Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
1 / 5
An dauko wannan littafi daga shafin https://taskarnovels.com.ng ku ziyarci shafin na https://taskarnovels.com.ng domin samun kayatattun littatafan hausa kama daga kan na yake yake dana soyayya Marubuci ko marubuciya zasu iya turo mana da littatafansu mu dora masu a shafinmu kyauta don masoyansu su rika Downloading a online, Sannan marubuta zasu iya turo mana da tarihin rahuwarsu da tarihin rubutunsu, dama sharhin littatafansu don masoyansu su gani kuma su karu da hakan Domin turo mana da littafi ko tarihin rayuwar marubuci ko marubuciya sai ayi mana magana ta whatssap da wannan nambar +2348140419490 A lura dakyau - kyauta muke saka littafi a shafinmu bama amsan ko sisin marubuci, duk wanda ya amshi kudinku da sunanmu babu ruwanmu, Alura dakyau - manazarta bama tura littafi ta private ku dena binmu private kuna neman mu tura maku littafi, duk mai bukatar littafi yaje website namu Alura da kyau - Littatfanmu suna fitowa cikin manhajoji uku ne PDF,TXT da DOC amman munfi amfani da PDF da TXT masu amfani da wayar android ko tablet ko computer zai fi kyau ku riga dauko PDF da DOC Masu amfani da kananan wayoyi java ko mara java TXT zakuna zaba don shine daidai wayarku This hausa novel was uploaded and downloaded from https://taskarnovels.com.ng You can download more hausa novels there Also you can send us your novel to upload it in our website for your fans to download it online It is free we do not charge for uploading novel Also if you are an Author be it online or Non online you can send us your biography including your book summary,commentary and others via this number +2348140419490 its free we do not charge for our services Note that - we do not charge for our services we uploaded novels and posted biography free, any person that collect your money in our name is your fault do not blame us Note that - pls readers stop calling us and be asking us to send you a novels we are not sending novels through whatssap or private our novels is public at any day, any time you can visits our site and download it Note that - our ebooks came as PDF,TXT or DOC format but the popular format are PDF or TXT, those with android or tablet or pc we suggest you to download PDF or DOC those with java phone or non-java phone we recommend you to download TXT This Novel is downloaded from https://taskarnovels.com.ng to download more hausa novels visits our site at www.taskarnovels.com.ng For feedback and support Facebook : https://facebook.com/taskarnovels Twitter : https://twitter.com/taskarnovels Telegram : https://t.me/taskarnovels 𝐃 𝐔 𝐍 𝐈 𝐘 𝐀 𝐓 𝐀 ΜΆBΜΆOΜΆOΜΆK ΜΆ2 β±§Ι„β‚²Ι„β‚₯β‚³ π™‹π˜Όπ™‚π™€ 1 π˜Όπ™’π™—π™žπ™©π™žπ™€π™£ & 𝙨π™ͺπ™˜π™˜π™šπ™¨π™¨ π™ˆπ™ͺ𝙝𝙖𝙒𝙒𝙖𝙙 𝙛π™ͺ'𝙖𝙙 π™Ÿπ™–π™™π™™π™– "Hustle until you no longer need to introduce yourself,push your self because no one else is going to do it for you". Kalamansa na qarshe kenan da tarin mayan attajiran da sukayi meeting na qarshe dasu wanda keson saka share dinsu cikin sabon kamfanin da kwanaki bakwai suka rage masa ya budeshi. Kalamai ne da suka dauki hankulan mutanen dake wajen,wanda dasu aka kammala zaman. Sanda yake sallama dash fiye