Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
2 / 5
babanta ne ya fadu mata a rai ita kuma Amal sai ta zata kwaikwayonta take ta tashi ta dawo kusa da ita, umma ce tayi mata signal da ta ja ta toilet ai kuwa akayi saa ta bita. Ju dai taga ikon Allah don Amal ki tayi kowa ya taba ta karshe dai ita ta gyara mata jiki. Tun daga ranar wankin kashi da fitsarin Amal ya dawo gareta harda wanka domin duk wanda ya taba ta ba Ju ba to zata yini ta kwana kuka. A hankali Amal ta zama kamar yarinya karama Rayyan kam ra rabu da faraa tun ranar da ta fara ciwon don gani yake laifinsa ne. Malamai kam suna ta aikin magani da addua amma dama ciwo ke shiga farat daya sauki sai a hankali gashi aljanun da ake tunani sune a kanta sunki magana ma. Ranar da Ju zata tafi da sassafe umma ta buga kofar gidan mami don kwana tayi tunani. Lanti mai aiki ce ta bude mata sannan ta kira Mami. Bayan sun gaisa tace Asiya ina Abban yara shawara na kawo mana baki daya. Abba ya zauna shima sun gaisa da Umma tace to ni jiya hankalina ya tashi kan maganar komawar Juwairiyya gida. Ni dai indai da hali ku barni na roki Mariya ta barta a nan kafin Amal ta sami sauki. Kuna ganin irin artabun da ake da ita idan wani ya taba ta ba yar uwar ba. Na fadawa Baba yace muyi shawara tsakaninmu. Abba ya kalli Mami yace ya kika gani? Nasan yarinyar nan kawaici kawai tayi mana akan babanta. Shin Ju zata yarda ta zauna a kano kuwa??? 💕 JUWAIRIYYA 💞 4 Ju tayi mamaki da taje yiwa umma sallama tace mata jiki mota ai tare zamu tafi. Taje ta yiwa Hajja ma sallama harda kukanta, anyi sa'a Amal na bacci bata ga fitarsu ba. Da yake tafiyar ba mai nisa bace basu dade ba suka isa ita dai Ju sai tunani take kala kala game da dalilin biyota da Umma tayi. Motar na tsayawa Ju ta ruga da gudu ta shiga gida ba ko sallama dakin babanta ta nufa ta fada masa a jiki sai kuka. Mama ta fito ta tari Umma duk suka tsaya kallon ikon Allah yadda Ju ta shige jikin babanta tana ta watso masa tambayoyi. Mama tace Zuwaira ba gaisuwa ai kuwa ta bata fuska Allah ni mama ba sunana zuwaira ba, Umma tayi murmushi tace yo tunda ita kin share ta ai dole tace miki zuwaira. Baba, Mama da Umma ne zaune a falo sai Ju a kasan kujerar da Baba yake zaune umma tace nasan dai Asiya tayi muku bayani tun kafin mu taho a waya amma duk da haka ina son jin ta bakinku. Mama tace Juwairiyya kalli can tana juyawa sai taga akwatinta ne sai wata ghana must go da ledar viva tace Mama kayan meye wannan. Mama tace mata munyi shawara da su Yaya akan zaki koma kano kafin Allah Yasa Amal taji sauki. Duk munsan yadda tafi yarda dake kuma ko dazu kafin ku iso da muka yi waya ina jin ihunta sun kasa bata abinci. Baba ya mika hannu yana laluben Ju sai ta rike hannun yace baki taba yi mun gardama ba idan ba akan dambe ba don Allah kada ki tashi hankali akan tafiyar nan. Umma tace ni muna komawa zan bayar da kudi a siyo miki waya ki rinka gaisawa da Baba kullum. ************************* A haka dai aka lallaba Ju suka dawo kano tare da alkawarin zaa saka ta makaranta ranar litinin don ta cigaba da karatun ta. Mami ba karamin farin ciki tayi ba da yadda Ju ta kwantar da hankalinta bayan sun dawo ita ma Umma ta cika alkawari ta bata sabuwar waya karama tace idan aka koma makaranta tayi kokari zata canja mata da mai kyau. A falon Hajja su Ju suna zaune da Yasmin sai ga Yaya Sagir da