan ni zanje kano na dawo anjima zanzo saiki faɗamin da gaske kike sona zaki aure ni?"
Fucewa yayi daga gidan har zuwa inda tawagar fadawa suke waɗanda zasuyi masa rakiya zuwa kano, zai biya ta masarauta yakai sakon mai martaba.
Sai bayan sallar La'asar Turaki ya shuga gidanmu dake tarauni mai gadi bai tsaya tambaya ba yabuɗe masu get tawagar motocin guda biyar suka shuga ciki, Turaki ya shuga main falo da sallama, gidan shuru kamar ba kowa saida yasake sallama sannan hanne mai aiki ta futo, murmushi tayi dan ta ganesa saidai jikinta yai sanyi sosai dan ganinsa saiya tuna mata da Uncle Fahad mutumin kirki,gaishesa tayi sannan ta wuce ciki ta sanar da su Ummi zuwansa tare suka futo da Mami ya zube kasan carfet yana gaidasu, tuni hawaye yafara wanke fuskar Mami Ummi dake ciccin magani ta ce
"Fu'ad sai yau Allah yakawo ka kai mana gaisuwar Fahad samada shekaru uku da rasuwarsa"
Arazane yaɗago yana kallon Ummi muryarsa tana rawa ya ce "Ummi ban gane ba mai kike faɗa haka ina Fahad"
Mami da har tafara kuka ta ce "Fahad Allah yai masa rasuwa wata biyar da bikinsa yan fashi suka shugar masa gida suka kashe sa"
"Innalillahi wa'inna ilaihir raji'un, la'ilaha illallah muhammadan rasulilla"abinda Turaki yake iya faɗa kenan kafin yafashe da matsanancin kuka..
07039793439
[6/10, 7:37 AM] maman sauban: 🌹 *KUKAN ZUCIYA*🌹
Story and writtin by
Mamie Yusuf Daboo🥰
☀️ *First Class Writer Assosuciasion*☀️
Home Of Qualities And Trusted Writer's Of Tha Nation
MARUBUCIYAR
HALIN RAYUWA
SOYAYYA DA ZUMUNTA
SANYIN IDANIYA
AIMANAH
YANAYIN RAYUWA
AND NOW KUKAN ZUCIYA
25&26
Kuka yake sosai yajima yana kukan wanda kukan nasa ya kuma karyarwa da Mami zuciya ta wuce ɗakinta itama tana kuka,ya jima yana kuka har sanda Yaya Jabeer yadawo yai masa rakiya makabartar da'aka binne Ankul, sosai yai masa addu'a kafin zuciyarsa ta karye yashuga basa hakuri kan rashin zuwansa, kamar wani mahaukaci haka yake zaro zance naban hakuri kamar wanda yake magana da yarayyan mutum, har saida Yaya Jabeer ya rukosa suka futo zuwa wajan mota har sannan kuka yake, bayan sun dawo gida Abinci Ummi ta kawowa Fu'ad ba yanda zaiyi haka yafara tsakurar abincin dan yafaɗawa Ummi shifa a koshe yake amma ta kafe saiya ci, zuba idanu yake yaga gilmawar Su'ad amma shuru ba alamarta, kunya tasa yakasa tambayar ina take, gabansa yabuga da karfi har saida yasa hannu ya dafe kirjinsa ya lumshe idanu yana addu'ar Allah yasa ba wani auran tayi ba, tabbas idan akace Su'ad ta auri wani bayan Uncle to kuwa ya cika mara sa'a a rayuwa, lumshe ido yayi tareda kwantar da kansa saman seater yanajin zuciyarsa naci gaba da bugawa kamar zata fasa kirjinsa ta fito saboda fargaba.
Tun daga bakin gate na gidanmu nasan yau munada babban bako ganin manya manya motoci acikin gidan, can gefe na faka motata Ameera ta kalleni da alamar tambaya ta ce
"Anty yau wa muka samu a gidan nan yacika da fadawa haka?"
