Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
2 / 6
ya kama muzurai yana mai qus-qus. Gimbiya Lashmin ta gyara zama kuma tayi gyaran murya sannan ta dubi Safwan tace. “Tsakanin attajiri Huzulu da Saurayi Amzad waye ya kawo qarar wani?” Safwan yace. “Ubangiji Dullas ya taimakeki Gimbiya ai yaro Amzad ne ya kawo qarar attajiri Huzulu” Koda jin haka sai Lashmin tayi murmushi sannan tace. “Ai dama abune mayuwanci attajiri ya kawo qarar talaka sai dai talakan ya kawo qarar attajiri saboda har kullum talaka ba zai iya danne haqqin attajiri ba tunda anfishi sanin komai da kowa kuma an fishi qima da daraja, maza a karantomin wannan qarar doming a dukkan alamu zan yanke hukuncinta a cikin qanqanin lokaci”. Koda jin wannan batu sai hankalin attajiri Huzulu ya dugunzuma ainun ya buxe baki kamar zaice wani abu amma sai Gimbiya Lashmin tayi masa nini da yayi shiru tace. “Kai ba’a magana a gaban kotu face an baka izinin yi” cikin alamun kunya da rashin gaskiya attajiri Huzulu ya yi shiru yana mai sunkuyar da kansa qas. Mai gabatar da qara Safwan bin ma’aruf yayi gyaran murya a lokacin da fadar ta suka yi tsit tamkar 24 BAYAN MUTUWA ruwa ya ci kowa sannan yace saurayi Amzad yana qarar attajiri Huzulu akan cewa ya kwace masa gidansa nag ado wanda mahaifinsa ya mutu ya bari a matsayin bashin da yake bin mahaifinsa, bayan mahaifinsa ya mutu, baya ga wannan gidan akwai rumfunan kasuwa guda uku wadanda yace tun kafin mahaifin Amzad ya mutu ya bashi su jingina kuma bai dawo da kuxin da ya araba har ajalinsa ya cika. Bayan rumfuna uku akwai babbar gona guda xaya wacce ke can kusa da kogin Luzim a bayan gari. A yanzu haka duk faxin garinnan babu inda ake noman kayan lambu sama da wannan gona kuma a tsawon shekaru ashirin da biyar da mutuwar mahaifin Amzad daidai da rana xaya ba a tava daina noma a cikin gonar ba kuma duk amfanin da aka samu Attajiri Huzulu ne yake riqewa. Bai tava baiwa mahaifiyar Amzad koda sisin kwabo ba, tun kafin ma ta haifi Amzad saboda tana xauke da junan biyun Amzad da watanni shida Allah ya yi wa mahaifinsa rasuwa” Koda Safwan ya zo nan a bayaninsa sai Gimbiya Lashmin tayi sauri ta xaga masa hannu tace. “Dakata haka haba ai wannan shari’ar ta wuce duk yadda nake zato, ina mai tabbatar muku za 25 BAYAN MUTUWA mu iya shafe wata guda muna yinta bamu qare ba duk da cewar za mu iya gano mai gaskiya a tsakanin attajirin da saurayin a cikin sa’a xaya jal” koda jin wannan batun sai kowa ya kamu da tsananin mamaki a cikin fadar. Su kansu manyan alqalai na qasar sai suka kasa gano manufar Gimbiya Lashmin da kuma yadda zata yi ta iya warware wannan qara da kuma dalilin da yasa tace za a iya gano mai gaskiya a cikin sa a xaya saboda basuga hujjojin da zata iya amfani da su ba. Kamar Lashmin tasan abin dake zukatan jama’a da sauran alqalan qasar sai kawai aka ga ta miqe tsaye daga kan karagar mulki ta tako kafafunta ta zo har gaban attajiri Huzulu ta dubeshi a cikin nutsuwa tace. “Shin gaskiya ne kana bin mahaifin Amzad bashin da darajarsa ta kai ta gidansa, rumfunan kasuwarsa guda uku da kuma babbar gonarsa dake can bayan gari, gonar da babu kamarta a duk faxin