Yaya Rayyan sun shigo da ledoji masu dauke da note books,text books da sauran kayan makaranta na kannensu. Rayyan ya kalli Ju da take fama da Amal akan ledar pure water yace ke aji nawa zaki shiga ne. Tace SS 3 ya sake cewa science class ko arts? Tace science. Hajja tace wace makarantar za a kaita. Rayyan yace ta su Fauza, ya dubi yan matan yace kuzo ku ware books dinku ku bar bata sauran notebooks din gobe ku shirya da wuri don ni zan kaiku saboda zan biya kudin nata books din. Abdul autan su Amal yace wai ke Ju nufinki aji daya zamu shiga tace kaima ka kusa candy yaya Abdul? Yace ke fa yar kauye ce meye wani candy ana zaune kalau, graduation ake cewa. Ta murguda baki tace to kawai ka gyara min mana sai kace min yar kauye, ai wudil ba kauye bane. kowa yayi dariya banda Rayyan wanda a halin yanzu damuwarsa tafi farincikin sa yawa saboda ciwon Amal. Magani kullum nema ake kuma Alhamdulillah ta rage yawan kukan nan sai dai behaviours din yara. Mami ta kawo kudin da Abba ya bata dubu dari ta bawa Rayyan lokacin da suke shirin tafiya makaranta tace gashi babban yaya ku tafi da wannan idan ana bukatar kari sai ka fada min. Yace haba Mami ai tunda dalilin Amal aka dawo da ita kano ni zan biya kudin. A mota kannen nasa suka same shi Fauza mayyar zaman gaba tayi sauri ta shiga sai su Yasmin su uku a baya Ju a tsakiyarsu ita da Abdul. Ya Rayyan yace meye haka zama kusa da namiji tace to ba wa na bane. Yace da Abdul get out ko kunya baka ji zama cikin mata. Ke fauza fita ki koma baya kuma daga yau ko driver ne zai kaiku kada na sake ganinka a baya. Suna fara tafiya Fauza tace Ju wallahi ki dena magana idan Ya Rayyan nayi don baya so. Tace to Allah Ya bani iko. An zaunar da Ju a wani empty class da papers biyar da ake son yi mata gwaji ko ta cancanci class din da zaa sa ta na maths, english, biology, physics da chemistry. To fa nan ake yinta Ju dai ba turanci sosai saboda yanayin lalacewar govt schools kafin kace meye wannan dai ta gama maths da physics don tana son lissafi sauran papers din kuma abinda ta fahimta tayi wanda bata gane ba tayi kwabarta. Ko da ta gama wata malama ce tazo ta mayar da ita office din principal inda Ya Rayyan yake jiranta. Principal din Mr Ayodele yace da Rayyan ya tafi da ita gida gobe su dawo bayan anyi marking. Rayyan yayi godiya yace ta taso su tafi. Washegari Ya Rayyan ya koma school din shi kadai don principal din yayi masa waya yace ya barta a gida yazo shi kadai. Result din Ju ya gani taci maths da physics ba laifin amma sauran dai ba bayani tun ba English ba. Ko da rashin cin jarabawar bai masa dadi ba wani sentence daya karanta ya mugun bashi dariya ta rubuta ( My ankle is the bery wickedest man in wudil). A zuciyarsa yace lallai yarinyar nan ta tsani wannan kawun nata. Ya ce da Mr Ayodele wane class yake jin zaa sata don ta sami ilimi mai kyau. Mr Ayodele yace idan zai yarda zaa mayar da ita SS1. Ya Rayyan yace shi yafi son JS 3 don yana son a gyara mata turanci yadda zata fahimci karatu sosai. Sai da ya karbo duk books din da zata bukata da uniform ya biya school fees sannan ya tafi wurin aiki. Bayan magrib Rayyan ya sami Mami yayi mata bayani tace JS 3 Rayyan to wallahi kai da kanwarka ni ba ruwana ta fada tana dariya. Ju da ta shiga daki da tulin littafai zata rubuta suna a jiki sai taga duk ansa JS 3 a jiki ta fito tace Yaya ai duk na JS3 ne Allah Yasa ban riga nasa suna ba sai ka mayar musu. Yayi wani dan murmushi yace ai a nan za a saka ki sunce baki iya turanci ba. Tabdi wannan ai yafi karfin repeating Ju mai shirin candy bana an maka mata demotion. 