Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
1 / 5
An dauko wannan littafi daga shafin https://taskarnovels.com.ng ku ziyarci shafin na https://taskarnovels.com.ng domin samun kayatattun littatafan hausa kama daga kan na yake yake dana soyayya Marubuci ko marubuciya zasu iya turo mana da littatafansu mu dora masu a shafinmu kyauta don masoyansu su rika Downloading a online, Sannan marubuta zasu iya turo mana da tarihin rahuwarsu da tarihin rubutunsu, dama sharhin littatafansu don masoyansu su gani kuma su karu da hakan Domin turo mana da littafi ko tarihin rayuwar marubuci ko marubuciya sai ayi mana magana ta whatssap da wannan nambar +2348140419490 A lura dakyau - kyauta muke saka littafi a shafinmu bama amsan ko sisin marubuci, duk wanda ya amshi kudinku da sunanmu babu ruwanmu, Alura dakyau - manazarta bama tura littafi ta private ku dena binmu private kuna neman mu tura maku littafi, duk mai bukatar littafi yaje website namu Alura da kyau - Littatfanmu suna fitowa cikin manhajoji uku ne PDF,TXT da DOC amman munfi amfani da PDF da TXT masu amfani da wayar android ko tablet ko computer zai fi kyau ku riga dauko PDF da DOC Masu amfani da kananan wayoyi java ko mara java TXT zakuna zaba don shine daidai wayarku This hausa novel was uploaded and downloaded from https://taskarnovels.com.ng You can download more hausa novels there Also you can send us your novel to upload it in our website for your fans to download it online It is free we do not charge for uploading novel Also if you are an Author be it online or Non online you can send us your biography including your book summary,commentary and others via this number +2348140419490 its free we do not charge for our services Note that - we do not charge for our services we uploaded novels and posted biography free, any person that collect your money in our name is your fault do not blame us Note that - pls readers stop calling us and be asking us to send you a novels we are not sending novels through whatssap or private our novels is public at any day, any time you can visits our site and download it Note that - our ebooks came as PDF,TXT or DOC format but the popular format are PDF or TXT, those with android or tablet or pc we suggest you to download PDF or DOC those with java phone or non-java phone we recommend you to download TXT This Novel is downloaded from https://taskarnovels.com.ng to download more hausa novels visits our site at www.taskarnovels.com.ng For feedback and support Facebook : https://facebook.com/taskarnovels Twitter : https://twitter.com/taskarnovels Telegram : https://t.me/taskarnovels Copied By HAYATU BABA ZUBAIRU (admin Arewa hausa novels Novels villa Duniyan novels Hayat hausa novels Hausa novels and fashion And Cool novel, makeup and cooking) WHATSAPP NO: +2347039625239 💕 JUWAIRIYYA💞 Zuciyarta cike da fushi tana ta sauri kamar ta tashi sama. Duk wannan saurin tsoronta daya kada Tasi ya shiga gida kafin ta cimmasa. Yau sai ta masa dukan tsiya wallahi don ita bata tsoron ta mutu bare tayi rai. Nafisa ce ta taba ta tace Yaya kinga Tasi chan da abokansa. Kafin ta gama magana yayar tata ta ruga da gudu taci kwalar Tasi cikin fushi tace kai don ubanka me ka fadawa malam dazu a islamiyya. Ya make mata hannu tare da cewa gaskiya na fada masa, ba wani abu yasa kuke makara ba