da rabin hankalinsa yana kan wayarsa da tun dazun ya lura tana haske. Sai da gurin ya rage saura shi daya da hudu daga cikin guard dinsa da wannan karon dasu yayi tafiyar wadanda ke nesa da inda yake,ya miqa hannu a nutse yana jawo wayar gami da fesar da iska me dumi daga bakinsa. Cikin kowanne motsi yana jin farinciki na yadda al'amuran bude kamfanin ke gudana da dukkan wani haske qyalli da kuma alamu na nasara,bai taba qwallafa rai akan wani abu kaman haka ba,baisan me yasa dukka tunaninsa da hankalinsa suka raja'a wajen son ganin cikar wannan mafarkin nasa ba. Tunda yazo samu cikakken zama na awa biyu cur ba,saidai idan dare yayi ya wafci wasu awanni ya tilastawa kansa kwanciya ya huta. Kowanne minti idan ya shude da amfaninsa a wajensa,ko baya din dama shi mutum ne me girmama lokaci tare da bashi muhimmanci qwarai. Sunan farouq kawai daya gani ya sakashi gyara zama yana furta "Ya salam" Qasa qasa fuskarsa nason fidda wannan sihirtaccen murmushin nasa da ba kasafai ake samun dacen ganinsa ba. Wani sirri ne kwance cikin murmushinsa dake qara masa haiba da kwarjini da fitar asalin kyan da ubangiji ya huwace masa. Yasan zayasha qorafi ne kawai wajen farouq din......don yace masa zai kirashi har baisan adadi ba......hakanan bazai ma iya tuna awar qarshe da sukayi waya ba. "Hala baka da wani abu me muhimmanci cikin rayuwarka sama da business dinka?" Kalmar da farouq ya fara jera masa kenan. Boyayyen murmushi ya saki yana daga dogayen qafafunsa ya aza saman dunqulallen table din gabansa me azabar kyau. Wani irin shaquwa da fahimtar juna ce tsakaninsu dake sanyasu iya fahimtar mode din juna koda basa kallon fuskokin juna. Yasan zaiji fiye da haka ma a bakin farouq din,don muryarsa a dake take da alama har kan fuskarsa akwai alamu na qosawa "Idan ka cire ku family na.......tabbas ba abinda ya fishi muhimmanci cikin duka kaf rayuwata". "Aurenka da yarinyar su a wanne muhalli ka sakasu?....." Ya sake masa tambayar kansa tsaye cikin salo na kaiwa maqura da son masa titsiye. "Aure?....yarinya?" Ya maimaita maganar har ga Allah cikin son neman qarin haske. "Eheeennn" Farouq ya fada a taqaice,cikin ransa yana jin rainin hankalin jadda yana neman fin qarfin tunaninsa muddin ya gaya masa ya manta da lamarin auren dake gabansa. "Mmtsewww......au" Fuad ya furta wani siririn murmushi yana sake qwace masa. Sai a yanzun kwanyar tayo masa tariyar karatun baya na abinda ya baro a nigeria. Kusan gaba daya sabgar ta shafe daga tunaninsa,abinda ya sanya a gaba ya mamaye tunanin komai daga kansa. "Am sorry......kasan halin......" "......halin mijin aljana.......zata sakashi ya aikata fiye da haka ma,saidai alhmdlh.....duk abinta a wannan karon munci qarfinta,kuma in sha Allah dan uwana bazai mutu babu aure ba". Dariya sosai ta qwace ma fu'ad din ganin yadda farouq din ke maganar very serious,abinda ya jima baiyi ba,ya rasa abinda yasa suka damu da auren nan......ya fuskanci gaba dayansu murna suke dashi.....ya karanci dukkaninsu sun daukeshi serious kuma da gaske suke lamuran baki daya.....ciki harda MAAMAH duk da akwai qatotuwar ayar tambaya a kanta......don ya sani,koda yaushe ita ungulu bata jewar banza. "Ka duba email dinka na sauke