Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

kumbura,Ya Allah da zawo,da kashin jini,da amai da gudawa colera,ciwon zuciya, ciwon kafa,ya Allah da ciwon Kai,Dana mara,ciwon Sanyi irin naw,,,,tunawa tayi zata tona kanta tace Allah karka bari ta auru,Allah kasa tayi kwantai,ba ita ba samun bazawari,Allah Danta Ashraf da take ji dashi Allah kasa ayi Masa sharri irin nawa ya fado gidan Nan,Allah ka hadani da Ashraf Dan Mummy a Nan gidan yari,Allah basai na fita ba Allah a Nan gidan,Allah ka bani ikon cin ubansa,kar naji tsoro,kar ya min kwar jini,naci ubansa daidai yanda ya kamata.

Su Malam Sharu suna addua sai suka tsaya kallon adduar Jamilu suna dariya Yana gama adduar suka ga ya mike yace na tafi wajen abokina mutumin kirki Ashe Yana da kirki duk gidan Nan babu me kirkinsa idan Kun ganshi ku dinga girmamashi wlh ga kudi ga kyau ga kirki iya kirki yau da shi muka samu ladar ciyayya ma yaci abincina naci nasa,Malam Garzali yaji wani mahaukacin kishi yace kaga Jamilu ka rabu da yaran masu kudi ka fiye rawar Kai ka kula ka tsare mutuncinka ato Ina baka shawara kar a Maka wayo kana yaro a lalataka Jamilu,Jamilu kayiwa kanka fada tam shike nan.
Naila tace a'a mutumin kirki ne wannan duk gidan Nan nafi kaunarsa,Wanda nake jira Allah ya hadani da shi Dan Mummy ne wallahi bala'i da masifa har sai na aro ta Ummata,rashin mutunci da tuggu kuwa shima sai na Nemo Kari sai na kusa halaka shi da sharrina,Malam Sharu yace wannan yaro Ashraf ya shiga uku har na fara tausayinsa mu kanmu da ba abinda ya hadamu ka buwaye mu bare shi,Naila ta fice abinta harda shafa turarenta sabo da Spark dan gayu ne.

Yana dawowa daga masallaci ya samu Jamilu ya shugo,yace Kai naci Dan tuwonka Yana Nan shine harda zuwa da wuri,Naila tace Ina laifi Dana jira akayi Sallah ma ko tuwonka ne? an kawo Maka ne daga gidanku? Spark uban isa da gadara yanzu kirki anjima rashin mutunci,yace gashi can dauki abinka,ya furta da gadara da kyar yake magana yana bata rai,Naila taji haushi tace koshi kayi shi yasa ka fada min haka taje ta dauki abincinta ta tattara da nasa gaba daya tayi waje,ya fito da sauri ya fisgota, shi mantawa yake Jamilu baida karfi,Naila sai gata ta zube a kasa har gwiwarta ta fashe,yace sorry, da sauri ya daga Jamilu yaji shi shafal ba nauyi,jikinsa wani shegen laushi haka,tsoro ya kama Spark yaja baya Yana kallon Jamilu,yace anya Jamilu bazan Maka tsirara ba kuwa na gani namiji ne ko mace,please muje ka tube wandonka,ni ba gay bane ba abinda zanji kawai so nake na tabbatar,Naila tace au ta haka ka bullo fyade zaka min dama ance yaran masu kudi Yan iska ne to duk gidan yarin Nan sai na fada musu Kai Gay ne,Spark ya zaro ido yace na janye maganata karka bata min Suna Ina respecting din kaina da kaina.

