Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
1 / 6
An dauko wannan littafi daga shafin https://taskarnovels.com.ng ku ziyarci shafin na https://taskarnovels.com.ng domin samun kayatattun littatafan hausa kama daga kan na yake yake dana soyayya Marubuci ko marubuciya zasu iya turo mana da littatafansu mu dora masu a shafinmu kyauta don masoyansu su rika Downloading a online, Sannan marubuta zasu iya turo mana da tarihin rahuwarsu da tarihin rubutunsu, dama sharhin littatafansu don masoyansu su gani kuma su karu da hakan Domin turo mana da littafi ko tarihin rayuwar marubuci ko marubuciya sai ayi mana magana ta whatssap da wannan nambar +2348140419490 A lura dakyau - kyauta muke saka littafi a shafinmu bama amsan ko sisin marubuci, duk wanda ya amshi kudinku da sunanmu babu ruwanmu, Alura dakyau - manazarta bama tura littafi ta private ku dena binmu private kuna neman mu tura maku littafi, duk mai bukatar littafi yaje website namu Alura da kyau - Littatfanmu suna fitowa cikin manhajoji uku ne PDF,TXT da DOC amman munfi amfani da PDF da TXT masu amfani da wayar android ko tablet ko computer zai fi kyau ku riga dauko PDF da DOC Masu amfani da kananan wayoyi java ko mara java TXT zakuna zaba don shine daidai wayarku This hausa novel was uploaded and downloaded from https://taskarnovels.com.ng You can download more hausa novels there Also you can send us your novel to upload it in our website for your fans to download it online It is free we do not charge for uploading novel Also if you are an Author be it online or Non online you can send us your biography including your book summary,commentary and others via this number +2348140419490 its free we do not charge for our services Note that - we do not charge for our services we uploaded novels and posted biography free, any person that collect your money in our name is your fault do not blame us Note that - pls readers stop calling us and be asking us to send you a novels we are not sending novels through whatssap or private our novels is public at any day, any time you can visits our site and download it Note that - our ebooks came as PDF,TXT or DOC format but the popular format are PDF or TXT, those with android or tablet or pc we suggest you to download PDF or DOC those with java phone or non-java phone we recommend you to download TXT This Novel is downloaded from https://taskarnovels.com.ng to download more hausa novels visits our site at www.taskarnovels.com.ng For feedback and support Facebook : https://facebook.com/taskarnovels Twitter : https://twitter.com/taskarnovels Telegram : https://t.me/taskarnovels BAYAN MUTUWA BAYAN MUTUWA Abdul-aziz Madakin Gini 1 BAYAN MUTUWA HAKKIN MALLAKA 2022 BUGU NA BIYU 2023 Bugu na uku 2024 2 BAYAN MUTUWA Bayan mutuwa K wance take akan luntsumeman gado irin na su na sarakuna tana ta faman sharar barci tamkar wata gawa, ko alamar tashi bata da niya, kallo xaya za ka yi mata a cikin rigar barcin da take sanye kasan Allah ya yi baiwarsa domin indai batu na kyau ne bata da tsara a nahiyar gaba xaya. Gimbiya lashmin ta kasance doguwar mace mai matsakaicin kaurin jiki,qirjinta