Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register


An dauko wannan littafi daga shafin https://taskarnovels.com.ng ku ziyarci shafin na https://taskarnovels.com.ng domin samun kayatattun littatafan hausa kama daga kan na yake yake dana soyayya




Marubuci ko marubuciya zasu iya turo mana da littatafansu mu dora masu a shafinmu kyauta don masoyansu su rika Downloading a online,



Sannan marubuta zasu iya turo mana da tarihin rahuwarsu da tarihin rubutunsu, dama sharhin littatafansu don masoyansu su gani kuma su karu da hakan

Domin turo mana da littafi ko tarihin rayuwar marubuci ko marubuciya sai ayi mana magana ta whatssap da wannan nambar +2348140419490



A lura dakyau - kyauta muke saka littafi a shafinmu bama amsan ko sisin marubuci, duk wanda ya amshi kudinku da sunanmu babu ruwanmu,



Alura dakyau - manazarta bama tura littafi ta private ku dena binmu private kuna neman mu tura maku littafi, duk mai bukatar littafi yaje website namu



Alura da kyau - Littatfanmu suna fitowa cikin manhajoji uku ne PDF,TXT da DOC amman munfi amfani da PDF da TXT masu amfani da wayar android ko tablet ko computer zai fi kyau ku riga dauko PDF da DOC



Masu amfani da kananan wayoyi java ko mara java TXT zakuna zaba don shine daidai wayarku


This hausa novel was uploaded and downloaded from https://taskarnovels.com.ng

You can download more hausa novels there

Also you can send us your novel to upload it in our website for your fans to download it online

It is free we do not charge for uploading novel

Also if you are an Author be it online or Non online you can send us your biography including your book summary,commentary and others via this number +2348140419490 its free we do not charge for our services



Note that - we do not charge for our services we uploaded novels and posted biography free, any person that collect your money in our name is your fault do not blame us



Note that - pls readers stop calling us and be asking us to send you a novels we are not sending novels through whatssap or private our novels is public at any day, any time you can visits our site and download it



Note that - our ebooks came as PDF,TXT or DOC format but the popular format are PDF or TXT, those with android or tablet or pc we suggest you to download PDF or DOC
those with java phone or non-java phone we recommend you to download TXT



This Novel is downloaded from https://taskarnovels.com.ng
to download more hausa novels visits our site at www.taskarnovels.com.ng

For feedback and support

Facebook : https://facebook.com/taskarnovels

Twitter : https://twitter.com/taskarnovels

Telegram : https://t.me/taskarnovels

WACE CE YAR DAJI

Written
BY
FAtima Alaramma Alaramma
(Falaramma)


Kyakkyawan lafazi wajen runutu.
Ina san rubutu sbd rubutu muradi na ne.

*Gajeran labari ne wannan*





Na sadaukar ga wannan book din ne ga kai na, ina roƙon ubangiji yayi min jagorah arayiwa ta yaku sa na dace.