qasar nan?” koda jin wannan tambayar sai attajiri Huzulu ya gyaxa kai yace. “Wannan gaskiya ne kuma ina da shaidu akan haka gami da rubutacciyar takarda mai xauke da saka hannunsa da kuma saka hannuna akan duk kuxaxen 26 BAYAN MUTUWA da ya zo ya karva a hannuna da zumar zai biyanio kafin cikar wani wa’adi na kwanaki har ajalinsa ya riske shi bai gama biyana waxannan kuxaxen ba shi dalilin daya saka na riqe gidajensa, gonarsa da rumfunansa na kasuwa” Koda jin wannan batun sai Gimbiya Lashmin ta gyaxa kai kuma tayi murmushi sannan ta sake duban attajiri Huzulu tace. “Shin kuxaxen da mahaifin Amzad ya karva a hannunka duka ya karve su ne a rana guda ko kuma ya karve sune daban-daban akan ko wacce kadara tasa?” Hazalu yace. “Ai ya karve sune daban-daban, misali lokacin da yake so zai gina waxannan rumfuna na kasuwa guda uku bashi da kuxin aikin sai ya zo wurina na bashi rancen dinare dubu xari biyu da arba’in bisa sharaxin cewa idan ya kammala ginin zai bayar da hayar rumfar duk wata zai riqa bani dinare dubu hamsin har tsawon wata shida a sananne zai kammala biyana, a watan farko da zai fara biyana wannan kuxin ajalinsa ya same shi, tsawon shekara guda ba a bani ko kwabo ba. Duk sanda naje wajen matarsa na nemi haqqina sai tace dani itama ba a bata ko sisi ba ta ma san a hannun wa rumfunan suke ba, ya shugabata 27 BAYAN MUTUWA kinga kenan na tafka asara na tsawon watanni shida kuma inda kuxina a hannuna suke da sun ninka kansu, bisa wannan dalilin na riqe duk kadarorinsa a maimakon kuxaxena daya karva na fitar da matarsa daga cikin gidan na zuba ‘yan haya a ciki. Dangane da yadda aka yi na mallake rumfunan kasuwarsa kuwa guda uku shi ne bayan ya karvi wannan kuxin na farko dinare dubu xari biyu da arba’in, a tsakiyar watan da zai biyani ya sake dawowa ya ranci dinare dubu xari biyar ya sayi irin da zai shuka a wannan gona tasa wadda ya gada a wajen ubansa kuma ya biya ma’aikata suka nomata bisa sharaxin cewar bayan yayi girbi zai biyani dunare dubu xari takwas. Har bayan shekara biyu da mutuwarsa ba a bani kuxina ba, bisa wannan dalilin na riqe takardun rumfuna guda uku. Ana I gobe zai rasu Mahaifin Amzad ya sake dawowa gareni ya ranci dinare miliyan xaya ya sayi raquma,alfadarai da jakuna waxanda za su riqa safarar amfanin gonarsa izuwa qauyuka da birane dake cikin qasar nan kuma ya biya ma’aikata da za su yi masa wannan aikin rabin wahalarsu tun ma kafin kaka ta zo, da sharaxin wata biyu da shuxewar kaka zai biyani dinare miliyan xaya da rabi, sai da aka yi kaka uku ba 28 BAYAN MUTUWA a bani ko dinare xaya ba, bisa wannan dalilin na riqe gonarsa ta zama tawa”. Lokacin da attajiri Huzulu ya zo nan ciki dogon jawabinsa sai kawai aka ga hawaye yana zubowa daga idanuwan Gimbiya Lashmin nan take ta dubi Attajiri Huzulu cikin alamun tsananin fushi tana mai daka masa tsawa tace. “Tabbas ka cika shugaban azzaluman duniya, da farko dai na yarda cewar mahaifin Amzad ya ranci duk kuxaxen da ka faxa a hannunka bisa amincewar zai biyaka kuxin ruwa to amma idan aka yi la’akari da irin kuxaxen da aka samu a rumfunansa na kasuwa da kuma gonarsa a wannan tsawon shekaru ashirin