💕 JUWAIRIYYA 💞 5 Kan uban can shine abinda ya fara fitowa daga bakin Ju sannan tace wallahi bazan yarda ba Mami ce dai ta doke bakin tace haba Juwairiyya kullum sai an miki fadan ki dena magana idan babba nayi . Tace Mami kiyi hakuri kinji wai JS 3 zai kaini. Ajin da Yasmin take fa kenan. Rayyan dai yau dariyar mugunta yake ji ya juya zai fita sai ya dawo yace Allah idan kika sake zagi a gidan nan ranki sai ya baci. Abin takaici baya karewa don Abdul tsokanar Ju ya rinka yi yana kiranta candy. Ranar da kuka tayi bacci. Da gari ya waye taje ta gaishe da Hajja da Umma sannan ta bawa Amal abinci suka tafi makaranta. Abin mamaki Abdul bai kara tsokanarta ba su Fauza da take tsammanin zasu yi suma kowa bakinsa kanin kafarsa. Ashe Rayyan yayi musu warning duk wanda yayi mata dariya zai gamu dashi. A makaranta Ju taji dadi sosai da taga ajinsu akwai matan da suka fita tsaho banda maza ma. Dama ita ba wani tsaho gareta ba jikinta madaidaici ba rama ba kiba. Tana da kyau daidai ga dan dimple a kumatunta na dama. A ranar farko yan ajinsu sun fahimci Ju ta iya mmaths don ba su da yawa a ajin kuma malaman suna involving dinsu a ayyukan da suke. A fannin magana dai tunda akayi mata dariya bata sake ba. Su kuma da malami ya shigo ana tambaya sai suce Ju ta amsa yadda suka ji Yasmin na kiranta. Satin ta daya da fara zuwa duk ta zama a takure saboda yadda yan ajinsu ke damunta har wasu students dinma. Yasmin da abin ya isheta ta fadawa Ya Rayyan wanda kullum yake nuna halin ko in kula a gabanta. Har school din yaje ya sami principal yace idan bazai tsawatar da students akan kanwarsa ba zai canja mata school. Ju bata san me yake faruwa ba taga canji sosai don a assembly Mr Ayodele yace zai dau mataki akan masu takurawa new students. *********************** Abu kamar wasa term ya kusa karewa kuma su Mami suna kokari every two weeks ana kaita wudil taga iyayenta. Batun ciwon Amal kam ta rage kuka amma har yanzu bata iya yiwa kanta komai. Ta dai iya kiran Ju kamar ita ta rada mata. Kowa a gidan yana yaba yadda Ju take kokari wurin kula da Amal. Yaya Sagir kuma ya zama mai koya mata assignment don Ju ta dage sai ta iya turanci. Wata rana tana zaune suna lesson da Yaya Sagir ita da Yasmin sai ga Rayyan ya shigo falon ya zauna yana shan tea. Tana ganinsa ta dena karatun da take Ya sagir yace mata cigaba mana ta dan bata rai ta cigaba da cewa ( wicked, wickeder , wickedest) nan take Rayyan saboda kokarin gintse dariya ya kware da tea. Sagir yace wallahi zamu baku mamaki idan muka fara tsara ku da grammer. Karshen term Ju tayi ta 23 cikin mutum 25. Tana zuwa gida ta tarar da Rayyan sun dawo daga asibiti da Amal Fauza cikin murna tace Yaya kaga result dina ta 4 nayi yace kinyi kokari akwai kyauta ya kalli sauran ku fa. Kowa yayi kokari dai banda Ju wadda yace zai sa a maida ta JS 1 idan ta dauki sama da ta 20 next term. ********************** Alhamdulillah Ju ta gama JS 3 lafiya don result dinta na karshe ta 19 tayi. Rayyan yayi farin ciki da hakan duk da bai nuna mata ba. Sai dai yadda ya fuskanta tafi kokari a fannin lissafi gashi bata yi kokori sosai ba ance bazaa