Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
3 / 6
ta riqa xagawa Amzad hannu shima sai ya rinqa xaga mata hannu har aka hau kan doki da ita aka ruga da gudu suka qule ya daina hangota, a sannan ne mahaifin Amzad ya kama hannunsa ya jashi suka nausa cikin birni. 47 BAYAN MUTUWA A lokacin da sarki salhan ya zo nan a tunaninsa sai hawaye ya zubo masa ya dubi Gimbiya Lashmin yace. “Yanzu ashe tun daga wannan ranar da Amzad ya ceci rayuwarki kika kamu da son shi?” koda jin wannan tambayar sai itama Gimbiya Lashmin ta zubar da hawaye sannan ta zura hannu aljihun rigarta ta fiddo wannan sarqa ta Amzad ta nunawa sarki tace. “Qwarai kuwa tsawon waxannan shekarun ina ajiye da sarqa Amzad kuma ina begensa a cikin zuciyata dare da rana. Tambayar da nake son na yi maka mene ne ya hana Amzad zuwa wajen da nake ya karvi sarqarsa dake hannuna? Mene ne dalilin daya saka duk sa’adda nace kasa aje a nemo Amzad da mahaifinsa sai kace har izuwa tsawon waxannan shekarun kace an halaka shi, nima kuma ka saka aka tsare ni a cikin gidan sarauta baka barina na fita sai da sharaxin wajen da zani nan xin zanje, ka hanani samun sakewa da zan yi bincike akan sa har zuwa girmana. Tabbas ka jefani a cikin kurkukun soyayya wanda yafi rijiya gaba dubu, ka sanya min xaci a zuciya wanda yafi azabar fitar rai, kuma ka dusashe 48 BAYAN MUTUWA min hasken idanu da baqin ciki da yafi dare duhu, tsawon shekaru sha xaya kenan ban ga masoyina ba Amzad rabona da shi tun ina da shekaru bakwai a duniya sai yau da aka gurfanar dashi a gabana domin na yi masa shari’a da azzalumin attajiri Huzulu. To ka sani ko ka bani amsar tambayoyina ko kaqi a yau xinnan sai naje na baiwa Amzad sarqarsa wacce na cire a wuyansa tun muna yara a ranar day a ceci rayuwata. Ko kana so ko baka so yakai Abbana sai na cika alqawarina a gareshi na bashi abin da yafi komai daraja a wajena kuma ba komaibane face soyayyata da kuma aurena”. Lokacin da Gimbiya Lashmin ta zo nan a zancenta sai shima sarki sairan ya ji hawaye sun suvuce masa don haka sai ya kamo Gimbiya Lashmin ya rungumeta a qirjinsa yana kuka yace. “Ki gafarta min yake ‘yarta kiyi sani cewa akwai dalili mai qarfi wanda yasa na raba rayuwarki da Amzad xan Nazmir waxanda suka ceto rayuwarmu a tare kuma a lokaci guda, dalili kuwa shi ne bayan anyi mana magani ni da sarkin yaqi wato an cire kibiyoyin dake jikinmu an sa mana magani don kashe dafin kibiyar sai kawai muka ga bokana wato Darzas ya baiyana tsulum a gabanmu. 49 BAYAN MUTUWA Boka Darzas ya dubeni cikin damuwa yace “Ya shugabana kayi sani cewar ba wani bane ya turo dakarun sumame su kasheka ba face sarki zardar na birnin mailus, kuma munafikin da ya sanar da su cewar zaka fita yawon rangaxi ba wani bane face bawanka yunus mai kula da dawakanka na hawa, musamman sarki mailas ya siyar da shi izuwa fa farakenku suka zo dashi nan qasar,kai kuma ka siye shi a matsayin bawa har ka aminta da shi, saboda qwazon shi a wajen aiki da qwarewarsa wajen kiwon dawakai.ban gano wannan sirrin ba sai yanzu da zan zo wajenka na yi bincike akan kawo wannan harin. Abu na gaba da zan sanar maka kar ka sake kabar wata