Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
dan wani abu muka ki fada muku ba illa saboda munsan baxaku bari muje ba Hmm a bar maganar se munje gida amma ban son ku sanarwa ahmad wannsn maganar?am i clear? Uhm Gud **** Hajiya da maryama sun ji dadin gani su sunje lafiya sun dawo lafiya Ta cika su da snacks da abinci kai hajiya irin wannsn gara ai se mu kasa tashi Ai haka nake so Hajiya Uhm ina jinka Hajiya nida ya fsruk munyi muku laifi To daga dawowa? Me kuka aikata? Munje dikko Da sauri ta juyo tana sakin cup din hannun ta kallon su ta dinga yi dayan bayan daya dan jin karin bayani . Maryama tace duk a yaushe kuka je? jiya muka je muka dawo yau *OMG* kun san me kuka yi kuwa? In ahmad yaji magansr nsn Aunty mun gaji da wannan rayuwar ta wahala mun gaji Inji faruk taya muna da yar'uwa amma mu kasa ganin ta shekara kusan ashirin da daya kennsn amma bamu santa ba ku tausaya mana da kun ga yadda taji dadi da ganin mu ba Amma... Kyale su maryama sun yi daidai sun girma ai Inji ahmad ashe ya dawo yana jin su Bani ruwa na sha dan Allah aunty To ahmad sannu da shigowa youwa Ya zauna wani satin za a tura consignment din suks amsa da to Yana shan ruwan ya buda fulas ya debi abincin ysna ci Ku kuma fa baxaku ci wani abu ba ? Ko ba kwa jin yunwa? Junan su suka kala cike da mamaki ba haka suka zata ba Mubarak ya dauko wayarsa ya tura text wa abban su Yana jin alamun shigar sako amma be duba ba seda ya gama cin abincin tukuna Ya dauko wayar ya duba hoto ya gani a kasa kuma an rubuta _kanwata aisha humaira ahmad kumo_ Murmushi yayi amma silently a fakaice se kuma ya maida wayar sa cikin aljihun sa ya mike hajiya zan shiga na huta To ahmadu seka fito To.hajiya. *** _hajiya ta ce mubarak fada min ya jikata take?_ _hajiya kinga hoton ta ma kyakyawa ce kinsan kamar su daya da abba ya fada ysna nuna mata hoton aisha humaira hawaye suka taron mata a ido na dadi yace kingan ta ko me kyau ga surutu in fada miki kinga wannan hoton kinsan waye tare da ita?aa fada min mijin ta ne haba miji?eh mijin ta kuma yayan ta kace kun sha hira da ita ka fada mata labarina?uhm uhm na fi so kuje ku gsnts ds ksnku ta ganku kums dan tana kewar ku da yawa musammsn ma abba dan Allah ki lsllaba abba kuje inda take wallshi tana son ganin abba_ _ban san ya zanyi da ahmadu ba tsoro yake ko me Allah kadai ya sani nsyi magiysr amma yaki zuwa aunty mariya ta amshi wayar masha Allah tabsrkallah tayi kyau sossai mubarak ya adda? Tana nan lafiya tana gaishe ki_ _Allah sarki dada ta fada ta share hawayen ta_ _dakin sa da ya shiga wayar sa ya dauko kawai ya duba hoton da kyau ba karamin kama suke da juna ba shi da its kamar photocopy din sa alhamdulilahi Allsh nagode maka daka bsni wannsn kyauta Allah ta jiksn ki aisha Allah kai rahama kabarinki tabbas kenmata ce me hakuri matar kwarai daga ksn ki ban kuma yin wani aure ba bazan iya bawa kowa darajr ki ba nayi rashin mata ni kadai nasan yadda nake ji a raina wajan nisanta kaina daga diyata amma komsi yayi fsrko zai karshe hsr ya zamo labari zan je na samu diyata na nemi yafiyarta na bata duk wata kulawa da bsn bata ba a lokacin da take da bukata_ _Ya share kwallar sa ya shiga wanka_ ~FALO~ kai mubarak kira ta mana ka fada mata mun karaso lafiya au na manta wallahi nasan tana can tana zuba ido a screen din wayar ta Shi yasa na ce ka kira ta