bata science ba. Ya dai roki alfarma idan an dawo hutu s sake mata exam a eng don yanzu da kanshi zai koya mata. Mami ba karamin jin dadin yadda ake Ju ke kula da Amal take ba. Idan tana period ma da kanta take canja pad. Allah kadai zai saka ma yarinyar nan abinda take yawan fada kenan. Wani malami aka samu irin masu aiki tsakani da Allah Ya tsaya sosai da addua cikin ikon Allah aljanin dake kan Amal yayi magana yace turo shi akayi amma yaki fadan ko waye. idan akayi ruqiya sai ya fita malam na tafiya ya dawo yace shi kawai a kwance auren. Haka dai ake fama da adduar Allah Ya kawo sauki. Rayyan ya aika yafi sau uku Ju tazo lesson taki don ita tsoronsa ma take yanzu sai da ya hada ta da Abba ta fara zuwa. Idan yana yi mata magana ba amsa idan yayi fada tayi kuka. Daya ga itama akwai taurin kai sai ya rabu da ita da sharadin idan akayi mata exam bata ci ba zaisa a mayar da ita js1. Ju da murna tace ta yarda. Tun daga lokacin kullum Ju tana karatu da duba dictionary bata tashi idan ba sallah ko kula da wani abin da Amal ke so ba. a dakin Hajja dama take karatun tare da Amal tana yan wasaninta. Sati biyu da fara karatun nan na Ju suna daki da Amal cikinta ya wani murda saboda bata wani cin abinci kamar wasa da farko ta share sai gashi ya kara da ciwo sosai tana ta yiwa Amal alama da ta kira wani don ta kasa tashi amma ita bata gane ba sai ma ta kwanta a kasa yadda Ju tayi tana kwaikwayonta. Hajja ce taji shirun nasu yayi yawa ta tashi ta bude kofar dakin abinda ta gani ne ya sata salati da karfi har Umma dake falon ta yi saurin tasowa. Ju ce kwance a kasa sumammiya kamar babu rai tare da ita Yau kuma me ya sami Ju din Baba Idris. 💕 JUWAIRIYYA 💞 7 A falo Ju ta hadu da Mami da Ya Sagir suna hira. Mami tace wa ya taba min ke naga kina ta kumbura bakin nan na tsiwa. Ju tace Ya Rayyan ne ya koro ni, Mami a gabansa fa ya hauni da fada. Ya Sagir da bai gane me akeyi ba yace gaban wa am confused. Ya Rayyan daya shigo a lokacin yace gaban Lawal mai shago mana. Cikin fushi ya cigaba da kallon Ju yace wai ni waye ma ya baki izinin fita. Ya Sagir yace Mami Ju zance take yi ban sani ba. Mami taga yara zasu mata taron dangi tace kwana hudu kenan yana turowa kiranta ina hanawa dazu Hajja tace kada na sake hanata fita don dole tayi aure wata rana. Ya Sagir yace to ni zan mata magana ai su bata gama secondary ba. Ya Rayyan kwance akan gado yana kallon hotunan Amal cikin zuciyarsa yana dada tausayin halin data shiga dalilin auren su amma abinda yafi damunsa yadda Ju ke neman zama centre of his thoughts. Wai shine har yake fadawa wani shine mijin yarinyar nan mai tsiwa. Ya tashi ya dauko papers din jarabawar da aka yi mata farkon shigarta makaranta ya sha dariya. Karshe dai alwala yayi ya sallah tare dadewa yana addua musamman ga matarsa Amal. Lokacin WAEC ya matso su Ju an maida hankali ga karatu don ita bata da burin da ya wuce ta zama likitan ido ta taimakawa babanta. Ita da Yasmin sun dage da karatu cikin ikon Allah sunyi sun gama lafiya. Result din Jamb ne ya fara fitowa ita tana da 214 Yasmin kuma 221. Kowa ya tayasu murna. Kanwar Ju ma Nafisa wadda saboda demotion din da akayi mata tare suka gama itama ta sami 187. *********************** Hajja tasa 'ya'yanta maza a gaba tace shawara na ke son kawo muku wadda kuma zancen gaskiya da Umma muka fara yi don ita tazo da maganar. Abba