face rike sandar tsohonku da kuke aje bara. Abokansa kuwa sai ihu da dariya suna fadin sai 'ya'yan Idi makaho. Zuciyar mata fa tazo wuya nan ta rufe ido tana kai musu dukan mahaukata. Da Allah Ya bata sa'a ta kama kwalar Tasi sai kokawa ta kachame. Nafisa da Bidaya suna ganin abin ya baci sai gida da gudu. Mama tana kwasar tuwo ta gansu a gigice ta fara fadan yau ma tseren kuka yi ko kamar maza. Bidaya tace Mama Yaya Ju ce suke fada da Tasin Baba Ya'u. Nan take ta saki marar dake hannunta tana kwalawa Ismail kira. Ya fito yace mama naji abinda suka ce muje ki raka ni Bidaya. Akan Tasi ya hango ta tana tula masa kasa a baki yara sun taro ana ta wakar ku casu bamban ku casu. Ismail yayi sauri ya finciko kanwarsa tare da bata kyawawan mari har biyu sannan yaja hannunta gida. A tsakar gida suka riski iyayenta wanda tun kafin su iso ake jiwo kukanta daga soro don ta maru. Mama cikin fushi itama ta damko ta ta fara duka tana fada. Yanzu Juwairiyya bakya jin dadi sai kin dauko min magana ko. Ta cigaba da cewa shekarunki goma sha hudu fa amma bazaki dena dambe da maza ba. Na fada miki ke macece ba namiji ba yayyanki maza ma wallahi basuyi abinda kike ba. Duk wannan abin da ake Juwairiyya bata ce komai ba kukan ma ta dena ganin yadda babanta yake lalube da hannunsa yana kokarin hana mama dukanta. Yace Mariya kiyi hakuri don Allah ki bar dukanta. Juwairiyya ta kama hannun babanta ta zaunar dashi akan tabarma. Yana zama ya lalubi kunnenta yace wai meyasa bakya jin magana. Ta share hawayen idonta tace Baba zaginmu suke harda cewa bara muke raka ka. Wallahi idan zasu zageka sau dubu zan rama sau dubu ai ba tsoronsu nake ba. Ismail yayi saurin doke mata baki wato ana miki fada ke ko gezau bakiyi ba har kina dada maida martani. Baba yace bari dukanta haka. Ya sake rike mata hannu yace Juwairiyya kinsan dai dani da baban Tasi wa da kani ne ko. Ta kada baki tace ai ba babarku daya ba. Mama ta jefa mata harara tace wai baza kiyi shiru ba. Baba ya cigaba da cewa ki rinka hakuri akan duk abinda zasu fada miki ko yan uwanki. Kinga Ismail da yayanku Najib basa kula su, kuma ma ai duk garin nan babu wanda zaice ya taba ganina da kwanon bara. Nan duk 'ya'yansa dake wurin suka yi murmushi saboda yanayin da ya fadi maganar banda mama da ta ce Alhaji kaine kake sa yaran nan basa daukar maganarka da girma saboda kana musu wasa. Yace to kowa ya kallo ni nan suna kallon shi kuwa ya sha kunu a dole ya bata rai suka sake yin murmushi Ju kuwa har sautin dariyarta ake ji. Yace don Allah ku dena biye musu ko me zasu fada. Lalurar makanta jarabawa ce daga Allah. Da ina da idona rangadau farare kal kamar na Najib da Ismail. Kuyi hakuri yan mata bansan yaya naku suke ba. Amma dai abinda nake so ku gane shine ni bana bakin ciki da niimar da Allah Yayi min da kuma cikin ikon Sa yanzu ma da lalurar tazo bamu kasance cikin kaskanci ba. Zai cigaba da magana yaji kiran sallah sai yace a tashi ayi alwala Allah Yayi muku albarka. Ju ta debo wa babanta ruwa ta zuba masa yayi alwala ismail yayi masa jagora zuwa masallaci ********************** Bayan kwana biyu da fadan Ju da Tasi tana dawowa daga makarantar boko taci karo dashi a kwanar gidan liman shima ya taso da yan korarsa a baya Lado da Haladu. Suka fara binta da sauri dama yaci alwashin rama abinda tayi masa a rannan duk da rashin mutumcin da