Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
5 / 6
zata nuna masa ya tuna duka abinda ya faru a baya a tsakaninsu da ita. Ni na san sato Amzad daga cikin birnin misira abune mai sauqi a wajen mutanenka, ya kai sarkin varayi ya za ai a sato sarqar dake wajen gimbiya lashmin alhalin dare da rana tana wuyanta a xaure, kuma ko wanka zata shiga kewaye bata cireta? Ko sau xaya bata tava cireta ba tun sanda ta cire sarqa a wuyan Amzad sa’ar da suna yara a lokacin da aka rabasu. Idan na samu Amzad da sarqa na samu cikaken lagonta kuma duka umarnin dana bata dole ta bi saboda zata iya salwantar da rayuwarta da mulkinta saboda Amzad. 97 BAYAN MUTUWA Naji ka tambayi wai mene nawa lagon? Zan iya sanar da kai nawa lagon amman sai idan kaima ka sanar da ni naka lagon” Koda jin haka sai sarkin varayi ya bushe da dariya sannan ya risina gaban Attajiri Huzulu yace “Tuba nake ya shugabana haqiqa na yi kuskure kuma ba zan qara ba, yanzu ina neman izininka a yau xinan zan tura zaqaquran yarana guda biyu izuwa cikin birnin misira. Mace xaya namiji xaya su ne Inzal da Karimat. Imzal zai sato Amzad ita kuma Karimat zata sato wannan sarqa dake wuyan Gimbiya Lashmin” Lokacin da sarkin varayi ya zo nan a zancensa sai attajiri huzulu ya yi shiru yana tunani har izuwa tsawon ‘yan daqiqu sannan ya miqe tsaye ya yi xan taku uku ya juyo ya fuskanci sarkin varayi yace. “Ko shakka banayi Imzal zai iya sato Amzad amma karimat ba zata iya sato sarqa gimbiya lashmin ba, idan kuma ta samu nasara satota zan kuwa bata kyautar dukiyar da babu ita babu talauci har izuwa qarshen rayuwarta. Maza a kirawo Inzal sa Karimat su 98 BAYAN MUTUWA yi shiri su tafi izuwa birnin misira” Kafin Attajiri huzulu ya gama rufe bakinsa tuni an kirawo Inzal sa Karimat sun bayyana a gaban sarki varayi. Shi dai Inzal wani kyakkyawan saurayi ne mai kwarjinin gaske kuma ya cava ado kai da ganinsa kasan cewa xan sarkine ko wani xan babban attajiri kuma fuskarsa tana xauke na xauke da alamun mutum mai tausayi da jin qai sai dai kash akasin hakanne a cikin zuciyarsa domin mutune mai tsananin mugunta da rashin imani. Ita kuma karimat mace ce doguwa mai qirar kalangu kuma baqar fata. Ba za a kirata kyakkyawa ba kuma ba za a kirata mummuna ba. Tana da yalwar gashin kai domin ya zubo har qasan kwankwasonta, kaurin jikinta madaidaicine ba yabo ba falasa, duk da kasancewar karima a qarqashin sarkin varayi take ba zaman kanta take ba, amma jikinta luwai-luwai yake kamar na jarirai, hakane zai tabbatar maka tana samun jin daxi da hutu sosai. Karimat tana xaya daga cikin manya-manya hadiman sarkin varayi wanda ya aminta 99 BAYAN MUTUWA da su, kuma yana qaunarta yana son ma ya mallaketa a matsayin matarsa ta uku, amma saboda yana da wani buri guda xaya wanda ita kaxai zata iya cire masa shi don haka ya dakata da batun aurenta. Saboda gaba xaya hadiman sarkin varayi sun san yana sonta don haka ko kusantarta basa yi, shima sarkin varayin baya zuwa inda take idan ta zo fadarsa to zata je aiwatar da wani aiki na musamman. Lokacin da karimat da inzal suka tsaya a gaban su sarkin varayi, attajiri Huzulu ya yi arba da ita sai ya ji ya kamu da tsananin sha’awarta don haka bai san lokacin daya qura mata idanu ko qiftawa baya yi ba. Sai da sarkin varayi ya tava hannunsa ya yi firgigi kamar ya tashi daga bacci sannan ya basar sarkin varayi ya yi murmushin qarfin hali. “Amman wannan hadimar taka mai kyauce” Sarkin varayi ya murmushi yace “Ai wannan ne aiki na qarshe da zata yi ta zama matata”Koda jin haka sai jikin Attajiri Huzulu ya yi sanyi ya kauda kai ga barin 100 BAYAN MUTUWA kallonta, shima sarki varayi yace “Ya ka ganta? Zata iya wannan aikin ko ba zata iya ba?”