yace Hajja mu ai umarni zaki bamu ba shawara ba. Tace hmm kaji shi bayan ku akan 'ya'yanku sai anbi a hankali. Baba yayi dariya yace to muna sauraronki. Hajja ta gyara zama tace to ba wani abu bane akan yarinyar nan Juwairiyya ne, idan banyi kuskure ba ta kusa cika shekara hudu a gidan nan kuma duk tsahon lokacin nan a kula da yarmu tayi. Baba yace hakane nima kaina ina tunanin me zamuyi mu saka mata da alkhairi. Hajja maida kallonta ga Abba tace Bashir kana ganin zaka yarda Rayyan ya auri juwairiyya? Gaba dayansu basuyi tunanin jin wannan maganar ba. Hajja bata kula da yadda suka razana ba ta cigaba da cewa yarinyar nan taci kashi da fitsarin yayarta ba tare da ta taba bata rai ba. Allah Ya sani ina tausayin Habiba amma kuma har yanzu bata sami lafiya ba. Idan Juwairiyya tayi aure a wani gidan wa zata yarda ya taba ta. Duk kunsan yadda take kuka idan Juwairiyyan ta tafi makaranta. Abba yayi shiru sai kawai hawaye ya digo daga fuskarsa ya kalli dan uwansa yace Yaya abinda Hajja ta fada gaskiya ne. Shi kanshi Rayyan har kunyarsa nake ji ya gina gida ya kasa tarewa kullum sai dai yaje aiki ya dawo ga shekaru na karuwa. Yaya indai ka aminci to ni bani da matsala akan hadin nan. ************************** Kowa ya tashi da tunani a ransa amma Abba tsoronsa daya yadda Mami zata karbi maganar. Kwana biyu yana ta juya zancen a ransa karshe dai ya sami dama da ta kawo masa zancen taga alamun Sagir fa yana son Ju. Abba yace ya fada mata ne tace a'a naga alamu ne dai sai ya fada mata shawarar da Hajja ta kawo. Mami sai kuka wiwi kamar yarinya tace yanzu Abban Sagir haka Amal zata kare rayuwarta? Ni bana kin ya auri Ju domin yata ce amma misali Amal ta warke fa. Ni Asiya na shiga uku Abba yace haba yaushe zaki rinka maganar kin shiga uku bayan kinsan babu tsumi ko dabara idan ba abinda Allah Ya tsara ba. Kada muso kanmu mu cutar da wasu. Ki duba yadda yaron nan hatta da abincin da Amal take ci shi yake siya kuma baya tunanin wani aure ya hakura ya zauna da ita a haka. Kada muyi zalunci saboda son yarmu idan hakan alkhairi ne to muyi fatan Allah Ya tabbatar da faruwar sa. Daren ranar dai Abba da Mami kusan kwana suka yi sallah Allah maji rokon bawa sai Ya sassauta musu al amarin a zukatan su.. ************************* Yau Ju an tashi da farin ciki domin kuwa wudil zata ta kwana biyu. Sai da tazo tafiya da kyar aka rabata da Amal duk suna kuka Ju har waje tana jin muryar Amal tana kiranta. Ya Sagir ne zai kaita dasu Yasmin yan rakiya. Fauza ana exams a buk tana karanta Economics bata sami zuwa ba. Koda ta isa gida murna take taga Yaya Najib sarkin cin zali don ta kwana biyu basu hadu ba saboda yana aiki a kaduna. Ya yi musu gyara a gida harda fenti Ya Ismail kuma yana bautar kasa a Kwara state. Gida dai sai murna ake da zuwan Ju. Washegari abin mamaki sai ga Abba da Baba da wani Kawun su kanin babansu. Bayan sun gaisa da Baba suka gabatar da abinda ya kawo su na son nemarwa Rayyan auren Ju. Baba yace Alhaji Bashir ban tari numfashinka ba amma yaron nan ba shine mijin Amal ba. Abba ya amsa da shine...sai baba yace to don Allah ku bani mintuna kadan ina zuwa. Sandarsa yasa ya shiga cikin gida ya nufi daki tunda yau da gobe tasa yana iya yawoba gidansa. A daki sautin kukan mama yaji yace Mariya me ya faru? Tace yanzu muka gama magana da yaya da kuma Dada akan abinda ya kawo su