Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

yaya aj,shiru yayi bai tankamata ba jin wata murya mai sanyi nakwala kiran sumy!sumy!wanda har sautin yake ratso kunnuwansa daga cikin wayar ..




Chanza firar da dayan bangaren akayi shi ya tabbatar yakara tabbatar masa da muryar da yaji,Ajiyar zuciya yasauke ab'oye ya makarnata ya furtamata kamar basu yi wannan gaisuwar ba inda take furtamasa ya aiki,lfylau ya furta itama tana furta karatu alhmdllh,Bayan jin ta amsa ma wadda ke kiran sunan nata,ta hanyar furta na,am nisa lafiya wannnan kira haka da murmushi a fuskarta ta furta kizo anfara shirin" imlie " dan suna matukar son shirin wanda starlife suke haskawa akullum mai dogon zango ,musamman nisa wadda sunan ta yake (yuhanisa)tana mugun son shirin dan ita takoyawa sumy sonsa,a cewar ta jarumin mijin imlie na farko yana kama da yaya aj dinta dan tana mugun son aj kamar ranta,sumy kadai tasan da maganar sai kuma wasu daga cikin kawayensu.......



Fahimtar da nisa tayi sumy waya take kuma da yayansu ganin yadda ta natsu,yasanya A hankali ta karaso kan gadon tana mai fadin allah yasa baiji ni ba tana rufe dan karamain bakinta,Murmushi ne ya subucewa dr.aj jin radar da tayuwa sumy,sannnan ya furtawa sumy bata wayar,A hankali sumee take mikamata wayar itama tana murmushi da addu,ar Allah yabawa kawartata ya yannasu ta yi wucewar ta falo...


A bangaren dr AA najinsan kuma yaciga da buga game dinsa,dan tun dazu Aj yamayar da wayar handsfree sanadiyyar rashin network na kirki da babu baiji sosai..

..........Shiru ne ya biyo baya bayan ta amshi wayar,A hankali tace yaya ina wuni murmushi yasaki yana furta kinmanta mu yanzu dare ne,laah ta furta tana rufe bakinta mai kama dana yayanta,tamboyi yamata game da kart tana amsa masa da alhmdllh cikin dan rashin sakewa dashi


Shiru ne yabiyo baya sai kuma ta katse shirun nasu,ta hanyar furta masa ina yaya Ammar ?

yana jin sautin Muryar kanwartasa sai dai yayi kamar baiji ba,duk da kallon da aj ke masa domin sarai yasan yanajinsu ...


Jin tana magiyar abatashi inyana kusa yasanya a hanklai yabaro kan kujera din sa yake yadaw kan hannun kujerar da aj kezaune,dan jin raunanniyar muryar kanwartasa tana rkon akan kawai taji muryarsa yasan duk laifinsa ne da baya cewa abasu waya inyakira,tunda basu da waya har yanzu basu bada izinin abasu ba wayan saboda kallon kananan yara da suke musu,ganin haryanzu basu gama secondry ba,a yanzu suna ss 3ne akarshen shekara zasu gama..



Hello!"yaya A ta furta tana sakin kayataccen murmushinta da hr aj dake kusa dashi yaji sautinsa dan yacire handsfree din bayan amsar wayar daga hannun aj..


Shima murmushin yasaki yasaki har saida dimple dinsa suka loba gwanin burgewa dama ayanzu duk kaga murmushinsa irin haka mahaifiyar sa ce ko kanwarsa wadda takasance ita ce autar su,suna mugun son juna datausayin junansu musamman Babban yayannasu da ayanzu yake abun tausayi...

hw are u ?fn ta furtamasa,ya schl da krt yakara tambayar ta ta furta masa Alhmdllh,Anbar doja koh tace ce eh cikin murmushi toh acigaba da kokari duk da bai yadda da maganar taba yasan su da rashin son zuwa makaranta tun suna kananan .