da xaya ai kaci ribar data ninka kuxin daka bashi sau dubunnai. Kawai don kana binsa bashin kuxaxen da gaba xaya adadinsu bai haura dinare miliyan biyu ba sai ka cinye masa gaba xayan dukiyarsa wacce a halin yanzu idan idan qiyasta darajarta za a yi darajarta tafi dinare miliyan xari biyar sannan kuma dukiyar ta haura miliyan dubu goma. Sannan kuma kowa a garin nan ya sa ni kafin ka mallaki rumfunan kasuwa da waxan nan gonakin baka da jarin daya fi dinare miliyan biyar amma yau 29 BAYAN MUTUWA an wayi gari babu mai cinikin gidaje da gonakai wanda ya fika qarfin jari. To idan baka sani ba yanzu ka sani cewar wannan matsala taku kai da Amzad tun ina yarinya qarama na san da ita. Ansha kawo wannan qarar gaban mahaifina amma sai wasu daga cikin ‘yan majalisarsa su sa a kori qarar a baka gaskiya, badan komai ba sai don kana binsu izuwa gidajen su a sirrance xaya bayan xaya kana shaka musu cin hanci na maqudan kuxaxe. Na daxe ina jiran wannan ranar da zan samu damar cikakken bincike akan wannan qarar na qwatowa Amzad da mahaifiyarsa haqqinsu amma ban samu ba sai yau, ka sani babu cuta babu cutarwa, kaje ka zo da duk takardu da kuma shaidun bashin daka baiwa Mahaifin Amzad, shima Amzad zai zo da irinsu waxanda mahaifinsa ya mutu ya bari, bayan an zo da su kotu zata saka a yi lissafi na iya adadin hakkinka daya kamata a biyaka a cikin dukiyar da mahaifin Amzad ya bari sannan ayi lisafin a gani, tsakanin kai da shi wane zai yiwa wani ciko a tsawon waxannan shekaru ashirin da xaya” Koda jin wannan batu sai Attajiri Huzulu ya taqarqare ya kwarara uban ihu tamkar mahaukaci sabon shiga. 30 BAYAN MUTUWA Sannan ya kalli Gimbiya Lashmin cikin tsananin fushi da qiyayya yace. BAYAN MUTUWA 3 ‘K e yarinya ce abinda mahaifinki yabarshi a rufe baki isa ki tona shi ba...” Kafin Huzulu ya gama rufe bakinsa tuni Gimbiya Lashmin ta sharara masa mari, ta dubi wasu dakaru uku dake tsaye kusa da shi tace musu. Koda ganin wannan al’amari sai hankalin lashmin ya dugunzuma ainun tace a cikin ranta, anya kuwa sarki ba yaudarata yayi bay ace jarrabawa zai yi, babu mamaki ya sauka ne daga kan karagarsa ya bar mata, koda gama ayyana hakan sai idanunta suka ciko da hawaye, koda taji qwallah tana shirin suvice masa sai tayi sauri ta sunkuyar da kanta qas don kada wani ya gani ta share hawayen. Tace a cikin ranta ina ma Allah bai yiyota ‘yar sarki ba. Da dai ace ita ba kowabace face ‘yar talakawa fitik masu neman abin da 31 BAYAN MUTUWA za suci kullum da ya fiye mata farin ciki da kwanciyar hankali a rayuwarta Haka dai su Gimbiya Lashmin suka ci gaba da tafiya a cikin gidan sarautar ana biye da ita xu tamkar wata tauraruwa mai tsananin haske a tsakiyar dubunnan taurari har aka iso cikin babbar fada ta gidan sarautar. Daga dakarun tsaron sai qananan fadawa sai kuma mutanen gari a zazzaune wato a tsaitsaye a cikin fadar. Koda shigowar Gimbiya Lashmin tare da ma’aikata masu take mata baya sai duk mutanen dake zaune suka miqe. Koda aka ga Gimbiya Lashmin ta fito a maimakon sarki sai kowa ya cika da mamaki, aka wangame baki ana kallonta kawai, kai tsaye Lashmin ta nufi wajen da karagar mulki take