babarsa taje tayiwa maman su Ju har gida da wanda babansa yayiwa babanta a kofar gida. Ju dai ko a jikinta data gansu duk da cewar ita kadai ce yau abokiyar tafiyar tata Madina bata je makaranta ba saboda ranar hutu ce garesu yan aji biyar an gama jarabawar kwalifayin zasu dan kwana biyu a gida kafin sakamako ya fito. Tasi da abokansa suka samu suka tare mata hanya yace ke ubanwa kika zubawa kasa a baki shekaranjiya?Tace uhmm wai dani kake? Yace hade girar sama da kasa ya sake maimata tambayarsa. Tace to ubanka na zubawa mai jajayen hakora. Tasi yace yarinya yau kin gama yawo. Ya cakume ta zasu fara kokawa ta aje jakarta a gefe ta Allah Ya gani bani na takali fadan nan ba.tana fadin haka ta kai masa duka a ciki nan fa maxa uku suka far mata suna dukanta amma bakinta yaki mutuwa sai masifa take tana dukansu itama. Liman ne ya fito yaga abinda ke faruwa yayi musu tsawa suka tsere. Ju kuwa yau an mata taron dangi hijabinta ya yage har kasa ga wuyan riga shima ya yage har kusan cibiyarta. Gashi ita yarinya ce mai garin jiki kirginta ya kusa gama cika. sai da liman yace wuce ki tafi gida ta kula da yadda kayanta suka yi budu budu ga yagewa. Yau tasan ta gama yawo a wurin mama. ********************** Ju ta bayan gidansu ta zaga ta taka wani kututturen itace ta haura katanga. Tana dira bidaya tana watsa shara nan take ta kwala ihu. Mama ce tazo da gudu tana tambayar lafiya.itama turus tayi yadda ba don jininta bace itama bata gane ju ba. Bidaya kuwa runtse ido tayi tana fadin mama aljani. Mama kam ko baa fada ba tasan yau ma yar tata tayi sanaar da ta saba. Batare da cewa komai ba ta koma da baya taje ta tada Najib wanda bai dade da dawowa daga makatanta ba yana level 3 a jamiar garinsu wato wudil wadda aka fi kira da KUST. Tace fito a hankali kada babanku yaji ina jiranka a wurin shanya. Ai nan ya sameta da wayar redio a hannu ta bashi ta nemi wuri ta zauna a kasa tace zanemin 'yar iskar yarinyar nan wadda bata jin magana. Najib dama haka nan ma cin zali ne dashi bare an bashi license. Nan ya fara dukanta ko tambayar baasi babu. Kamar kullum yauma ba ihu sai hawaye da take zubarwa a zuciyarta kuwa tana kara rayawa wallahi duk wanda zai zagar mata uba Allah ne zai raba ta dashi. Ju kenan ta baba idris. Tun da ta fara wayo ta gane babanta makaho ne take tausayinsa. Wani lokacin sai ta sami loko tayi ta kuka saboda tausayinsa. Akan baba Ju ta fara qiyamul layl tunda wata rana malamin su yace duk mai yinta komai ya roka Allah zai amsa. Mama da kanta ta fuskanci hankalin Ju kamar baya tare da ita tace wa Najib ya kyale ta. Suna juyawa suka ga baba a tsaye rike da hannun bidaya. Yace idan kun gama dukan ku bani 'yata. Ju wadda kanta yake a durkushe tana jin muryar Baba sai kuka mai tsuma zuciya taje ta kankame shi tace wallahi baba na tsane su kuma bazan yafewa duk wanda ya zage ka ba. Wannan abu yasa Mama kuka itama. Suka koma dakin Baba gaba dayansu sai yace a fita a barshi da mama da ju. Kowa na fita yace Juwairiyya kina so inyi fushi dake ne. Tayin saurin cewa a'a. Yace to daga yau idan kika sake fada a waje a kaina bani ba...bata bari ya karasa ba tace WALLAHI WALLAHI WALLAHI bazan kara ba.Sai yace tashi kije Allah Yayi miki albarka. Tana fita yace mariya yarinyar nan ta gado fushinki. Ita kanta mama yadda Baba ke magana ya bata tausayi domin tunda ya kamu da