A hankali ya tsinkayi muryar ta tana tamabayar sa,yaya A yaushe zaku zo kugammu?murmushi yasaki yana fadin ashe kina gidan maaminah yayi hakan ne dan kawar da tambayar tata,ehh ta furta yau sati na daya,ohk!ya furta tare da tambayar ta inasu husnat da sumayya,"duk suna falo ta furta to ki gaidasu,toh ta furta cikin sanyin jiki jin yakawar da tambayar da tamasa don dama ta harbo jiginsa....

Yanzu dai je ki bawa maaminah wayan dan haka yake kiran kanwar ta mahaifiyarsa,mahaifiyar Aj,Hajiya husaina,kai yaya batasan andauko wayanta ba nima na isko sumy da itane,kuma yanzu intaga mundauko fada zatayi,murmushi yayi dan yasan halin mamin da bata daukar wargi duk da zaman ta nason barkwanc,kuma dama yasan basu fada mata zasu dauka ba,tunda yasan basuda waya,murmushi yakara saki yana mai fadin "to kudaina daukar mata bada izininta ba,babu kyau hakan,kurika tambayarta indai kungayamata ta "ya 'yanku zaku kira zata baku kunji koh"tau yaya in sha Allah ta furta.....


"in sha Allah inkuka samu result mai kyau a qualified exams naku zan siya muku waya mai kyau,murmushi tasaki mai hade da dariy tana fadin dagaske yayah ,kansa yadaga kamar yana gabanta yana furta eh,i love you so much yayah,proud of you the best brother in the world takai karshen maganar cikin farin ciki marar misltuwa domin dama sun matsu asiya musu wayoyi saboda mafi yawancin kawayen su na da ita,"me too ya furta cikin farincikin dayasamu kansa aciki Bye ki je ki aje waya yanzu kar taganku koh,toh yya tafurta tana masa godiya da sallama suna yanke kiran.........

Kowa ransa fess,cikin murmushin sa mai kara kawata fuskarsa ya juya ya dubi aj yana furta masa take your phone yana kara furta bari inje in dauro alwallah naga isha'i tagabato,da ohk kawai Aj ya bisa,shima yana mikewa yarage voluke din tv yana chanza tasha izuwa inda ake kira,ar qur'ani,ya wuce upstair shima tare da wayansa shaf shaf dukkaninsu suka dauro alwallah suka wuce masallaci don gabatar da sallar isha'i acikin jam'i....


Bayan dawowarsu aj kashe wutar falon da tvn kowa ya wuce nasa bedroom din dan yin bacci bayan sunyi sallama wannan kenan.........


BACK TO THE PRESENT .....

Murmushi kawai Dr aj yakara saki bayan gama tunano abunda yafaru kwana biyar da suka wuce yana mamakin hali irin na abokin nasa kuma dan uwansa.


Godiya bodyguard din nasu suka k'ara masa kafin suka koma gurin da dr .Ammar d'in yake tsaye shima suka kara masa godiya da basa hakuri,karbar jakar hannun sa daynsu yayi domin kaima sa office nasa.


Wanda shima bangaren dr aj hakance ta kasance agurinsa..

A hankali suka doshi hadadden hall din da yake cikin wannan katafaariyar asibitin ta mumbai wadda take da dubbanin tarihi na cigaban da ake samu ta hanyar kula da marassa lafiya shigarsu katafaren hall din daya tara dubbanin likitotah masu ji da kud'i da wanka,kowa yana zaune akan kujerar da take mallakinsa wadda ke dauke da sunansa.


A Hankali suka fara gudanar da taron cikin kwanciyar hankali,dama suna meeting din ne kan cases da ake yawan samu ne akan yawan mutuwar mata awajen haihuwa,suna son gano dalilin da silar faruwr hakan cikin alumma.......


..........................................

Kudai kucigaba da bibiyar 💞alkalamina…………A sannu zan warware muku wannan labari maicike sa tausayi,nishadi ilman tawarwa,soyayya,sarauta,cin amana,ga xumuncibugu da kari kuma ta,addanci wanda yakasance abunda yake ciwa alummar mu tuwo akwarya ganin yadda shuwagabbani suka zuba ido aalamarin da har yanxu ankasa samun mai yin katutu da al amarin,ganin kamar sunfi karfinsu wanda kuma ba haka bane,mu munsan addua bata bar komai insunfikarfinsu ai basu fi karfin ubangiji ba....sannnu bata hana zuwa sai dai adade ba,aje inji hausawa,dan haka karku sanya kucigaba bibiyar labarin....