Naila tace to karka sake ce min haka yace never, muje zaka ci abincin? yace ni da zaka bar min abincin ma nafi son haka,Naila tace to muyi musaya Kaci nawa naci naka,yace good,ta koma ta shige ciki ya shiga shima Yana jinjina anya Jamilu ba mace bane,Haka yayi shuru ya zauna Yana kallon News,Naila ta dauki nasa snacks tana ci abinta cikin Jin dadi,shi kuwa baya cin tuwo ma a gida amma gidan yari tasa wai shine ke yin wayo akan a bar Masa tuwo,tsaki yaja yace akan tuwo da shinkafa duk mutuncina ya zube wai yau ni Spark nace wa wani katon zindiki sorry akan tuwo,bazan yafewa kaina ba yaja tuwon Yana fushi Yana cika Yana batsewa haka ya fara cinye tuwonsa Yana Santi,yace uhm Poor Umma da iya girki,maganarce ta fito fili Allah yasa Naila bata ji ba da ya gane kurensa akan iyayenta bata wasa.

Naila tace ance ku masu kudi Kun San juna watarana Kuna haduwa a wajen da sai me kudi ke zuwa,idan a Abuja kake Dan Allah kasan wani Ashraf babarsa dai wacce ta Raine shi Mummy ake ce mata duk family dinsu sojoji ne yawanci,ance ai shegen Ashraf din nata ya fara aikin soja ya bar aikin ya koma business sabo da shi bakin Dan iska ne,ance ai matsiyacin ya tara kudi,naji danginsu kowa sai yace Ashraf,baka sanshi ba? Tunda Spark yake bai taba dariya irin ta yau ba,ya dinga dariya a ransa yace Allah ya taimakeni ban fadawa Jamilu ni bane Alhmdllh da Ashraf ya sanni,Allah yasa bai San nasan shi Mummy tayiwa sharri ba,Naila ta tsaya tana kallonsa Yana ta dariya

Tace ka sanshi dan iskan algungumin? Spark yace ai abokina nane, Alhmdllh ta mikawa Spark hannu tace mu gaisa ya mika hannu suka gaisa yaji wani shegen shock duk jikinsa ya dauki vibration,itama Naila haka taji da sauri ya janye hannunsa yayi wani Sanyi itama haka,tunawa yayi namiji ne da sauri ya girgiza kansa ya dawo daidai,tace zaka min hanyar ganinsa idan Allah yasa na fita daga Nan gidan, Kai wannan dan nata sai na Masa akuya,wlh sai na huce a kansa Dan iska matsiyaci,mutumin banza Allah yasa ya talauce ga mijinta ya mutu ta rasa ko suturar sawa inshaallah sai na taimaka Masa da shi da ita,jahilan banza jahilan wofi, Spark yaji ana ta Masa mummunar addua shi ba da laifi ba yace Kai Jamilu addua akewa mutum kace Allah ya shirya Ashraf.

Naila tace wlh bazan ce ba sai dai na tsine Masa na sake tambade Masa albarka mutumin banza wa ya sani ma ko a turai din Mata yake bibiya Yana can Yana sheka iskanci da mata,shi baiyi aure yayi ibadar Allah ba ya zama Dan kwararo shine turai shine kudu Lagos wajen mata,Dan Bariki, Mayen mata,Ashraf yayi dariya kamar cikinsa zai ciwo yace wait Jamilu kazafi fa kake Masa ba wani kazafi ai mun sani yaran masu kudi me suka sani in banda lalata mata Yana can ya zama Dan aci kullum sai kace Ronaldo kullum aci kwallo haka ya Maida mata,zai gane kurensa Ina Nan Ina addua Allah ya hadani da shi sai na kwankwatse Masa Hallare, Spark yayi dariya kamar ba gobe,Naila tace wallahi tun a waya zaka hadani da shi na fara rage zafi da zagi na fara rage hanya kafin mu hadu,Ba fa shi ya maka laifi ba Jamilu,Naila tace nima ai ba Ummata ce tayiwa mummy laifi ba ta kare akan Dan Umma to nima akan Danta zan kare.....