. Attajiri Huzulu ya yi murmushi yace “Ai da ganin kura zata ci mutum” sarkin varayi yace “Ta qware wajen iya qissa da shirya makirci ga iya magana na turata izuwa qasashe saba’in da biyu ta jagoranci gagarumar sata a masarautun amma ko sau xaya ba a tava samun rashin nasara ba, karimat mace ce mai tsananin sa’a aduk abinda ta saka a gaba, wannan ce sata ta saba’in da uku na kuma yi mata alqawarin shi ne aikinta na qarshe wanda zan ‘yanta ta na aureta”Koda sarkin varayi ya zo qarshen maganarsa sai murmushi ya suvuce wa karimat ta kamu da tsananin farin ciki amma a farin cikinta babu batun aure da sarkin varayi domin shi ne mutum na qarshe data tsana a duniya, ba komai ya saka ta tsaneshi ba face tun tana da shekara shida a duniya ya xaukota daga qasarsu bayan ya kashe iyayenta ya kwshe dukiyarsu, ya tafi da ita ya baiwa matarsa ita ta riqeta ta riqa bata horo na koyon sata, yaqi da jarumta a haka 101 BAYAN MUTUWA ta girma ta cika shekara ashirin da xaya ta zama gagarumar varauniya mashahuriya. Abinda sarkin varayi bai sani ba ko yaushe da dare sai karimat ta yi mafarkin abinda ya faru ga iyayenta tun tana shekara shida, amafarki tana ganin lokacin da sarkin varayi ya zare takobi ya sare mahaifiyarta da mahaifinta ita kuma tana zaune tana kuka ya sureta ya fice da ita daga cikin gidan tana ihu tana kiran sunan iyayenta. A kan idanunta sarki varayi ya saka aka cinawa gidansu wuta ya qone qurmus. A qarqashin zuciyar karimat ta ci burin cewar komai daxewa sai ta xauki fansar ran iyayenta a kan sarkin varayi. Sarkin varayi ya dubi inzal da karimat yace “Za ku tafi izuwa birnin misira yanzu kai zaka sato Amzad wanda ake shari’arsa da maigirma Huzulu ita kuma karimat zaki sato mana sarqa wuyan Gimbiya lashmin, bana son ku shafe sama da kwanaki bakwai a cikin birni ba tare da kun kammala aikinku ba, maza kuje sarkin gida ya baku dawakai da guzuri yanzu ku tafi” 102 BAYAN MUTUWA Da jin haka sai Inzal da Karimat suka rusuna sannan suka juya tare ficewa daga cikin fadar. Fitarsu ke da wuya sai attajiri Huzulu da sarkin varayi suka dubi juna suka bushe da dariya farin ciki saboda ji suke kamar buqatarsu ta gama biya. Wannan shi ne abinda ya faru a fadar sarkin varayi, fadar da ake yiwa laqabi da darul uzur inda attajiri huzulu ya vuya bayan ya gudu daga babbar kurkuku na birnin misira. A can birnin misira kuma lokacin da sarki yaqi ya baro gidan sarauta bayan ya gana da gimbiya lashmin sai zuciyarsa ta cika maqil da wasi-wasi gami da 103 BAYAN MUTUWA firgici. Ba komai ne yasa ya tsinci kansa a cikin wasuwasu gami da fargaba. Ba komai ne yasa ya tsinci kansa ba face tunanin hanyar fa ya kamata yabi ya samu nasarar taimakon lashmin domin ta cika burinta. A wannan lokaci yana tafiyane yana ta sauri domin ya isa gidansa ya zauna yayi tunani mai zurfi domin samun mafita kwatsam sai yaga mutum tsaye akansa nan take zuciyar sarki yaqi ta buga da qarfi tsaya cak a inda yake suka fara kallon-kallo da mutumin dake tsaye a gabansa. Ba wani bane wannan mutum face sarki Raihan wato mahaifin gimbiya lashmin cikin alamun tsananin mamaki gami da tsoro sarki yaqi ya qaraso kusa da sarki Raihan ya zube qasa ya kwashi gaisuwa sannan ya miqe tsaye ya dubeshi kansa na sunkuye cikin biyayya yace “Ya shugabana mene ne ya fito da kai daga gidan sarauta ka