a cike yake kuma tana da tudun baya, wuyanta dogo ne, tana da daradaran idanuwa gami da siririn dogon hanci, bakinta xan qarami ne kamar an yanka da wuqa mai xauke da lava masu tashin gaske. A yanzu haka da take kwance tana barci fuskarta cike take da annuri gamida wani irin murmushi irin wanda ka iya sabauta duk xa namiji daya haxa idanu da ita. 3 BAYAN MUTUWA A wannan lokacin gari yaw aye har hasken rana ya hudo ta cikin tagar xakin, gaba xaya kuyanginta na tsaitsaye zagaye da gadon da take kwance suna son su tasheta daga barci amma tsoro ya hanasu duk da cewar kuwa mahaifiyar Lashmin xince ta bayar da umarnin a rinka tashinta daga barcin a daidai irin wannan lokacin. Ba komai ne yasa kuyangin suke tsoron Gimbiya Lashmin ba face ita a rayuwarta ta tsani ayi mata bauta tafi son tayi komai da kanta. Sarauta da kuma daular data ke ciki ko kaxan bata dameta ba, inda son ranta ne tafi son tayi rayuwa irin ta sauran talakawan gari, kai inda za a qyaleta zata iya barin birinsu na Basra ta tafi can wani garin inda ba a santa ba tayi sabuwar rayuwa cikin qasqanci ba tare da wani yasan matsayinta ba. Kuyangin na tsaitsaye cikin halin tsananin tsoro da damuwa saboda gudun kada su yi laifi biyu. Laifin na farko shi ne basu bi umarnin mahaifiyar Lashmin ba sun tashe ta daga barci. Laifi na biyu kuma suna tsoron karya dokar Gimbiya Lashmin ta cewar kada wanda ya sake tashinta daga barci har sai ta farka da kanta. 4 BAYAN MUTUWA Kwatsam sai suka ga Gimbiya Lashmin ta yi juyi akan gadon kuma ta miqe zaune zumbur daga kwance kamar wadda ta farka daga mugun mafarki. Koda taga kuyanginta a tsaitsaiye kewaye da ita sai ya qyalqyale da dariya tace. “Na tashi da kaina ko? Babu wanda ya tashe ni daga barci ko?” koda jin wannan tambayar sai shugaban kuyangin nata mai suna Ilela ta dubeta cikin murmushi da girmamawa tace. “Ya shugabata babu wanda ya tasheki daga barci kece kika farka da kanki” koda jin haka sai farin ciki ya lulluve Gimbiya Lashmin tace. “Yauwa haka nake so ya kasance ina iya yin komai da kaina ba sai kunyi min ba,yanzu kuma zanje kewaye na yi wa kaina wanka” Koda jin haka sai hankalin ilela dana sauran kuyangin ya duguzunma ainun. Ilela ta dubi Gimbiya Lashmin a lokacin da idanunta suka zazzaro, fuskarta na nuna alamun tsananin tsoro tace. “Gimbiya ki rufa mana asiri kiyi sani cewa idan mahaifiyarki ta samu labarin cewar yau kinyi wanka da kanki sai tasa anyi mana horo mai tsanani...” Kafin Ilela ta gama rufe bakinta tuni Gimbiya 5 BAYAN MUTUWA Lashmin ta tari numfashinta tana mai doka mata tsawa tace. “Yanzu shi kenan ni har abada bazan tava samun ‘yancina ba? Tun ina jaririya ake yi min komai ba’a tava barina na yi wani abu ba, hatta goge haqora das a takalmi. Ni kam na tsani gidannan na tsani komai da kowa dake cikinsa”. Koda Gimbiya Lashmin ta zo nan a zancenta sai kawai ta ji muryar mahaifiyarta tana mai cewa. “Qwarai kuwa duk abinda kike faxa gaskiya ne, kuma kisani bama ke ba hatta mahaifinki ma sau xaya ya tava sa takalmi da hannunsa wannan itace al’adar gidannan kuma wannan al’adae ba zata tava sauyawa ba har abada muddin ire-iren gidan na raye a doron