Gidan Baban Asmau tuni sunyi hakuri suna ta uzurinsu an daure Spark,Amma Maman Asmau wato marikiyarta itakam Yar uwar Maman su Spark ce itama kanwarsu ce,abin Yana damunta bata ji dadin kulle Spark ba ai shima danta ne,a dalilin haka gashi Mima ta daina shiga harkarta bare Mummy kamar ba Yan uwa ba gaba suke da ita,Kanwar Asmau wace ake kira da Safna itama zata kai 26yrs ta gama degree har aiki tanayi a asibiti,itace kadai tafi kowa damuwa a gidan ta shiga wani hali,tunda aka kashe Asmau take ta faman ramewa tana damuwa sosai watarana ma sai ta kulle daki tayi ta faman kuka,kowa yasan yanda suka Shaku da Asmau kamar me kullum suna tare dakinsu daya,har addua ake mata sabo da yanda ta fice a hayyacinta,aikin ma ta daina zuwa ba irin lallabata da ba ayi ba taki hakuri,ta samu babansu tace wlh Abbu Spark bazai kashe Asmau ba,kawai furuci yayi a dai dai kaddara ta fada Masa,Dan Allah kasa a sake shi idan yaso tunda ana so lallai sai an hadin zumunci ni me zai Hana na maye gurbin Asmau ko da ace baya so na nima zanyi hakuri na zauna dashi sabo da na cikawa Asmau Yar uwata burinta,Ni a maye gurbin Asmau Dani,Abbu ya Kifa mata Mari ya sake Kifa mata Mari yayi ball da ita yace har abada bani ba hada alaka da Spark Kuma bazai taba fitowa ba,mahaukaciya wacce Bata kishin Yar uwarta Dabba wacce bata San me take ba get out,ta mike Zumbur ta fice tana sharbar kuka tace Allah kaga niyyata ta alkhairi ce amma Abbu yaki ta fada dakin Mahaifiyarsu Tana kuka Mama kinga Abbu ne akan nace ya saki Spark ni a maye gurbin Asmau dani shine ya mareni ya min duka, Mama tace maganinki kenan ai na hanaki zancen,nifa so nake na taimaki Spark a fitar dashi,Mama tace duk da bani na haifi Asmau ba wlh ko ba a kulle Spark ba bazai aureki ba kema,wannan yaron bashi da ta Ido shi yasa nake baya baya da shi,kina dai gani Yan uwana sun san Asmau bani na haifeta ba amma gaba suke dani,abin ya kwabe da yawa kiyi hakuri.