tana tafiyar qasaita kamar wani toron giwa. Hatta yanayin tafiyarta irin ta sarki sairan ce. Haqiqa komai yana bin jini in da ace shigar maza Lashmin ta yi kuma ta rufe fuskarta to da kowa zai xauka sarki ne ya shigo fadar ba Gimbiya Lashmin ba. Da isar gimbiya Lashmin kan karagar mulkin sai ta zauna ta harxe qafa xaya bisa xaya tamkar dama can ta saba zama akan karagar. A sannane sauran jama’a kowa ya koma inda yake ya 32 BAYAN MUTUWA zauna kuma a daidai wannan lokacin manya fadawa da ‘yan majalisu qasar suka fara shigowa. Duk wanda ya shigo yayi arba da Gimbiya Lashmin zaune akan karaga mulki sai ya kamu da tsananin mamaki gami da tsoro don ba a san dalilin faruwar wannan canjin ba alhalin sarki yana raye. Koda ganin wannan al’amari sai hankalin lashmin ya dugunzuma ainun tace a cikin ranta, anya kuwa sarki ba yaudarata yayi bay ace jarrabawa zai yi, babu mamaki ya sauka ne daga kan karagarsa ya bar mata, koda gama ayyana hakan sai idanunta suka ciko da hawaye, koda taji qwallah tana shirin suvice masa sai tayi sauri ta sunkuyar da kanta qas don kada wani ya gani ta share hawayen. Tace a cikin ranta ina ma Allah bai yiyota ‘yar sarki ba. Da dai ace ita ba kowabace face ‘yar talakawa fitik masu neman abin da za suci kullum da ya fiye mata farin ciki da kwanciyar hankali a rayuwarta Haka dai su Gimbiya Lashmin suka ci gaba da tafiya a cikin gidan sarautar ana biye da ita xu tamkar wata tauraruwa mai tsananin haske a tsakiyar dubunnan taurari har aka iso cikin babbar fada ta gidan sarautar. 33 BAYAN MUTUWA Daga dakarun tsaron sai qananan fadawa sai kuma mutanen gari a zazzaune wato a tsaitsaye a cikin fadar. Koda shigowar Gimbiya Lashmin tare da ma’aikata masu take mata baya sai duk mutanen dake zaune suka miqe. Koda aka ga Gimbiya Lashmin ta fito a maimakon sarki sai kowa ya cika da mamaki, aka wangame baki ana kallonta kawai, kai tsaye Lashmin ta nufi wajen da karagar mulki take tana tafiyar qasaita kamar wani toron giwa. Hatta yanayin tafiyarta irin ta sarki sairan ce. Haqiqa komai yana bin jini in da ace shigar maza Lashmin ta yi kuma ta rufe fuskarta to da kowa zai xauka sarki ne ya shigo fadar ba Gimbiya Lashmin ba. Da isar gimbiya Lashmin kan karagar mulkin sai ta zauna ta harxe qafa xaya bisa xaya tamkar dama can ta saba zama akan karagar. A sannane sauran jama’a kowa ya koma inda yake ya zauna kuma a daidai wannan lokacin manya fadawa da ‘yan majalisu qasar suka fara shigowa. Duk wanda ya shigo yayi arba da Gimbiya Lashmin zaune akan karaga mulki sai ya kamu da tsananin mamaki gami da tsoro don ba a san dalilin faruwar wannan canjin ba alhalin sarki yana raye. 34 BAYAN MUTUWA K awai sai sarkin yaqi ya miqe ya qwalawa dakarunsa kira, nan take sai ga Dakaru sama da mutum xari uku sun rugo izuwa gabansa Lashmin ta sake duban sarkin yaqi tace. “Idan kuka kai shi can kurkuku ku sanar da cewar kar abar kowa ya kawo masa ziyara koda kuwa iyalansa ne kuma koda mai kawo masa abinci kada ya shiga wajensa shi kaxai kuma sai an tabbatar da cewar an cajeshi yayin shigarsa da fitowarsa. Sarkin yaqi ya risina yace “Angama ya shugabata” Nan take aka tusa qeyar attajiri