qasa” Cikin matuqar damuwa Gimbiya Lashmin ta waiga bayanta ta dubi mahaifiyarta a lokacin da ta shigo cikin turakar kuma ta durfafo inda take da isowarta gareta sai ta kama hannunta ta jata izuwa cikin kewaye kuma ta yafito kuyangin da hannun suka biyo bayansu. Haka dai taci gaba da lallava Gimbiya Lashmin tana faxa mata kalmomi masu taushi gami da kwantar da hankali har suka iso gaban bahon wankanta wanda aka yi shi da zinare cike da ruwan 6 BAYAN MUTUWA xumi ga qamshin turaren miski na tashi a cikinsa kuma ga waxansu ganyayen fure ruwan xorawa a kansa. Ba tare da vata wani lokaci ba kuyangi huxu suka kwavewa Gimbiya Lashmin rigarta ta barci suka shigar da ita cikin bahon wanka suka shiga yi mata wanka suna cuxa sassan jikinta a lokacin da mahaifiyarta ta koma gefe xaya ta zuba musu idanu kawai. Nan take Gimbiya Lashmin ta ji wani irin mugun baqin ciki yayi mata katutu a cikin ranta don haka bata san sa’adda idanunta suka ciko da qwalla ba har hawaye ya suvuce mata. Haka dai ta haqura bisa dole har aka gama yi mata wanka. Bayan an gama wanka wankanne aka fito da ita daga ciki aka tsane dukkan danshin dake jikinta sannan aka shafe duka jikinta da man zaitun. Daganan kuma sai aka kawo tufafi irin nasu na ‘ya ‘yan sarakuna mai tsananin kyau da tsada aka sanya mata. Koda aka kawo Gimbiya Lashmin gaban madubi ta kalli kanta taga irin tsananin kyau da Allah ya bata da kuma yadda tufafin jikinta ya dace da kyawun nata bata san sanda ta saki murmushi ba. 7 BAYAN MUTUWA Tace a cikin ranta haqiqa duk ‘xa namijin daya sameni a matsayin abokiyar rayuwarsa ba qaramin dace ya yi ba”. Bayan Gimbiya Lashmin ta gama duba kyawunta a gaban madubi sai kuma aka tafi da iya izuwa cikin wani dogon xaki wanda ananne suke cin abinci ita da iyayenta. Babu komai a cikin wannan xakin face wani dogon teburi wanda tsawonsa yakai kamu saba’in faxinsa kuma kamu ashirin ne kacal. Duk girman wannan tebur kujeru uku ne kacal a qarqashinsa. Biyuu na can qarshensa a jere, xaya kuma na farkonsa, bisa teburin an zuba kwanukan abinci sama da kala xari biyu kowane kwanon na xauke da abinci iri daban-daban. A gaban kowane kwanon akwai kuyanga guda xaya wacce ta ruqe falan da cokali, kawai jira take a bata umarni ta zubo abinci ta kawo. Da shigowar Gimbiya Lashmin cikin wannan xakin cin abinci sai ta iske iyayenta zaune akan waxannan kujerun guda biyu dake can qarshen teburin, tuni sun rigata halattar xakin koda suma suka yi arba da ita sai sarki Sairan ya dubi matarsa Gimbiya Marita yace. 8 BAYAN MUTUWA ‘Yau kuma me aka yiwa Gimbiya Lashmin naga ko kaxan babu annuri akan fuskarta?” koda jin wannan tambayar sai Marita ta yi xan guntun murmushi tace. “Babu abinda aka yi mata, halin natane dai wanda kasanta da shi. Har yanzu taki karvar ni’imar da Allah ya bata, kullum so take a barta ta yi komai da kanta” Koda jin wannan batun sai nan da nan fuskar sarki Sairan ta sauya yanayi daga annuri zuwa fushi, bai san sanda ya doki teburin ba da tafin hannunsa al’amarin daya razana Marita. Gimbiya Lashmin da gaba xaya kuyangin dake tsaitsaye a gabansu, kawai sai ya miqe tsaye ya taho izuwa ga Gimbiya Lashmin