Sharhi Dan Allah



Free page

Accnt no
0175487861

Katin MTN
08061929616


Yan Niger
+22790795939






AsmaBaffa
[12/8/2023, 6:56 PM] AsmaBaffa: 🏫 TANTIRIYA 🏫
A GIDAN YARI


26-30


Official

By
AsmaBaffa



SADAUKARWA NE
GARE KI❤️
AIDA MAMAN TASNIM



Page naki ne
YAR LELEN ROYAL STAR



MASU AUDIO BAN YARDA A JUYA MIN NOVEL ZUWA AUDIO BA IZINI BA



*_Albishir! Albishir!! Albishir!!!_*
*_Jama'ar Annabi inayi muku Albishir da cewa nakawo muku wannan shahararre Kuma ingantaccen gida, gidan da suka darje suka rairaye suke kawo Muku kayiyyaki masu dankaren kyau da Kuma inganci abisa farashi dai dai da Aljihun ku_*
*_Hajiyata, kanwata, Aunty na, kinaso kisamu kaya Wadanda ba kamarasu? Kayanda idan kika shirya kika fito kizama abin kallo a wurin Yan uwanki?_*
*_dama wadanda zasu ganki ahanya?_*
*_sbd yadda Zaki fita daban da saura?_*
*_Kinaso Idan kikayi shiri arinka tambayanki a ina kika saye wannan kayan?_*
*_Zakije gidan biki ko gidan suna Amma kina tunanin kayan dazaki saka saboda kiyi fita ta Alfarma ta kece raini?_*

```ARZUQLANA GALLERY```

*_sunkawo muku duk Wani abu Wanda zakuna bukata kama daga:_*
```Laces
Atampha
Shadda
Abayas
Materials
Gyale
Takalma
Jaka
Kayan Kitchen
Bangles n jewelries```
*And many more*

```GIDAN KYAU, GIDAN QUALITY, GIDAN SAUKI, GIDAN KWALISA, DA ADO```

*_Wani abin sedai kunbiyomu zaku Gani da idanunku_*

*_sunayin kasuwancinsu bisa gaskia da Amana, ba cuta ba cutarwa_*

*_koda bakida kudin Siya Muna gayyatarki dan ki tallata kema kisamu naki_*


*_Yar uwa kasance a gidan, da abaki labari gwanda ki bayar_*
https://chat.whatsapp.com/FRJAnQZXm0t7rAroZWlMnQ




Spark suna zaune Yana faman Jin me Jamilu ke fada Yana ta Shan zagi a wajen Jamilu shi da Mummy, katseta yayi yace yanzu ka samo min me aikin? Naila tace gani wai zanyi indai zaka biyani,Kai ba karfi ba kace zaka yi,Ae zanyi haka Ina so,yace ba damuwa,Naila tace bari na tafi dare zaiyi,ka zauna a nan mana zan biya Maka kudin kwana mu zauna tare nima na huta zaman shuru,Naila tace a'a tafiya zanyi,Baki ya tabe tare da furta alright you can go,Naila tace aha sai da safe,ko kula Jamilu baiyi ba ya mike Yana taku dai dai ya shige bedroom dinsa,Naila ta juya ta fice.

Tana fita taga kartai sun hargitsa gidan suna ta fada ana kokarin rabasu,tsoro taji ta juyo da gudu tana haki ta shiga dukan kofar Spark kamar zata balleta domin shi ya sa key,wanka yake yi amma ihun Jamilu yaji Yana cewa abude wayyo,da sauri ya daura towel Dan guntu jikinsa duk kumfa ya bude kofar,ta fado ciki tana haki zata yi kuka tace fada akeyi saura kadan jifan dutse ya fasa min Ido,murmushi ya saki tare da furta shine Kuma abin kuka ko kunya baka ji sai kace mace yaja tsaki tare shigewa toilet abinsa,sai bayan ya gama wankansa sannan ya fito,jikinsa Naila ta saci kallonsa a ranta ta furta wow idonta ta dauke a kansa kar ya kamata taga bai son kallo, gashinsa yake gogewa da Karamin towel,Naila sai faman kallonsa take ta saki baki,kamar wata wawiya, Juyowa ya sake yi da sauri tayi kasa da kanta ta koma kallon kafafunsa masu kyau farare sanye cikin takalma slifas, gashinsa ya busar ya fara taje shi,Naila taga duk su lotion dinsa masu tsada da sauri ta Kalli skin dinta ita, tace shi yasa ni bana shining Dan hasken nawa ma sai guduwa yake,wai ni ya haka ne ai kuwa bai isa ba wlh duk da ya fini haske sai na kamo shi.