Eh kirata nima naji muryar jikata! Kiranta ya soma yi yasa a handsfree bugu byu ta dauka lokacin tana kwance kan masdook yana shafa mata kan ta suna hira Hamma ya bugo hamma ya bugo ki dauka mana to kar ta tsinke au Hello hamma ya kuka je gida? Kunje lafiya ko?ya hanya kunci abinci? Kun huta? Hamma masdook ya dungure mata kai ke sokuwa ce wallahi ki barshi ya amsa daya se tambayoyi kike aika masa wanne ze ji? Au am so exicted kawai Ta murguda masa baki ni ba sokuwa bace Mubarak yayi murmushi yace ya fsruk kana jin su ko sun fara ai aisha da surutu take Mun xo lafiys lou kuma muna kewar ku ku dukka Muma haka ga hajiya ku gaisa da ita Tom Hajiya ina wuni? Lafiya lou aishatu ya gida ? Lafiya lou hajiya kaka nan fa kuma suka fara hira a tsakanin su. Har bacci ya fara daukan ta Maddook ma sun gaisa da ita hajiyar. Ba karamin dadi naji ba hamma wajan gaisawa da hajiya saura abba na rungumeta ysyi sannsn yayi peacking din ta a goshi muje na raka ki gun dada kar ki min bacci a nan ki jsza min daukar ki ga nauyi kina da Kirjin sa ta doka yayi tarin karya kai ai kece action humaira din don karfi suna hira suka shiga cikin gidan har dki ya rakata ya koma nasu bangaren. Yana shiga yaji sako ya shigo masa _mr.arrogant gudnyt and i love u ♡_ Smiling yayi _it's mr.arrogant saying gudnyt to mrs .arrogant love u to ♡_ *_washe gari_* Dukkan su a dakin dada suna hira suka yi break ana ta hira da misalin karfe shabiyu suka shirya da nas da amira da humaira da masdook da yusuf dan komawa gida zasu sauke su amira sannsn su wuce kano Amira ta tsaya ta window ta rada wa humaira abu a kunne suka kyalkyale da dariya Masdook yace ai se anyi gulma ai se anyi ni na sani Se anjima kuje lafiya amin. Da suka isa kano ma sun sauke nas a gidan shi tukuna sannan suka koma gida suna shiga ya rungumota yana shinshinar jikin ta tana nokewa hamma bara...shhh kar kice komai daukarta yayi cak ya nufi daki da ita ya kwantar da ita ksn gado ya soma romancing dinta ta ko ina dana ga zai lula wata duniyar sena ja musu kofa na kulle na koma masu gadin gidan dan be kulle kof ba saboda zumudi. Se wajan magrib suka fito suna sheki sunyi kyau tana sanye da karamar top da short haka shima suks xsuns Ya zaki zauna kums To mezan yi abinci mana tab wallshi na gaji sede ka girka mana yau ja gajiyar dani kuma amarya nake ba aikin da zan yi ma 😜 Kin fiya ragwanta humaira ko zs a yi second round ne Hah! Wallahi kai mugu ne ya juyo yana mata cakulkuli ta dinga dariya dan Allah ka bari hamma dan Allah to waye zeyi girkin? Ni zanyi amma seka taimaka min Allah jikina ciwo yake kai din janab bana wasa bane Haka nake so ki san cewa mijinki gwarzo ne a ksn ki Uhm aiko na sani *_weekend mubarak_* _daga khairi_ [6:27PM, 3/14/2017] Kairat Up: ✨✨✨✨✨✨✨ *Aisha Humaira* ✨✨✨✨✨✨✨ *Na* *Khairat up* *73* *©* *_daga fadar hikima writers association_* _don't listen to the saying of eyes,those eyes also decives,try to identfy the right eyes that suits u_ Seda ta gama kuksn ta sannsn ta fita falo ta zsuna yau bata da niyan dora musu girki ma sam sam aisha me kike nufi ne? A ina? Girki dare nayi And ? Kallon ta kawai yayi ya gyda kansa ya shige daki jim kadan ya fito tare da khadija ya dau key din sa ya yi waje aisha se mun dawo tsabsr takaici da bakin ciki kasa magana ma tayi ni hamma ze wa wannan wulakancin? Shi kuma