Ban bata amsa ba sakamakon gabana da yai wata irin faɗuwa, na futo daga motar na ruko laidar hannuna dana siyo mana yoghurt Ameera tuni ta shuge ciki ni kuma saida na tsaya na kulle motar sannan na shuga zuwa ciki, lumshe idanuna nayi saboda wani daddaɗan kamshin turare dana shaka tabbas nasan kamshi nan amma na rasa a inda nasansa, cigaba nayi da tafiya har zuwa falo na uku inda komai nawa ya tsaya cak na wucin gadi sakamakon idonsa daya shuga cikin nawa ledar hannuna na saki sannan na wuce ɗakina da gudu ina sakin wani marayan kuka😥ganinsa danayi yatuna min da masoyina Fahad, sosai nake kuka har zuwa sanda Ummi ta shugo ɗakina
"Wai wannan kukan na menene najin daɗin ganin Fu'ad ne kona me?"
"Ummi Uncle! dana gansa sai naga kamar zan gansa tareda Uncle ɗina,ban saba ganinsa shi kaɗai ba ko yaushe zan gansa yana tare da Uncle ɗina, Ummi da gaske Uncle yatafi kenan bazai kuma dawowa ba?"bazai sake rayuwa tare damu ba?"shi kenan mun rabu, bazan sake ganin saba bare naji ko muryarsa!"
"Su'ad zaki fara ko, to kije sitting room Fu'ad ɗin yana can zai maki gaisuwa"
"Gaisuwa kuma Ummi shekara nawa da mutuwar Uncle maiya hana sa zuwa sai yau yaga damar zuwa"
"Idan kikaje sai kiji dalilinsa na kin zuwan" tana gama faɗar haka ta fuce daga cikin ɗakin, ban futa ba har saida Amira tazo tace "Ummi tace lalle ki futo wajan Uncle Fu'ad karta shugo ta sameki"
Da sauri na ɗago na kalli Ameera sai kuma na duro daga gadon na yafa mayafina na fuce daga ɗakin.
Zaune na same sa ya saka kansa cikin kafafuwansa sallamar danai tasa ya ɗago yana kallona da jajayan idanunsa dasuka sha kuka, kujeran dake kallon wacce yake kai na zauna batare da na gaidashi ba dan Allah yagani batun yau ba nakejin haushin Fu'ad saboda nasan yanda suke da Fahad bai kamata ace har zuwa shekarun nan baizo gaisuwa ba.
"Ashe Fahad mutuwa yayi?"mai yasa ba'a gayamin ba?"ina can ina rayuwa ashe nayi rashin aboki amini ɗan uwa"
"Ashe dama ka damu dashi ainazaci daka damu dashi daka nemesa a tsawon wannan lokacin"
"Bana kasar nan Princess ina london shekaru uku kenan, yanzu hakama saboda shi nabaro tarin ayyukan dake gabana nazo kawai danna gansa saboda ina kiran lambobinsa basa shugowa, gaya min ina yan fashin da suka kashemin aboki an yanke masu hukunci"
"E! an yanke masu, amma Zainaba har yanzu tana raye a gidan yari"
"Maiya kawo Zainaba cikin wannan zancan" komai daya faru na kwashe na gaya masa, idanunsa yai ja sosai alamar ɓacin rai ya ce "Matsalar kasan nan kenan shi kenan ita baza'a kasheta ba yanzu ba time damunje gidan yarin amma zan dawo nan da friday yazama dole akashe ta kamar yanda takashe min aboki" mikewa yayi yana kallona ya ce
"Zan koma sai...shuru yayi bai karasa ba sakamakon shugowar Ameera ta miko min wayata tace "Anty gashi Yaya Nurein ke kiranki" amsar wayar nayi ita kuma ta futa, kara wayan nayi a kunnena ina murmushi
"Ina kika shuga kika bar wayarki inata kira?"