NEXT PAGE TOMORROW IN SHA ALLAH

KUTAYANI SHARING BOOK DIN NAN PLS DOMIN AKWAI DARASI MAI YAWA ACIKI ...................



💫 A MAFARKI NASANTA💫

In my dream i know her

By

Pha'eezah Almustapha

Daga Alkalamin✍️✍️

💫Fa'eeh BG💫


Dedicated to my lovely sis lailat Almustapha Murai💔


*PERFECT ESSENTIAL WRITER'S ASSOCIATION📚🖊️



💫P.E.W.A💫



Home of perfect writer's together we stand🤝


ESSENTIAL WRITER'S📚🖊️


pen 🖊️*Is mightier than the sword🗡️*

---------------------------------------------

TYPING📲📲📲



EPISODE1️⃣

FREE PAGE1️⃣7️⃣


WANENE DR.AMMAR(AA)

cikakken sunansa Abdulrashid Aliyu Ahmad,haifaffen garin Gusau,jihar Zamfara,Dane Ga sarki Aliyu Murai,sunan mahaifiyarsa hassana hamza wadda suke kira da unni,mama kenan ayaren (korea) mahaifinsa da mahaifiyarsa Auren soyayya sukayi,kuma auren zumunta,Mahaifinsa sarki Aliyu murai rikakken Dan kasuwa ne,wanda yake da kaloli kuma manyan kamfanona akasashen daban daban a duniya,A yanzu haka shine yake rike da sarautar ta zamfara A babbar masarautar murai ta Gusau'Ammar shine d'aa na farko ga iyayensa,sai mai bimasa hamza wanda yaci sunan kakansa na uwa,ana masa lakani da mahir,sai Auta yuhanisa inda taci sunan yayar kakarta ta uwa,suna kiranta da nisa,Ammar yana da shekara ishirin da takwas aduniya,mahir kuma yanada shekara goma sha biyar,sai nisa tana da shekara goma sha takwas aduniya,Mahaifiyar sa gimbiya hassana "yace ga wan mahaifin su sarki Ali Sarki,Hamza murai kenan,takasance yan biyu ita da mahaifiyar aj,sai autar su laila,sunan mahaifiyar su fateema suna kiranta Ammie,Ammar yaci sunan k'anin mahaifinsa Abdul rashid wanda shine autan su sarki Ali su uku ne maza,suna da mace daya mai suna khadija,suna kiranta mama dije wadda ke aure agarin kano tana auren wani custom,tana ya guda sunanta umaimah,wadda ita kadaice rabonta,tun rasuwar yan biyun ta na fari,sai kuma umar shine ke bima sarki Ali murai,Sai Abdul rashid ,sannan khadija,sunan mahaifiyar su sadiya suna kiranta hajiyar safkare,a takaice hajia,dukkanin su sunyi aure,..........Dr.Ammar yayi karatunsa tundaga secondry har tertiary a kasar india inda kuma kuma yasamu aiki achan shida aj,Dr ammar mutun ne mai tsantseni ga tsandar tsiya duk da yana da laziness bai yadda yasaka ma kansa kanzanta ba,baida daukar raini,dan gayu ne na asali,baida daukar raini,kuma bai da wulakanta talaka hasalima shi mai tausayinsune,mutun daya ne yake iya wa da halinsa shine dr aj kuma shine babban abokin sa,domin sun kasan ce kamar yan biyu kamar yadda iyayensu suke,dr ammar dai kyakkyawa ne na karshe,har yanzu bai da budurwa duk da harin da yan mata suke kawo masa,natayin soyayyarsu,mutun daya ce tazame masa kamar cingum itace dr malini,domin Allah yasanya mata wani sonshi duk d yana kokarin nuna mata bata cikin tsarinsa hakan baisa tayi sanya ba wannnan kenan...