shigo cikin gari a wannan lokacin? Sa’ar da sarki Raihan ya ji wannan tambayar sai ya yi ajiyar zuciya sai yace “Na xauki karagata na baiwa ‘yaarta a ranar data hau ta yi abinda na kasa yi a 104 BAYAN MUTUWA shekara ashirin da biyar tunda ta sami nasarar kawar da babban maqiyina daga cikin birnina amma kuma ta tsokano mana tsoliyar dodone, na samu labarin cewar atttajiri Husulu ya gudu daga kurkuku, tunda na samu wannan labarin na kasa ci da sha kuma na kasa bacci, saboda nasan cewar qarshen mulkinmu ya zo kuma adalci ga talakawa ya qare ni da duka zuri’arta da dukkan masu biyayya a gareni ta su ta qare domin attajiri Huzulu ba zai barmu muci gaba da rayuwa ba, ko dai a murqushe qasarmu gaba xaya ko muyu ragas mu da attajiri Huzulu da jama’arsa Yanzu dai kaine kaxai abin dogarot a shin zaka iya taimakon ‘yarta akan aiwatar da shirinta na daqile attajiri Huzulu? Abune na siyar da rai domin babu tabbacin nasara a cikinsa, abune mai matuqar wahala idan kana ganin ba zaka iya taimakonta ba to ina da zavi na biyu, shi ne dani da gimbiya da duk masoyana mu bi dare mu sulale mu gudu mu yi qaura daga garin”. 105 BAYAN MUTUWA Lokacin da sarki ya zo nan sai hankalin sarkin yaqi ya dugunzuma ainun fiye da kowanne lokaci ya rasa abinda ke masa daxi a duniya ya yi shiru suna kallon juna har izuwa tsawon daqiqa biyar daga bisani kuma sai sarki yaqi ya kalli sarki cikin nutsuwa yace. “Ya shugabana nan ba wajen da za mu yi wannan maganar bane, saboda babu sirri kuma ka yi ganganci da kake fitowa daga gida a irin wannan lokacin saboda maqiya za su iya sakawa a saceka” Sarki raihan ya yi murmushi yace “Babu wani maqiyi daya fini sanin birni misira da kuma mutanen da suke cikinsa, nasan hanyoyin da zanbi ba tare dana haxu da wani tsautsayi ba, duk wani baqo da zai shigo garinan ina ganinsa kuma ko da zai voye fuskarsa sai da na ganka yanzu sannan na buxe fuskarta koma na gama nazarin wannan wurin da muke tsaye. Yanzu mu wuce izuwa gidankaa domin mu zauna mu tattauna tabbas akwai shawarwari da zan baka za su yi matuqar taimaka maka”. 106 BAYAN MUTUWA Sarki Raihan yana gama faxar haka sai ya xauki mayafin dake kafaxarsa ya xora akan fuskarsa ya rufe fuskarsa da shi yadda idanunsa kaxai ake gani sannan ya kama hannun sarki yaqi ya jashi suka nausa cikin gari izuwa hanyar da zata kaisu gidan sarki yaqi. Al’amarin Gimbiya lashmin kuwa bayan sun rabu da sarki yaqi ta shiga turakarta sai ta shiga sabon tunani mai zurfi inda ta ji cewar babu abinda take so a cikin faxin duniya sama da mallakar Amzad a matsayin abokin rayuwarta. Nan take ta tambayi kanta a cikin zuciya tace ta yaya zan kwato dukanin dukiyar Amzad daga hannun Attajiri Huzulu a cikin kwanaki biyu kacal? Ta yaya zan gani inda attajiri Huzulu yaje ya voye na saka a kamoshi a gurfana da shi a gabana a tsakanin yau zuwa gobe? Yin haka abune mai wuya amma kuma ai mulki ba wasabane. Me mulki yana yin komai indai abun mai yiwuwane a doron qasa. Matakin da zan bi ya zama dole a gobe a zo da Amzad fada na ganshi ya ganni kuma na tuno masa da koni wacce a gareshi, mataki na biyu a daren yau dolene na 107 BAYAN MUTUWA gana da babban bokan attajiri Huzulu wato boka zallazi domin ziyara zan kai masa ta bazata tunda shima nasan lagonsa lallai zai taimakamin akan attajiri Huzulu koda gama aiyana wannan al’amarin sai gimbiya lashmin ta qwalawa ilela kira ta shigo turakar da gudu ta zube qasa a gabanta, lashmin ta dubeta tace. “Mike tsaye muyi magana ki kalleni ido cikin ido” Da jin haka