maka saqo......ka duba urgently" "Alright" Ya amsa masa suna katse wayar dukansu. Yasan tsaf xaya iya mancewa idan bai duba saqon yanzu ba kaman yadda farouq ya buqata. Don haka kanshi tsaye ya bude email dinsa. Baibi takan sabbin saqonni da ya fahimta kaman akwaisu ba,kanshi tsaye ya bude saqon farouq din. Daya bayan daya yake bin hotunan daya turo da kallo ba don yana fahimta can can ba. Hotuna ne na style readymade na kayan maza masu azabar kyau da aji da wani fitaccen kamfanin fidda readymade suturu ke samarwa. Company ne da sanya suturar data fits daga cikinsa sai wane da wane......sai mutanen da suka amsa sunan shegu ne su ta fannin kudi da dukiya. A idanu kayan sunyi kyau,saidai shi baisan me zaiyi dasu ba,don haka ya jawo daya wayar tashi ba tare daya dauke dubansa daga kan hotunan kayan ba ya dannawa farouq din kira. "Am coming" Abinda yaji farouq din ya fara fadi kenan da alama yana magana da wasu ne daga gefe "Have you seen it?" Idanunsa ya lumshe kadan sannan ya budesu "Yes I have.....but bansan me zanyi dasu ba......hala ka fara preparation na bude garment company ne?". Wani qululun takaici ya tsayewa farouq a wuya,seriously mutumin nan da gasken gaske yake ya fara mantawa da cewa aure zaiyi. Duka ya sakar masa ragamar komai a hannunsa ba tare da damuwa ko tambayar ya ake ciki ba ko meke faruwa ba. "Na rantse da Allah sa'arka daya baka kusa dani......shin wai ka manta yarinyar mutane da zaka aura wadda ka kaiwa sadaki?,in all likelihood ka samu memory formation right?" . Wannan karon ma saida sautin dariyarsa ya isa har kunnen farouq ''Calmdown mana dude......abun yayi zafi ne har haka?" "Yama fi haka zafi" Ya fada yana jin ya tuqewa halin fu'ad din. "To am sorry......amma dai ka sani......ina da abubuwa masu muhimmanci da yawa a gabana.....kai din kuma wakili nane a ko ina......duk abinda ya dace ka zartar ka zartar....na baka wuqa da nama" Ya fada calmly,don bayason ya sake tunzura farouq din,tunda yana ganin yana iya bakin qoqarinsa a abinda shi a nasa ganin baikai muhimmanci da suke bashi ba. Dan shurun da farouq din yayi da yadda ya sauke numfashi ya tabbatar masa fushinsa ya sauka,dama ko can basa wani dogon fushi da juna,da farouq ya zazzage abinda ke cikinsa shikenan,shine dama me yawan kauda kai.....zaka jima kana masa abu amma miskilancinsa bai bari ya nuna maka har kasan kana masa ba daidai ba,har sai sanda ya gama taraka tukunna. "Kayi magana dasu abdulghafar......for now ya kamata su sassauta tsaronsu akan yarinyar" "For what reason?" Fu'ad ya maida masa kanshi tsaye yana gyara zamansa sosai saman lallausar kujerar da yake zaune akai. "Ina ganin kaman ya kamata ta sake.....duk da dama dole ka bata security da guard,ko don yanayin halin tsaro da qasar ke ciki,sannan zuwa yanzu ta zama part of us......wanda duk xai d'amfara da sunanmu dole a bashi tsaro" "Forget about it farouq......she's gonna be able to do what you....." Sai kuma ya fasa qarasawa yana jan siririn tsaki. Shi sam sam koda sau daya bai taba jin wani abu da yayi kama da yarda ko gasgata yarinyar ba.....akwai abubuwa da yawa da uake suspecting a kanta,wanda ya sake qaruwa tun daga lokacin data bayyanar masa a mazaunin ZABIN