Alh. Baba yace to me kuka yanke tace ka amince don duk shawarar da suka bani kenan saboda tunda aka fara maganar auren nan idan ma munki to zasu nema masa wata karshenta ya rabu da Amal din. Kuka yaci karfinta tace ko kadan ba irin rayuwar danake wa Juwairiyya fata ba kenan amma wai mahaifiyarsa ce ta kawo shawarar kada mu aurar da ita a rabasu. Ta share hawaye tace kuna kasan ina tausayawa Yaya kafin najib ya kawo karfi duk dawainiyarsu ta karatu ta dauke mana. Fatana Allah Yasa abin nan ya kara mana zumunci. Yace amin nagode Mariya da dukkan abinda kuke yi min ke da yar uwarki. Baba ya fita ya koma falon waje yace da bakinsa yaushe kuke son a daura auren kunga ni banyi wani shiri ba ko zaku bani lokaci. Abba yace haba Alhaji Idris juwairiyya ai yata ce don nafi ka morarta idan ka amince a yau zas daura auren. Bidaya Baba ya kira yace ta kira masa Najib da yazo ya tura shi kiran mal Yau da Liman da wasu yan uwansu da abokan arziki. Bayan sallar laasar aka daura auren Rayyan Umar Tafida wanda wurin aikinsu aka tura shi Germany na sati biyu da Juwairiyya Idris Muhammad wadda ke daki suna hira da su Nafisa bata san me yake faruwa ba. Akwai rigima a gaba daga dukkan alamu 💕 JUWAIRIYYA 💞 6 Umma waya ta dauka ta kira Baba ta gaya masa yanayin data tarar da Ju yace to ta sami daya daga cikin samarin gida ya daga ta a sata a mota su taho yana asibiti. Kafin ta gama wayar Hajja ta kira Mami sun shigo tare da Ya Aliyu kowa a rude. Aliyu na kokarin daga Ju sai ga Rayyan ya shigo yace masa ya matsa shi ya dauko ta kamar wata jaririya ya sata a bayan mota Umma na gaba ita kuma Mami sa Ya Aliyu suka biyo bayansu. A asibitin ma Ya Rayyan bai jira nurses ba ya sake daukan Ju ya shige ciki babansa ya fito daga office tare da Aliyu daya fada masa sun iso ya shiga zai dubata sai wata dr din tace yallabai ka bari naje idan ba kasa zan kira ka don iyaye basa iya duba yaransu sosai. Ba musu ya koma office don ya yarda da ita yace su jira shi a nan reception. Ya Rayyan duk ya kasa zaune ya kasa tsaya ashe duk abinda yake Umma na lura dashi amma bata ce komai ba. Bayan anyiwa Ju allurai ansa mata drip likitan data duba ta ta wuce office din Dr Umar Tafida tace yallabai yarinyar nan fa yunwa ke damunta don idan ta tashi zansa ayi mata test inajin ulcer ma ta kamata. Ya mike da hanzari what did you just say Dr Rufaida? Yarinyar nan fa 'yace a wurina kuma a gida na ma take. Tare suka fito Baba ya hau fada ko suna maltreating din yar mutane don tana kula da tasu. ********************** Sai washegari bayan Ju ta dan dawo hayyacinta Mami ta tambayeta meyasa bata cin abinci tace karatu take kuma ita mntawa take da abincin don kada yaya Rayyan ya mayar da ita js1. Mami dai tayi mata fada sannan ta hada ta da mama da baba a waya suka gaisa. Rayyan ko kadan baiji dadin dalilin da Ju ta bayar ba abin duk ya dame shi harda bawa mami hakuri ya ce bai san zata dauki maganar da gaske ba. Kayan fruits, snacks da sauran kayan kwalama haka ya rinka siyowa kullum yana kawowa Ju bayan kwana uku aka sallameta. Tun daga lokacin kullum ya dawo sai ya tambayi su Yasmin ko taci abinci. Wannan abin ma da yake Umma na kallo tana sake sake a zuci. Ju dai kwalliya ta biya kudin sabulu don kuwa taci jarabawar eng din saboda haka an bata science class. Rayyan ya daukarwa kansa siyo maltina, hollandia da su viju don kannensa