sai Illela ta miqe ta dubeta cikin nutsuwa Gimbiya Lashmin tace. “Ina son a cikin darenan na kai ziyara can bayan gari wajen boka zillazi a sirrance ba tare da wani ya ganmu ba, kece kaxai zaki rakani, bana son a ga fitarmu daga cikin gidanan ko dawowarmu sannan kuma ina son mu tafi da akwatinan ta lu’u lu’un sarki ki riqe mu tafi da ita” Koda jin wannan maganar sai Ilela ta firgita ainun jikinta ya kama rawa a lokacin da idanunta suka zaro tamkar tayi arba da mutuwa tace. “Haba ya shugabata ki sani ya shugabata duka dukiyar sarki babu abu mai darajar wannan akwatin ta 108 BAYAN MUTUWA lu’u lu’u a duk nahiyar nan gaba xaya, shin saceta kike so muyi?” Gimbiya Lashmin ta girgiza kai alamar cewar ba haka ba tace. “Fansa zan bayar a matsayin raina dana Abbana da kuma amzadm ki sani ba domin komai boka zulazi yake taimakon attajiri Huzulu sai saboda ya yi masa alqawarin cewa da zarar ya karvi karagar gidannan zai bashi akwatin lu’u lu’un sarki. Ita kuma wannan akwatin babu mai tavashi da hannunsa ba tare da hannun ya guntule ba har sai ya zama sarki garinan duk wanda ya mallaki wannan akwatin zai zama duka nahiyar babu mai kuxinsa, kuma dole sai mai mikin garin ya xauketa da hannunsa ya damqa maka sannan zaka ci gajiyarta. An turo varayi sama da dubu ashirin izuwa gidan sarautar domin su sace wannan akwati amma dukansu da guntulallen hannu suke komawa, ki sani idan na xauketa na saka a cikin jakarnan ta akwati zan iya baki ki riqe, duk abinda nake buqata nasan zaki iya shi yasa na umarceki da ki ruga kije ki aiwatar da shirye-shirye na wannan fitar da za mu yi a 109 BAYAN MUTUWA cikin wannan dare” Ba tare da wata gardama ba Ilela ta risina tace. “Angama ya shugabata” Cikin hanzari Ilela ta juya ta fice, ita kuma Gimbiya lashmin sai ta juya ta shiga cikin turakarta ta soma shirin fita. Al’amarin Inzal da karimat da xan saqo makanu suka baro fadar Darul uzu amma da ya rage sauran baifi tafiyar rabin sa’aba a iso birni misira sai suka tsaya suka yada zango shi kuma makanu ya wuce gaba izuwa birni misira. Bayan tafiyar makanu ne Inzal da Karimat suka fara hira inda ya dubeta yace. “To ke yanzu ta yaya zaki sami damar sato sarqa dake wuyanta?” Koda jin wannan tambayar sai karimat ta sauke ajiyar zuciya cikin alamun karayar zuciya sannan ta dubi Inzal tace “Bani da wta dabara a cikin zuciyata amma kuma ka sani cewa ni ban tava karaya bisa kowane irin aiki da zanyi ba komai 110 BAYAN MUTUWA wahalarsa da haxarinsa, kai kuma fa? Shin kana ganin sato Amzad abune mai sauqi, alhalin dole Gimbiya lashmin ta saka cikaken tsaro tunda tasan dole attajiri Huzulu ya saka a farauceshi” Inzal ya numfasa yace. “Maganarki gaskiyace amma ki sani indai gari yayi duhu a lokacin da na shiga cikin birni misira to ko da gaba xaya dakarun qasar suka kewaye xakin to sai na shiga” Koda gama faxin haka sai suka ga wata gada ta giftasu cikin hanzari Inzal ya miqe tsaye zumbur yace. “Ke jirani anan ina zuwa” A guje ya bi wannan gadar izuwa cikin daji karimat ta bishi da kallo har sai daya qule ya vace mata da gani faruwar hakan ke da wuya sai taji motsin tafiya a can bayanta nesa kaxan da sauri ta juya ta ruga ta vuya a can bayan bishiya kawai sai taga wasu mutane sun nufi can hanyar da ta nufi wani qaton kogo, nan take zuciyarta ta cika da tambayoyi su wane waxannan mutanen kuma me su ka zo yi alhalin gari ya soma duhu kuma akan hanyar da babu mai binta domin hanya ce data nufi gidan 111 BAYAN MUTUWA boka zullazi tana gama faxin haka sai ta