Huzulu aka fice da shi daga cikin fadar a wulaqance abin da ko a mafarki ba a tava zaton cewar zai tava faruwa ba. Bayan an fice da attajiri Huzulu sai Gimbiya Lashmin tasa aka sallami kowa a fadar har da saurayi Amzad kuwa amman kafin ya tafi sai ya faxi qasa a 35 BAYAN MUTUWA gaban Lashmin ya fashe da kukan farin ciki kuma ya kama yi mata godiya kamar bazai daina ba har sai da ta daka masa tsawa a gaban Dakaru da kuyanginta sannan ya shiga taitayinsa sannan ta dubeshi tace. “Ban taimakeka domin komai ba sai domin na kawo sauyi a wannan qasar tamu na kawar da zalunci na shimfixa adalci, ko kai na kama da rashin gaskiya sai na hukunta ka, ka sani cewar kaima yanzu rayuwarka na cikin hatsari saboda haka dolene na haxaka da Dakaru waxanda za su baka kariya kuma ba zaka ci gaba da zama a wannan gidan hayan ba” Koda jin haka sai Amzad ya dubi Gimbiya Lashmin cikin alamun tsananin damuwa yace. “To mahaifiyata fa? Wacce yanzu haka tana can gidan tana jiran dawowata? Kin san cewa ta tsufa ainun bata gani kuma bata iya tafiya” Koda jin haka sai Lashmin tayi murmushi tace. “Kada ka damu tuni tun kafin ma a fara yin wannan shari’a taku nasa an xauketa an akita can gidan sarki dake bayan gari, kuma yanzu can za a kaika wajenta. Na tabbatar da cewar can za ku sami cikakken tsaro har izuwa ranar da za a kammala wannan shari’a taku” Koda gama faxin haka sai Lashmin ta dubi mataimakin sarkin yaqi tace. 36 BAYAN MUTUWA “Yakai muzainu wannan aikin kane, ka jagoranci Dakaru xari ku raka Amzad izuwa can gidan sarki na bayan gari kuma ka zauna tare da shi acan har izuwa tsawon lokacin dana neme ku” koda jin haka sai Muzainu ya dubeta cikin tsananin damuwa yace mata. “Ya shugabata idan sarkin yaqi baya nan nima bana nan akwai matsala ta tsaro a gidanna fa” Gimbiya Lashmin tace. “Ai nasan da haka amman kada ka manta cewa kafin kafin ma ka isa can inda na aikeka tuni sarkin yaqi ya dawo daga can kurkuku ko kuma kana zaton cewa za a kawo mana harin sumame a cikin wannan xan tsukukun lokacin?” Muzainu ya yi murmushi yace. “Aa bah aka bane kawai dai bana son ni da sarkin yaqi muyi laifi ne a wajen mahaifinki” koda jin haka sai Lashmin ta yi murmushi tace. “Ai yanzu ni ce akan karagar mulki ba mahaifina ba, saboda haka idan ma laifi ne ni za kuyiwa bashi ba, indai kana tsoron tuggun attajiri Huzulu ne to ka kwantar da hankalinka domin na xauki matakan tsaro tsaurara akan hakan”. Nan take Muzainu ya kama hannun Amzad ya jashi suka nufi qofar fita daga fadar dakaru na take 37 BAYAN MUTUWA musu baya. Sauran qiris Amzad ya fice ta cikin qofar fadar sai ya juyo suka haxa idanu shi da Gimbiya Lashmin take yaga ta yi masa wani irin kallo wanda ya ximataushi ya jefashi ciki tsananin, mamaki,wasuwasu, fargaba da rashin fahimta lokaci guda duk su biyun suka juyawa junansu baya ta nufi hanyar da zata kaita cikin gidan sarautar shi kuma ya fice daga fadar yana mai bin Muzainu a baya. Da sauri, dakaru sun kewaye shi suna gudugudu sauri-sauri. Lokacin da Gimbiya Lashmin ta shiga cikin gidan sarauta sai ta nufi turakar mahaifinta sarki Salhan kai tsaye tana isa babban falonsa sai ta iske shi a zaune