alaqa ta soyayya ta qulu a tsakanin Gimbiya Lashmin da Amzad xan Nazmir waxanda suka ceci rayuwarka xa zu a qofar birninnan daga hannun dakarun sumame, domin bincike ya nuna ba za su tava zama abokan rayuwar juna ba, kuma qarshen soyayyar tasu tana qunshe da baqin ciki a gare su da duk masoyansu” Boka Darzas yana gama faxin haka sai ya vace vat. 50 BAYAN MUTUWA S arki Salhan ya dubi Gimbiya Lashmin ya ci gaba da magana “Bisa wannan dalilin tun daga wannan ranar na sanya hijabi a tsakaninki da Amzad har mahaifinsa ya rasu ban bari kun sake ganin junaba. Ki yafe min yake ‘yarta, lallai ki yafe min na yi miki babban laifi amma son da nake miki ne gami da son ganin kyakkyawar rayuwarki a gaba yasa na yanke wannan hukunci”. koda sarki salhan ya zo nan a zancensa sai Gimbiya Lashmin ta fashe da matsanancin kuka, al’amarin daya karya zukatan iyayenta kenan suka kamu da tsananin tausayinta. Don haka sai mahaifiyarta ta janyota ta rungumeta a kan qirjinta tana mai rarrashinta tana bata baki har izuwa tsawon ‘yan daqiqai amma bata daina kukan ba, daga can sai Lashmin ta janye jikinta daga cikin na mahaifiyarta ta miqe tsaye ta dubi sarqa tace. “Ya kai Abbana kayi sani cewar babu wani qarfi wanda ya isa ya dates so na gaskiya a tsakanin masoya,addini ko sihiri, dukiya ko talauci,wuya da daxi basa raba masoya sai dai mutuwa da qaddara. ni banyi imani da dukkan abinda bokayen ku ke faxaba muddin ya shafi soyayyata, idan kuma har abinda suka faxa ya zama gaskiya to na yarda na mutu akan qirjin 51 BAYAN MUTUWA masoyina domin shi ne abinda ya fiye min komai farin ciki a rayuwata” koda gama faxin haka sai Gimbiya Lashmin ta miqe tsaye da sauri ta juya ta fice daga cikin turakar mahaifiyarta na kwala mata kira amman ko waigowa ba. Koda ganin haka sai mahaifiyar tata ta miqe da sauri da nufin taje ta ruqo ta amman sai sarki ya yi wuf ya runqota ya dakatar da ita yace mata. “Kar ki kuskura ki dakatar da zuciyarta da take ruruwa da wutar soyayya, domin daidai take da mahaukacin zakin da ya fusata a cikin daji a lokacin da yake fama da tsananin yunwa,kinsa cewa idanunta a rufe suke zai iya banke kowa” Koda jin wannan batun sai mahaifiyar Lashmin ta koma ta zauna kusa dashi ta xora kanta akan qirjinsa a lokacin da hawaye ya zubo mata shi kuma ya qanqameta a jikinsa tana mai cewa. “Haqiqa ‘ya tayi gadon ubanta akan zafin soyayya ko kuwa ka mance ne da yadda muka mallaki junanmu, mun sha baqar wahala da gwagwarmaya?” koda jin wannan batu sai hawaye ya suvutowa sarki salhan yace. “Zan iya mancewa da komai na rayuwata amma ba zan iya mancewa da tarihin soyayyata ba 52 BAYAN MUTUWA yake matata, a duniya banga abin da yafi soyayya daxi da haxari ba, kuma babban kuskure da mutum zai yi a rayuwarsa shi ne yace zai shiga tsakanin masoya” Koda jin wannan batun sai hankalin mahaifiyar Lashmin ya dugunzuma ainun ta janye jikinta daga na sarki suka fuskanci juna ta dubeshi cikin alamun tsananin damuwa tace. “Wai shin yanzu kana nufin kenan zaka kyale Lashmin ta yi soyayya da Amzad xan Nazmir alhalin kasan cewar qarshen soyayyar tasu mummun qarshe ne da mugun baqin ciki?” Koda jin wannan