ya tareta tun gabanin ta zauna akan kujerarta, take jikin Gimbiya Lashmin ya kama karkarwa saboda tsananin tsoron mahaifinta data ji ya kamata. Koda sarki sairan ya iso daf da lashmin yadda suna iya jin numfashin juna sai ya dubi gaba xaya kuyangin dake cikin xakin yayi musu wata inkiya. Take kuyangin suka fice suka barsu su uku kacal. Fitarsu ke da wuya sai sarki Sairan ya dakawa Lashmin tsawa ta sake firgita ainun taji kamar hantar cikinta zata faso cikinta ta faxo qasa yace. 9 BAYAN MUTUWA “Sau nawa zan gaya miki cewar kada ki qara nunawa kuyanginki cewar bakya son ayi miki hidima? Sau nawa zan gaya miki cewar ki zamo mai izza,girman kai da nuna isa?” koda jin waxannan tambayoyin sai Lashmin ta sunkuyar da kanta ta kas tayi shiru kamar wadda ruwa ya ci kuma jikinta ya ci gaba da karkarwa fiye da farko. Cikin xaga murya sarki sairan yace “Wannan shi ne cikar mulki da iko, idan baki da su ba za ki iya hawa kan karagata ba, dole mai mulki ya zama yafi kowa tausayi da rashin imani, domin ya iya zarta da mulkinsa daidai, ke kuma tausayi gareki zallah ba ki da rashin imani, dole mai mulki ya zama mai girman kai gami da izza, ke kuma sauqin kai ne dake tamkar ruwan sanyi. Dole ne ki zamo mai zafi ga talakawanki kuma ki zamo mai jin qansu da taimakonsu. Babu irin horon da bansa an baki ba akan haka amma ba kya amfani da su. To ki sani cewa daga yau na kafa miki doka ba zaki sake fita ko ina ba daga cikin gidannan har sai kin fara aiwatar da horon da nasa aka baki a aikace saboda haka zan baki riqon karagata na tsawon kwana bakwai, idan kika tsalake wannan jarrabawa za ki ci gaba da fita rangwadinki 10 BAYAN MUTUWA zuwa duk inda kike so, idan kuma kika kasa hayewa wannan jarrabawar har abada kin daina fita koda daga cikin turakarki har zuwa ranar da zan bar wannan duniyar”. Koda gama faxin hakan sai sarki sairan ya juya ya koma can inda matarsa marita ke zaune ya zauna yana mai tafa hannayensa biyu. Nan take kuyangin suka dawo cikin xakin kowacce ta tsaya a inda take da, a sannan ne itama Gimbiya Lashmin ta zauna akan kujera jikinta a matuqar sanyaye kuma hankalinta ya dugunzuma saboda tasan halin mahaifinta, indai ya furta zai yi abu tofa sai ya aiwatar da shi. Ba tare da vata wani lokaci ba suka fara cin abinci duka su uku. Nan take Gimbiya Lashmin ta yi abinda basu tava ganin tayi ba domin kuyangar dake kusa da ita ta duba ta daka mata tsawa tace. ‘Maza ki xebo min abinci da na saba faraway da shi mana, ko kuma sai na hamvareki da qafata tukunna” Jikin kuyangar yana rawa tayi sauri ta zuba mata abinci akan falan ta ajiye a gabanta. Koda ganin haka sai farin ciki ya lulluve sarki saihan ya dubi marita yace. 11 BAYAN MUTUWA “Ta fara sauyawa fa” Koda jin haka sai marita ta yi dariya tace. “Ai kasan duk duniya babu abinda Gimbiya Lashmin take so sama da zuwa cikin jeji kuma ta yawata izuwa sauran birane da qauyukan qasar nan” Sa’adda sarki saihan ya ji haka sai ya yi murmushi yace. “Ai duk wannan mai sauqi ne muddin zata zama kamar ni” Koda jin haka sai marita tayi sauri ta ajiye cokalin da take cin abinci da shi ta dubi sarki saihan cikin alamun razani tace. “Ta yaya ‘yarta zata zama kamar ka? Alhalin ta kasance ‘ya mace kuma bata kasance jaruma ba?” Da jin haka sai sarki saihan ya bushe da dariya sannan yace. “Ai ba ina nufin ta zama jaruma ba, ko mayaqiya ina nufin zuciyarta ta zamo dakakkiya irin ta sarakai wadanxa za su iya tafiyar da mulkinsu” Marita tayi ajiyar zuciya tace. “Da sannu ‘yarta zata kai wannan matsayin da kake so ammafa dolene sai kayi haquri kuma ka jira lokacin, ni yanzu babban abinda yake damuna batun auren wannan yarinya. A gaba xaya qasar nan babu wata ‘ya mace mai kyau da farin jininta ‘ya ‘yan 12 BAYAN MUTUWA sarakai da ‘ya ‘yan manya attajirai da yawa sun nemi auren Gimbiya amma kaqi basu. Shin kamanta cewa itace kaxai ‘ya a garemu? Shin ka manta cewa girma ya fara kamamu? Me yasa baka son muga jikokin mu? Kasani cewa ko Lashmin ta zama sarauniyar qasar nan dole ne tayi aure. Zaifi kyau tun yanzu ma ka sauka daga kan karagarta ka bata kuma ka zava mata mijin daya dace da ita. Koda jin wannan batu sai sarki saihan ya gyaxa kai sanan ya kawo gwauron numfashi ya ajiye yace. “Ina nan ina tunani da aiki akan haka kuma nan bada daxewa ba komai zai kammala. Kinsani cewa dolene nayi wa ‘yarmu zave mai kyau kuma mafi alheri a gareta domin bayanmu ta yi kyau kuma ta xore” Haka dai sarki sairan da marita suka yi ta tattaunawa akan gimbiya Lashmin ita kuma lashmin sai ta ci gaba da cin abincinta kawai tunda bata jin abinda suke tattauna saboda nisan dake tsakaninsu amman kuma ta tsargu cewa akanta suke magana bisa ganin yadda suke yawan kallonta. Bayan sun kammala cin abinci kowanne su an wanke hannunsa an goge maiqon dake bakinsa sai suka miqe tsaye tare, sarki ya fito Lashmin da hannu ta taho garesu. Da zuwanta sai ta faxa kan qirjinsa 13 BAYAN MUTUWA suka rungume juna sannan ya janye jikinsa daga cikin nata ya sumbaci goshinta yace. “Kamar yanda na gaya miki xazu yaune za ki fara yin jarrabawar don haka nan da cikar rabin sa’a kije ki gama shiri ina son ki shammaci kowa kawai sai dai fadawa na da sauran jama’ar gari su ganki akan karagata, bayanin farko da za ki soma yi musu ina kwance bana jin daxi shi yasa kika wakilceni, daga nan sai kici gaba da gudanar da al’amuranki na mulki kamar yadda kika ga ina yi kullum” koda gama faxin haka sai sarki ya kama hannun marita ya jata suka fice daga cikin xakin cin abinci suka bar Gimbiya Lashmin a tsaye cikin fargaba, tunani gami da mamakin dalilin da yasa yau rana xaya sarki ya yanke wannan hukuncin na yi mata wannan jarrabawa. Babban tashin hankalita shi ne yadda zata gabatar da shari’a a fada tayi hukunci ga wanda aka zallunta kowa wanda ya aikata laifi. Duk abin da ya shafi sai an zubar da jini ko an musgunawa wani Lashmin bata son shi, saboda tsananin tausayinta amma kuma yanzu bata da wani zavi wanda yafi tayi wannan hukunci bisa dole don kada sarki ya kafa mata takunkumi fita rangadi da koma katse mata burinta na son yawantawa a cikin kasar. 