tare da mahaifiyarta a cikin nishaxi suna ciyeciye da shaye-shaye har suna yin soyayya irin tasu ta manya. Al’amarin day a yi matuqar bata mamaki kenan domin a zatonta zata zo ta riskeshi ne a cikin tsananin fushi bisa abinda ta aikata yau a fada domin ta tabbatar da cewar tuni labari ya riskeshi. Koda sarki Salhan yaga Gimbiya Lashmin ta durfafo inda suke zaune sai ya miqe tsaye zumbur cikin matuqar farin ciki ya tarbeta yana mai rungumeta gami da sumbatar goshinta sannan yace. 38 BAYAN MUTUWA “Yake ‘yarta kiyi sani cewar yaune nayi alfahari dake a matsayin ‘yarta wacce zata iya gadata. Sai yaune na tabbatar da cewar ke jinina ce. Domin kin cire min qaton dutsen daya danne ni tsawon shekaru ashirin da biyar, na daxe ina son hukunta attajiri Huzulu amma na kasa amma ke gashi cikin daqiqu kaxan kin hukunta shi kuma a lokacin da ya dace ya karvi irin hukuncin da kika yi masa. A iya tunanina duk wanda ya mutu shi kenan komai na shi ya tafi kenan. Nazmir mahaifin Amzad ya mutu da tsawon shakaru ashirin da biyar dukiyarsa ta tafi ga hannun azzalumi Huzulu amma yau gashi za ki dawo da wannan dukiyar izuwa hannun tsatsonsa, wannan fa shi ne RAYUWA BAYAN MUTUWA sai yanzu a bayan mutuwar Nazmir sannan iyalansa za su yi sabuwar rayuwa irin wacce basu tava yinta ba, domin idan wannan dukiyar ta koma hannun su, babu sa’ansu a tarin dukiya a gaba xaya wannan nahiyar tamu. Lallai kuwa idan kika samu wannan nasara kinyi abinda har abada ba za a manta da ke ba a tarihin qasar nan, shi kuma Amzad ba shi da abinda zai iya biyanki da shi har izuwa qarshen rayuwarsa” Koda jin 39 BAYAN MUTUWA wannan batu sai gimbiya Lashmin tayi murmushi sannan tace. “Akwai abinda Amzad zai iya biyana da shi, ba komai bane face zuciyarsa da soyayyarsa, burina kawai ya so ni kuma ya qauna ce ni qaunar da babu algus a cikinta, ya riqe min alqawari na soyayya har izuwa ranar da zamu zamo abokan rayuwar juna domin mu samu zuri’a ta gari” koda Gimbiya Lashmin ta zo nan a jawabinta sai mamaki ya turniqe sarki da mahaifiyar Lashmin suka zazzaro idanuwa suka kasa cewa komai. Daga can sai sarki ya dubeta yace mata “Yaushe kika fara ganin Amzad hard a za ki ce kin kamu da son sa haka?” Koda jin wannan tambaya sai hawaye ya zubo wa gimbiya Lashmin sannan tace. ‘Na fara son Amzad tun ina da shekara bakwai a duniya, yakai Abbana shin zaka iya tunawa da wata rana da yammaci sakaliya sa’adda ka fita wani rangadi tare da ni” Koda jin wannan batu sai sarki salhan ya xaga kansa sama ya faxa kogin tunani. Kimanin shekaru goma sha xaya da suka gabata sarki salhan ya fita rangaxi a cikin keken dokinsa tare da ‘yarsa Gimbiya Lashmin a lokacin 40 BAYAN MUTUWA tana da shekara bakwai kacal a duniya. Dakaru kimanin xari uku ne ke kwaye da su suna tafiya a gefen wani daji dake daf da birnin nasu na misra sai kawai suka ji ana harbor musu kibiyoyi. Ashe Dakarun sumame ne suka kawo wa sarki hari. Nan take cikin gaggawa dakaru suka yanyame keken dokin sarki suka kareshi da manyan garkuwoyinsu don kada wata kibiyar ta zo ta sameshi ko ta soki Gimbiya Lashmin. Ana cikin hakanne sarkin yaqi ya leqo cikin keken dokin ya dube shi