resturant suka je da khadija suka ci abinci tare daga nan ya kaita gidan kanin baban ta dake dawaki road suka gaisa da matan sa sannsn suka yi yahuza suya ya siyo nama da youghrt ya dawo cikin motar saura na ice cream ya fada yana murza hannayen sa ya biya ta oisis ya siyo ice cream din sannan suka tafi gida. Be samu humaira a falo ba amma yasan tana daki ya shiga dakin bayan sunyi sallama da khadija kan ta shirya da wuri gobe wajan takwas zasu wuce asibitin baya son african time na mata To hamma seda safe Allah tashe mu lafiya amsa ya bata ledar ta sannan ya leqa dakin bata nsn kennan tana dKin sama Saman steps ya hau ya shiga dakin ta tana kwance ko a ksn kujera tana tunsni kan sa ya girgiza ya karasa kusa da ita ya tsuguna a kasan kamshin turaren sa shi ya isar mata da sakon shigowarsa dada kulle idan tayi Haba sweet mata ta ni na isa kallon wata da sunan soyayya bayan ke kin san fa matsayin khadija a guna ko dan darajar mama bszan hanata zama a gida na ba nasan aishata will understand me fahimta ce ke aisha humaira ki cire zargin cewa akwai wata bayan ke a cikin rayuwata insha Allah da yardar me duka me kowa da komai kin gama samun masdook kina ganin a iya wuni daya gaba daya na rame na zama abun tausayi saboda rashin samun kulawar ki humaira ta a taimaka a min afuwa kinji matata kanwata anminiyata Ni ka rabu dani ai ban ce ma komai ba kinji yadda zuciyata take bugawa dari dari kawai aisha take kira ke ni in banda shirmen ki ta tuyo tana kallon sa aa ai magana zan miki ba ba a nake miki ba ta murguds masa dan bakin ta in bsnda abunki humaira me zan kalla a sauran mata gaki komai ya ji baki san matsayin ki ba da girmsn ki a gareni ke ni duk sauran matan nan muna mata nake ganin su. Ai dadin baki ko hamma kai expert ne a yin sa Kinga naman nan na sanyi daure muci ki sha ice cream din su mu cigaba daga inda aka dora ba abunda kiks ci fa yau ina kallon ki Ai baka damu na ci din ba ne Wai kin san ko yadda nake ji dake har fushi naso nsyi irin wadda na saba yi ta da in koma masdook muhammad dikko na da amma a ksn ki na kasa kin gama da rayuwata wallahi humaira ban san irin son da nake miki ba humaira. Bani naman ta amsa tana ci tana gamawa ta mike ta yi hanyar wadrope ta dauko towel da gown ya yi maza ya bita ya hadata da wardrope din ya soma aika mata da kissises ta ko ina na jikin ta huma...ir..a kiyi hakuri ki tausaya min ya sa hsnnun sa ya zare mata zip din rigarta tsugunawa tayi a kasa ta runtse idanta gam gam heartbeat dinta yana bugawa gudu gudu sauri sauri. Seda yasan yadda yayi ya lallaba matarsa suka lula duniyar maji dadi. *** _bayan wata daya_ Dada na zaune a tsakar gida ita da inono da mardiya matar isyaku suna tankade dan yin girkin dare Sallama suka ji daga waje Ta amsa tare da cewa a shigo Yana shigowa dada ta mike cike da mamkin wanda take gani shi kuma tsugunswa yayi har kasa ya gaida dada bata idda amsawa ba ya sa gwiwowin sa a kasa ya hade hannayen sa biyu ya na zubda hawaye ya ce *dada na jigata haka,na wahala,na gaji,na kasa kara dannewa,na kasa bin abunda nayi alkawari na daina kunyar na daina zagin kaina a daki kawai abu daya nake da buksta yanzu kafin na koma gun mahilicina hakki yana damuna dada ki tausya ki yafe ni da aikin dana aikata dada kin kasance uwa me tarin kulawa ga yayanta da basu tarbiya kin kasance uwa me tausayi