SAI DR.AJ

Cikakken sunansa dr Al amin jabir muhammad soja,dane ga leutenant jabir muhammad wanda yakasance army ne na nigeria,shine shugaban sojojin arewa,sunan mahaifiyarsa husaina inda suke kiranta ummi,Aj yanada kanne uku inda namijin dake bimasa yarasu tun yana karami mai sunan mahaifinsu jabir ,sai mai bima margayi jabir sunanta sumayya,sai Auta Asma'u suna husnat,wadda taci sunan kakarta su ta wurin uba,Aj sa,a ne da dr. ammar kwana arba'in ne tsakaninsu,Sai sumee wadda take da shekaru sha tara sai auta husna nada shekara goma sha uku,aj da sun taso komai sunayinsa atare,Aj shima baida wata tsayayyar budurwa har yanzu Wannnan kenan...


*MUDAWO LABARI*

------------------------------------------------------------------

*~~NIGERIA ZAMFARA~~*

*~~ BUG~~*

*~~UNGUWAR SABON GARI~~~*


...........Bayan fitowar Baba Adee daga wanka Ya shiryawar sa cikin shiga ta kamala dai dai rufin asiri cikin yadinsa mai kyau black,bayan fitowar sa wanka wanda da taimakon Bba Asabe ya shirya wanda kuma shine dalilin saukarsa da wuri dama shi ba mutun bane mai riko..

" A bangaren su Halee kuwa bayan kammala shirin su na zuwa islamiyyya suka dauki jakun kunansu,sunfito rass dasu cikin uniform ash colour hijab har kasa masu kyau sai sheki sukeyi,dukannin su sun amshe su musamman ma Halee wadda farar fatar ta tak'ara haskawa, kyakkayawar fuskar ta ta fito rass doguwar fuskar ta kara yin wani shaf mai kyau cikin dogon hijab dinta gwanin burgewa,sunata zuba kamshi mai dadi,wanda sai ka matso su zakaji shi,ba mai cutarwa ba kamar dai yadda aka annabi ya siffanta turaren mata,

'Dan Baba Adee akwai son kamshi domin mafi yawancin tsarabarsu ta turare ce,shiyasa koda yaushe zakaji su cikin kamshi....


Sallama sukayiwa Baba Adee da Baba Asabe Dake zaune a barandar gidan suna dan taba fira jefi jefi...


Miji da mata sai Allah..


ficewa Gidan sukayi bayan amsa addu,o'in da yasaba yimusu inyana gida...


Bayan wucewar su Halee islamiyya,shima Baba Adee yaficewar sa zuwa masallacin unguwartasu dan gabatar da la,asar kan lokaci.....


*~~GUSAU,ZAMAFARA~~*

Gusau ta sambo mai dimbin al umma noma shine abun alfaharinku,Gusau Babban birni ne na jahar Zamfara wanda yatara dubbanin Al umma ta kowane sashenn yarukka da yan kasuwa,musamman manoma,da ma aikatan gwamnati da manyan yan siyasa,Babban Abunda yake abun burgewa agaresu shine yadda sukayi riko da aladunsu,da addini da kuma sarautunsu,sai kuma abun da yake mai mahimmanci da suka rike shine Bin shari'ar musulunci,gari ne daza kasamu suna bin dokar musulunci wanda ko gidan karuwai zai yi wuyar samu a jihar...


*MASARAUTAR MURAI*

Babbar masarauta ce dake cikin jihar zamfara gusau wadda gaba daya nigeria suna alfahari da ita domin kafaffiyar masarauta ce tun zamanin Sarki Ali murai wanda shine sarki nafarko wanda yafara yin sarauta ajihar tun zamaninsu shehu usman dan fodiyo Na sokoto,shiyasa takasance mai mai dimbin tarihi...


'kuma shine yayi ruwa yayi tsaki gurin kafa wannan masarauta mai tarin Al ummah ,wadda tazamo abar alfahari a idon al ummar nigeria jin irin kokarin da sarki Ali murai yayi gurin kafa masarautar..