su sha ko su tafi dashi makaranta amma Umma da yanzu bata da aiki sai lura da dan nata tasan saboda Ju ya siya. ************************* Kwanci tashi ba wuya a wurin Allah Ju yau sun rubuta exam dinsu ta karshe a SS2. Amma ita farin cikinta biyu ne don kuwa yau zaayi musu walimar sauka a gida Baba da sauran yan gidansu duk zasu zo. Gidan Marigaya Tafida yau a cike yake yayyen Rayyan mata su biyu Yaya Kubra da Ummi suma sunzo da yaransu. Ju dai hankalinta bai kwanta ba sai da taga shigowar yan gidansu. Baba taje ta rungume ta suma kuka. Hajja tace maimakon kiyi murna sai kuka kuma Zuwaira. Ju ta bata rai Hajja nifa ba sunana Zuwaira ba. Nan dai akaje kowa ya zauna ga kawayensu da suka gayyata da malamin da yake musu karatu a gida. Taro yayi albarka su Ju sun sha wani lace mai kyau da Abba ya dinka musu shi kuma Abdul shadda yasa kalar lace din. Kowa da kyautar da ya basu Ya Rayyan kuwa waya duk ya basu mai kyau. Ana cikin taro Amal ta fara tari wanda karshe sai da tayi amai a jikin Ju. Bata ko nuna damuwa ba taja hannunta suka koma cikin gida ta gyara mata jiki. Mami ta kalli yadda yarta ta zama babbar mace lokaci guda har tana kula da wata tayi hamdala domin Juwairiyya ta sa ta fita kunyar yayarta. ************************ Yana shigo da motarsa ya haske musu ido. Ba wasu bane Ju ce da wani dan makotansu daya dage yana sonta. Yauma Mami ce ta takura mata sai ta fita. Rayyan ba karamin bacin rai yaji ba wanda shima baisan dalili ba. Yana fitowa saurayin mai suna Lawal yayi saurin miko masa hannu su gaisa. Rayyan ya wani gintse fuska da kyar ya mika hannu. Lawal yace Alh Rayyan yanzu ni ka zama yayana. Ina fata zaka min kamfen wurin kanwwar taka. Ju kuma irin kunyar nan wa ya kamaka kana zance ta sunkuyar da fuska tace Ya Rayyan sannu da zuwa. Yace daka mata tsawa ke da izinin wa kika fito. Come on get inside. Ta zumbura baki ta shige wannan ai dizgawa ne a gaban saurayi Allah Yasa ma bata fara sonsa ba. Tana tafiya ya juya ga Lawal yace Mal kayi hakuri yarinyar nan tana da miji kada ka sake zuwa nemanta. Lawal cikin mamaki yace yallabai na tambaya tace babu kusan minti 30 da fitowarta babu wanda yace ta koma. Rayyan yace to ni nace don ni ne mijin. Ikon Allah wai dama Rayyan yana son Ju ne??? 💕 JUWAIRIYYA 💞 8 Rayyan tsaye a reception yana ta kallon agogo ya gaji da jiran abokinsa Abbas wanda suka yi alkawarin haduwa a reception din hotel din da akayi musu masauki zasu je shopping domin sun gama abinda ya kawo a germany saura kwana biyu su koma gida nigeria. Da gudu Abbas ya fito daga elevator yana bashi hakuri. Rayyan sanye yake da wani ash din wando da riga light blue kayan sun masa kyau. Fuskar nan tasha gyara don shi baya aske gemu duka yana barin kadan wanda ya hade da gashin bakinsa. Da yake shi fari ne sai gashin yake masa kyau. Suna tafiya Abbas wanda tuni ya kawo kudin auren Fauza yace mu shiga kantin kayan matan can kasan mai hada lefe idonsa idon kayan mata. Rayyan yayi dariya to bana son rashin kunya dai kanwata ce. Dukkansu sunyi siyayya shi Rayyan banda Amal harda kannensa ya hada. Zai je wurin biyan kudi ya hangi wata farar night gown sleeveless wadda bazata wuce gwiwa ba kawai sai yayi imagining Ju a cikinta nan da nan yayi tsaki Abbas yace mutumina lfy. Rayyan wanda hannunsa har ya kai kan rigar yace yarinyar nan is getting under my

Chapter 2 of 5