tambayar sai hawaye ya sake suvuce wa sarki sairan yace. “Y azan yi da qaddara? ko na bar Gimbiya ko na hanata saduwa da Amzad ba zan iya cire son sa ba daga zuciyarta, idan kuwa akwai sonsa a ranta idan muka matsa akan rabu su za mu iya rasata gaba xaya, wanne za mu zava a ciki yanzu? Ni dake muna son farin cikinta a yanzu idan muka hanata kuma a qarshe mu rasata ko kuwa mu barta ta mutu a cikin farin ciki. Shi kansa mahaifin Amzad yasan da wannan matsalar tun kafin ya rasu kuma mahaifiyarsa ma ta sani,bisa wannan dalilin suka nemi taimakon boka marigayi zardash ya saka Amzad ya mance da duk 53 BAYAN MUTUWA abinda ya faru tsakaninsa da Lashmin a wannan lokacin da suke yara amman ya tabbatar mana da cewa duk ranar da yaga wannan sarqa tasa wacce Lashmin ta cire a wuyansa to sai ya tuna da komai” Koda jin wannan batu sai hankalin mahaifiyar Lashmin ya dugunzuma ainun fiye da koyaushe ta kamu da tsananin baqin ciki kuma ta fashe da matsanancin kuka tana mai cewa. “Mene ne dalilin daya sa tuntuni baka sanar da ni wannan sirrinba, lallai inda nasan dashi da sai nasan hanyar da na bi nasa Gimbiya ta manta da Amzad kuma da sai nasa ta yi aure domin mu ga jikan mu da idanuwa kafin mutuwarmu amma yanzu baqin alwalami ya gama bushewa domin wannan burin na mu ba zai tava cika ba” Koda jin wannan batun sai sarki salhan ya sake kamo matar tasa ya rungumeta a kan qirjinsa suka fashe da kuka a tare. Komai rashin tausayin zuciyar mutum idan ya dubi waxannan ma’aurata a wannan lokacin da suke yin wannan kuka na takaici da baqin ciki dolene ya kamu da tsananin tausayinsu ba zai san sa’adda shima zai zubar da hawaye ba. Wannan shi ne abinda ya faru tsakanin Gimbiya Lashmin da iyayenta a can gidan sarauta. 54 BAYAN MUTUWA Al’amarin Amzad kuwa lokacin da mataimakin sarkin yaqi tare da dakarunsa suka tafi das hi izuwa can gidan sarki na bayan gari sai kansa ya xaure kuma mamaki da wasi-wasi suka turnuqeshi, abu na farko daya fara tambayar kansa shi ne wai shin mene ne dalilin da yasa sarki ya sauka daga kan karagarsa ya baiwa ‘yarsa Gimbiya Lashmin hart a kwato masa ‘yancinsa alhalin a tsawon shekaru baya sarki ya kasa yi masa wannan taimakon. Amzad ya sani cewa mahaifinsa gagarumin attajirine domin ya mutu ya bar dukiya mai tsananin yawan da babu mai kamarta a gaba xaya birnin misra amma bayan mutuwar tasa ne shi da mahaifiyarsa suka faxa cikin tarkon attajiri Huzulu har ya zamana cewa sun rasa komai nasu suka zama talakawan da suka fi kowa babu domin da qyar da sixin goshi Amzad ya tsira da jaki guda xaya wanda yake sana’ar dakon tubalin gini dashi. Da hakane yake samo abinda za su ci abinci shi da mahaifiyarsa, sai dai ta kai basu da gidan kwana kuma basu da komai basu da kowa face jakin nasa guda xaya. 55 BAYAN MUTUWA Komai zafi komai sanyi sai dai su rakave a kangwaye ko rusashen gida su kwana, sau tari idan zai tafi sana’arsa ta dako sai dai yakai mahaifiyarsa ajiya izuwa maqotansu,inya dawo sai ya zo ya xauketa akan jakinsa su tafi inda za su kwana. Kullum haka suke yin wannan rayuwa cikin qunci, talauci da matsanancin baqin ciki, a duk sa’adda mahaifiyarsa ta tuno da