MAAMAH. "Do you have concern about her actions?" Farouq ya tambayeshi yana tattara masa hankalinsa. "Manta kawai......mu ajiye wannan,baka tambayeni akan komai ba dude?". Yayi maganar calmly kaman zancan business din yafi bashi peace akan batun auren. "Akan komai?,akan business dinka?,wannan shine kadai damuwarka?" "Wani abu daban daya kamata na damu dashi sama da haka?". Numfashi sosai farouq yaja,yana tsoron yadda fu'ad gaba daya baya bawa harkar nan muhimmanci,yana tsoron faruwar wani abu......careless din yayi yawa har haka,yana jin kamar ya kashe wayar kawai,to amma ya sani wannan shine abu na qarshe da zaiwa fu'ad ya bata masa rai,ya tsani a kashe masa waya sam sam. Yadda yake masa bayanin nasarorin da sauran abinda ya rage ya sake bashi tabbacin business dinsa shine gaba da komai. Sunyi magana har ta kusan awa guda kafin su yanke sadarwar dake tsakaninsu. Sanda yake qoqarin minimizing email din idanunsa suka sauka kan wani sabon adreshin email din dake dauke da sabbin saqonni guda uku,kamar zai share ya wuce sai baiyi hakan ba,ya danna ya budeshi ya fara bin saqonni da kallo. 𝐃 𝐔 𝐍 𝐈 𝐘 𝐀 𝐓 𝐀 ΜΆBΜΆOΜΆOΜΆK ΜΆ2 β±§Ι„β‚²Ι„β‚₯β‚³ π™‹π˜Όπ™‚π™€ 2 Kallon farko zaka fahimci ya bada dukka hankalinsa akan abinda yake ganin gilmawarsa cikin wayar tasa. Saqonni ne kusan guda uku,kala daban daban,saidai kuma kowanne saqo daya yakeson isar masa. _mr muhammad jadda,You hereby warned to stop all activities related to lunching your company_ saqon farko kenan. A nutse ya sauke idonsa zuwa ga email na biyu _Not heeding this warning may put your personal and professional assets at risk_ . Sake matsawa yayi zuwa saqo na uku shima still dai kakkaifan jan kunne ne zalla a cikinsa. _Ignoring this warning may lead to financial losses and reputational damage_ still dai qasansa shima wani saqonne _Proceed with caution,as this may have unintended consequences_. Tsam yayi da ransa,yana sake bin saqonnin daki daki yana bitarsu. Wannan wanne irin barazana ce haka me girma?,daga wanne sashe ta bullo?,su waye keda alhakin aiwatar da hakan?. Ya jima da sani......ba sanin jiya ko kuma yau ba.....sana'arshi sana'a ce dake dauke da tarin hamayya gogayya da kuma abokan adawa na sarari dana boye,wani irin matsayi ne da Allah ya bashi wanda bai taba tunanin samuwarsa a qananun shekaru irin nashi ba. Akwai tarin mutanen da suka fishi jimawa cikin harkar.....saidai har yanzu basu samu irin nasibin daya samu ba. Gyara zamansa ya sakeyi da kyau yana furzar da iska daga bakinsa. Ya sani,zai iya bincike akan ainihin adreshin,saidai kuma yasan zai wahala ya iya reaching komai akai koda yaso samun haka. Beside ma,isn't the first time daya fara samun ire iren wadannan saqonnin,wanda daga qarshe yake cimma daga wanne waje suke?. Ba abinda ya taba girgizashi ko ya daga masa hankali kwata kwata,amma kuma hakanan yaji wannan saqon ya tsaye masa a rai. Bai sani ba.....ko don saqon yazo masa ne a daidai sanda yake da burin aiwatar da abinda ya qwallafawa ransa na cikar burinsa?. Yadda yake a tsaye a siffa da zati me taba zuciya,haka zuciyarsa take a tsaye. Ba komai ke bashi tsoro ko firgitashi ko sanyashi yaja baya akan abinda ya fuskanta ya kuma qudira zai aiwatar