"Nayi bako ne ina sitting room nabar wayan a ɗakina"
"Bako Su'ad maiyazo yi wajanki" murmushi nayi ina kallon Fu'ad ta gefan ido ganin yanda ya kafeni da idanunsa yana aunamin wani kallo dana kasa gane na mene, hakan yasa na kara narkar da murya cikeda shakawaɓa na ce
"Kai Hubby maine na damuwa abokin Uncle ne fa yazomin gaisuwa kaima kasan babu wani a zuciyata inba kai...ban karasa ba naga Fu'ad a kaina yana huci ya fisge wayar yasa ta a aljihunsa yafuce daga ɗakin a fusace, murmushi nayi inabin bayansa
"Kabani wayata nidai" bai juyo ba yaci gaba da tafiyarsa ina biye dashi har mukaje falon karshe, saida yakama handling na kofa ba tare daya juyo ba ya ce
"Karki sake naga kafarki a compound wallahi sai ranki ya ɓaci harni zaki rainawa hankali a gabana kina kiran wani da Hubby"
Dariya yabani sosai amma na maze nace "To naga mijina ne sainaki kiransa da Hubby dan kana wajan nidai ka bani wayata in kuma baka da wayane tona bar maka" juyowa yayi ya kalleni yai kwafa tareda girgiza kai yafuce da sauri, dariya nayi nima na juya zuwa ciki ina murmushi...
Tunda yashuga mota ransa ke ɓace ko kallon Chiroma dake masa hira baiyi ba yana kallo kiran Baraka yana shugowa harya katse bai ɗagaba sai dare sosai suka shuga garin nasu dan suna tsaya yin sallar mangariba da insha data riskesu a hanya,yana shiga gida wanka yayi yai shirin barci sai sannan yakira Baraka bugun farko kuwa ta ɗaga kamar daman jiran kiran nasa take, gaishesa tayi kana ta ce
"Dan Allah Abban Su'ad zan biyi su Usman zasu taho nageria duk zaman nan bayamin daɗi gashi kai har yanzu baka dawo ba kusan satinka biyu kenan"
"Bance ki tawo ba ki zauna nima na kusa dawowa" rokonsa tashugayi hardai ya sakko ya barta ta biyo Usman ɗin su tawo tare, yana ajje wayar ya ɗauki wayar Su'ad duk yanda yaso ya gano pin ɗin scirity dake jiki kasawa yayi sai ajje wayar yayi da niyyar gobe zai bawa Chiroma asan yanda za'ayi a cire masa scurity ɗin jiki.
Nikam tunda na koma ɗaki nake cikin nishaɗi wanda na rasa na menene fushin da Fu'ad yayi yatabbatarmin da har yanzu yana sona saidai niɗin ina sonsa har yanzu tambayar danaiwa zuciyata kenan inma ina sonsa ina zankai soyayyar Nurein anya inna juya masa baya banci amanarsa ba, amma to Fu'ad har yanzu bayada aure ko yanada shi kilama bayan mata harda yara, shuru nayi tareda jan uban tagumi anan har Ameera ta shugo ta sameni,wayar Mami ce a hanunta ta ce
"Anty Game fa nake amma Nurein sai kira yake Mami tace nakawo maki ina kika saka wayarki?" amsar wayar nayi na kirasa tambayar daya faramin
"Ina wayarki?"maine tsakaninki da Turaki Fu'ad an tabbatarmin shine yazo gunki yau"
Murmushi nayi inabin wayar da kallo nace "Wayata ta faɗa ruwa, Fu'ad kuma banida wata alaka da shi a yanzu kawai yazo gaisuwar abokinsa ne"
"Abaya akwai wata alakar kenan?" ya tambayeni ransa ɓace bai jira amsata ba yaci gaba da magana "Su'ad gaskiyya bazan laminci ganinki da wani ba kibani dama kawai na turo manya na indai da gaske kike sona kuma zaki aure ni"
"Amma kasan tsakanina dakai ba yaudara ko?"
