Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
koshi ta faɗa tana ƙoƙarin hawa gado.. temaka mata yayi yana cewa kin dai gasa jikin ki ko tace shi ne jikin ki zai saki.., daga mai kai tayi magani ya ɓallo mata. dauko ruwa yayi ya miƙo mata yana cewa kisha zaki kara jin daɗin jikin ki.. amsa tayi ta sha tana runtsai idon ta, kauda kai tayi tana mai da kai ta kwanta. ranar haka ya yuni yana hidimar najlah tayi kuka ta gaji ta hakura sai kuma, takara ci gaba da kuka gaba ki ɗaya, ya rasa yadda zai yi da ita sai ririta, ta yake kamar kwai shaf ya manta da zancen jawaher da take asibiti. bayan ya dawo daga masallaci anyi sallar isha ya zauna yana kallon ta , yace '' najlah ni ko daukar ki zan yi na kaiki gidan Hisham safeera ce ta duba ki ta , ƙara dubawa domin wannan kukan da kika yuni kina yi kar ya lalata ciwon ki.. ni wallahi ba inda zani haka kurum ta ga gaba na.. shiru yayi ya zuba mata ido tun da yake be taɓa ganin wannan rigimar ba ga uwar shagwaɓa da take mai gaba ki ɗaya ta susuta shi..ta hana shi sakat idan tana wani abin sai ya shagala da kallon ta. dauke kai tayi tana turo bakin ta , tace '' uhmm yaya.., Jawad yace '' na'am najlah.., hawaye ta share tace '' yanzu tafiya zakai ka kwanta ko..?, eh akwai abin da zan miki ne..? yaya toilet zan shiga ina jin fitsari amma ban san ta ina zai fito ba ciwo na.. karki damu be shafi nan...ba da sauri ta kalle sa tace '' ta nuna maka ka gani ne..?, eh nagani.. da sauri ta ɗora hannu akai tana zaro ido tace '' dan Allah fa.., uhmmm na gani shikkenan ta kashe ni haka kurum ta nuna maka wallahi taci amanar aikin likita.. NAJLAH wallahi idan baki dena kukan nan ba ranki zai ɓaci wai me kika dauke ni ne tun ɗazu nake lallaɓa ki , kina kuka yanzu daga faɗar magana sai kuka, shi wannan kukan magani ne? abinci kinki ci na tambaye ki me kike so kinyi shiru.., ina kike so na saka rayuwa ta..?, ne kalli wunin yau yadda nayi shi ko baccin ɗazu dana kwanta kika zunduma ihu sai dana tashi amma ina zuwa naganki a yadda na barki.., shiru tayi tana kwanciya , tamkar ba da ita yake ba , ganin zai tafi yana shirin kashe mata fitila tace '' dan Allah ka dawo nan dakin ka shinfiɗa blanket a kasan gadon nan , ka kwanta.., to zanyi haka..yanzu zan tafi nayi wanka ne na shirya sai na dawo.. Najlah tace '' nima zan yi wanka..sai nayi fitsari, to ya faɗa yana daukar ta toilet ya kai ta ya nannaɗe mata riga ya saka ta akan masan zama riƙe shi tayi gam tana kuka tace '' yaki zubowa wallahi ciwo wayyo Allah na Hajiya ta wayyo aunty Hafsah wayyo Abba wayyo aunty rafi'at..., yau jawad yayi dana sani yafi sau nawa , gaba ki ɗaya ya damu kan'sa ganin halin da take ciki daman, ga ciwon najlah raki, ya lafiyar kura ɓalle tayi zawo hakuri ya rage mai shi yanzu wannan yadda ake faɗar ciki idan ta samu besan ya zai ba.., kwata kwata be dauki abin haka ba , jawaher tayi amma be kai na , najlah ba. dakyar ta cije tayi fitsari. fita yayi tai tsari sannan ya dawo ya haɗa mata ruwa ya fita, cikin sauri yake hawa sama dakin sa ya shiga da sauri ya dauki wayar sa ganin ana kira number inna ce , ɗagawa yayi yana karawa a kunne yace '' Assalamu alaiki.., haba Jawad ina ya ban ka sallah zaka , kasa alwala tun jiya da ka saka, kafa ka tafi yarinyar nan , na cikin mawuyacin hali ko a jikin ka shi ne baka dawo ba tun safe nake zuba ido ganin kai baka san zuru ba shi ne na kirawo wa ka barni tun kayan da na zo dasu jiya.. dafa kan'sa yayi yana cewa '' inna kiyi hakuri wallahi Allah aiki ne yayi min yawa , bawai ina sane naki zuwa ba insha'Allahu gobe zan kawo miki ya jikin nata.., uhmm da sauki anma ce a siya wannan maganin aeropin paracetamol.. kudin su dubu biyar.. dan jim yayi yana mamakin son kudi irin nama matar nan komai a asibitin bayarwa suke sai dai kawai su cira a kudin ka shine take mai wannan lissafin amma saboda ita din uwa ce sai yace '' insha'Allahu idan nazo zan baki.., yauwa sai anjima ko bari su gaisa ba suyi ba dariya yayi kai idan da ranka zaka sha kallo banda kudin data kwace shi ne yanzu take neman dubu goma.. shiga toilet yayi ya cire kayan sa , ta sakarwa kan'sa shower tana rufe idon sa , wani irin sanyi yake ji na ratsa shi da nutsuwa, albarka kuwa shi kansa besan iya adadin da ya sakawa najlah ba... ★★★. buɗe maltina tayi tana cewa mutuwar wani tashin wani rabon naci nawa kason Ubangiji ya kawo ni nan , Allah ya hana jaburu zuwa domin ɗazu yace besan me take kullawa ba zai zo ayi komai dashi tasan son zuciyar sa , jaburu a yanayin satar sa ko mutum ya samu damar sacewa sacewa zai yi , idan yazo nan shikkenan tata ta kare wuf wuf zai yi ya dinga kwashe komai da sauri ta dauki waya tana kallon jawaher tace '' wallahi jawaher idan jaburu yazo tofa komai ya tsaya min gwara na