irin daular da suke ciki sa’adda mahaifinsa ke raye sai tayi ta kuka tana tsinnewa attajiri Huzulu. Da qyar Amzad ke rarashinta yana gaya mata maganganu masu daxi domin hankalinta ya kwanta. Abu na biyu daya jefa Amzad cikin tsananin mamaki shi ne wannan kallon da Gimbiya Lashmin ta yi masa a lokacin da zai fita daga cikin fada. Shi dai a rayuwarsa babu waya ‘ya mace data tava yi masa irinsa face Gimbiya Lashmin. Kallo ne wanda indai aka yiwa mutum sai ya tabbatar da cewa akwai qauna ga wanda yayi masa akan wane dalili Gimbiya zata so ni ina matsayin talaka fitik wanda bai shafi jinin sarauta ba. Ai ko a mafarki soyayya ba zata qullu a tsakanin mu ba, domin qwarya sai dai tabi qwarya, 56 BAYAN MUTUWA dan tabi akwashi kuwa fashewa zata yi. Haka dai Amzad ya yi ta wannan tunanin gami da saukar da ajiyar zuciya, a haka har suka iso wannan gidan na sarki salhan dake can bayan gari. Kai tsaye mataimakin sarkin yaqi ya shige dashi har can cikin gidan. Suna isa babban falo na gidan sai Amzad ya hango mahaifiyarsa zaune bisa teburin cin abinci an cava mata ado da tufafi na isa sannan ga abinci kalakala irin na manyan attajirai da sarakai a gabanta, kuyangi na zuba mata dukanin kalar abinci da take so tana ci cikin tsananin farin ciki. Yanayin tafiyar Amzad kawai mahaifiyar tasa taji sai ta miqe tsaye cikin murna ta buxe hannayenta tana mai cewa. “Taho gareni ya kai xana, zo ka bani labari wane gaggarumin aiki ka yi ga sarki wanda ya saka har aka bamu wannan daular?” Cikin tsananin farin ciki Amzad ya qarasa wajen mahaifiyar tasa ya rungumeta sannan ya zaunar da ita akan kujerar da take zaune da. A sannan ne mataimakin sarkin yaqi ya sallami gaba xaya kuyangin dake wajen suka fice daga falon suka barsu su uku kacal. Kafin Amzad ya buxe 57 BAYAN MUTUWA baki ya baiwa mahaifiyar tasa amsar tambayarta sai mataimakin sarkin yaqin ya tari numfashinsa yace. “Yake ummul Amzad kiyi sani cewa Allah ne ya dube ku ya yi muku rahama bisa tsohon zalluncin da aka yi muku na tsawon shekaru, a yau ne ‘yar sarki Gimbiya Lashmin ta karvi aro karagar sarki saboda shi bashi da lafiya, a yau xin ta saka aka fito da duk takardun shari’oin da ake kawowa fada ta dubasu amma sai ya zavo taku shari’ar kacal ta saka aka kirawo attajiri Huzulu tare da xanki Amzad aka gabatar da shari’ar a gaban mutanen fada. A yanzu haka maganar da nake yi miki Gimbiya tasa an aika da attajiri Huzulu kurkuku an tsareshi kuma za a ci gaba da bincike har a gano gaskiyarku a karve duk dukiyar ku dake hannunsa a dawo muku da ita” Koda mataimakin sarkin yaqi ya zo nan a jawabinsa sai mahaifiyar Amzad ta kamu da tsananin farin ciki bata san sa’adda ta fashe da kuka ba, kuma tayi suvutar baki tace. “Yanzu ashe dama akwai ranar da ‘yar sarki zata tuno da halaccin da muka yi mata?” koda jin wannan batu sai mamaki ya turniqe Amzad ya dubi mahaifiyar tasa yace. 58 BAYAN MUTUWA “Yake Umma wane irin halacci ne muka yiwa Gimbiya Lashmin?” koda jin wannan tambayar sai tayi saurin ta wayance tace. “Aa ina nufin nace dama sarki zai tuno da irin biyayyar da mahaifinka yayi masa a rayuwa, ai a lokacin da mahaifinka yana raye