Mutane daban daban daga cikin ya yan Ali murai sun rike sarautar wannann masarauta har izuwa yanzu da ake k'ara samun cigaba...


Tattab'a kunnen Ali murai a yanzu shiyake mulkar masarautar,inda take samun kulaawa dakuma Al.ummar dake karkashin ta,Ahannun d'an d'an sarki Ahmad..


WASH TYPING AKWAI WAHALA...KUYI MANAGE DA WANNAN....BANJIN DADIN JIKI NANE.....


GOBE IN SHA ALLAH ZAKU SAMUN KARIN PAGE


Kuyi sharing,

Sannan ku danna min like akasan page din....


Ina godiya sosai masoyan amafarki

Halee tace agaishe ku...


💫FA'EEH BG💫


💫A MAFARKI NASANTA💫

In my dream i know her

By

Pha'eezah Almustapha

Daga Alkalamin✍️✍️

💫Fa'eeh BG💫


Dedicated to my lovely sis lailat Almustapha Murai💔


------------------------------------------------------------

*PERFECT ESSENTIAL WRITER'S ASSOCIATION📚🖊️


💫P.E.W.A.💫


Home of perfect essential writer's together we stand🤝


ESSENTIAL WRITER'S📚🖊️



Pen🖊️*is migthier than the sword🗡️*


------------------------------------------------------------

EPISODE 1️⃣

FREE PAGE1️⃣8️⃣↔


TYPING📲📲📲


*TUSHEN MASARAUTA*


"Ali murai shine Asalin wanda yarik'a masarautar yana da mata kwaya d'aya tal,sunan ta Hajiya lubah (iyami) da "ya "ya maza biyar,d'an sa nafarko sunan sa bello,sai nabiyu sunan sa Haruna,na ukun Abdul aziz,sai na hud'unsu Isma'il,sai Autansu yahaya..


Bayan rasuwar sarki Ali murai sai aka nad'a d'ansa na farko Bello wanda shi yacigaba da kula da masarautar yana da mata d'aya da y'a y'a hud'u namiji biyu mace biyu,Bayan wasu shekaru shima Bello yakwanta dama,wanda mutuwartashi ta kowa ya jita A Masarautar saboda sak halinsa irin na mahaifinsa sarki Ali murai,Mahaifiyarsa takoka da rashinsa da y"an uwansa da ma Alummar Masarautar.


Bayan gama zaman makoki Aka nad'a d'an uwansa Haruna,Haruna yak'arb'i mulki cikin salama ,Sai bayan shekaru sittin sannan Allah yakarbi ransa..



..Abdul Aziz Yakarb'a shi kwata kwata ma bai ka shekara hamsin ba akan karagar mulkin saboda ciwon daya ci k'arfin sa na k'oda,sai aka nad'a Isma'il,Bayan Nad'in Ism'el,Sarki Abdul aziz yakwanta dama....


Isma'el ya cigaba da mulkin masarautar Bayan shekara saba'in bisa karagar mulki yakwanta dama,wanda bayan rasuwar sa,Anyi rigima sosai da Yahaya danshi kwata kwata bayason sarautar,acewar sa kayan wahala ce da takura,bai karb'a har sai da mahaifiyar su iyami ta kwanta ciwo akan hakan,ciwon zuciyaar ta yatashi wanda yasameta tun bayan rasuwar mijinta sarki Ali murai,sanadin bak'in cikin

Yahaya da yakafe bazai k'arb'i masarautar ba,masarautar da mijinta sarki Ali murai yasga gwagwarmaya wurin ginata,daga k'arshe dai yakarb'a ganin yadda ran mahaifiyar sa ya b'aci gashi harda kwantawa ciwo....