lalurar nan baya ko daga murya yace yana gudun kada ladan hakurinsa ya ragu. Mama tace Alhaji yau fa duk kayan jikinta a yage suke gashi kamar an mata wanka da kasa. Yarinyar nan mace ce amma abinda take ko namiji ne dole ayi masa fada.Baba yace mu cigaba da yi mata adduar shiriya da kuma sassautawar zuciya. ******************** Hajiya Asiya ta dubi yar uwarta tace ni tun ranar da kika min waya akan fadan da Juwairiyya tayi hankali na bai kwanta ba don babansu Amal baya nan ne da washegari zaki ganni a garin nan. Idan kin yarda mariya ki barni na tafi da ita kano tunda ta gama jarabawa kafin result ya fito. Mama tace anya yaya ayi haka da dai kin bari sai nan da sati ukun muzo bikin Amal tare. Yarinyar nan kawa zucin gida gareta gashi duk safiya da dare sai tazo taga babanta. Haj Asiya tace wai kin manta yadda kike likewa baba ne da kamar kaska ta fada taba dariya. Kuma yarinyar nan ina ga kawai tausayin babanta take yi. Ga karayar arziki ga makanta lokaci guda dole a tausaya masa. Ki bari mu tafi muyi shirye shiryen bikin yayarta Amal da ita tunda su nafisa basu yi hutu ba ga Alhaji bazaki iya zuwa da wuri ba. Baba ma ya amince bayan da mama tayi masa bayanin shawarar da yayarta ta kawo. Ju kuwa an gama hada kaya da murnar zuwa wurin yaya amal sai dai kafin ta isha ta lallaba ta fita taje gidan wan mahaifinta wanda shine silar karayar arzikinsa da makantarsa ta sami Baaba mai koko tana tatar gasara ta tsaya ta kama kugu tana murguda baki tace mai koko zan tafi kano gobe nasan duk kowa yana ciki suna sanaar kallo to ki fada musu duk wanda ya zagar min uba ko yan gidanmu Allah Ya isa. Tana fadin haka ta ruga ta koma gida. Mai koko ta bata sami mayar da magana ba ta rike baki tace bari malam ya dawo idan bamuyi da gaske ba yarinyar nan zata tona mana asiri wata rana. Sai mun sake haduwa da jin rayuwar Juwairiyya (Ju) a kano da asirin da su Mai koko suke tsoron ta bayyana. 💕 JUWAIRIYYA💞 2 Jan motar su Haj Asiya ke da wuya mal Yau ya fita shima bayan sun gama shawara da maikoko. Bakin titi yaje ya tari mota sai wani kauye. Boka Dillin yana ganinsa yace mugu dan masara yau kuma bayan wa kake son gani. Mal Yau ya zauna a inda ya saba idan tasa ta kawo shi yace yarinyar kanina ke neman ballo min ruwa kasan na fada maka tasan komai don ma kayi kokarin rike bakinta ne. Amma fa bata tsorona yanzu kada wata rana tayi magana. Sannan akwai yayar babarta kusan ita ce gatsnsu yanzu. Itama ina son a hada su duk a tada musu hankali. Tazo ta dauki Zuwairan sun tafi kano bikin yarta. Boka yayi dariyar mugunta yace indai wannan ce matsalar to an gama fadi wata idan akwai. ************************* Ana bude gate din gidan Haj Asiya wani dadi ya rufe Ju. Ita dai tana son gidan mami kamar yadda yaranta da suma yan gidansu suke kiran Hajiyan. Bari uku ne a cikin tankamemen gidan. Daya na Alh Bashir mijin mamin sai na wansa Dr Umar sai kuma na babarsu Hajja a tsakiya. Mami tace Juwairiyya muje mu far gaida Hajja ko. Tace to Mami ai ni ina sonta tunda tana zuwa duba Baba. Mami tayi murmushi ita kam ta rasa yadda akayi yarinyar nan take son babanta haka. Suna shiga Ju taga 'ya'yan wan babansu Amal da take kusan saar su Fauza da Yasmin sun takurawa Hajja wai sai sun daura mata gwaggwaro da biki tunda bikin jikokinta biyu zaayi. ita kuma Hajja ta dage tana turewa abin ya ba Ju dariya