yayi hidima da dukiyarsa a gidan sarauta sosai don haka na yi mamakin yadda aka yi sarki ya mance da bayansa yaqi ya neme mu ya taimaka mana” Koda jin wannan batu sai Amzad ya yi murmushi yace. “Haba yake umma, in banda abinki kuma ai su masu mulki suna da yawan mantuwa, sannan kuma kinsan ance ba a mugun sarki sai mugun bafade ai makusantansu ne suke hanasu yin aikin alheri. Wata qila yana son ya taimaka mana koma yana aiko mana da taimakon fadawansa na dannewa bamu sani ba”. Koda jin haka sai mataimakin sarkin yaqi yace. “Qwarai kuwa ai abin dake faruwa kenan” Amzad yace. 59 BAYAN MUTUWA BAYAN MUTUWA 5 ‘To amma mene ne dalilin dayasa duk a tsawon shekarunnan ko sau xaya sarki bai tuno da shari’armu bad a attajiri Huzulu sai a yau rana xaya da ‘yarsa ta hau karagar mulki ta tuno damu kuma har tayi mana wannan gagarumin taimako tamkar muna binta bashin wani abu a rayuwa? Alhalin bata ma san mahaifina ba bata irin gudumawar daya basu” Koda jin wannan tambayar sai mataimakin sarkin yaqi ya yi caraf yace. “Ai kasan babu mamaki shi sarki baya son ya vatawa fadawansa shi yasa ya kasa yin komai akan wannan shari’a taku tsawon shekarun da aka xiba musamman tunda duk manya fadawansa yaran attajiri Huzulu ne amma ai ita Gimbiya Lashmin babu ruwanta da fadawan sarki tunda yarinyace, duk abinda ya zo mata a cikin rai shi zata aiwatar”. Koda jin haka sai mahaifiyar Amzad ta gyaxa kai tace. “Na yarda da maganar ka” Nan take mataimakin sarkin yaqi ya miqe tsaye ya dubi Amzad yace masa. 60 BAYAN MUTUWA “Ni zan koma wajen dakaru domin na daxa tabbatar da tsaro kamar yadda aka uwarceni, ina son ku saki jikinku kuji daxinku duk abinda kuke buqata akwaishi a cikin gidannan kawai ku tambayi kuyangi” Amzad ya yi murmushi gami da godiya ga mataimakin sarkin yaqi shi kuma sai yace. “Ai bani za ka yiwa godiya ba face Gimbiya Lashmin kuma kusani cewa a koyaushe zata iya kawo muku ziyara ba zato” Koda jin haka sai Amzad ya dube shi cike da mamaki yace. “Haba ya za a yi Gimbiya Lashmin ta zo nan saboda mu kawai” Mataimakin sarkin yaqi ya yi xan guntun murmushi yace. “Baka yi mamakin yanda ta wulaqanta attajiri Huzulu ba saboda kai sai zuwanta nan? Ina yi muku sallama kuyi barci mai daxi sai da safe” Koda gama faxin hakan sai mataimakin sarkin yaqi ya juya ya fice daga cikin falon ya bar Amzad da mahaifiyarsa nan dai suka qarasa cin abinci nasu. Suna gamawa sai kuyangi suka kawo musu ruwa da qyalle mai kyau suka wanke hannayensu suka goge danshin hannunsu. A sannan ne xaya daga cikin kuyangin ta dubesu tace. 61 BAYAN MUTUWA “Yanzu zan sa a raka ku izuwa xakin barcin kowannanku” Koda jin haka sai Amzad yace. “Aa kada ku rabani da mahaifiyata, ban tava kwana ba tare da ita ba” Koda jin haka sai gaba xaya kuyangin suka bushe da dariya, babbar cikin su wacce ta fara magana da farko ta dubeshi cikin mamaki tace. “Yanzu kai da girma nan naka kana cikakken saurayi amma baka tava rabuwa da shimfixar mahaifiyar ka ba, sai kace wani qaramin yaro?” Amzad ya gyaxa kai cikin murmushi yace. “Qwarai kuwa domin bani da kowa a cikin wannan duniya face wannan mahaifiyar tawa, bani da uwa bani da