'Anyi bikin nad'in sarauta da ba'a tab'a yin irinsa ba alokacin kowa kaga fuskar sa da annashuwa da farinciki kamar sauran lokutta domin sun san cewa ba su shiga mugun hannu ba dan duk cikin ya"yan sarki Ali murai babu wanda yamusu mugun riko,Yahaya yakarbi mulki cikin aminci tare da alkawalin kula da Alummar masarautar,yana da shekara talatin akaragar mulki matar shi tahaifi namiji wanda shikad'ai ne rabonta har tabar duniya,yaron yaci sunan margayi tsohon sarki Bello,bayan wasu yan shekaru,Kwatsam ranar aka wayi gari da mutuwar sarki Yahaya murai,wanda mutuwar sa ta girgiza kowa musamman yaronsa sa Bello,Bayan rasuwar sa da kwanakki itama tsohuwa Iyami mai ran k'arfe ta kwanta dama,tana da shekaru D'ari da hud'u a Duniya.


Wanda kowa yaji mutuwar wayen nan bayin Allah Acikin Masarautar da ma wajen Masarautar..

Bayan rasuwar yahya Anyi rigima sosai A fada akan wayenda za,a dora akwai d'an wajen margayi bello da yace yanaso sai kuma d'an wajen magaji wanda yaya ne ga Sarki Ali murai,daga k'arshe dai Muhammadu bello D'an wajen sarki Yahaya shi aka bawa bisa ga chanchantarsa duk da akwai k'aranta atare dashi dan duk sun girme masa.


Anyi nad'in sarauta tareda Daurin Auren Sarki Bello Alokacin yana da shekara ishirin da hud'u A duniya,Bayan hawansa akaragar mulkin yana d'a yan uwansa manyan muk'a man masarauta,domin cigaban Alumma .


Ya Auri yar wajen sarkin zazzau na hud'u alokacin mai suna Gimbiya Ruk'ayya bayan shekara gimbiya Rukayya ta haihu ta samu yan Biyu maza,Alokacin ne kuma matar tsohon sarki margayi yahaya uwar muhammadu bello tabar duniya,Anyi taron suna cikin alhinin wannan rashi,tacigaba rainon yan biyu dinta,Bayan wasu shekaru tasamu wani cikin inda tahaifi Namiji yaci suna Aliyu,sunan tsohon sarki...

'A Daren sunan Aliyu ne wani Babban tashin hankali yafaru inda wuta ta kama ad'akin su hassan da husaini duk suka k'one k'urmus sanadiyyar wutar lantarki suda mahaifiyar su gimbiya Ruk'ayya wadda taje dubasu daga nan ta musu Addu,ar kwanciya bacci duk da tasan cewa bazasu kwanta hakan nan domin takoyar dasu,alokacin suna shekara shidda A duniya,Mutuwar data girgiza Sarki Bello da kuma masarautar wanda sai da sarki Bello yasuma alokacin da aka sanar dashi,Bayan jimamin rashin Sarki Bello yaci gaba da rainon D'an sa Ali....


**Bayan shekara guda sarki Bello yayi Aure ya Auri wadda take baiwa ce Amasarautar, ya Aureta ne saboda ganin irin kulawar da take bawa Aliyu wanda kuma ita kad'ai yake yadda da ita,Sai ya " yenta ta kuma ya Aureta domin samun farin cikin D'an sa tilo daya.

Lafiya lau masarauta take tafiya tareda cigaba mai yawa,Bayan wasu shekaru Sarki Bello na Biyu yabar Duniya yana da shekaru hamsin akan karagar mulki,inda yabar Aliyu cikin maraici mai yawa duk da wannan yentacciyar Baiwa mai suna Nana Asma'u tana sonshi tana bashi kulawa mai kyau saboda yadda take jinsa kamar d'anta na cikinta..




BAyan gama jimamin mutuwar sarki Bello na || biyu aka nad'a d'ansa Aliyu alokacin yanaa da shekaru ishirin da hud'u a duniya.


Bayan na d'insa da shekara guda yayi Aure ya Auri yar masarautar sokoto jikar yar sarkin musulmi na ||| na uku;mai suna ummulkhairi ana kiranta gimbiya (umma),Bikin yatar dubbanin Al umma takowace masarautun nigeria da manyan yan siyasa,masu kudi..Ankawo Amarya lafiya cikin fada acikin sashen ta mai kyau,suna cin Amarcin su lafiya lau tare da zaman Amana....

Komai yana tafiya dai dai ta b'angaren mulki yadda yakamata.