ba.....don haka wannan saqon ma sai ya sanyashi cikin sahun sauran saqonni marasa muhimmanci,wadanda ba komai bane a ciki face zallar barazana maras muhimmanci a wajensa. "Hasbiyallahu wa ni'imal wakil,hasbiyallahu la'ilaha illahuwa alaihi tawakkaltu wa huwa rabbul arshil azeem" Ya furta a nutse,take taji zuciyarsa tana sake samun nutsuwa da aminci. Komai ya tattare yana duba lokaci,cikin jikinsa yake jin ya gaji,yana buqatar cikakken hutu kafin gobe,so samu yabar qasar nan da kwanaki biyar,to amma ya fahimci zai wahala dama ta bashi hakan. Sanda suke takawa da guard dinsa zuwa mazaunin motocinsa guda biyu kira ya shigo wayarsa. A gajiye ya zura hannunsa a side pocket dinsa ya zaluqota. Taku biyu baya sukayi dukkaninsu,wanda wannan kuma sabonsu ne,don basu tsaiwa a waje muddin zai amsa waya,saidai idan shine ya buqaci hakan. Sosai ya zubawa sunan ido yana kallonsa,yayin da zuciyarsa ta cika da wasi wasi da saqe saqen abinda kunnuwansa zasu iya jiye masa daga bakinta. Yaci gaba da irga bugawar da wayar keyi,wanda yake jinsa kamar daidai da bugawar numfashinsa. Ko a tarihi,ko kuma a labari yana kyautata zaton shi din yana cikin mutane sahun farko da idan labarinsu zai fita a kundin littafin al'ajabi zai ja hankalin mutane da dama. Kiran uwa na daya daga cikin kiran dake sanya dukkanin yaro alfahari.......kiran uwa na daga cikin kiran da kowanne yaro ke fatan gani a kowacce rana.....kiran uwa kira ne dake iya juya zuciyar kowanne yaro daga baqinciki zuwa farinciki.....amma banda su......banda tasu mahaifiyar......banda kuma nasu kiran wanda ba komai a cikinsa face zallar ko kwanto da didibniya tsakanin lalubo alkhairi ko sharrinsa. Yana daga cikin motor qafafunsa suna waje ya zauna,yana qoqarin lalubo nutsuwarsa da yakan rasa a duk sanda kiranta ya riskeshi ya daga wayar. Alamun daga kiran ya sanyata sake hada nutsuwarta waje daya,gami da dagawa hajja furaira hannu wadda ke lissafo mata tsare tsare na abubuwan da suka shirya gudanarwa a wata shimfidaddiyar farar takarda. Tsit wajen yayi,bakajin motsin komai da kowa,abinda zai sanya wanda ke nesa irin fu'ad din xaya dauka ita kadai ce wanze a dakin. "Barka da warhaka" Ya furta da muryar nan tasa dake da tasirin kwarjini me yawa da haiba a ciki. "Barka kade.....ina fata kana lafiya?" Ta masa tambayar data zamo abu mafi dadewa baiji ba daga bakinta. Duk da zuciyarsa ta kasa yarda haka siddan tayi kiransa amma ya hadiye wannan.....ko yaya yaji dadin tambayar cikin ransa koda kuwa da manufa aka yita "Alhamdulillah.....Allah yasa kuma hakan" Dan murmushi ta saki,zuciyarta tana ayyano nesanta zuwa kusa da ita. "Lafiyarmu qalau,sai shirye shirye da muke yi gadan gadan". Bai wani fahimci shirye shiryen da take magana a kansu tashin farko ba......har sai data dora da nata bayanin. " Na kiraka ne don na shaida maka.....ina buqatar wasu kudade da zan qarasa duk hidimomin da suka ragen.....ta bangaranka da kuma bangaren ita kanta amaryarka......don kasan hidimar biki ba qaramin abu bane,......bare ni da zan aurar da dan fari......kuma ita kanta yarinyar ya kamata ace ita,danginta da dukkan wani dage da jibi da ita yasan cewa tabbas da gaske mamallakin diamond company zata