Bismillahi,rahamanurrahim


pg 1 - 50 completed

Yau ma kamar kullum, ahankali nafara bude idona dan ganin aina nake cikin nutsuwa nabude idona ban saukeshi ako inaba sai awata katuwar bishiya, danake kasanta wadda yawan reshanta yacika gaba da bayan ta cikin, dimau cewa name ke zaune tare da dafe kai na wajen da idanu na ya kai ne naga , da jin Allah ne Wanda ba kowa kuma bakomai acikinshi face manyan duwatsu da kuma manya manyan bishiyu, tun danake bantaba ganin gigitaccen daji mai duhu irin shi ba take idanu na sukacika da hawaye na tausayin kaina, wannan wacce irin kaddara ce nake cikinta ni sabrah, tasha kuka sosai sannan tamike daga kasan bishiyar tafara tafiya ahankali gakuma tsoro dayake mamaye azuciyarta.
Ta ƙasan bishiyun takebi har tafita, ƙasan wannan bishiya tashiga wata, daidai wata katuwar bishiya ta tsaya chak sakama kon wani motsi da takejih acikin bishiyar nan take jikin ta yahau tsuma cikin ta yahau kugi, gumi yafara ketu mata tako'ina. Ta kuma kasa ko motsawah, ahankali taga gefen bishiyar dake gabanta wani katan kogo nabishiya ta kurawa wajen idanu dangani takeyi kamar daga cikin bishiyar motsin yake fitowa.
Ai kuwa cikin nu tsuwa na hango wata matashiyar yarin ya tana fitowa daga kogon cikin tsoro nake kallan yarin yar dan gani nake tamkar ba mutum bace, tayama za,asamu dan Adam awannan dajin gaskiya banyarda ba,sabrah ta faɗa, sosai nake kallan yarin yar har takarasa bakin wata bishiyar nan ma hankali na yaƙara tashi dan wata mata nagani azau ne abakin wata bishiyar yarin yar nagani ta tsugun na a gaban matar ta dauki hannun ta tana tayimata wani abun bata jima tana yima ta ba naga tamiƙi tabi wata bayan bishiya ahankali na karaso wajen matar dan gane wa ida nu na abinda yake gani daga nesa.
Sai alokacin ne ma nafahimci matar makauni yace batagani dan harda sanda nagani agefenta, kallo daya zakayiwa matar kasan ba wani cikakken hankali ne da ita bah gashi kuma duk jikin ta dau ɗace gakuma kanta da yayi kurah wannan kenan.
Da hanzari nabi bayan wannan yarin ya dana gani ina ta sauri ina bin shatar kafar ta harna kai bakin wani katan dutse na han gota zata shiga cikin shi dasauri na kuma binta har tashige kasan du-tsen ni kuwa ina kaiwa bakin dutsen zan shiga naga wani irin duhu Mara misaltuwa Wanda ko hannu baka iya gani take tsoro ya mama ye min zuciya da kuma tu na nuka da ban da ban dasuka shiga zuciyata.
Amma sbd ina san sa nin wace ce wannan yarin ya da kuma waccen matar sai kawai wani kwarin gwiwa ya zumin sai kawai na saka kai, na bita nayi tafiya mai ni san ba tare da na san inda na kesa kai na ba ko ƙafa ta kafin daga bisa ni nafara gani haske kadan kadan.
Ahankali nafara kallan ko ina acikin dutsen ba komai a ci kishi sai wasu irin bishiyu masu ban tsoro, ahaka dai har na kara so bakin kogon a nan ne naga haske ya mamaye ko ina sai kuma nafara ganin kyawawan bishiyu masu saka nishadi da farinciki na shagala da kallan bishiyun ne ban aune ba naga yarin yar a gaba na tareda tarin kayan fruit ahan nun ta.
Take tsoru yacikani jiki na yadauki rawa marata tacika da fitsari saboda irin kallan da yarin yar take min ita kuwa yarin yar kallan da takeyi saboda abin da yabata mamaki shi ne bata taba ganin halitta irin ta taba dama akwai mai irin su aduniya? dama basu kadai ne suke rayuwa ba?.
Ni kuma sai alokacin nake kallan ta sosai, yarin ya ce karama wadda bazata wuce shekara goma sha biyu ba amma kyakkyawar gaske ce tahadu tako ina duk da ƙan- ƙantar shekarun ta amma behana fito da kyau din taba. Sai dai babu wata suttura ajikin ta sai ta ganyayakin bishiya Wanda su suka zame mata sutturah. Ahankali ta kara matsowa inda nake tare da daga han nun ta zata shafamin fuska nan ne hankalina ya dauke nakasa gane komi, ita kuwa yarin ya kawai ne ma ta tayi tarasa dan wa'yanda suka kawoni sun dauke ni.