14 BAYAN MUTUWA Lashmin na tsaye a cikin xakin cin abinci tana ta tunani har izuwa tsawon daqiqu masu xan yawa har sai da shugabar kuyanginta ta shigo ta dafa kafaxarta sannan ta dawo cikin haiyacinta ta dubeta a razane kamar wacce ta farka daga mafarkin ban tsoro, shugabar kuyangan tace. “Ranki ya daxe shin kin manta ne cewa za mu yi miki shirin zuwa fada?” koda jin haka sai Lashmin ta saukar da ajiyar zuciya tace. “Haka ne fa muje mana” Nan take shugabar kuyanginta ta wuce gaba Lashmin na biye da ita sannan sauran kuyangin suka take musu baya. Cikin qanqanin lokaci aka sauyawa Gimbiya Lashmin tufafi aka sanya mata irin tufafin shiga dafa. Aka kawo mata alkyabba irin ta mata mai darajar gaske aka yafa mata kuma aka xora mata hular mulki ta lu’u lu’u akanta. Hakan ne ita kanta Lashmin da ta dubi kanta a cikin madubi taga yadda wannan shigar tayi mata kyau sai ta dubi shugabar kuyanginta tace. “Tabbas mulki yana da daxi, amman bana son shi saboda har naji wani irin girman kai ya fara shiga jikina saboda kawai na sanya wannan tufafin na alfarma. To idan kuma na shiga fada fa naga 15 BAYAN MUTUWA fadawa,bayi da hadimai sun fara gaisheni suna girmamani? Ni kam idan na gama wannan jarrabawar da sarki zai yi min bazan sake yarda na sanya irin wannan tufafin ba har abada, maza mu wuce zuwa fada. Saboda sarki ya bani umarnin lallai na riga fadawansa zuwa fada” Nan take shugaban kunyangi ta sake yiwa Gimbiya Lashmin jagora suka fice daga cikin turakarta suna fita sai dakarun dake tsaron lafiyarta su arba’in suka rufa mata baya, tun a qofar turakarta Lashmin taga sabon sauyi, domin gaba xaya hadiman da suke binta sarki duk wajen da zai je ta gani tsaye suna jiranta. Ai kuwa tana fitowa sai dukkansu suka zube qasa gabanta suka kwashi gaisuwa sannan kowannen su ya kama aikinsa kamar yadda suka saba. Duk inda suka wuce a cikin gidan sarautar sai taga ana girmamata ainun fiye da yadda aka saba yiwa sarki shi ake yi mata domin nan take aka fara buga mata tambura ana busa kakaki da algaita, kuma gaba xaya jama’ar gidan suka rinqa zuwa suna zubewa qasa suna kwasar gaisuwa. 16 BAYAN MUTUWA BAYAN MUTUWA 2 oda ganin wannan al’amari sai hankalin lashmin ya dugunzuma ainun tace a cikin ranta, anya kuwa sarki ba yaudarata yayi bay ace jarrabawa zai yi, babu mamaki ya sauka ne daga kan karagarsa ya bar mata, koda gama ayyana hakan sai idanunta suka ciko da hawaye, koda taji qwallah tana shirin suvice masa sai tayi sauri ta sunkuyar da kanta qas don kada wani ya gani ta share hawayen. Tace a cikin ranta ina ma Allah bai yiyota ‘yar sarki ba. Da dai ace ita ba kowabace face ‘yar talakawa fitik masu neman abin da za suci kullum da ya fiye mata farin ciki da kwanciyar hankali a rayuwarta Haka dai su Gimbiya Lashmin suka ci gaba da tafiya a cikin gidan sarautar ana biye da ita xu tamkar wata tauraruwa mai tsananin haske a tsakiyar dubunnan taurari har aka iso cikin babbar fada ta gidan sarautar. Daga dakarun tsaron sai qananan fadawa sai kuma mutanen gari a zazzaune wato a tsaitsaye a cikin fadar. Koda shigowar Gimbiya Lashmin tare da ma’aikata masu take mata baya sai duk mutanen dake K 17 BAYAN MUTUWA zaune suka miqe. Koda aka ga Gimbiya Lashmin ta fito a maimakon sarki sai kowa ya cika da mamaki, aka wangame baki ana kallonta kawai, kai tsaye Lashmin ta nufi wajen da karagar mulki take tana tafiyar