"Ki tabbatarmin da hakan ta hanyar bani izinin turowa gidanku a saka mana rana"
"Naji to na amince ka turo ɗin" kashe wayar yayi tareda mikewa zuwa ciki sashin Abbansa yasan yanzu acan zai tadda Mamansa, ilai kuwa kamar yanda yazata ɗin tana sashin suna tareda Abba sunacin abinci saida yajira suka gama kafin yafara magana
"Abba daman akwai wacce nake zuwa wajanta to sai akace na turo manya shine nace bari na gaya maka"
Mama ta kama baki alamar mamaki tace "Ikon Allah daman wai kanada budurwa Nurein amma baka taɓa zancanta ba dani harna fara magana da innarku saude a haɗaka da Halima ɗiyarta wace wannan kuwa"
"Ma'ma Su'ad sunanta yar kawarki Mami" mug ɗin hannunta datake shan yoghourt ne ya suɓuce ya faɗi tana kallonsa da mamaki
"Yanzu Nurein duk yammatan dake garin nan karasa wazaka aura sai bazawara kana saurayinka" mur yasha kamar bai taɓa dariya ba yana kalon Abbansa dayai shuru yana kallonsu
"Abba ai auran bazawara ba haramun bane ko?" yatambayi Abban nasa
"Hakane Nurein ba haramun bane sunna ce ma, nayi farin ciki da faruwar hakan gobe zan yiwa Alhaji islama'il magana sai suje"
"Yauwa Abba na gode Allah ya kara girma"
"Kai saurareni kajini da kyau, na rantse da Allah ko bayan raina ka auri yarinyar nan ban yafe ba! bandama rigima irintaka ina kai ina ita shekara nawa ka bata yarinyar ma da'ake zargin ita ta kashe mijinta..."kinga ya isheki haka kai Nurein jeka ciki" Abba ta inda yake shuga bata nan yake futa ba tas ya wanke maman ya tashi ya shuge ɗakinsa, itako kwafa tayi ta koma nata ɗakin tana zagayan neman mafuta.
Chiroma da computer ɗinsa yai amfani ya cire tsaron dake cikin wayar Su'ad yabawa Turaki, ahankali yake duba wayar harya shugo wajan sakonni sosai yasha mamakin irin zafafan sakonni da Nurein ke aikowa da Su'ad itama bata sanya wajan maida masa da martani, kansa yaji ya sara masa tareda wani irin bugawa da kirjinsa yayi har saida ya dafe wajan, duk Chiroma yana kallonsa baice komaiba dan yanada labarin soyayyar sa da Fu'ad, wanka Fu'ad yashuga ya futo ya shirya cikin bakar jallabiya mai gajeran hannu ya nufi sashin Umma, yanda yake tafiya cikin sanyin jiki yasa Umma take kallonsa da tausayawa harya zauna kujerar kusada ita yana gaidata
"Al'ameen ashe abokinka Allah yai masa rasuwa ɗazu Chiroma ke gayamin daya shugo nan Allah yai masa rahma"
"Ameen Umma yanzuma zuwa nayi nace a shirya Baby Su'ad zamuje kano dana ce sai friday zan shuga saboda case ɗin waɗanda suka kashe sa, amma bazan iya bari har sai zuwa juma'a ba"
"Ok tana ciki tareda Juhaina inagama tai mata wanka tun ɗazu" mikewa yayi ya shuga ɗakin Juhaina, tana zaune gefan gado kusada ita Baby Su'ad ce tana wasa da teddy da sallama ya shuga ɗakin ya zauna saman kujera yana kallon Juhaina datai kasa da kanta, da gudu Baby Su'ad tazo ta faɗa jikinsa ya rungumeta yana kallon Juhaina yace