Ita kuwa yarin ya girgiza kai kawai tayi taci gaba da tafiya amma aran ta lamarin ya bata mama ki, to wacce wannan yarin ya? Kuma waccen matar? Meyasa bata gani? Menene ya kawo su wannan dajin? Shin muta ne ne su? Meya sa basa magana? Wane yake kawo sabrah dajin? Wane ya dauke ta? saboda me zai dauke ta? Dan amsa wadan nan tan bayoyi ku biyu ni kuji yadda zata kaya.
Ahankali taci gaba da tafiyar ta harta kara so bakin bishiyar wadda tazame musa tamkar daki tashiga bata jima ba tafito tare da wannan matar tariko han nun ta, ta kawo ta bakin bishiyar ta zau nar da ita sannan ta koma dakin ta dauko wannan fruit din tasoma bata abaki tanaci cikin nutsuwa.
Daga Baya can kawai wannan mata ta fashe da kuka mai abin tausayi takuma taune har shenta take Jini yafara zuba sosai, yarin yar nagani ta zubamata idanu tana kallanta saboda idan da sabo tasa ba ganin kullum idan tana bata abinci sai tayi wannan kukan nan tsananin kukan ne yasan ya idanun ta suka dena gani amman kullun idan yarin yarnan ta tan bayeta dalilin kukan nata sai tace nima din bansan mai yasa nake kuka ba.
kuma akoda yaushe yarin yar takan tanbayi wannan matar tace "wai wacceni"? Kuma kema "wacce awajena"? Amma amsar daya ce akullum nima bansaniba abinda matar take gayamata ke nan ,acikin kowanne karshen wata na ranar Friday hanka linta yakan iya dawowa jikinta har tayiwa yarin yar magana amma daga ranar ta wuce tofa shikenan babu magana sai dai sudinga yin magana ta hannayensu, sai da tayi mai isarta sannan tayijn shiru itakuwa yarin yar ta tashi ta dauko maganin da take sakawa matar tazo tabude bakinnata tasaka mata sannan ta mike takoma gefenta itama taci fruit sannan ta dawo takwanta akan cinyar wannan matar. tayi shiru tana tunanin abinda ya faru jiyah wannan kenan. Katafaran falo nashigo Wanda yaji kayan alatu acikinshi ba karamar tafiya naciba a falon kafin inkaraso inda wata lafiyayyar hajiya ke zaune ba Karya, taci wani arnen lace sarka da dan kunnan da agogon hannunta duk na diamond ne takalmin dake kafar tama anyimai ado da diamond din harta gilas din idon ta, sai zuba uban kamshi ta keyi tana latsa wayar ta ahankali gefe wasu mutane ne azaune sun baibaye ta duk kan nunsu kan su akasa yake suna dan fifitata ahankali, daga gani batan baya wannan gidan, gidan mulkine dakuma sarauta amma gidan ya hadu ba karya, yauma kamar kullum Yusuf ne yashigo agigice da alama daga barci ya tashi yafadu falon ahauka ce bai tsaya ko inaba sai kan cinyar wannan hajjiya yakuma fashe mata da kuka, dago watayi tace wa wadannan bayinnata kutashi kuje aikuwa take suka fuce, shikuwa Yusuf din kara kukan yayi yace mom why why me yasa mom, dagowa tayi tana kallansa cin nutsuwa Yusuf nagaji da lamarinka ya kake so nayi kasan zan iya komi akanka Dan Allah kafadamin meke damunka yau kimanin wata daya kenan agigice kake tashi daga barci kadinga fadamin irin wannan magan ganun anya ba aljanune suka fara taba kaba, alokacin ne Yusuf ya dago jajayen idanunsa yafara magana mom kinyi abinda baki kyau taba mom meyasa kika aikata hakan mom kinsan wanne haline take ciki kawai dan duniya haba mom yana kaiwa nan yakara fashewa da wani kukan tamkar karamin yaro, me kake nufi Yusuf menene abun da kake nufi ban fahim ce kaba pls mom karki nuna baki gane ba nasan kinsan mena kenufi amma kike nuna kamar baki sani ba, mom wllh kiji tsoran Allah wllh baki yiwa mama Fatima adalci ba duk abin da tayi maki aduniya ko maki yinta ba zaiyi mata haka ba dan Allah mama ki warware abindaba ika aikata haba mom, kara fashewa yayi da kukan wannan wacce irin rayuwa ce mom kika dauka, nasani Allah yayi Khadija ba matata bace kuma har yanzun inasan yar uwata dan Allah mom kasa karasawa yayi saboda tsabar kuka da bakin ciki, ya kuma daura da cewa sannan kika saka mutane suka manta da lamarinta suka manta da anhalicce ta aduniya hatta yan uwanta da mijinta hatta mahaifinta