qasaita kamar wani toron giwa. Hatta yanayin tafiyarta irin ta sarki sairan ce. Haqiqa komai yana bin jini in da ace shigar maza Lashmin ta yi kuma ta rufe fuskarta to da kowa zai xauka sarki ne ya shigo fadar ba Gimbiya Lashmin ba. Da isar gimbiya Lashmin kan karagar mulkin sai ta zauna ta harxe qafa xaya bisa xaya tamkar dama can ta saba zama akan karagar. A sannane sauran jama’a kowa ya koma inda yake ya zauna kuma a daidai wannan lokacin manya fadawa da ‘yan majalisu qasar suka fara shigowa. Duk wanda ya shigo yayi arba da Gimbiya Lashmin zaune akan karaga mulki sai ya kamu da tsananin mamaki gami da tsoro don ba a san dalilin faruwar wannan canjin ba alhalin sarki yana raye. okacin da Gimbiya Lashmin ta lura da gaba xaya fadawa da ‘yan majalisu sun hallara sai ta yi gyaran murya take fadar tayi tsit aka saurara domin aji abinda zai fito daga bakinta. Duk wanda ta kalla sai taga yana muzurai L 18 BAYAN MUTUWA gami da haxiyar miyau kamar su tashi su matse bakinta tayi bayanin dole. A zuciyarta sai tace oh kaga miyagun banza kawai so suke suji wata maganar ta sharri bata alheri ba, domin su san yadda za su qula wani mugun makircin. Kawai sai aka ga Lashmin ta fara da yin murmushi sannan tace. “Yaku jama’ar wannan birni na sham kuyi sani cewar mahaifina bashi da lafiya amma duba ba wani ciwo mai tsanani bane don haka zan ci gaba da wakiltarsa har izuwa tsawon xan lokaci kafin ya warware, ina mai yi muku alqawari da cewar zan tafiyar da mulki bisa adalci kamar yadda mahaifina ke zarta da shi. Saboda haka ina fatan cewar ‘yan majalisa da dukkan dakaru da sauran shugabanni na birni da qauye za su bani haxin kai kamar yadda suka saba baiwa mahaifina. Yanzu take ina son a ci gaba da zarta da komai kamar yadda aka saba kuma zan saurari qara guda uku kacal a zaman da za mu yi yanzu, ina masu gabatar da qara?” Koda jin wannan tambayar sai wani dattijo daga cikin fadawan ya matso gaba kusa da 19 BAYAN MUTUWA karagar mulkinta a vangaren hannun dama ya zube qasa ya kwashi gaisuwa sannan yace. “Ya shugabata ni ne mai gabatar da qara a wannan fadar tsawon shekara talatin baya kamar yadda kika sani” Koda jin haka sai Lashmin ta yi murmushi tace. “Gaskiya ya kai Safwan bin ma’aruf bin kananata, tun kafin a auri mahafiyata kake wannan aikin. Kai ne ka gabatar da qarar waziri Dulnur wanda ya kashe amininsa ya aure matarsa kuma ya mallake dukiyarsa kimanin shekara talatin da shida baya anan fadar, da taimakon ka ne gaskiya ta bayyana har ka saka sarki kan’an ya yankewa waziri Dainur hukuncin kisa aka tsireshi a tsakiyar kasuwa ko ba haka abin ya faru ba?” Safwan ya risina yace. “Haka yake ranki ya daxe” Nan take jama’ar da suke cikin fadar suka kamu da tsananin mamaki bisa jin yadda Gimbiya Lashmin ta riqe wannan tsohon tarihin domin lokacin da al’amarin ya faru ba a ma san zata zo duniya ba. Lashmin ta dubi Safwan bin ma’aruf tace. “Karanto mini shari’ar farko na ji a kuma shigo da wanda ya kawo qarar da kuma wanda ake qara” koda jin wannan umarni sai Safwan ya miqe 20 BAYAN MUTUWA tsaye yaje bakin qofar da ake shigowa da masu shari’a yace. “Ina attajiri Huzulu da kuma saurayi