"ɗago ki kalleni magana zamuyi ta fahimta, batun yau ba nasan kina sona ajiya naso na faranta maki ta hanyar auranki amma wani dalili mai karfi ya gifta wanda yasa na fasa, nasan kinsan labarin Su'ad da irin son danake mata jiya naje garinsu na samu mijinta ya rasu, zan maye gurbinsa zan auri Su'ad a wannan karan insha Allah ina sonta! wani irin so nake mata wanda bantaɓa yiwa wata ɗiya mace ba a duniya son danake mata yasa bazan iya haɗata dake ba, Baraka ma bansan yanda zanyi da'ita ba! idan kinada wani dayake sonki ki basa dama yafuto idan kuma babu ina neman alfarmar ki karɓi tayin soyayyar da Chiroma yai maki"
Da sauri ta ɗago tana kallon Fu'ad har sannan idanunta na zubda hawaye tace "Shi kenan na hakura dakai amma kasani zuciyata tana sonka! nabaka zaɓi ka zaɓarmin Chiroma ko Abdallah ɗan sarkin gombe"
Shuru yayi yana nazari kana ya ce "Ke wanne yafi kyanta maki arai ke zaki zauna da abinki bani zan zauna maki ba tayaya zan maki zaɓi"
"Nazaɓi Abdallah inaso nai naisa dakai bazan iya auran Chiroma ba saboda nasan ko yaushe kuna tare zan rinka ganinka akai akai wanda hakan zai iya haifar min da matsala"
"Shi kenan zanyiwa mai martaba magana ki faɗawa Abdallah ɗin yaturo a tsaida rana kawai" mikewa yayi ya futa, Juhaina tabi bayansa da kallo yana futa ta kifa kan gadon ta fashe da kuka, shi kenan Su'ad ta rusa mata burinta, batajin zata taɓa son yarinyar nan da yaya Turaki ke matuwar so sai tayi duk wani abu datasan zai bakanta mata rai a duk ranar data shigo gidan...
07039793439
[6/11, 9:46 AM] maman sauban: 🌹 *KUKAN ZUCIYA*🌹
Story and writting by
Mamie Yusuf Daboo🥰
☀️ *First Class Writer Assosuciasion*☀️
Home Of Qualities And Trusted Writer's Of Tha Nation
MARUBUCIYAR
HALIN RAYUWA
SOYAYYA DA ZUMUNTA
SANYIN IDANIYA
AIMANAH
YANAYIN RAYUWA
AND NOW KUKAN ZUCIYA
27&28
Ashe batada rabon auran Turaki ta leko ta koma yayi mata😰kuka take sosai har Umma ta shugo ta sameta, faɗa tai mata sosai tariga tasan son datakewa Turaki.
Shi kuwa a nasa ɓangaran shirinsa yake hankali kwance yau jinsa yake cikin wani irin nishaɗi wanda yajima baijisa a cikiba gefe kuma ga kewar Fahad datake damunsa, a haka yagama shirinsa cikin bakin materi'al mai ɗigon fari, ya kafa hula zanna bukar wacce aka ɗinkata da bakin zare sosai shugar tai masa kyau yasha naɗin rawani baki, cikin kwanciyar hankali da nutsuwa yake tuka motarsa Baby Su'ad na zaune gefansa tana shan ice cream ɗin daya sai mata a hanya, surutu take masa shi sam hankalinsa ba'a kanta yake ba yanaga Su'ad hangota yake da tunanin yanda zasu kaya a karo na biyu shin zata amshi soyayyarsa ko zata ki, a yanda ya fahimceta jiya kamar ta manta da shi Nurein yake ko wa shine a gabanta, tabbas a wannan karon jiyake komai zai faru saidai yafuru amma bazai taɓa bari ta kuɓuce masa a wannan karon ba.