ba kyatunanin cikin dake jikinta, wani banzan kallo ta watsamai sannan ta dura da cewa Yusuf anyakuwa baka hauka ce ba wai akan wa kake magana ban gane bah wacce kuma Khadija Yusuf dama kanada wata yar uwa, wadda kaso aura aka hanaka to yaushe ma ka isa auren shika runka nawa kwata kwata me ka tara aduniya meka ke dashi wanda nida kai zamu rayu dashi haba Yusuf ya kakeso kazama sha sha sha ne to ni dai bari in tashi in baka guri dan naga baka da lafiya, shi kuwa kallan mom tashi ya keyi da tsananin mamaki, mom tana nufin bata gane meya ke nufiba kodai target ne dan ta shashantar da zan can ne amma indai haka ne mom dinshi ta zama makirar mace wadda shai dan yake buga mata ganga, lalai shi zai San yadda zayyi domin ceto Khadija daga halin da take ciki wannan kenan. Zau ne take kusa da wannan mata ta zuba mata idanu tana ganin tsan tsar kamar su da wannan mata kamar har ta bace, ga kuma wani tsan tsar tausayi ta da Allah ya dura mata batan San ganin wani Abu yasa meta ko yana cutar da ita, Kuma ako da yau she babban abin da yake daga mata hankali shine kukan da wannan mata take yi duk da har yanzun bata San wace agare ta ba, kamar daga sama taji kalaman wannan matar suna dakar kunnan ta my blood tafara lalube ahankali dama ako da yaushe idan tadawo hayya cinta abinda take fadi kenan sai kuma kuka Mara iyaka, ahankali ta kara matso wa kusa da ita ta kama han nun ta tahade shi da nafa tafara yi mata rubutu akan hannun kamar yadda tasa ba aikuwa ta rungu meta tace ina sanki my blood ke din jinina ce nice mahaifi yarki 'yata take tafashe da kukan ita kuwa bata Masan meta ke fada ba dan ita batasan magana bah idan ba rubutun han nuba, aikuwa da tafahimci hakan tuni tafara yimi ta rubutun ahannunta aikuwa tashiga fahimta sosai alokacin ne tasan wannan itace mahaifiyar ta amma bata gane komi daga wannan bah wannan kenan. Ban garen Yusuf fita yayi zuwa dakin shi yayi wanka bayan yagama kukan sa sannan ya zuba ran tsartsiyar shadda mai kyau da tsada sannan ya wuce fadar mai marta ba yana shiga fadah suka fara girma mashi suna gaisheshi har kasa yana amsawa tare da sakin fuska kafin ya dangana ga mahaifin na shi cikin girmamawa ya gaidashi sannan yayi mai sannu da fadah, sarkine ya tsura mai idanu kafin yace "dana mai yake damun kane haka", baga daya kasauya yan zun ko abinci cikake bakaci haba my son kafadawa mahaifin ka damuwarka cikin dan basarwa Yusuf ya dago ya kalli mahifin na shi sannan yace Allah Abu babu komi kawai dai sha'anine na rayuwar duniya, aa Yusuf baka saba yimin karyaba, Allah Abu to shikenan tun da kace haka Allah ya shiga lamarin ameen yace sannan yayi shiru yana kallan mahifinna shi, acikin zuciyar shi yake fada yanzun mom abinda kikayi kenan kina tunanin wannan hakkin zai kaiki, mutum da yarike maki danki da Amana amma shine Wanda zaki tarwatsawa farinciki why mom why, hawaye ne suka fuskar shi, gashi kinjefa shi wani yana yi Wanda shikan shi baisan meke damun shiba duk saboda duniya, shikuwa Abu arikice yake kallan dan nashi ya jawo shi jikinshi yace kafada min meke damunka my son kaki kasan nima halin dazan shiga saboda kaki sanarmin wllh bana san ganinka a irin wannan halin, Yusuf rushe wa ya kuma da kuka mara misali dan ya rasama ta inda zaifari Abu kayi hakuri kayafemin Abu na inacikin matsala amma kayimin addua saboda bazan iya gayamaka ba amma ina Neman adduar ka da kuma yimin fatan nasarah, shiru yayi yana jin tausa yinshi har ranshi kafin ya dago dashi yace to shikenan my son insha Allah zan ta yaka ya dago dashi ya gogemai hawa yanshi sannan ya zuba mai idanu ya dago yace Abu bari infita zuwa gidan su Habib to shikenan nan bari akira driver aa Abu zanje da kaina to shikenan Allah ya kiyaye hanya duk abin da su keyi mom najinsu gaba daya hankalinta ya tashi saboda karya fada duk da ko yafadar balallai su tunu komiba hankalin