Amzad a shigo da su”. Nan take sai ga wani dogon mutum ma’abocin kwarjini a cikin suture masu tsada ya shigo cikin fadar fuskarsa cike da annuri. Kallo xaya zaka yi masa kasan cewar babu wani abu da yake damunsa a rayuwa, yana tafe yana murmushi. Wanda ke biye da shi kuwa wani matashin kyakkyawan saurayine wanda kana yi masa kallo xaya zaka gane cewa in ba don talauci ba da bai kasance ramamme ba kuma da kyawunsa ya ninka hakan sau uku. Kai da ganinsa kasan yana fama da aikin wahala kafin ya samu abinda zai kai bakinsa, biye da waxannan mutane biyu dakarun fada ne. Koda Gimbiya da wannan matashin saurayin mai suna Amzad suka haxa idanuwa karon farko sai kowannensu yaji zuciyarsa ta buga da qarfi. Cikin hanzari Amzad ya sunkuyar da kansa qas don kada qurawa Lashmin idanu ya zama laifi ayi masa wani hukunci akan haka. 21 BAYAN MUTUWA Batare da vata wani lokaci ba aka gurfana da attajiri Huzulu da Saurayi Amzad a gaban Gimbiya Lashmin. Nanfa fadar tayi tsit tamkar mutuwa ta gifta sai da Lashmin ta qarewa attajirin Huzulu da Amzad kallo, tayi nazarinsu sosai sannan ta dubi Safwan bin ma’aruf tace. “Kafin a gabatar da wannan qarar ina son ayi mini bayani akan matsayin wanda ake qarar da wanda ya kawo qarar, ina son nasan sana’o’insu, mu’amalarsu da mutane da koma inda kowannensu ke da zama” koda jin haka sai mamaki ya kama gaba xayan jama’ar dake cikin fadar hatta manyan alqalai kuma na dukan kotunan qasar saboda wannan wani sabon salone bisa tsarin shari’ar qasar, Lashmin tazo da shi. Mai gabatar da qara Safwan bin mu’aruf ya juya ya fuskanci Gimbiya Lashmin yace. “Da farko dais hi wannan attajiri wanda kowa a garinnan ya sani da suna Huzulu yana zaune ne a unguwar sarakai kuma bashi da wata sana’a wacce ta wuce siye da siyar da gidaje da kuma bayar da hayar gida ko gona ko rumfar kasuwa. A cikin wannan birnin namu na Misra an tabbatar da cewa yafi kowa yawon gidaje da gonakai da kuma rumfunan kasuwa 22 BAYAN MUTUWA don haka ko sauran attajirai masu yin harkokin fatauci kalilan ne suka fishi yawan tsabar kuxi a hannu a qasar nan gaba xaya. Shi kuma wannan saurayi mai suna Amzad bashi da wata sana’a wacce tafi dakon tubalin gini ya kanje ya nemi aikin dakon tubali yana kaiwa inda ake gini abiyashi, wannan ita kaxai ce mu’amalar data haxashi da mutane. A kullum idan ya tashi daga aiki da yamma da zarar ya wanke jikinshi zai tafi ne izuwa can gidansu wanda ke kusa da gidan attajiri Huzulu a unguwar sarakai ya kaiwa mahaifiyarsa abincin da zata ci. Ita dai wannan mahaifiya tasu ta kasance tsohuwa tukuf, saboda tsufan ma bata gani da idanunta kuma bata iya taka qafafunta, ko kewaye zata shiga sai dai Amzad ya xauketa a hannunsa ya kaita” koda Safwan ya zo daidai nan a bayaninsa sai Gimbiya Lashmin ta xaga masa hannu kuma ta tari numfashinsa tana mai cewa. “Me yasa kake wuce gona da iri akan bayanin Amzad, amma sa’adda kake bayanin attajiri Huzulu sai ka taqaita komai yasa?” Koda jin wannan tambayar sai idanun Safwan suka zazzaro gaba xayan jama’ar dake cikin fadarma sai suka kama muzurai. 23 BAYAN MUTUWA Shi kansa attajiri Huzulu sai yayi fiqi-fiqi da shi

Chapter 1 of 6