saka yar ɗagwas ta hana shi zuwa.. da kallo jawaher ta bita domin tun ɗazu take mamakin INNA har karyar da tayi tana jin ta kash bata san wane ya faɗawa INNA wannan maganar ba. ta kwaso jiki ta tawo gashi nan ko ɗazu sai da sukai fada da wata nurse ba'a isa a faɗa mata gaskiya ba sai tahau tijara yawa a gidan dambe aka raine ta. juyar da kai tayi dakyar tana fatan Allah ya kawo jujal yayi gaba da ita ko nawa ne zata bashi ya tattara ta su koma BINYERI. uhmmm kyayi kya gama sai wani kallo kike bina dashi wallahi jawa da ace ba'a gida na haife ki ba ta tabbas ce wa zanyi chanza min ke aka yi duk wani take taken ki ina lura tun jiya sai wani hade rai kike kina fici fici da ido, kamar kwallon a gwaluma ke daman ido ba ido ba.. karawa wayar tayi a kunne tace '' yauwa yar ɗagwas wani temakon za kiyi min kina jina naji kinyi shiru alooo aloo aloo (Hello ) ciro ta tayi a kunne dubawa tayi ashe ta , ta goce mita ta dinga yi tana ci gaba da shan maltinar ta, wata gyatsa tayi ta miƙe kafafuwan ta , tana cewa malam yaso yi min tsakiyar da babu ruwa ya cuce ni , ina can a zaune ko ficika baki san ki turo mib ba gaskiya jawa ban san inda kika gado wannan bakin halin ba.. ta fadi haka gana ƙoƙarin zira batirin wayar ta , ta ★★★ fitowa yayi daure da towel a kugun sa da wani kuma a hannu yana tsane gashin kansa zama yayi akan dressing mirror chair yana dauko mai ya soma shafawa zuciyar sa na gurin najlah ko yanzu ta gama zai je dai ya gani.. shaf shaf ya gama ya zura wando three-quarter daukan blanket yayi ya dauki wayar sa ya fita samin ta yayi a ƙasa daga ita sai toilet tana jan ajiyar zuciya.. ajiye kayan hannun sa yayi yana durkusawa yace '' har kin gama baki jira nazo na dauke ki ba..?, habawa najlah firgita tayi ganin sa ba kaya da sauri tayi baya towel din'ta ne ya kunce ba karamin gigita tayi ba da ganin sa da tayi ba kaya, jikin ta ya hau sama zikiri JAWAD da sauri ya riƙe ta yace.... Alhamdulilah ayau na kawo karshen book 1 Wannan litattafin na kudi ne 1k 8141785374 Amina alhasan Muhammad opay Turo da shedar biya ta wannan number 09061890481 Idan baki shirya ba , karki min magana dan Allah An dauko wannan littafi daga shafin https://taskarnovels.com.ng ku ziyarci shafin na https://taskarnovels.com.ng domin samun kayatattun littatafan hausa kama daga kan na yake yake dana soyayya Marubuci ko marubuciya zasu iya turo mana da littatafansu mu dora masu a shafinmu kyauta don masoyansu su rika Downloading a online, Sannan marubuta zasu iya turo mana da tarihin rahuwarsu da tarihin rubutunsu, dama sharhin littatafansu don masoyansu su gani kuma su karu da hakan Domin turo mana da littafi ko tarihin rayuwar marubuci ko marubuciya sai ayi mana magana ta whatssap da wannan nambar +2348140419490 A lura dakyau - kyauta muke saka littafi a shafinmu bama amsan ko sisin marubuci, duk wanda ya amshi kudinku da sunanmu babu ruwanmu, Alura dakyau - manazarta bama tura littafi ta private ku dena binmu private kuna neman mu tura maku littafi, duk mai bukatar littafi yaje website namu Alura da kyau - Littatfanmu suna fitowa cikin manhajoji uku ne PDF,TXT da DOC amman munfi amfani da PDF da TXT masu amfani da wayar android ko tablet ko computer zai fi kyau ku riga dauko PDF da DOC Masu amfani da kananan wayoyi java ko mara java TXT zakuna zaba don shine daidai wayarku This hausa novel was uploaded and downloaded from https://taskarnovels.com.ng You can download more hausa novels there Also you can send us your novel to upload it in our website for your fans to download it online It is free we do not charge for uploading novel Also if you are an Author be it online or Non online you can send us your biography including your book summary,commentary and others via this number +2348140419490 its free we do not charge for our services Note that - we do not charge for our services we uploaded novels and posted biography free, any person that collect your money in our name is your fault do not blame us Note that - pls readers stop calling us and be asking us to send you a novels we are not sending novels through whatssap or private our novels is public at any day, any time you can visits our site and download it Note that - our ebooks came as PDF,TXT or DOC format but the popular format are PDF or TXT, those with android or tablet or pc we suggest you to download PDF or DOC those with java phone or non-java phone we recommend you to download TXT This Novel is downloaded from https://taskarnovels.com.ng to download more hausa novels visits our site at www.taskarnovels.com.ng For feedback and support Facebook : https://facebook.com/taskarnovels Twitter : https://twitter.com/taskarnovels Telegram : https://t.me/taskarnovels

Chapter 20 of 20