da hakuri dada ki yafe ma wannan dan naki a sanda abubuwa suka faru dada shaidan ya shiga tsakani ga kaidin mata dada abu daya idanuwana suke da muradin gani abu daya kunnuwana suke da bukatar ji abu daya hannuwana suke da bukatsr tabawa dada ki yafeni in ga humaira dada ki yafe ni inji kalmar abba daga bskin humaira dada ki yafe ni hannuwa na su rike na humaira dada jinina nake son gani dada ina da komai amma bani da komai na rasa aishata ruhina bazan koma gun Allah ba ban ga jinina ba jinin aisha* Mike tsaye ahmad bari kuka haka aisha ai taka ce ni ban hanaka aisha ba illa na rike alkawarin marigayiya ne ahmd duk abunda ya faru mukadiri ne daga Allah kuma ta faru ba yadda za ayi dama ni laifin ka da nake gani rashin waiwayar mu da kayi ka watsar da al'amuran diysrka kasan da ita kuma ahmad ni bana kin ka domin kai din abunda aisha ke so ne ban san mesa kaki zuwa inda take ba ko sau daya amma a nan kuskuren ka yake na watsi da diyarka wadda ko hula baka taba aiko mata ba baka san yarintar ta ba baka kuma san girman ta ba baka san halin da take ciki ba da dai baka sani ba shi ne an zalince ka amma kasan da ita Allah ya kiyaye gaba Dada baki zuwa ba da gayya illa ina bin alfarmar da aisha ta nema a gurina Aisha ta tura min da wasika ta hannun aunty Eh tabbas ni na bada wannan takarda. A cikin takardar aisha ta nemi alfarma a gurina _bana kin ka ahmad kuma ban dau abunda ka min a matsayin cin fuska ba illa kadarata kuma ko kadan ban rike ka ba ko dan darajar hajiya bazan ki jinin ta ba ahmad ina gadon asibiti nake rubuta ma wannan wasikar tamkar wasiya ce na baka ahmad na soka kuma bszan daina ba naso munyi wata rayuwa me tsawo me dadi da fadi da kwanciyar hankali sede Allah be nufa ba bazaka manta dani ba ko dan yara biyu da na bar maka ka rike_ _mubarak ka kula dashi amma diyar dana haifa bazata iya xama a gidan ku ba sabda matar ka bazan yarda a hallakata ba_ _dan ba abunda bazata iya ba amma ina neman alfarma a_ _gareka ka min wannan hallacin in har ka taba sona koda inci daya ne ahmad ka_ nesanta kan ka daga _gun diyar dana haifa har se ta kai munzalin_ _da ya kamata kasanta wato bayan girmanta ka nesanta ta daga_ _wahala da bakin ciki na gidan ka ka bar min ita gun dada ban son_ _wata alaka ta hada ka da ita har se sanda ta mallaki hankalin ta_ _duk tsiya zata neme ka ina so ka bawa mubarak labarin_ _rayuwata a gidan ka ina so ka rike shi_ _amana ka hada kan sa da danuwan sa faruk don duk yayan ka ne karsu raba kan su ka rike su amana in zaka iya ka koya wa kan ka rashina da rashin diyarka ina son ka ahmad kayi kokarin gyara gidan ka na barka lafiya taka har abada aisha humaira mubarak dikko_ Dada taya zanki bin zancen aisha to na kai kasa bazan iya ba ki bani diyata dada Ahmad kar ka damu aisha ai dama taka ce sede tana gidan mijinta a kano Hawayen dadi suka zubo masa ya riko hsnnayen dada dame zan saka miki da wacca kalma zan gode miki dada kin gama min komai dan kin rike min amanar diyata dada Allah saka miki da alkairi ya sa ki gidan aljanna ba abunda zan iya saka miki dashi dan girman ki ya wuce misali. Ahmad shiga ka zauna a ciki bara a sama maka abu kaci ka sha hanya ina hajiyar taka? Tana kumo amma jibi zasu zo da su mubarak To masha Allah Allah ya kawo su lafiya amin . Nan aka fara hidima da shi a gidan su baffa ma nan suka same shi