tana kokarin karasawa gaban Hajjan su gaisa taji ta taka wani abu, kafin ta ankara ta juyu kuwa aka hankada ta ta fadi kada kanta ya bugu da hannun kujera. Tan take kowa hankalinsa ya dawo gare ta wanda ta taka kuwa cikin fushi ya tashi yace are you stupid? kina tafiya bakya kallon gabanki. Hajja tace Asiya duba min goshin yarinyar nan. Kai Rayyan tun dazu nace ka tashi daga kwanciyar nan kayi hanya kaki. Ju kafin Mami ta taba ta ta shafa goshinta taga jini ai nan taķe ta manta da manya a gabanta tace kan uba ka fasa min goshi. Allah Ya isa, kazo ka kwanta kan hanya kuma ni ina jin na taka maka kafa niyata na juyu na baka hakuri. Mami ta daka mata tsawa tace ke Juwairiyya bana son rashin kunya. Ta juya ga Rayyan tace yi hakuri babban yaya. Sai a lokacin ya durkusa ya gaishe da mami sannan kafin ya fita yace ni dai Mami indai wannan ce mai aikin da zaa daukarwa Amal na mun yafe. Hajja tace kuga yaro mara kunya babar matar taka kake fadawa haka? To yarta ce itama.Mami tace Hajja ya zaki korar min da. Duk suka yi dariya sannan suka gaisa ******* *************** Bayan anyi sallar azahar Ju da Amal sun cin abinci tare suna hira Mami ta fito daga daki ta zauna kan kujera tace Amal idan anyi laasar ki dauki Juwairiyya kuje ku gaida Dada. Tace to Mami amma motata tun safe Abdul zaije siyo min mai giyar ta makale sai dai mal Garba ya kaimu a taki. Mami tace na aike shi gidan mai turaren wuta. Abdul yace dazu naji Ya Rayyan yace zaije yau. Mami tace to ka fada masa akwai yan rakiya. Amma jira su gama cin abincin ka raka kanwarka ta gaida Umma. Sunje sun gaida Umma matar Baba Umaru har Ju ta zauna hira wajen su Fauza don ita Mami duk yaranta shida maza ne sai Amal ita kadai. Bayan laasar sun fito zuwa gwangwazo gidan kakarsu babar su Mami wato Dada sai Ju ta hango Ya Rayyan tsaye jikin mota ai kuwa ta taba Amal tace yaya da wancan mutumin zamu je. Tace eh Ju tace shine fa don wulakanci yace min mai aiki. Amal ta kwashe da dariya tace kin dai rama ko. Tace a'a amma zan rama. Abdul autan mami wanda dashi zaa yace ke Ju shine angon fa. Ta zare ido tace angon wa yace na yaya Amal. Ju sai tayi tsit da baki har sukavkarasa mota. Suna shiga Amal tace Ya Rayyan shine ka kira kanwata mai aiki ko. Yana kokarin ribas da mota yace yi hakuri amarya ai ban sani ba.kanwar taki ce akwai baki kamar reza. Ju dai da tasan angon yayarta ne da tayi shiru da bakinta amma jin yace bakinta kamar reza yasa ta bata rai. Shi kuwa sai ya cigaba da cewa she talks alot, i could hear her voice from my room. To Ju taga abin kamar da rainin hankali wai ana magana da turanci a gabanta tace a ranta wallahi sai na rama. Ko yaya Rayyan kalli mudubin zai duba bayansa sai yayi ido hudu da Ju ita kuma tana lura da hakan da ya kallo sai ta murguda baki a haka har suka isa gidan Dada. ********************* Kwanan Ju uku a gidan Mami amma duk gidan ya fara isarta. Sau biyu tun zuwants ta hadu da Ya Rayyan amma yana ganinta yake bata rai. Inda sabo ta saba da ganin mutanen da basa sonta a gidan baba Yau amma abinda yasa wannan ke damunta tausayin Yaya Amal take ace mutum irin wannan zata aura mara fara yadda take da son mutane. Yau gidan Hajja a cike yake da baki 'ya'yanta mata Hassana, Usaina da Habiba na duk sun zo saboda taron gaggawa da Hajja ta kira sati biyu kafin a fara biki. Babu kowa a falon sai