Juyowa yayi haka kawai yaji shi Sam a mace yake kallon Jamilu ya rasa dalili magana yayi a gadarance yace koma Palo zan shirya,Jamilu yayi murmushi Yana kallon Spark yace Ina namiji me zan gani a jikinka,ni ko towel dinka ka cire ba ruwana ba abinda zan Gani abinda kake dashi nima Ina da shi, Spark yace Allah? tace sosai fa,yace to a Kalli juna wallahi na yarda ka tube wandonka ni ma zan cire towel din, Naila a ranta tace wannan fa ya uzura min tsakani da Allah kar ya gane ni,a fili tace sai kace wasu yara,wato na ganeka so kake yi muyi wasan bayan murfin kofa na yara to bazan yi ba na girma ni,idan mace kake bukata ka San ya zaka yi ka samu wata ta bude Maka Garejinta ka shiga amma ni namiji ne,me yasa kuke zargin macece ni ta ya zan shugo Nan ba a gane ba Kuma,to a wajen Yan sanda ma daga ni sai gajeren wando da singlet,Inama kasan Mummy da nace ka tambayeta kaji ai ita ta ganni a haka,Spark yace na yarda to ka fiye surutu Kuma ka daina kallona.

Naila da sauri ta dauke kanta amma ta manta ta sake sakin baki tana kallon kyakyawar surar Spark, ta wani bude baki ta sake shi,a haka ya fara shafa mai Yana Juyowa again ya kama Jamilu,da sauri Naila ta mike zumbur tace na tafi,ko magana baiyi ba Yana jinta ta bude kofa ta fice, a tsorace take tafiya tana addua a bakinta har ta fada dakinsu Inda ta samu malaman sun fara bacci ma,tace an gaji da tilawar kenan,tazo ta kwanta tare da jawo sabuwar wayarta ta kunna tana Gani ta hadu a fili tace wannan tafi karfina kyan wayar Nan Yaya Mohsin wlh shine Dan gayu ni Ina gidan yari wa zan birge da waya Ina cikin wahala ai gara na rike Yar karamata burin kwaila, ta jona abarta a charge ta cika full sannan ta zare ta Maida cikin kwalin ta ajiye tace sai sunzo ziyara na bashi ita.

Bangaren mata a gidan yari Beauty kwance take a Saman gadonta tana ta faman tunanin Jamilu tana matukar kaunar Jamilu,Surarsa take kissimawa a ranta kawai ta hango Jamilu wani kyakyawan matashi hadadde me dauke da faffadan kirji, damatsansa wasu manya alamar Yana Gym,murmushi ta saki cike da shauki ta juya a Saman bed din tare da rungume wata teddy dinta da Maminsu ta kawo mata, ta sake juyawa tayi mika tare da sake kankame pillow tace wato Allah haka yake ikonsa idan yaga dama ba Inda bazai hadaka da mijinka ba,gashi nan shima sharri aka Masa kamar yanda nima haka bari Daddyna ya fitar dani wlh sai na fitar da Jamilu ko arzikin Daddy zai kare muje muyi auren mu,wayyoooo jamiluna ta fara Shure Shure a Saman pillow tace yanda nake Allah ya bani kyau na ba laifi, gani da haske na, chass dani,nasan sai na birge Jamiluna.
Sake hango damatsan Jamilu tayi a ranta Yana taku ingarman namiji take ta hangowa,wani irin zaratan Maza,ranar haka Beauty ta kwana tana faman nazari akan Jamilu masoyinta, Garzali kuwa a daren har Istihara yayi ko zai samu a nuna masa a mafarkin ko Jamilu mace ne amma sai ya hango Jamilu da katon Hajiya Babba,a firgice ya farka Yana neman tsari da wannan mafarkin shi Kam,yace inshaallah ba haka bane idan kuwa hakane to Jamilu mata Maza ne,haka ya koma ya kwanta.

Washe gari da asuba Naila suna tafiya masallaci tayi sauri ta tashi tare da yin alwala tayi sallarta tayi addua sosai Allah ya rufa mata asiri kar a ganeta,tace naga makiya sun fara sa Ido a kaina,tana cire Hijab din Malam Sharu Yana shugowa saura kadan ya kamata Allah ya kiyaye amma yaga kamar ta zare abu daga kanta, gashi da sauran duhu da sauri ta daga bargonta ta jefa a kasa ya kunna haske da sauri yaga ba komai ya kalleta sosai Naila ta daga hannu haka tana addua,Malam Sharu yace wai Kai Jamilu wanne addini kake yi? ayi mutum baya zuwa jam'i,Naila tace ban yarda da limamin ba bazan taba bin kowa sallah ba a gidan Nan duk babu na gari bare a bishi sallah,kowa shegen kansa ne mummunan Abu ya aikata aka kawo shi akan me zanbi mutum sallah, bazan bi kowa ba,ban yarda da Imanin kowa ba a gidan Nan, tawa Sallar nake yi.