Yau tun safe banida aikinyi sai barci tun goma na safe danai break nasake kwanciya saboda gidan ba kowa saini kaɗai sai hanne mai aikin gidanmu, ina sanye cikin kayan barci dogon wando da riga iya cinya sai hula dana saka akaina barci make sosai sonake na huta kafin huɗu na yamma na shiga shagonmu yau Mami ce acan nasan kuma zuwa yamma zata dawo ni na karɓeta wajan ba laifi sosai muke samun costomer masu zuwa gyaran gashi wasu kuma kunshi ko kitso dan wajan ba abinda bamayi harda kwalliyar amare.
Cikin barci naji ana dukan kofata a hankali, buɗe idona na kalli agogo 11:45 am dirowa nayi daga kan gadon ina turo baki da jin haushin wacce ke bugomin kofa ta katsemin barcina mai daɗi nasanma hanne ce, hakan yasa na buɗe kofar idanuna rufe nake magana ina mika da'alamar barcin bai isheni ba
"Dan Allah hanne maine haka ina barci na mai daɗi harda mafarki kikazo kika tasheni" nakarasa faɗe ina mika tareda buɗe ido zaro idanu nayi😳 ina komawa da baya ganin wanda ke tsaye a bakin kofar cikeda mamaki na ce
"Fu'ad lafiya da safiyar nan?" da gudu wata kyakkyawar baby tazo tarikeni cikin muryarsu ta yara tace "momma kicewa Papi ya maidani wajan Nani na nidai banason nan" rungume yarinyar nayi koba tambaya kamanninta kaɗai sun tabbatar minda yar Fu'ad ce ɗagowa nayi ina kallonsa naga yanda ya kafeni da idanunsa kallona yake bako kiftawa, da sauri na kalli jikina kama hannun yarinyar nayi muka koma cikin ɗakina, nauyayyar ajjiyar zuciya ya sauke ya juya ya koma main falo ya zauna.
Ina shuga ɗaki wanka na faɗa agurguje na futo na bar Baby ita kaɗai cream kawai na murza na zura doguwar riga na tareda hijab na ɗauki Baby muka futo, sosai ta lafe ajikina na ɗago fuskarta ina mata murmushi na ce
"Ya sunanki?"
"Aminatu Su'ad Ameen" lumshe idanuna nayi sakamakon wani daɗi daya ziyarce ni ko tantama babu Fu'ad sunana ya sakawa yarsa.
Wani abu naji yatokaremin a kirji wanda babu ko tantama nasan kishine kenan wata ya aura bayan mun rabo, ashe daman zai iya auren wata inba niba, hamdala nayi a zuciyata tunawa da nayi yanda narinka masa addu'ar Allah yabasa wacce tafini kila Allah ne ya amsa addu'ata yabasa wata, saida na zauna kujerar nesa dashi kaɗan na ɗora Baby a kan cinyata sannan na kwalawa Hanne kira takozo da saurinta
"Hanne kawomin abinci na bawa Baby na tasha hanya ki haɗomin da yoghourt bamai sanyi sosai ba"Baby na ai zakisha yoghourt ko?" na faɗa ina kallon fuskar Baby Su'ad
"Kin manta dani ne?"
"Maizan maka to kaje matarka ta baka" nafaɗi haka ina shafa kan Baby da naji ta shuga raina sosai jinta nake kamar nina haifeta, wasu hawaye suka zubomin dana tuna da tunifa nizan haifi yarinyar nan, da'ace Uncle yanada lafiya da tuni nima kila na haifi kamar wannan,
"Subhanalla wannan hawayan fa, nifa ba kuka nazo kiminba zuwa nayi mu dai daita kanmu sonake na aureki nan bada jimawa ba, Su'ad kamar yanda kika sani abaya haka yake har yanzu soyayyarki tana nan cikin zuciyata"
"Dakata Fu'ad kamanta duk wata soyayya da mukai dakai abaya yanzu babu ita a zuciyata bana sonka bazan iya auranka ba alhalin kanada wata matar wacce nasan ita kafara so kafinni"
"Kema kinsan ba wacce nakeso nan duniya inba keba, kalli Baby Su'ad dake hannunki kawai zai tabbatar maki da kaunar danake maki, dan Allah ki ajje batun wata matata kizo mu sasanta kanmu muyi aure shine burinmu"
Wallahi kaji na rantse bazan aureka ba, tuni na samu wanda nakeso kuma zan aura bazan taɓa yaudararsa ba" ina gama faɗin haka na saɓa Baby a kafaɗa na wuce danning da'ita nabarsa nan zaune, na kula ba karamin haushi yaji ba nan yabarmin Su'ad yai tafiyarsa nayi zaton zai dawo ya ɗakketa amma har yamma shuru harsu Mami suka dawo suna tambayata ina na sami yarinya nagaya masu yar Fu'ad ce.