suka dasa wata hirar ta ya bsyan rabuwa. A nan dada taji ma ai sun rabu da tsohuwar matar tasa tun tutuni da daddewa ma. ***** *KANO TA DABO* Hamma uhm Ina ji a jikina wani abun alkairi na bina Uhmyayi murmushi haka ne humaira Kasan me? Uhm uhm sekin fada Hamma mubarak yace min yana da surprise da ze min To me wannsn Nima ban sani ba wallahi amma am excited naji me ze min Nima kinga kin sani a suspense ai gwara se mu shiga suspence din tare ni da kai mu dukka Ya yi kissing bakinta ai kece mu dukka din ta ja hancin sa Ouch kin fiya cin zalli fa Ta masa fruny face yayi dariya mara ji kawai Ya shafa dan cikin ta yaushe zan yi ajiya ne naga kullum aiki ne amma har yau ba result lafiya ko. Kai zan tambya kila aikin naka beyi sossai Kai lallai ma ke din nan duk akin danake kina korata kice baya yuwuwa?zaki sani yau in na kamaki ki sekin ce dan Allah in bari ku huta Ta sa masa dariya A nan suka yi ta hira tana tsokanar sa yana basarwa daga karshe ya sunkuceta ya yi daki da ita. Asuba ta gari masoya. [6:28PM, 3/14/2017] Kairat Up: ✨✨✨✨✨✨✨ *Aisha Humaira* ✨✨✨✨✨✨✨ *Na* *Khairat up* *74-75* *daga fadar* *©* *hikima writers association* Da misalin karfe uku da rabi na rana aisha zaune ita kadai ta dawo da wuri dan lecture daya kawai suka yi ta gama sakwara se nishi take dan daka dan ma maigidan yace shi yake so yau da bazata yi ba bata son dakan sakwara tayi miyar agushi taji nama da kaza zako zako a ciki da busasshen kifi yaji kayan hadi da gyada a ciki ta jera tebur kawai jiran dawowarsa take tadan kishingida taji tsayuwar motoci kusan guda biyu ta ce aa yau da bako yazo min? Ta cigaba da zama seda aka buga kararawa tukuna ta mike cike da zumudi ta duba ta dan ramin kofar taga hamma mubarak da hamma ni'imatullahi a tsayi da sauri ta bude tayi wani ihun dadi Sannu da zuwa hamma sannu da zuwa Kafin yace oh ke kam kin fiya ihu ba cewa mu shigo ciki? To mu shiga hamma ya hanya? Suna shiga wata motar ta kuma tsayawa Yau ksm kace gidan nawa ya yi albarka su waye kuma? Da dada,da mijinki,da hajiya,da aunty maryama,da baffa idi da baffa...bari bari fada hamma nasan housefull kuka zo min ki tsaya mana kiji da wa kuma Aa i cant gwara na karasa na gan su da ido na dada fa kace ka barni naje na yi tsalle kanta Yana dariya ta fita daga falon tayi waje da gudu wani tsalle ta daka kan dada tana ihu sannun ki dada kingan ki yau a gidan aisha humaira naji dadin ganin ki Humaira ki na nutsuwa mana Hararsa tayi cikin wasa Ya maida mata Baffa idi ya mata dakuwa Tayi kasa da kai taja dada zuwa cikim gidan bakin ta yaki ruhuwa dan murnar dadin ganin dada Aisha kina da bako fa a waje baki kula ba? Bako kuma,waye? Wani bawan Allah ne To bara naje na ga Aa zauna masdook shigo dashi Ai tunda suka shigo tare da hamma masdook ta saki baki galala tana kallon sa cike da mamaki da al'ajabi ta kalli wannan ta kalli wancan Ma.. Dada Abbana ne? Uhm shi ne aisha abban kine ahmad ne yazo ganin diyarsa Hawayen da suka taron mata a fuska suka karasa zubowa se kuma ta mike ta karasa kusa da shi tana hawaye Ashe zan ga abbana? Ashe zan gan shi a duniya na furta wannan kalmar ta abba? Ya Allah !Allah nagode maka Allah nagode maka kaine abun godiya kai ne me yadda kaso a san da kaso a lokacin da ka so dada,hamma,yau ga Abban *aisha humaira*ina kallon sa yana kallona wanda zan kalla nace Abbana Ta