uba maraya na taso, bani da damuwa ko ‘yar uwa kuma ban tava yin aboki ba ko qawa. Bani da budurwa ta yaya kike tsammanin zan iya rabuwa da uwata a dare xaya alhalin tun sa’adda take dauke da cikina muke tare kawo i yanzu?” koda Amzad ya zo nan a zancensa sai jikin gaba xayan kuyangin ya yi sanyi suka kamu da tsananin mamakinsa gami da tausayinsa cikin qaramar murya shugabar kuyangin ta dubi wata daga cikinsu tace. “Maza ki kai su babban xakin barci na gidannan, haqiqa raba wannan uwa da xanta ba qaramin aiki bane” Nan take aka yiwa Amzad da 62 BAYAN MUTUWA mahaifiyarsa jagora izuwa cikin wani qaton xakin barci maixauke da wani shimfixexen luntsumemen gado wanda yasha shimfixu masu taushi gami da qaton bargo da kuma matasan kai guda huxu. Da yake lokaci ne na sanyi sai Amzad ya kama mahaifiyarsa ya kwantar da ita akan gadon sannan shima ya kwanta a kusa da ita ya janyo qaton bargon ya lulluve jikinsu gaba xaya. Koda mahaifiyar tasa taji tsananin taushin katifar da suke kwance akai kuma taji xumin qaton bargon da suke lulluve das hi sai ta kama kuka tace. “Yakai xana ka yi sani cewa a rayuwata ban tava zaton cewa za mu sake tsintar kanmu a cikin irin wannan daular ba wacce rabon mu da ita tsawon shekaru ashirin da biyar kenan tun kafin ka zo wannan duniya lokacin da mahaifinka ke raye” koda jin wannan batu sai hawaye ya zubowa Amzad yace. ‘Yake Ummina na so ace kina gani da idanunki domin kiga irin hawayen farincikin dake zubo akan kumatuna kuma kiga irin kayan alatun dake cikin gidannan, ki tuna cewa munsha kwana a kasa bisa tabarma kuma a filin Allah inda ruwa da iska ke qarewa a kan mu amman yau gamu a cikin qereren 63 BAYAN MUTUWA gida na kwatance bisa gado na alfarma kuma munci irin abinci da sai mai isane ke cinsa. Wai shin da me za mu iya sakawa wannan ‘yar sarki?” koda jin wannan tambayar sai hankalin Mahaifiyar tasa ya dugunzuma ta rasa abinda za ta ce masa, kawai sai tace ai. “ Kawai sai dai muce Allah ya saka masa da alheri” ta xan yi shiru taci gaba da cewa da shi. ‘Kai kar ka cikani da tambaya ka hanani barci akan wannan daddaxan gado sai da safe” Tana gama faxin hakan sai ta sake jan bargo ta lulluve fuskarta gaba xaua ko da ganin haka sai shima Amzad ya lulluve fuskarsa nan danan kawai barci ya sacesu ba tare da sun sani ba. Al’amarin sarkin yaqi kuwa lokacin da ya tafi da attajiri Huzulu izuwa can babban kurkuku na birnin Misra basu fuskanci wata matsala ba babu wani hari da aka kai musu har suka isa kurkuku. Da zuwan su sai sarkin yaqi ya isar da saqon gimbiya Lashmin izuwa ga shugaban masu gadin kurkukun cikin biyayya shugaban wani narkeken qato mai qirar mutanen farko ya risina ga sarkin yaqi cikin biyayya yace, 64 BAYAN MUTUWA ‘An gama ya shugabana” Nan take aka saka wasu masu gadin kurkukun subiyo suka karvi attajiri Huzulu daga hannun dakarun sarkin yaqi aka zuba masa sarqi a hannunsa da kafafunsa kawai sai suka ji attajiri Hauzulu ya taqarqare ya bushe da dariyar mugunta, al’amarin da ya yi matuqar baiwa sarkin yaqi tsoro da mamaki kenan. Daga can attajiri Huzulu ya murtuke fuska ya dubi sarkin yaqi yace masa. “Wannan gidan da kuka