cikin alamun tsananin tashin hankali yace. “Ya shugabana maqiyane suka kawo mana harin bazato, duk yadda aka yi suna da xan leqen asiri a cikin fadarmu ta haka ne suka samu labarin wannan fitowar ta mu” Koda jin haka sai sarki salham ya girgiza kai yace. “Tabbas zancenka gaskiya ne amma sai bayan mun tsira sannan za mu yi bincike mu gano ko wanene wannan munafikin,wai shin adadin dakarun sumamen zai kai nawa?” Sarkin yaqi yace. “Ya shugabana sun ninkamu sau uku idan muka bari suka iso nan suka riskeka bani da tabbacin kai da Gimbiya za ku tsira, abu mafi kyau shi ne 41 BAYAN MUTUWA yanzu ku fito mu ruga izuwa cikin daji mu da tsirarun dakaru inyaso sauran Dakarun mu suyi kamar kana cikin wannan keken dokin su ci gaba da tsoronsa. Kafin a cim masu munyi nisa a cikin dajin mun zagaya tacan mun koma cikin birnin mu” Koda jin wannan batu sai sarki salham ya dubi sarkin yaqi cikin fushi yace. “Yanzu kana nufin mu gudu mubar sauran jama’ar mu anan a kashe su a banza kenan?” Sarkin yaqi yace. “Ai tun tuni sun siyar da rayukan su domin kare naka dana iyalinka don tsare darajar qasarmu, ka tuna cewar idan aka kasheka anan cikin dajin tamkar anci birnin mu da yaqine. Idan waxan nan abokan gabar suka san cewar sun gama da kai ai kuwa komawa za su yi suyi gaggarumin shirin yaqi su zo su baje birnin namu gaba xaya, jinin mutanen mu nawa ne zai zuba anan? Adadin dukiya nawa ne zata salwanta, kaga kenan ashe rayuwarka zata kuvutar da miliyoyin mutane da miliyoyin dukiya”. Koda jin wannan batun sai sarki salhim ya yi wuf ya xauki Gimbiya Lashmin ya goyata a bayansa ya xaureta tamau sannan ya zare takobinsa 42 BAYAN MUTUWA kuma ya xauki garkuwarsa ya fito daga cikin keken dokin. Nan yake shi da sarkin yaqi da tsirarun dakarun waxanda basufi su arba’inba suka ruga izuwa cikin daji suka bar sauran dakarun tsaye a gaban keken dokin suna gadinsa. Tafiyar su sarki ke da wuya sai ga dakarun sumamen sun iso bisa dawakansu da yawa. Koda suka hango keken dokin sarki sai dukkaninsu suka zare takubbansu suka afkawa dakarun dake tsaron keken dokin aka ruguntsime da yaqi. Duk da cewar dakarun sumamen sun ninka dakarun sarki salhan sau uku sai da aka shafe sa a guda cif ana baqin gumurzu sannan aka qarar da dakarun sarki.koda aka gama karkashe su aka leqa cikin keken dokin sai aka ga wayam. Nan take shugaban dakarun sumamen ya kurma ihu! Yace. “Tabbas waxannan mutanen yaudarar mu suka yi, tun xa zu sarkin misra ya fice daga cikin keken dokinnan ya gudu ku zo mu bi sawun su” Yana gama faxin hakan sai ya zaburi dokinsa yabi hanyar da su sarki salhan suka bi. 43 BAYAN MUTUWA Suma saran dakarun sai suka rufa musu baya suka rinka tsala gudu tamkar dawakan nasu za su tashi sama. ** Al’amarin sarki salhan da sarkin yaqi da tsirarun dakaru kuwa tunda suka fara gudu basu tsaya ba, cikin sa a kuwa suka hango qofar birnin misra daga can nesa tazarar kimanin zango xari. Nan take farin ciki ya lulluve su suka qara gudun su, sai daya kasance bai fi sauran taku baifi saba’in ba tsakaninsu da bakin qofar garin sai kawai suka hango dakarun sumame acan bayan su kaxan sun durfafo inda suke a guje bisa