yayanta maza da matansu sai matan da kuma Amal da Rayyan. Baba Umaru ne ya fara magana da tambayar yaran shin a falon nan akwai wanda ya taba baku shawarar auren juna? Suka ce a'a. Yace madalla. Ku kuka hada kanku sannan kuka sanar damu sai yanzu saura sati biyu auren ku Amal kice kin fasa. Amal wadda kanta a kasa yake tunda aka fara magana tace wallahi Baba idan na aure shi wani mugun abu zai same ni kila ma na mutu. Rayyan wanda ko daren jiya bayan sun gama hira sun dade kuma a waya abin sai ya zo masa wani iri don shi duk a tunaninsa irin nasihar nan aka zo yi musu. A firgice ya dago kai yace Amal what did you just say?. Mami tace na shiga uku Amal lafiyarki kuwa. Anti Usaina tace ni dai yau bayan asuba ta kira ni ta fada min tana kuka shiyasa nazo na sanar da yaya. Hajja tace zo nan Habiba dayake shine sunan Amal na gaskiya. Me ya hadaki da dan uwanki. Cikin kuka tace ba komai. Babanta wanda ya rasa abin fada ya dafe kai yayi shiru, Mami itama cikin kukan tace Alhaji kana jin abinda yarinyar nan take baka ce komai ba. Nan dai ya dago kai yace Rayyan kana son auren nan? Yace eh Abba amma ..... bai karasa magana ba Abba ya mike ya fita. Baa jima ba ya dawo tare da Sagir dansa da kuma Aliyu wanda yake bin Rayyan ya dubi yayansa yace ni dai indan har kun amince a daura auren nan yanzu naga iya gudun ruwanta. Ya dubi Amal yace uwata yau ba don abin nan na gida bane so kike ki mayar dani karamin mutum. Anti Hassana tace yaya Bashir abi maganar nan a hankali. Ta kalli Rayyan tace ka fada mana gaskiya me ya hada ku. Shi da jin abin nan yake kamar wani mummunan mafarki yace wallahi anti babu komai, Amal tace na gaya muku babu komai auren ne bana so. Nan babanta ya kwada mata mari. Baba umaru yace meye haka Bashir ina wuri kana zartar da hukunci. Hajja kam kuka take sosai don tashin hankali ganin haka dai aka yi shawara akan a daura auren idan ma hure mata kunne ake sa yi maganin abin. A gabansu Abba Bashir ya bada duba dari a matsayin waliyin Rayyan shi kuma Baba Umaru ya karba sauran yaransu maza suka yi sheda. Sagir na gama addua Amal cikin wata irin murya kamar ta maza mara dadin sauraro tace kun daurawa kanku bala'i. Tana fadin haka ta fadi timmm a kasa. Nan da nan kowa yayi kanta cikin rudewa ana salati. Wai meke shirin faruwa a gidan Hajja ne daga zuwan Ju? 💕 JUWAIRIYYA 💞 3 Sagir da Rayyan ne akan Amal suna kokarin dagata amma duk sun kasa. Baba Umaru yace wai me kuke jira ne ku dago ta akai ta dakin Hajja. Sagir yace Baba mun kasa fa. Nan dai hankali ya sake tashi Abba ya fita ya kira liman aka zo ana ta karatun Qur'ani da adduoi. Ju da sauran yaran da baa barsu sun shiga bangaren Hajja ba duk hankalinsu ya tashi don ko baa fada ba sun san ba lafiya yadda suka ga manya suna ta shige da fice. Sai bayan magriba Amal ta farka daga yanayin data shiga ta fara kuka. Anyi anyi tayi shiru abu ya gagara karshe dai gidan Marigayi Tafida Abubakar ranar baayi kwanan farinciki ba. Duk wannan tashin hankali Mami ko kadan batayi kuka ba don sai a yau ma ta kara yarda kuka rahama ga bawa. Asubar fari ta kira kanwarta Mariya a waya ta sanar da ita duk abinda ya faru, sai a lokacin mami tayi kuka tace mariya ban fadawa Dada ba.Mama tace karki damu in shaa Allah yau zan zo. Bayan sun gama waya tayiwa Baban su Ju bayani shima hankalinsa ba karamin tashi yayi ba kuma yayi