kawoni ji nake kamar a cikin gidana kuka kawoni, na rantse da darajar iyayena da kuma darajar abin bautarmu kana barin nan da tazarar sa’a xaya jal za a zo a fitar da ni daga cikin wannan kurkukun”. D aga can sai attajiri Huzulu ya murtuke fuskarsa ya dubi sarkin yaqi yace “Wannan gidan da kuka kawoni ji nake kamar a cikin gidana nake. Na rantse da darajar iyayena da kuma darajar abin bautarmu kana barin nan da tazarar sa’a xaya jal za’a zo a fitar da ni daga cikin wannan kurkuku” Ya xan yi 65 BAYAN MUTUWA shiru na wani xan lokaci yana kallonsa sannan ya ci gaba da magana cikin izza. “Ga saqo kaje ka gayawa Gimbiya kace da ita ni attajiri Huzulu na rantse da jinin uwata da ubana ita bata isa ta iya tozartani ba a cikin wannan duniyar, ka yaga mata cewa na gaba ya yi gaba na baya sai labari. Sannan ka shaida mata cewa lallai ta tabbatar da cewar ta mori jin daxin wannan mulki da take kai a iya tsawon ‘yan kwanakin da sarki ya ara mata domin kwanakin na qarewa zata zama baiwata, domin misra gaba xaya zata zama tawa. Saqo na qarshe a gareta ka gaya mata cewa wannan wulaqancin da tayi mini saboda tsohon masoyinta tun quruciya ta yi shi a banza domin bazata iya karve dukiyarsa dake hannuna ba ta damqa masa, kuma har abada ita da shi ba za su tava zama abokan rayuwa ba” Koda attajiri Huzulu ya zo nan a zancensa sai sarkin yaqi ya fusata ainun ya gabza masa naushi a fuska. Saboda qarfin naushin sai da attajiri Huzulu ya faxi qasa jini ya furzo waje daga bakinsa. Attajiri Huzulu ya miqe tsaye ya shafa bakinsa yaga jini kawai sai ya sake bushewa da dariya sannan yace. 66 BAYAN MUTUWA “Kayi babbar nasara hard a ka samu ka naushi babban maqiyinka. Yau zan sanar dakai babban sirrin da baka sani ba, ni ne na kashe ubanka domin na sauya tsarin gidan sarauta mu saboda shi ne kaxai baya bani haxin kai a cikin ‘yan majalisar sarki” Koda jin wannan batu sai sarkin yaqi ya daddage ya kurma ihu kuma ya zare takobinsa ya xagata sama ya kaiwa attajiri Huzulu sara amma sai shugaban kurkukun ya yi wuf ya zare tasa takobin ya kare saran ya dube shi a fusace yace. “Ai yanzu baka da sauran iko akan wannan fursuna face mun sami umarni daga wajen sarki ko Gimbiya” Koda jin wannan batu sai sarkin yaqi ya kamu da tsananin baqin ciki gami da takaici domin inda yasan cewa attajiri Huzulu ne ya kashe masa mahaifinsa da tun xa zu akan hanya zai kashe shi sai dai ya fuskanci kowane irin hukunci daga wajen sarki. Cikin tsananin fushi sarkin yaqi ya dakawa shugaban dakarun gidan kurkukun tsawa yace. “Ka bani attajiri Huzulu na kashe shi yanzu take anan ko kuma kai na yaqeqa na kasheka” Koda jin haka sai gaba xaya Dakarun dake tsaron kurkukun suka rugo da gudu izuwa bayan shugaban nasu suka 67 BAYAN MUTUWA zazzare takubbansu sai gashi sarkin yaqi da dukkan dakarunsa sun zama ‘yan kaxan a cikinsu. Attajiri Huzulu ya sake bushewa da dariyar mugunta a karo na biyu ya dubi sarkin yaqi yace masa. “Kai yaro ni murucin kan dutse ne ban fito ba sai dana shirya. Bakin rijiya ba wajen wasan yaro bane. Kaje ka rungumi qaddara ka qarasa rayuwarka a matsayin bawan sarki idan kuwa kace zaka tavo tsuliyar