bi bayansu da sauri don kada su vace mata da gani amma da taga ta soma hangosu sai ta riqa binsu a hankali don kar suji motsinta su waigo su ganta. Haka suka ci gaba har suka iso bakin kogon tana ganin haka sai ta kuma voyewa a bayan wani dutse, ba wasu bane waxannan matan face Gimbiya lashmin da kuyangarta koda suka qarasa sai tace “Ya shugaban bokaye buxe mun qofa” Kafin Gimbiya Lashmin ta gama rufe bakinta sai ga tsaunin ya rabe gida biyu wata qofa ta bayyana, su Gimbiya Lashmin suka shiga bisa ga mamakin Karimat sai taga qofar bata rufe ba don haka sai ta nufi wajen da azama ta shige, ai kuwa tana shiga sai qofar ta koma ta rufe karimat ta juya a xan tsorace ta kalli qofar amma sai ta dake ta juya ta kunna kai cikin gidan. Wani falo ne qawatacce wanda komai na cikinsa anyisa da zallar zunare, wata karagace guda xaya jal wacce aka yita da shuxin zinare aka yita, zaune akan karagar wani dogon mutum ne mai matuqar kwarjini 112 BAYAN MUTUWA da cikar haiba, gashin kansa sajensa gami da gashin baki duk farare fat. Kallo xaya zaka yi masa kasan cewar ya haura shekara tamanin a duniya koda ya gango Gimbiya lashmin da Ilaila sun nufo shi hannun Ilaila xauke da akwatin lu’u lu’u sai fuskarshi ta faxaxa zuwa ga murmushi kafin su qaraso tuni ya miqe ya taresu fuskarsa cike da murmushi. Cikin girmamawa boka zillazi yace “Barka da zuwa ya sarauniyar duniya, ki sani cewar ya Gimbiya yau shekara sittin kenan ina zaune ina jiran wannan ranar da za ki zo ki damqa mun wannan akwatin ta zinare da hannunki, tabbas kin gama cika mun wannnan burin nawa na duniya ke ma ki sani cewar zuwa gobe da yamma naki burin zai cika” Da jin haka sai Gimbiya lashmin ta yi murmushi ta amshi akwatin lu’u lu’u daga hannun ilaila ta miqa masa koda ya amsa sai suka ji an zabga wata tsawa mai qarfi wacce ta tsorata Gimbiya lashmin amma sai suka ga boka zallazi ya qyalqyale da dariya ya juya ya nufi inda aka ajiye wata bishiyar qarfe ta zinare, yana zuwa ya xora 113 BAYAN MUTUWA akwatin akan bishiyar faruwar haka sai akwatin ta narke ta haxe da bishiyar kamar ba’a tava xorata a wajenba kuma sai aka sake zabga tsawa a karo na biyu wacce tasa gidan gaba xaya ya girgiza Gimbiya lashmin da ilaila sai da suka faxi suka yi saurin miqewa. A lokacin boka zallazi ya waigo ya dubi su Gimbiya ya yi murmushi sannan ya taho zuwa ya garesu yace mata “Yake gimbiya kiyi sani cewar yau ko raina kike so zan baki, domin kin cika mun burina daya gagari iyayena da kakanina, nasan cewar baki da buri daya wuce ki amso dukiyar Amzad daga hannun attajiri Huzulu kuma ki kawo qarshen zalluncinsa, kuma kina son mallakar amzad a matsayin abokin zamanki na dindin” Koda Gimbiya taji haka sai ta yi murmushi tace. “Duk abinda ka faxa gaskiya ka faxa”. “To nima dole na sallama komai nawa bisa sa’a kuma wanda zai miki jagora wajen cika wannan burin 114 BAYAN MUTUWA naki mutum xaya yana nan cikin kogon tare da mu”Jin haka sai su Gimbiya lashmin suka soma waige-waige amma ba su ga kowa ba sai tace masa. “Kace mu huxu ne amma ni banga kowa ba, sai mu uku” Jin haka sai ya qyalqyale da dariya kafin kuma ya murtuke fuska yace. “Ya karimat mai sa’a ya kamata ki fito haka ai ina sane na bar qofar a buxe kika shigo” Koda jin haka sai tabar bayan ginin data vuya ta fito su Gimbiya da Ilaila suka qare mata kallo suka ga basu tava ganin mace kamarta ba. Boka zallazi ya tako ya qaraso zuwa gareta ya zo ya tsaya yadda suna jin numfashin juna yace mata “Yau shekara goma sha shida kenan ina jiran