Fu'ad afusace yabar garin yanajin wani bakin ciki dayazo ya tokare masa a kirji harshi Su'ad zata kalla ta ce bazata aure shi ba, bayan ɗimbin soyayyar dasukayi abaya tun a hanya yafara jin zazzaɓi zazzaɓi da wani ciwon kai da kyar ya karasa gida, wasa wasa saiga ciwo ya kwantar dashi wani irin Zazzaɓi yake mai zafi da ciwon kai mai tsanani, shi kaɗai yake jinyarsa a ɗaki ko mutanan gida basu san bayada lafiya ba sai ranar da Baraka suka sauka a kasar itada Usman da matarsa, gidan mai martaba suka sauka Umma tai mata izinin shuga sashin Fu'ad ɗin bayan taci abinci ta ɗan huta.
Yana kwance lamo kan gado ta shugo ɗakin da sallama, ɗago kai kurum yayi yana kallonta baice mata komaiba yamaida kansa ya kwantar saman fulo, da sauri ta zauna kusa dashi ta taɓa jikinsa taji zafi zau gaba ɗaya ruɗewa tayi
"Abban Su'ad bakada lafiya daman kake zaune kai ɗaya a ɗaki" batajira cewarsa ba ta futa da sauri zuwa sashin Umma ta sanar mata, tare suka dawo ciki hankali tashe Umma ta kira sarkin mota Usman shiya ruko Fu'ad saboda gaba ɗaya jikinsa ya saki bayada wani kuzari, yanda kirjinsa ke bugawa yafi komai ɗaga masu hankali.
Baby Su'ad tana wajena yau kwannanta huɗu kenan mun shaku sosai kasancewar batada wuyar sabo, kullum tanamin zancan Papi zai zo yaɗauketa, dariya nake mata nace kin gaji da zama dani saita girgiza kai alamar a'a, tun ina zuba idanun ganin Fu'ad har nasoma fargabar maiya hanasa dawowa duk da daman na lura ba karamin kular dashi nayi ba, har sannan ba waya a hannuna sau tari data Mami nake amfani data tambayeni ina tawa ce mata nayi a makaranta ta faɗi ban ganta ba, yau satin Su'ad ɗaya a gidanmu tunda ta tashi take kuka ita wajan Papi zata ita nakaita wajan Papinta, jin kukan yayi yawa yasa Mami tace na shirya na maidata garinsu da mamaki nake kallonta na ce
"Mami ni ina nasan wani garin su inma nasa garin nasan gidanne?"
"Ga Shareef nan yana gari ki shirya ya kaiku" ba yanda nayi haka na shiryawa Baby kayanta dana sai mata da tarkacan kayan wasanta, muka doshi garin su Fu'ad tunda muka ɗauki hanya gabana yake faɗuwa haka kurum nakeji ajikina kamar akwai abinda yasami Fu'ad shiya hanasa zuwa ko kuma fushi yayi dani, Allah yasani har yanzu ina son Fu'ad amma banajin zan iya auransa saboda yanada mata son danake masa yasa bazan iya zama dashi yanada wata matar ba,