dodo wanda a halin yanzu barci ya keyi, tofa idan ya farka sunanka gawa” koda gama faxin hakan sai attajiri Huzulu ya dubi wannan narkeken qato wato shugaban Dakarun kurkukun yace. “Yakai mandazi maza kasa a kaini xakina” Ba tare da wata gardama ba kuwa mandazi yasa aka kwance sarqoqin dake jikin hannun attajiri Huzulu da qafafunsa aka ruke hannayensa aka tafi dashi, su kuwa su sarkin yaqi sai aka ritsasu da makamai har sai da aka ga sun juya sun fice daga cikin kurkukun gaba xaya sannan aka rabu dasu aka maida qofa aka rufe. Nan fa baqin ciki ya turnuke sarkin yaqi ya dubi gaba xaya yaransa yace “Haqiqa birnin misra bata sarki bace, ta attajiri Huzulu ce, Gimbiya ba zata iya yaqi da attajiri Huzulu ba tunda sarki ya kasa, mu qalilan ne a cikin wannan masarautar bama tare da 68 BAYAN MUTUWA Huzulu, duk abinda ya faxa sai ya faru, tabbas nan da cikar sa’a guda za a fitar da shi daga cikin wannan kurkuku” Koda jin wannan batun sai xaya daga cikin yaran nasa ya dube shi yace. “Haba ya shugabana ta yaya za a iya zuwa a fitar da attajiri Huzulu daga cikin wannan kurkuku mai tsananin tsaro haka alhalin sama da shekaru xari baya ba a tava samun fursunan daya tava guduwa ba daga cikinsa?” Koda jin wannan batun sai sarkin yaqi ya jinjina kai yace. “Ai kuwa yau za ka ga abin mamaki da idanunka, lallai abinda bai tava faruwa ba a qasarnan yau zai faru, yanzu abinda zai faru za mu samu waje mu voye mu zuba idanu muyi kallo kawai” Koda gama faxin haka sai sarkin yaqi yaja gaba xayan dakarunsa suka ruga izuwa can saman wani tsauni dake can nesa kaxan da inda kurkukun yake suka kwanta. Da yake akwai tarin bishiyoyi masu duhuwa akan tsaunin kuma gashi darene babu yadda za a iya mutum ya gane cewa akwai mutum a saman tsaunin. Haka dai su sarkin yaqi suka ci gaba da lamvo akan tsaunin har tsawon sa a guda basu ga wani abu ya faru ba, har sarkin yaqi ya yunqura zai tashi tsaye 69 BAYAN MUTUWA sai kawai ya hango wasu xaruruwan waxansu manya aljanu a can qololuwar sama sun tun karo wannan kurkukun tun da sarkin yaqi da dakarunsa suka zo duniya ba su tava ganin aljanu masu tsananin girma da muni irin su ba. Nan take wasu daga cikin yaran sarkin yaqi suka zube a sume,wasu suka haukace, shi kansa sarkin yaqi ba don yana da qarfin sihirin tsafiba da nan take zai haukace shima. 70 BAYAN MUTUWA ** Kai tsaye jibga-jibgan aljanun suka duro qasa bisa turba a tsakiyar kurkukun. Duk badakaren daya sha gabansu da nufin ya yaqesu sai dai aga naman jikinsa ya zagwanye ya zama kwarangwal,sutural jikinsa ce kaxai take ragewa zube a qasa. Al’amarin daya razana dukkanin dakarun kurkukun kenan suka rinqa rugawa da gudu suna vuya, kai bama dakarun kurkukun ba hatta fursunoni vuya suka rinqa yi duk da cewa sun sami damar guduwa saboda tsoron yin arba da waxannan mugayen aljanun. Ko bango aljanun suka dosa sai dai kaga yarushe ya zube qasa, qofar qarfe kuwa narkewa take ta zama ruwa. Shugaban Dakarun kurkukun kuwa wato mandazi da hannunsa ya buxe xakin da attajiri Huzulu ke ciki ya fito das hi ya damqawa aljanun. Ba tare da attajirin Huzulu ya yi wata razana ba kawai sai ya nufi

Chapter 3 of 6