rana da zaki xauki fansa iyayenki da sarki varayi ya kashe miki to yau ga dama ta samu mudin zaki yadda ki haxa kai da sarauniyata, shin za ki yi amfani da wannan damar ne ko za ki zavi xan abinda attajiri Huzulu yace zai baki? Ki sani idan kika taimaki 115 BAYAN MUTUWA sarauniya zata baki dukiyar ba zaki kasheta ba har qarshen rayuwari kuma ba zaki iya kasheta kuma zaki zama maxaukakiya wato za ki zauna a cikin ma su mulki riba biyu kenan kin jefi tsuntsu biyu da dutse xaya”Koda boka zullazi ya zo nan a maganarsa sai karimat ta yi murmushi tace. “Ya maxaukakin boka ai ka fini sanin kaina shin yanzu ta yaya zan bada gudumawa a cikin wannan maxaukakin aikin?” Koda ya ji haka sai ya yi murmushi yace. “Zan baku wani taimako yanzu nan yadda ku uku nan za ku tafi can fadar Darul uzur ku yaqi duka dakarun ku kamo sarki varayi da attajiri Huzulu ku kawo su cikin birnin misira a wulaqance ku yi masa hukunci da kuka ga dama” Ya dubi karimat yace “Yanzu zan baki amsar tambayarki” Yana rufe baki ya nufi wata qofa ya buxe ya shiga jim kaxan sai ya dawo xauke da kayan yaqi guda uku da takobi, mashi da kuma wata hular qarfe zalla ya miqawa lashmin takobin ita kuma karimat sai ya abata mashi sannan ya 116 BAYAN MUTUWA miqawa ilela hular qarfe duk su uku suna riqe da kayan yaqin sai suka ji wani irin qarfi na musamman ya shiga jikinsu cikin matuqar mamaki lashmin ta dubi boka zallazi tace. “Ya kai babban boka wannan wanne irin kayan yaqi ne haka na ma su qarfi sihiri. Na rantse da gemun mahaifina yanzu ina jin zan iya shafe kwana da yini ina yaqi” Ya bushe da dariya yace. “Ai kwana bakwai za ki yi batare da kin gaji ba, ki sani babu wani kaifi ko tsini da zai tava tasiri a tare dake, wannan takobin dana baiwa gimbiya sunanta saiful lujara, mashin dana baiwa karimat sunan shi galilil haras, ita kuma hular dana baiwa Ilaila sunanta Lamsara, ba a tava yin kayan yaqi da suka kai wannan daraja da kuma sihiri ba, kuma sunfi shekara dubu xaya da xari uku a hannun kakanin kakanina, yanzu na baku wannan kayan domin ku kawo qarshen zallunci attajiri Huzulu domin idan aka sake ya mallaki birnin misira to zai mallaki tsafina da kuma kayan yaqinan, ku sani kuma idan kun gama yaqi kun 117 BAYAN MUTUWA samu nasara waxannan kayan yaqi za su vace su koma can qasan teku su ci gaba da zamansu kuma har abada ba za a kuma samun wani mahaluki da zai xauko su ba har duniya ta gushe, maza ku tafi fadar darul uzur domin aiwatar da wannan babban aikin” Koda jin haka sai Gimbiya lashmin da karimat da Ilala suka juya suka nufi hanyar fita. Lashmin ta zare takobin saiful daga cikin kubeta, ilela ta saka hular lamsara, ita kuma karimat ta wulwula mashin galilin haras, bisa ga mamaki sai sukaga sun fice fit ta cikin garu sun nausa da gudu cikin daji wani irin gudu ban al’ajabi suke yi. Saboda qarfin gudun ya kai na tauraruwa mai wutsiya koma duk abinda suka riska a gabansu tsalleke shi suke su wuce komai faxinsa da tsawonsa maimakon su shafe rabin sa’a kafin su isa fadar Darul uzut sai gashi cikin daqiqa biyar kacal sun isa ai kuwa sai dakarun sarki varayi suka ta so musu aka ruguntsume da wani azababben yaqi, kamar mace ta saka tsintsiya ta share qofar xakinta haka Gimbiya 118 BAYAN MUTUWA lashmin da Ilela da karimat suka karkashe dakaru dubu uku da xoriya. Sai gasu a cikin fadar tsulum sun bayyana a gaban su attjiri Huzulu da sarkin varayi, cikin firgici sarkin varayi da attajiri Huzulu suka zare makamai suka yi xauki kansu lashmin da sara da