ta be kwanta ba sai da taga Yusuf ya tafi sannan tashige dakinta kai tsaye ta dauko wayarta takira hajiya maryam tana dagawa tace hajjiya ba lafiya meya farune hajjiya suwaiba wallahi Yusuf ne yata mafarkin wannan yarin yar wadda muka salwantar tsawan shekaru goma sha uku gashi yanzun yana gab da tonamin asiri, hajiya maryam tace ke ai bazai iyaba Dan koya fada bayarda zasuyi ba aa inasan adai je a sashi shima yamanta shidin fargaba ne a gare ni, toh shikenan zanje wajen malam din asan yadda za'ayi, to zantura maki da kudi yanzun ki tafi to shikenan, duk abinda takeyi akunnan Abu amma sai dai be fahimci komi ba kawai dai yana saurararta ya shigo dakin da murmushi yace madam kinanan, arazane ta juyu tace mashi eh cikin furjici kallanta yayi yaga bata da nutsuwa ya karasa gabanta yace habba my wife ko na baki tsoru ne tadan daidai ta kanta kafin tace ohhh kabani tsoro ne!, toh sorry, ya fada a takai ce tashi yayi kusa da ita yake tanba yarta ko tasan meyake damun Yusuf tace mai itama bata saniba idan tanba yarce ai shi zata tan baya, Shikuwa Yusuf bai tsaya ko ina ba sai gidan su Habib yayi sa,a kuwa yana nan ya zauna ya kalli abokin nashi sosai ba tare da yace komi ba, Habib ne ya kalle shi yace Yusuf me yake damun Kane haka Habib ina cikin matsalah Dan Allah kabani shawarah ina jinka Yusuf nan take ya bawa Habib labarin komi be boye maiba sosai Habib aminin Yusuf to a makaranta sosai Habib ya yimamaki sosai saboda me mom zata aikata hakan take Habib yashiya suka fita yace yasan yadda zasuyi kai tsaye suka je wajen wani malami suka yimai bayanin komai yajin jina lamarin sosai kafin daga bisani ya dago yace masu insha Allah za,ayi adduoi insha Allah komai zai daidai ta sosai suka bashi kudi sukace ayita sadaka asamu afara dawo da hankalin mutane kanta suka yimai godiya suka tafi sannan suka kara daukan hanyar gidan wani malamin shima suka sanar dashi shima yajinjina sosai nan yatafi cikin gida ya dawo yace masu lallai lamarinku yana da girma amma insha Allah za,atashi tsaye as an yadda za,ayi amma aiki akayi da manyan bakaken aljanu shima kudin ya ajemasa sannan suka fito zuwa gidan, Habib yace kaima kuma kadage da addua Allah yana sane damu zai kawo mafitah wannan kenan. Abu yana fita daga dakinta tamike takara kiran tace akara nisan tata daga inda take aka ce mata angamah wannan taka she wayar tace daga ni sai Yusuf zamuci dukiyarka sadiq dukiyar ka mallakin muce nangaba kadan nakashe ka kaga komi ya dawo namu wannan kenan. Suna zaune ita da mamar ta a bakin ruwa tana yimata wanka bayan ta gama mata tamayar mata da kayanta sannan tayi ita ma bayan ta kammala ta kama hannun mamar tata suwa wani katun lanbu ta zaunar da ita akusa da wani flowers masu kamshi ta zauna agabanta tana taba mata kuma tunda ita ma tana taba mata nata har suna dariya ana ganin hakoran ta suna kuma cin kafan fruit wannan kenan. Hajiya maryam tana karasawa gurin wannan boka cikin wani kasan tsauni sai kuma dakin bukka tace masa ga abinda take tafe da ita yace to shikenan angama ammafa tasani wannan yaro ba za'a iya rufe mai baki ba sai dai tayimai wasu yan dabaru kalar naku na mata to shikenan boka hajiya maryam tafa da ta kuma ce akara nisan tata daga inda take to shikenan bari ma induba yan zun kiganta take ya hau buge bugensa amma yakasa ganin komi aikuwa yace akwai matsala baba amma kice takara kiyayewa dan duk sanda wani yajita tana maganar to fa aranar zata koma mahauka ciya to shikenan tashi kitafi amma zan kara nisan tata daga inda take a yanzun to natafi tafito tatafi, shikuwa boka take yakara buga abubuwansu ya kuma cillata duniya danshi bai taba sanin akwai wata yartaba wannan kenan. Dariya take yi irin tasu ta mahauka ta har kana ganin hakoranta can kuma ta mike zunbur tsaye take idanunta suka canza zuwa bakake takwa Zaburah tazura aguje irin gudun mamaki dinnan