rike hannyensa ta dora goshin ta a kam su tana hawaye Abba ka dade baka zo ba Ka nisanta ni da kiran ka da suna abba Abba ni me nawa a sabanin ka da ummina da dada ? Da har ta shafe ni ban samu arzikin cin yarinta da ku ba bayan ina da dangin uba Abba *ba a min adalci ba* a *rayuwa ta* da ka hane ni da sanin *waye kai a gareni* Abba soyayyar uba nada muhimmanci a rayuwar ko wanne dan 'adam bayan ta uwa abba ni mesa baka yi tunanin ko da daga nesa ne ka kalle ni ko ka min magana ko ka gan ni? Abba bakin jinina ya kai haka? Yana hawaye ya girgiza mata kan sa kiyi hakuri humaira ni na kasance me laifi a gareki ban san mezan ce miki ba ban san da wane ido zan kalle ki ba ban san ta ins zan fara neman ahuwar ki ba aisha ki yafe ma mahaifinki da ya yi rashin kula da d'iya kamar ki Abba ka daina fadin haka ni nasan komai ka gani daga Allah ne yanzu lokaci ne abu daban lokaci ne na farin ciki abba nagodewa Allah da ya kuma hadani nida kai nasan waye mahaifina Yau duk wanda zai min tambya cewa ni din *yar waye*zan ce ni din diyarka ce abba zauna kaji Ta cika masa gaba da kaysn ciye ciye Yana fara'a yace duk ni kadai humaira? Uhn abba na Hajiya tace ba a ta kaka ko? Ai ku kun tsufa Aka sa dariya abban naki se ya rigani cikawq ni ina nan tare dake Humaira tayi dariya lallai ma hajiya sannu Masdook yace hajiya gaya mata kin fita kwari ita sabuwar jini ku tsohon hannu Aka yi dariya gaba daya dakin. Nan hira ta kacame ta bayan rabuwa ana ta raha kamar kar a rabu _dama komai yayi farko zai karshe har ya zamo labari komai na zaman duniya dan hakuri da juna ne da zaman lafiya_ Da daddare ko suna hira suna cin tuwon shinkafa da miyar kubewa danya cikin tray daya Aisha ta kalli hamma mubarak tana dariya hamma uhm aisha Kulle Kamar ya? Kai de kulle? Uhm cas Tom Youwa abbana Uhm aishata Abba kayi wa hamma aure shi da hamma faruk Kema kya fada sun fara tsufa ba magaji na gaji da neman masu mata ke kila kya samo musu Sossai ma abba ai sun yi mata fa sun rufe ka ne basu sanar da kai ba Aisha me haka? Me kuwa gaskiya zan fada musu ne ayi da wuri ko kuwa nasan fa kuna so kuna kaiwa kasuwa Eh lallai ma yarinyar nan Abba da fadimatu ta gidan mu da rabi'atu Kee aisha sharri inji dada Wallahi Allah dada da gaske nake miki in kuma sun karyata dada ki tamaye su kiji Megidana wai haka ne Shiru yayi be tanka ba dan aisha ta gama dashi wallahi shi kuma kunya ce dashi kamar me Ka fada min faruku haka ne? Dada ni mezan ce?ai tunda ta fada hakan ne Kinji ko dada kawai se munzo neman aure dikko Masdook ya mintsine ta a baya ta zabura wayyo Allah na hamma mena ma? Ai da sauri yayi waje dan aisha zata kunyata shi cikin su baffa aka sa dariya Dada tace meya miki? Mintsini na fa yayi? Kowa ya s driya wayanan yaran halin su sai su yan banxa To ai shi kenan mu dama haka muke su a dinga *zumunci* Allah ya tabbatar da mafi alkhairi Amin dada Ahmadu mu kuma daginmu sun kare a dikko ta katsina Aiko dai hajiya gashi nan dai zuri'ar tamu daga kumo zuwa dikko Allah dai ya kara tabbatar da mafi alkhairi a zamantakewar mu ina jin dadin wannsn *yanayin*Allah dai ya sada mu dukka a gidan aljanna amin ya Allah [6:28PM, 3/14/2017] Kairat Up: ✨✨✨✨✨✨✨ *Aisha Humaira* ✨✨✨✨✨✨✨ *Na* *Khairat up* *74-75* *daga fadar* *©* *hikima writers association* Da misalin karfe uku da rabi na rana aisha

Chapter 12 of 14