mats izinin tafiya. Mama ta barwa su Nafisa da babban yaya Najib sallahun yadda zasu kula da gidan da babansu kafin ta dawo. Fitarta ke da wuya wurin 7:30 na safe taci karo da Lawi dan baba Yau ko kallo bata ishe shi ba ya juya ya koma gida. Yana shiga yace da mahaifiyarsa naga ta fita amma ita da Ismail ne inajin tasha zasu. Har ya juya zai koma daki sai yaga yadda innar tasa ta washe baki. Yace wai inna meyasa tun jiya kika ce nasawa mutannen gidan can ido. Tayi murmushi har wawolunta na hakoran gaba ya bayyana tace kai dai jeka nagode. Da sauri maikoko ta shiga daki ta tashi malam Yau tace inajin fa abin ya tabbata don munafukar ta fita kuma inajin kano ta nufa. Yace ai kinsan aikinsa na kyau a hankali maji wane tashin hankalin ya tura mu. ********************** Rayyan ba karamin damuwa ya shiga ba da gari ya waye ya shiga bangaren Abba suka gaisa da Mami da Mama wadda take ta sharar hawaye bayan ta ga yadda Amal ta ke ance tunda ta farfado haka ta kwana kuka ba sauti sai hawaye. Rayyan ya zauna a kasa yace Mami Abba ya tashi kuwa kafin yayi shiru Abban ya ce gani Rayyan sannan ya zauna suka gaisa da mama. Rayyan yace Abba ni dai idan babu damuwa ko warware auren nan zaayi don ta sami lafiya. Bazan taba samun kwanciyar hankali ba nasan nine silar ciwon nan. Abba yayi murmushi yace yaro kenan ai rayuwa ba haka take ba. Ni bamu san Amal da lalurar aljanu ba amma wallahi bazan taba yi musu yadda suke so ba indai aure ne basa so tayi to sai dai suyi hakuri don Allah Yafi su. Zamu nema mata magani har Allah Ya bata lafiya. ka bar auren idan har sauki bai samu ba da kaina zan shige maka gaba kayi wani auren. Rayyan sai ya fara kuka kamar yaro wanda hakan yayi daidai da shigowar Ju falon tana ganin yana kuka tace yi hakuri zata sami lafiya in Allah Yarda. Takaici ne ya kama Rayyan ace sai a weakest moment dinsa yarinyar nan zata shigo harda wani bashi hakuri. Wasawasa yau sati biyu da fara ciwon Amal kullum zata fadi kamar sumammiya kuma tayi mugun nauyi idan ta farfado kuma sai kuka har cikin bacci tana hawaye. Da farko asibiti aka kaita tayi sati daya tasha allurai da drip amma duk a banza don ma asibitin na Baba Umaru ne so baa biyan kudin treatment. Hajja da Dada ne suka yanke shawarar a dawo da ita gida malamai suyi aikinsu. Mama dai kwananta goma a kano mami tace ta koma wudil kada abin ya zama rashin hankali ta bar yara da babansu shima kuma da tasa lalurar. A dole ta tafi don tasan hakan ne yafi dacewa amma kafin ta tafi mami ta roki alfarmar a bar mata Ju domin bata da waata mace ita take taimaka mata da ayyukan gida kafin su koma makaranta. Haka Ju ta zauna sai gashi cikin ikon Allah ita kadai Amal ke yarda ta taba ta ko malami ne yazo ita ke riko hannunta su fito falo don tuni aka barta a dakin Hajja. kullum safiya zata yi wa Mami shara da yan sauran ayyuka duk da akwai mai aiki. Idan ta gama zata je ta gaishe da Hajja ta bawa Amal abinci. ********************** Kwana biyu ya rage Ju ta koma Wudil sai amal ta dena magana. Ana zaune zata yi fitsari ko kashi sai dai aji wari dole tasa dena fito da ita. Wannan kukan ya ragu amma ta dena magana sai nuni idan ta ga dama. Ranar da ta fara fitsari a zaune Mami tasha kuka don taga alama yarta ta zama nakashashshiya akayi akayi ta tashi a gyarata taki. Ju tana ganin haka itama sai kuka don

Chapter 1 of 5