suka, ko da takubbansu suka haxu da saiful lujara da galili haras sai suka narke suka zama ruwa abinda ya yi matuqar ranazana su ke nan, nan suka zube qasa kafin su taso tuni Ilela ya bayyana a gabansu ta gwara musu hular lamshara nan take suka baje a wajen sumammu. Lokacin da sarkin varayi da attajiri Huzulu suka farfaxo sai suka tsinci kansu a zube a qasa a tsakiyar fadar birnin misira, attajiri Huzulu na duba gabansa sai ya yi arba da Gimbiya Lashmin da Amzad a zaune akan karaga xaya yana kallonsa yana masa murmushin mugunta, nan take Amzad ya miqa wa gimbiya hannu ya ta saka masa sarqa a cikin hannunsa ya soma juyata akan fuskar attajiri Huzulu yace. 119 BAYAN MUTUWA “Wannan sarqa ta amso mun haqqina dake wajenka kuma ta samar mun matsayi da xaukaka, duka dukiyar daka tara yanzu ta zama tawa kai kuma tsireka za ai bisa laifin fashi da makami tare da abokinka sarkin varayi” Yana rufe baki sai ga sarki sairan ya shigo fuskarsa cike da murmushi yace. “Tabbas yanzu za a tsireka” Masha Allah. QARSHE. 120 An dauko wannan littafi daga shafin https://taskarnovels.com.ng ku ziyarci shafin na https://taskarnovels.com.ng domin samun kayatattun littatafan hausa kama daga kan na yake yake dana soyayya Marubuci ko marubuciya zasu iya turo mana da littatafansu mu dora masu a shafinmu kyauta don masoyansu su rika Downloading a online, Sannan marubuta zasu iya turo mana da tarihin rahuwarsu da tarihin rubutunsu, dama sharhin littatafansu don masoyansu su gani kuma su karu da hakan Domin turo mana da littafi ko tarihin rayuwar marubuci ko marubuciya sai ayi mana magana ta whatssap da wannan nambar +2348140419490 A lura dakyau - kyauta muke saka littafi a shafinmu bama amsan ko sisin marubuci, duk wanda ya amshi kudinku da sunanmu babu ruwanmu, Alura dakyau - manazarta bama tura littafi ta private ku dena binmu private kuna neman mu tura maku littafi, duk mai bukatar littafi yaje website namu Alura da kyau - Littatfanmu suna fitowa cikin manhajoji uku ne PDF,TXT da DOC amman munfi amfani da PDF da TXT masu amfani da wayar android ko tablet ko computer zai fi kyau ku riga dauko PDF da DOC Masu amfani da kananan wayoyi java ko mara java TXT zakuna zaba don shine daidai wayarku This hausa novel was uploaded and downloaded from https://taskarnovels.com.ng You can download more hausa novels there Also you can send us your novel to upload it in our website for your fans to download it online It is free we do not charge for uploading novel Also if you are an Author be it online or Non online you can send us your biography including your book summary,commentary and others via this number +2348140419490 its free we do not charge for our services Note that - we do not charge for our services we uploaded novels and posted biography free, any person that collect your money in our name is your fault do not blame us Note that - pls readers stop calling us and be asking us to send you a novels we are not sending novels through whatssap or private our novels is public at any day, any time you can visits our site and download it Note that - our ebooks came as PDF,TXT or DOC format but the popular format are PDF or TXT, those with android or tablet or pc we suggest you to download PDF or DOC those with java phone or non-java phone we recommend you to download TXT This Novel is downloaded from https://taskarnovels.com.ng to download more hausa novels visits our site at www.taskarnovels.com.ng For feedback and support Facebook :

Chapter 5 of 6