aura.......banason harkar qaranta......ya kamata duniya kanta ta shaida d'ana zaiyi auren fari". Kusan koda yaushe fitar kalmomin bakinta suna zame masa tamkar makaranta ne......ya jima da sanin maamah din macace me son izza da nuna isa.......ya dauka wani tsohuwar dabi'a ce a tattare da ita.....amma xuwa yanzun ya sake amanna mutuwa ce kadai zata iya samun nasarar rabata da wannan halin. "Me ake buqata?" Ya tambayeta kai tsaye.....don shima da nashi plan din. Zuwa yanzu yana kallon komai ne tamkar a tafin hannunsa ake shiryashi,abinda ya rage masa ya sani kuma kadanne da bayajin zai zame masa me wahalar riska. "Kudi nakeso ka sakamin......sannan ka sakawa amaryarka......kamar million......." "Kiwa saddiq magana......zan gaya masa ya saka miki adadin abinda kike buqata" Ya yanke bayanin da taso yi masa da adadin kudaden da duk da yasan ya jima da fin qarfinsu........amma kuma ana nemansu ne a muhalli da gurbin da babu buqatar yawan wannan adadin. Murmushi ta saki tana jin wani dadi yana ratsa zuciyarta,tun a yanzu tana sake samun tabbacin nasarar dake bibiyarta,tana kuma fara jin qamshi da dadin da uwa keji a yayin da take gwada girman izzarta akan yaranta suke kuma bibiyarta sau da qafa akan duk wani buri ko quduri nata "Allah yayi maka albarka" Ta fada tana murmushi. Kalmar ta dinga masa amsa kuwwa cikin kunnuwansa,sai ya dinga jin kamar ba daga bakin maamah ta fito ba. Idan yace bazai iya tuna ranar data fadi wannan kalmar a kansa baiyi qarya ba. A hankali sai yaji kaman zuciyarsa tana rugujewa. Inama ace ta fadi kalmar ne domin cancanta da kamatar ta fadeta a kansa?,bawai don duniya ko wani abu dake cikinta ba?,bawai don son rai ko biyan buqatar rai ba. Da wannan murmushin dake sake yalwata saman fuskarta a kowacce rana ta ajjiye wayar saman table din gabanta. Qasaitaccen table ne da yazo cikin set na kayan furniture din da aka qawata sabon gidan nata data riga kowa tarewa a ciki. Gida ne datake jin zata kece biki na alfarma a ciki......zata daga sunanta da kuma martabarta a idanun qewaye dama duniya gaba daya. "Kowanne motsinsa sai ya dangantani da saddiq hamza kibiya" Ta fadi tana duban idanun hajja,har cikin ranta tana jin wata wuta tana ruruwa tare dason gaggautowar ranar da zata saka kakkaifar wuqarta ta yanke wannan alaqar da tafi mata kama da baqar alaqa. "Hanzarin na mene mariya?,saurin me kikeyi ne?,saura kwanaki nawa duka duka?" Hajja ta bata qwarin gwiwa tana cike da kwadayi da son jin abinda ya faru tsakaninta da fuad din. Kai maamah din ta jinjina tana son dawo da walwalarta kaman daxun. "Bai tsaya jin koma nawa nake buqata ba......kawai yace nayi magana da saddiq,shima zai masa magana na karbi abinda zan karba din......kinga zan karbi kaso biyu kenan......da nawa dana yarinyar can,zan san mata wani abu a ciki ne kawai.....sai na cire abinda zan cira a ciki.......zan ware na boka donshi kansa yawan kudin dana qara masa akan wanda ya buqata na fahimci ya qara masa azamar aikin nan.....hajja" Ta qarash da kiran sunanta da wani irin sauti dake nuna gajiya da zallar zaquwa. "Inaso yayimin aiki irin aikin da bai taba yin irinsa ba tunda ya fara harkan nan......inason yayimin kalar aikin da ba fuad ba......ko