tashi yarinyar tayi ta bita tana kiran sunanta tana gudu itamah amma kafin aje ko ina tanemeta tarasa haka tacigaba da tafiya tana kuka tana wata irin kara har dare yayi gashi sunbar dajin dasuke haka ta dane bishiya har gari yawaye, yau kimanin kwana biyu kenan baita ba dalilinta gaba daya yarin yar tashiga tashin hankali mara missali, kamar dai yadda malaman nan sukayi alkawari da su Yusuf sunfara addua sosai ba kama hannun yaro sosai sukeyi tare da almajiransu ko barci basayi, yau tana zau ne abakin bishiyar daga nesa sai tafara ganin wata inuwa na gaba tota tadaga kanta dan ganin wane amma sai taga mahaifiyar ta aikuwa ta tashi dagudu karasa inda take ta fashe mata da kuka tafara yimata rubutu ahannun itama ta rungu meta sannan suka nemi waje suka zauna bayan sun gama hutawa ta mike suka fara tafiya dan zuwa dajin dasuka bari wanda yaza memasu gida wannan kenan. Yau kima nin sati daya kenan anata addua sosai tana samun sauki dan tunaninta yafara da wowa kadan kadan har takan iya furta kalamai na magana yanzun ta kanyi wanka da kanta sannan taci fruit da kanta. Shikuwa Abu yanzun akullum idan ya zauna ajikinshi yake ji cewa kamar yarasa wani Abu muhimmi ajikinshi amma yarasa me nene sai kuma zuciyar shi da take yimasa nauyi akullum gaba daya duniyar bata mai dadi, meki wa yayi Dan zuwa bangaren mamarsa take fadawa suka take mashi baya har zuwa bangaren ta yana shiga ya nemi waje ya zauna saka makon bata falon, sai kuma ya juyo yace wa fadawanshi suje sujirashi awajen yamike zuwa dakinta yabude dakin dauke da sallama yashiga tana zaune tayi tagumi da alamu tunani take yi sosai saida ya kara sallama da karfi sannan ta dago tace my blood kai ne, eh nine mom harkasa ya tsugunna ya gaidata sannan yakoma kusa da ita ya zauna kallanshi sosai takeyi yace yaushe rabon da inganka my blood sai yayi kasa da kanshi, amma mene yake damunka ne nunfashi ya dauke sannan yace wllh mami narasa meke damuna cikin tsananin nan zuciyata wani nauyi takemun gashi tayitamin wasu irin tuna nunnuka shiru tayi fatin yace wllh nima haka ne dan jinake kamar narasa wani Abu babba ajikina Allah yasa dai lafiya ameen ina Yusuf jikana yaune kawai ban gamshi ba amma kullum sai yazu sai dare sosai yake barinnan. Yaune Yusuf da abokinshi suka koma wajen malaman nan dayan yana kwance ba lafiya Dan tunda yafara aikin bashida lafiya sukayi mai sannu ananne malamin yace mashi gaskiya wannan aikin baban aikine dan haka zakuje wajen wani malamina dan ni bazan iya aikinnan bah zakuyi kwana biyu ahanya amma bazaku dawoba zakuji yar uwarku da izinin Allah take ya rubuta masu address ya basu sukayi mai godiya sannan suka bashi wash kudade masu nauyi sannan suka tafi, dazuwan jibi idan Allah ya kaimu zasu tafi zuwa wajen malamin, abinda basu sani ba shine wadannan mutananne suke kokarin kaishi lahirah, wannan kenan, suna zuwa gidan wancen malamin shima yana kwance ba shi da lafiya shima yayi masu bayani sosai yace masu kunga wannan rashin lafiyar da nake fama dashi to harda wanya wanyan aljanun da nake fada dasu amma tabbas tana cikin matsalah Dan haka kugaggauta zuwa nima inata yi maku addua wannan kenan. Yusuf yana koma wa gida yasanar da Abu zaiyi tafiya zuwa wani aiki Abu yace Yusuf yanzun tafiya zakayi yace kasan banasan kana nesa dani nafiso indinga bude idona ina ganinka, Abu kasamin albarka natabbata zakayi alfahari da abinda zan dawomaka dashi insha Allah to shikenan tonda kace haka Allah yakaika lafiya kaida Habib zaku tafi ko,eh masha Allah amma kagayawa mami eh nagaya mata to shikenan my son. Zaune suke akogon bishiyar saka makon wata gigitacciyar iska da ta tasi wadda ko hannunka bazaka iya ganibah gaba dayansu jikinsu bari yakeyi Dan hatta bishiyar da suke ciki mutsawa takeyi

Book Chapters
Chapter 1
Chapter 2Chapter 3Chapter 4

Please Login or Register in order to submit comment