Malam Sharu yace Allah ya shiryeka ka gane jam'i ba abin wasa bane,Naila tace Ameen shi yasa ni ka ganni PHD ne dani wajen minding business dina,kaga shi yasa akace babu kyau shiga abinda ba ruwanka kasan irin hujja ta ne? Ina da hujja me tsauri amma mutane baku San wane mutum ba ko me yake Shirin yi sai ku dinga shiga lamarinsa,ko ka manta hadisin ne Yana daga kyan musulunci ka bar abinda ba ruwanka,to mu a arewa yanzu kowa nunawa yake yafi kowa ilimi,hankali,da wayewa,kowa yayi addininsa Malam Sharu nima addina nake yi ba ruwanku.

Malam Sharu yace mu dai gaskiya ce sai mun fada ko za a sa kanmu gabas a fille sai mun jawo aya da hadisin idan mutum bai dauka ba ruwansa,Naila tayi murmushi Allah ya bada sa'a, Kuma Ina tabbatar muku watarana sai kunji kunya,Kun sa min Ido,Kun San dalilina a dakin nan? Yace sai ka fada,Naila tace wani Assignment nake amsawa Ina gamawa zaku ga dalilin,Allah ya kaimu Jamilu cewar Malam Sharu.

Baccinta ta koma ta barsu sai wurin 11 ta tashi ko makarantar gidan yari Naila bata taba zuwa ba amma Spark shi Kuma Yana zuwa duka boko da ta addini,sai da tayi wanka ta shirya duk a cikin toilet sannanta fito da kayan data cire,tace ga zafi ga manyan kaya Ina fama wlh,ta wuce bangaren Spark masu tsaron wajen suka ce ya tafi makaranta,Naila ta dinga mamaki ta nufi makarantar, tun kafin ta karasa ta hango gashin kansa Yana sheki,dariya ta kamata tace dole kanwar naki shegiya wuya ta sake shekewa da dariya,Juyowa Spark yayi kenan ya hango Jamilu a window Yana ta faman Masa dariya,suna hada Ido tace ajeboooo.....ajeboota an koma yaki da jahilci sai dariya....dariya ma ta bawa Spark yace yaron nan ya takura min a rayuwa.

Ball taje ta karbo tace ba wata makaranta da zanyi wai shi irin yasan darajar ilimi to ai ba Wanda ya isa ya min dole sabo da haka ni ball zanyi,harda daga Masa ball din ya gani,tayi gaba filin wasan sai da yamma yawanci ake yin ball ita kadai a fili tana ta wasanta da ball bata iya komai ba,Spark ko gama lecture bai bari anyi ba ya fito ya taho wajen Jamilu,a hankali yake tafiya ana wani gayu ana basarwa hannu daya a aljihu anci kana nan kaya tracksuits ne a jikinsa rigar me hula a baya, bakake da ratsin fari,kafarsa sanye da Sneakers,Naila tace shegu kudi ko a Ina suke basa buya wa zai ce shi a gidan yari yake,ji yanda ma duk Yan bangaren da suke a VIP din nan sai kyau suke da kiba to zasu ci abinda suke so gashi basu fita ko Ina uhmm.

Karasowa yayi Inda Jamilu ke ball dinsa shi kadai,hannayensa duka ya zuba a aljihu yace saka muyi,Jamilu ya jefa ball suka fara Yana ta zubawa Jamilu yanka da oc ta ko Ina bai iya komai ba,sai dariya take tana so ta kwace ball din sai faman yanke Jamilu yake hannayensa ma a aljihu sai yanzu ya cire hannayen,Naila sai taro shi takeyi kar ya wuce da ball ya cinyeta, zuwa tayi tasa kafa a Jikin tasa kafar zata kwace kwallon ai sai ta Fadi tim a kasa,Jamilu ba karfi ko na anini,dariya yayi yace ka dinga sakin jiki haka wai ko yaro ne indai namiji ne ai Yana da karfi duk da Kai yaro ne,Naila sai tayi halin matan na son girma tace wlh a'a da kadan ka girmeni tab, Spark ya kalleta yace anya Jamilu anya kuwa,Mene? ta furta tana dariya, zo na taba kirjinka Jamilu,Naila ta hade rai tace idan gay kake yi ka Fadi gaskiya malam, kyale zancen yayi yace a ransa sai na taba kirjin Jamilu dole wlh, suka ci gaba da ball dinsu, Naila sai faduwa take ana zuba mata yanka, taci sa'a ta kwaci ball amma Bata yi komai ba ya kwace tace wlh ban yarda ba ya kamata a kawo rapefree,yace to a samo.