Bayan shekara d'aya gimbiya umma tahaifi santalelen d'anta namiji ranar suna yaro yaci sunan sa HAMZA ALIYU MURAI,Anyi taron biki lafiya,inda tacigaba da rainon yaronta,Bayan haihuwar Hamza da wata takwas tasake samun wani cikin alokacin gimbiya ummulkhairi taso zubarda cikin ganin Hamza ko shekara bai had'a kar yasha ciki,sai dai mai martaba sarki Aliyu yahana zubar da cikin sai dai yasa aka cire Hamza daga nono...


Taraini cikinta lafiya lau batare da tasha wuya ba,watannin haihuwar cikin nayi nak'uda ta motsa amma yaro yaki fitowa ak'arshe dai CS akayi mata aka ciro santalelen d'anta mai kama da uban sa sak,yaron yaci suna Ahmad...

.....Bayan wasu "yan shekaru sarki Aliyu D'an Bello jikan Yahaya D'an Sarki Ali Murai yabar Duniya alokacin,yabar Duniya da shekaru arba'in akaragar mulki,Mutuwar sa tagirgiza y"a yansa guda biyu a duniya da matar sa ummulkhairi,inda tacigaba da kula da yayanta cikin kulawa,Bayan Rasuwarsa da yan watanni Nana Asma'u matar margayi sarki Bello na || tabar duniya...


Sarautar dole aka bawa magajin gari rik'on kwarya kafin ya'yan sarki Ali su kai lokacin iya rike sarautar,domin dukkaninsu bazasu wuce shekara goma sha biyar Alokacin ba.


Bayan wasu shekaru Ahmad yayi aure ya auri matarsa Bafullatanar Adamawa itama yar gidan sarautace sunanta Haleematu sadiya suna kiranta hajiyar safkare wanda sunan da kakarta ta lakamatane,ya Aureta yana da sheakara ishirin da shidda aduniya sunyi Auren soyayya da gimbiya halimatu,kuma aloakacin ne aka damk'a sarauta hannun Ahmad duk da sai da akayi rigima dashi dan yace bazai karb'a ba sai dai abawa y"a yanshi tunda shine Babba,Dakyar aka samu yakarba bayan ya yan nasa ya sanya da mahaifiyarsu gimbiya ummulkhairi suka tasoshi gaba....

Anyi bikin nad'in sarauta lafiya cikin annashuwa da salama,ta fannin zaman takewarsa da matar sa masha Allah za,ace gwanin burgewa.


****Bayan shekara daya gimbiya halimatu sadiya ta haifi santalelen d'anta mai kama da ubansa sak jinin fulani,farin cikin wannan masarauta bazai boyu ba musamman sarki Ahmad da D'an uwansa hamza,wanda ke ji kamar shi akayiwa haihuwar...


*Ranar suna yaro yaci sunan kakan sa sarki Aliyu Bello jikan yahaya d'an Ali murai*yaro yasamu gata ta kowanne fanni,Alokacin shima Hamza yayi Aure ya Auri Gimbiya Hauwa'u yar masarautar Fulanin Bungud'u ana mata lak'ani da fulani,fulani macece mai fadin rai da rashin son talaka,da mugun son kanta,ba kamar gimbiya halimatu ba mutuniyar kirki mai mutunci,BAyan Aurensu da Hamza sai tafara nuna mishi ai sarautar dashi ta dace domin shine Babba yace abashi sarautar,ai shine dana farko ga sarki Ali Bello,sai ya rik'a nuna mata baida buk'ata,kullum haka suke rigima da ita,har zuwa lokacin da tasamu cikin Mustapha A lokacin kuwa matar sarki Ahmad Halimatu tasamu ciki na biyu ta haifi umar,sunan mahaifinta kenan,tana kiransa da emir,Bayan kamar wata takwas sai ga wani cikin na ukku inda ta tahaife sa lafiya,tasamu Abdul rashid,tacigaba da rainon ya yanta cikin kwanciyar hankali.