dawakai. A daidai wannan lokacin Nazmin mahaifin Amzad ya dawo daga gona yana save da fatanya a kafaxarsa kuma yana riqe da hannun xansa Amzad yaron da bai wuce shekara tara ba a duniya. Lokacin da su sarki salhan suka waiga bayansu yana goye da Gimbiya Lashmin suka hango dakarun sumame a bayansu sai suka qara qarfin gudunsu, koda ganin haka sai dakarun sumamen suka soma xana kibiyoyi akan baka suna harbinsu kuma suna daxa kusanto su. Nan fa suka soma yiwa dakarun 44 BAYAN MUTUWA sarki salhan xauki xai-xai suka riqa faxuwa qasa matattu. Har ya kasance sauran sarkin yaqi da sarki salhan kaxai suka rage a raye suna ta gudu. Tun daga nesa sarkin yaqi ya riqa qwalawa masu gadin qofar gari kira yana basu umarnin su buxe qofar amma da yake masu gadin basu shaida ko su wayeba sai sukaqi buxe qofar. A wannan lokacin Nazmir da xansa Amzad kuwa na daf da isa bakin qofar birnin Misra.koda suka jiyo gudun mutane biyu a bayansu sai suka waiwaya a firgice, take Nazmir yaga ashe sarki ne da sarkin yaqi suke wannan gudun na ceton ransu, kuma ga dakarun sumame can a bayansu sun durfafo sauran qiris su cimmasu, kawai sai Nazmir ya juya yana dakawa masu gadin tsawa yana musu ishira cewar sarki ne fa, nan take masu gadin suka yi sauri suka buxe qofar. Amman kuma sai masu gadin suka kasa fitowa domin kawowa sarki xauki saboda ganin yawan abokan gaba domin idan suka fito za a samu galabar shiga cikin birnin. 45 BAYAN MUTUWA BAYAN MUTUWA 4 Kawai sai gani aka yi kibiya ta soki sarki a cinya ya kife qasa, Lashmin dake goye a bayanshi sai ta faxi qasa ta riqa mirginawa izuwa baya can wajen da maqiya ke tahowa tana ihu, shima sarkin yaqi sai kibiya ta soke shi a gadon baya ya kife qasa. Koda ganin abinda ya faru sai Nazmir ya saki hannun xansa Amzad ya ruga da gudu izuwa inda sarki yake kwance ya sunkuceshi ya azashi a kaxarsa ya ruga da gudu dashi izuwa cikin birnin misra ko tunawa da batun xansa bai yi ba. Shima yaro Amzad sai ya ruga da gudu ya xauko Gimbiya Lashmin a kafaxarsa ya nufi qofar birnin misra, yana gudu ana harbor masa kibiyoyi har kibiya guda ta soke shi a hannu sai ya yi matuqar dauriya yaci gaba da gudu a haka jini na zuba a hannunsa ga lashmin a kafaxarsa yana layi jiri na xibansa amma sai daya shige cikin qofar birnin. 46 BAYAN MUTUWA Sarkin yaqi ne ya qaraso da qyar da gudu yana faxuwa yana tashi har ya shiga cikin qofar, ai kuwa yana shiga sai dakarun dake tsaron qofar garin suka yi sauri suka mayar da qofar suka rufeta kuma suka hau kan ganuwa suka xana kwari da bakansu. Koda ganin haka sai dakarun sumamen suka yi tirjiya, bisa dole suka kaxa dawakansu suka juya da baya cikin baqin cikin rashin samun nasarar kashe sarki salhan. A cikin birni kuwa ranga-ranga aka xauki sarki da sarkin yaqi aka tafi da su izuwa gidan sarauta. A lokacin wani bafaxe ya zo ya fizge Gimbiya Lashmin daga kan kafaxar Amzad sai tayi wuf ta fizge wata qaramar sarqa dake wuyan Amzad ta dubeshi cikin murmushi tace. “Har abada ba zan mance da kai ba, ka zo gidan sarki ka amshi sarqarka a hannuna, ni kuma zan saka maka da abinda yafi komai daraja a wajena”. Tana gama faxin haka sai

Chapter 2 of 6