Goje ne yazo wucewa Naila tace Goje yawwa tsaya ka zama alkalin wasannan idan anyi mugunta ka busa please,Goje ba usur ba komai yace ai na Saba da fito wajen kiran karena sanda Ina gida ku fara,suka fara har su Naila suka samu Yan kallo a wajen da yawa suka tsaya suna kallon Jamilu domin shike kawo su wajen, Spark Dan girman Kai ne baya harkar kowa.

Goje ya shiga da gajeren wandonsa da singleti ya saka kwallo a tsakiya sannan yayi fito da baki yace ku fara,Spark ya cillawa Naila ball ta fara tafiya yazo ya kwace Yana rabarta ta zube a kasa ta Fadi wai ya bigeta,alkalin wasa ya busa fiiit aka mikawa Naila ball ta buga wai an bugata da kasa, ta bugo kwallo Spark yaje ya kwace ta bishi zata kwace ya dinga yanketa Yana wasan kura da Naila Jamilu a filin, ta gaji ta manta ta rungumo kugunsa ta rike shi Kam Kam tana haki, Spark kamar gunki haka yayi poster ga Goje Yana ta busa anyi rike amma basa jinsa sai faman fito yake bakinsa har ya gaji,Yana zuwa ya dagawa Naila hannu yace an baki red card, sai lokacin suka dawo hayyacinsu ta sake shi da sauri tana dariya cikin hakki tace to kana gani zai kashe ni da gudu,Red card aka baki ki fita.

Akwai Wanda suke kira da Muler ya shugo yace shi suyi da Spark yace to,suka fara ball da Spark da Muler,Muler mugun kwaro ne a ball har ya fi ma Spark iyawa,Naila tana waje tsaiwa ta gagareta ma sabo da gajiya sai zama tayi a kujerar Yan kallo tana hutawa, mazan suna ta zuwa karshe ma shiga suka yi da yawa aka raba kwallo, harda Spark ko wanne gida da Goal keeper, suna ta yi Naila tana ta kallo tana nishadinta ganin yanda Spark yake kokari a ciki,ya iya ball sosai,sai da suka kwashe kusan 2hrs sannan Spark ya fito a gajiye ya barsu suna yi wani ya shiga a madadinsa,Naila da su Scoler Yan Daudu sun taru suna ta kallo su a dole mata ne,Scoler yace Ina zan iya hada jiki da Maza su balla ni Ina zaune cikin rufin asiri,wani labaran yace Kai Jamilu ka Mori saurayi Kalli yanda yake tafiya Inama nice,Naila tace gata sunanta Spark ai Yar budurwar tayi tsaya ma kuga ta karaso, Scoler harda fifita da hannunsa yace Dan Allah ya jikin Spark din Yana sparking kuwa ahhhh ahayye ke Kam Jamilu kin caba ga farin jini ,ni dai gaskiya kinci amanta ,Jamilu ya Kalli Scoler yace ai kasan so shi tsuntsu ne tashi yake daga kan wannan ya koma kan wannan,Labaran ya furta ai ni bana bakin ciki Kun dace tunda ban sameka ba Jamilu to uban kowa ya rasa,Tantiriya ta mike tace mun tafi Shan shayi ni da Baby Spark,Spark ya jita ya daure fuska ya tsani Dandaudu a duniya,ta bi bayan Spark suka tafi,Spark shi tunda ta rungumo kugunsa abinda yake ji a jikinsa game da Jamilu ya tashi hankalinsa, Sam tunani yake sosai akan abin Nan, me yasa wai ko ya suka hada jiki sai yaji shock,tsaki ya ja yana tafiya ya juyo ya Kalli Jamilu yace a Ina ake soya kwai? Jamilu yace kawo a siyo Maka,kudi ya zaro dubu daya yace guda biyu za a soya sai tea,Ina da bread,Naila tace to ni uku za a soya min Kai biyu

Please Login or Register in order to submit comment