Daga cikin abin bak'in cikin da yafaru Akwai rasuwar gimbiya ummulkhairi matar tsohon sarki Ali,Mahaifiyar sarki Ahmad da Hamza,sunyi rashin mahaifiyarsu abar kaunar...sai dai muce Allah yajikanta da al ummar musulmi baki daya.........


*Yaa Allah Duk wata mahaifiya 💔💔dake kwance akarkashin k'asa,Allah kajik'anta da rahaama,da musulmi baki daya,Yaaa Allah wayenda suke raye kuma ka k'ara musu lafiya mai amfani tare da tsawon rai mai albarka*🙏


Rashin uwa rashine 😭Babba Arayuwa

Allah yabar mu dasu 🙏

--------------------------------------------------------------



Matar Hamza Fulani tak'ara samun wani cikin nabiyu ta haifi d'anta namiji mai suna Muhammad ana masa lak'ani da Malan,tana da ya"ya biyu kenan.

Itama sarauniya halimatu taka'ara samun wani cikin bayan shekara uku inda ta haifi yarta mace mai suna khadija inda daga gareta haihuwar ta tsaya mata chak......

Sarauniya Halimatu yaranta sun taso cikin soyayyar junansu Da yan uwansu yan gurin magaji hamza,domin shi d'an uwansa ya nada magaji bayan rasuwar wanchan magajin.....

Duk da tsangwamar da Fulani take nuna musu amma hakan bai hanasu jan yan uwansu ajiki bah.


Ta b'angaren magaji Hamza kuwa yana shan matsin lamba gurin Hauwa'u (fulani )kan karbar mulki alokacin takara samun ciki tahaifi ya mace mai suna ummulkhairi suna kiranta (khairiyya) dan taci sunan kakar ta ne wanda daga gareta haihuwar ta tsaya ma fulani chak..

A lokacin Duk fulani tana masa matsin lamba wanda har tafara cin galaba akan sa,dan bata tsaya haka nan ba,sai da talek'a gurin malammaan tsibbo (bokaye) Wal iyazubillah....


bokaye mana domin tahakan ne wasu suke amfani dashi sai suce ai malami ne shi bokan,ana amfani da sunan malamman ana shirka ana cutar Al umma..ALLAH YAYI MUNA TSARI DASU...Masu zuwa gurin bokaye Allah yashiye su🙏

MU HADU GOBE IN ALLAH YAKAIMU

YAU KAM KUNSAMU LONG PAGE,DAN KONI NAJI AJIKI NA,KUNGA NA GOGE LAIFINA NA JIYA,DUK DA BANI DA LAFIYA NE


NAGODE SOSAI ALLAH YABAR KAUNA🙏

KUFARA SHIRI ANKUSA GAMA FREE PAGES,DAN BATUN SAMBAD'O KUD'INKU......


Kucigaba da bibiyar Alkalamina


Yau duk sai A hankali typing din domn page d in yatado mini da rashin da mukayi...Allah yajik'anku da rahama Baba Bello,kakana Baba Yahaya,Alhajin Auki,Mariya,gwaggo yar sarki, Allah yasa Aljannna takasance makomarku da dukkan musulmi baki daya..AMEEEN...


💫A MAFARKI NASANTA💫

In my dream i know her

By

Pha'eezah Almustapha

Daga Alkalamin✍️✍️

💫Fa'eeh BG💫


Dedicated to my lovely sis lailat Almustapha Murai💔


*Mun kusa gama free pages in sha Allah,Da mungama book one📖,Episode one kenan za,a fara payment,Na episode two*!!!✌✌💥💥


*TALLAH!!! TALLAH!!! TALLAH*

*Ina yan kasuwa masu son tallata hajarsu,ga dama tasamu domin Muna tallata kowace irin hajace daga jihohi daban daban harda ma k'asashe,akan farashe mai sauk'i,zaku iya tuntubarmu ta lambobin waya kamar haka*......

+ 2348069059746

+ 2349078741775


-----------------------------------------------------------

*PERFECT ESSENTIAL WRITER'S ASSOCIATION 📚🖊️


💫P.E.W.A.💫


Home of perfect essential

Please Login or Register in order to submit comment