tsuntsun gidan fu'ad sai ya zama me biyayya a gareni........inason yayimin aikin da sabreena zata koma tamkar bawa da ubangidansa a hannuna........bansan me yasa yarinyar ke yimin kwarjini ba,bansan me yasa nakeji wani abu daban ba idan ta kalleni......inason dukka wadannan abubuwan su shafe daga idanuna". Wani murmushi dake dauke da tarin boyayyun ma'anoni da rufaffun qudurori dake amsa kuwwa da amon nawa burin yana sama da naki hajja tayi,sannan ta harde qafarta tana cewa. "Dukka wannan qanqanin aiki ne a wajensa,kuma ko iya haka aka tsaya zaki bawa wani labarin zafin aikinsa......isassun mata kawai ke iya aiki dashi,matan manya da iyayen manyan mutane irinki,saboda daga sadakin aikinsa kawai zaki fahimci ba gama garin boka bane.....don haka ki rubuta ki ajjiye.....dukkanin wadannan burirrika naki tamkar sun gama cika ne......saidai banji share dita a wannan kasafin naki ba". Rausayar da kai maamah tayi tana sakin murmushin jin dadi. A qasan ranta tana mamakin son kudi tsantsa irin na hajja din,duk kuwa da cewa lullube take cikin wadata me tarin yawa.......saidai wadatar yaranta idan kaf idan aka hadesu batakai kaso daya cikin ukun abinda fuad ya mallaka ba shi kadai......amman duk da hakan bata raina kudi komai qanqantarsu(tabbacin zuciya ta zarme da yawa dason abun duniya,Allah ka kiyashemu). "Baki da dukkan wata damuwa hajja,kina da million uku a ciki,kafin alqalami ne kawai......kuma somin tabi,nan gaba kadan ke zaki dinga bada wannan adadin a matsayin taki kyautar" "Qwarai da gaske kuwa mariya" Hajjan ta fada kanta tsaye tana duban idanun maamah da wani irin confidence daya sanya maida hankalin maama duka a kanta. Wannan ya sanya ta sassauta kaifafa harshenta da nuna dukkanin qwarin gwiwar dake kan fuskarta. "Yaronki ai yarona ne mariya...ni nasan bani da haufi....ba zaki taba butulcemin ba" Ta sake yiwa kalamanta ado da wasu kalmomin "In sha Allahu" Maamah ta amsa tana rausayar dakai har yanzu murmushin na saman fuskarta,ta kuma jawo wayarta tana fadin "Bari na nemi musaddiq ya nemo yaron can,don da zafi zafi ake dukan qarfe......gobe nakeso muyi sammakon tafiya hado dukka ayyukan dama sauran bayanai......bikin nan da gaske tahowa yakeyi,kwana shida kacal ya rage......inason tasan da zaman kowacce doka qa'ida dama sharadi kafin ta samu lasisin karbar igiyoyin auren d'ana a kanta". Da wani kallo hajja ta bita kawai ba tare da tace komai ba.....saidai kuma can cikin wani saqo na zuciyar magana ce me yawa nauyi da kuma dogon xangon da bazai yiwu baki ya furtata ba. 𝐃 𝐔 𝐍 𝐈 𝐘 𝐀 𝐓 𝐀 ΜΆBΜΆOΜΆOΜΆK ΜΆ2 β±§Ι„β‚²Ι„β‚₯β‚³ π™‹π˜Όπ™‚π™€ 3 Daure da babban towol da kuma da kuma wani babba data lullufe jikinta kirif tun daga saman kanta take takowa daga cikin toilet din dake manne da falon tana dawowa cikin ainihin falon daya zama sansaninta a yanzu. Nan din wani kebantaccen guri ne cikin gidan nasu,da asalinsa ya zama muhalli ne na mahaifinsu,wanda tun bayan shudewarsa ba wanda yake ta'ammali da wajen,don gidan nasu ya wadaci kowa,kawai sai saman inda falon nasa yake ya zama wajen da akan bude ne kawai a share,sai idan wani taro ya tashi kuma cikin gidan sannan akan zauna a ciki har ayi a gama. A yanzun

Chapter 1 of 5