Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
6 / 6
yasan masifan xafida xugin da yakeji a ilahirinjikinsa domin Boka Barnohu yajefiSarkimmu da Macijin tsafi kuma maciji yacijeshi yasamishi bakin guba maikarya garkuwan cikin dan,adam lallai indan bamuyi wani abuba nanda Cikar kwanaki Bakwai tofa gubar xatai kacakaca daduk wata laka najikin Sarkimmu xai xamoshiba,amaceba kuma shiba,arayeba kuma har,abada baxaiwarkeba kuma baxai iya amfanama kansa komaiba saidai kawai yasaurari mutuwarsa dankari koda Jama,ar Sarki Kaushatu sukaji wannan bayani Sai sukaraya hankulansu sutashi xuciyarsu takama tafasa sufara shirin komawa baya domin daukan Fansa akan Dakarun Xumunci Koda Sarauniya Xa,uma tagane shirinsu saitakwarma ihu tacekai rundunar axxalumai masucike da burin Fansa kudakata Saisukaja dagasukatsaya Sannan tace ahalin yanxu bamuda lokacin daukar fansa aikimmu shine musamama Sarkimmu magani kafin Cutannan taci karfinsa Sannan tadubi Sarkin yaki Kanwar tace yaka namijin duniya yanxu menene mafuta Sarkin yaki yace mafuta Guda biyune kuma acikin biyun dolene muidaya Sarauniya xa,uma tace wadansu hanyoyine Sarkin yaki Kanwar yace hanya tafarko itace saimun tunkari kogin BaharJabal domin muriski koramar San,an watakamar koramace wanda take atsakanin manyan duwatsu Masu farin haske to indai muriski wannan Kogi na Sann,an har mukai nasara Tsunduma Sarki Kaushatu aciki yalume ruwan kogin yaratsa kowani Sassana jikinsa tolallai Sarki Kaushatu xairayu Kuma xaikara Karfin Dantse gamida Karfin Sihiri Sarkin yaki Kanwar yace to amma kusani tunkarar Bahar Jabal daidai yake da tunkarar mutuwa gabadagaba domin akwai masifu da balao,i marasa adadadi ahanya dakuma kewayan koramar San,an Xaicigava da bayanin mafita tabiyu Sai DODO Guraba yace aa Sarki yaki Kanwar lallai mu gwaraxane afannin yaki sannan muna fuskanta yakin Duniyane to akamme xamu tsaya xaban wata hanya mafi Sauki domin Samama shugaban lafiya yadaga Muryayace nidai ashawarata kawai mutunkari Bahar Jabal ko,amutu ko,airai natabbatu sai wasundangana da kogin San,an yace komai kukace maxaje bakidaya Runduna sukadauka Aljannu da mutanedodanni damiyagun halittu Mutafi mutafi mutafii San,ana Jinhaka sai SarauniyaZa,uma tai ihu tace tunda tawaga ta,amince mutafiiii take tawaga taiKudu domin riskan Bahar Jabal sukarisa koramar San,ana acan kumaBangaran Dakarun Xumunci sunkewaye Boka Barnuhu inda sukaitamar Magaunguna amma sai abin yaxamo abanxa babban abin tashin hankalin shine Ilahirin jikin Boka Barnuhu kwari,nnanne suke yawo ajikinsa tacikin cikinsa saidai kaga suna takai kawo asassan jikinsa bahalin tabasu duk inda akai kuskuren tabasu ko yunkurin kashesu tofasaikaga Sun karayawa dankari hankalin Dakarun Zumunci yatashi sukarasa abinyi Kowanne kansa yadauxafi cansai Sarauniya Atine Yarmama tasabi karanto wasu kalaman Surkulle tarika cikatana batsewa tana wani Damdam tana ham taiwani rubutu daga Sidirorin tsafi akasa tashare sannan takwashe kasan GurinTakwarara ihy takira wani suna Saubakwai Kumal kumal,,,,tawatsa kasar Sama aisai asaki wata tsawa da Walkiya mairitarwa gamida bantso NATSORATA NAFECCE RUNFAR SHAYI#BANGON!DUNIYA!PART!#36:: Lokacinda abarka tsawa gamida Walkiya mairaxanarwa saiga wani damitsitsin,aljani yabayyana da wani mangare rankai dasilalan kafafu dawasu kwalakwalan idanu jajaye Tamkar garwashin wuta yanada katon baki tamkar kofan gari tabbas duk wani shika shikan muni na bantsoro suntabbata ga wannan,ajani Yarika Kallon Dakarun Xumunci yana lashe baki Sarauniya Atine yarmama tadakamai tsawa tace kai Rakumi uban gararamba mugun bako nakowa matsatstsaku mai bakida yawa, shugabana bashida lafiyainabukatan taimakonka aljani Rafsago yadubi Boka Barnuhu wanda yake kwance ko numfashi baya iyayi wani haske yafuta a idanunsa yashigi Idanun Boka Barnuhu haskenyaratsa ilahirin jikin Boka Barnuhuamma ko motsi baiyiba Sai aljani Rafsago yakwarma ihu yace yaku Dakarun xumunci lallai kusani Shugabanku yana cikin Mawu yacin hali rayuwansa tana makale Sadauki Amirul Jaishi yace mekake nufi da rayuwan shugabanmu tana Makale aljani Rafsago yace inanufin nanda cikar kwanaki Bakwai xai mutu atare kuma alokaci Guda Dakarun xumunci sukwarara ihu gamidaXare takobi suka kewaye aljani Rafsago zasuimar wankan takubba Sarauniya atine takwarma ihu gamidadaka musu tsawa tanacewa aa maxaje kadafa kui kuskure cak sukatsaya Atine yar mama taceda aljaniRafsago kai uban Gararamba ina mafuta,yace yanxu Yaxama dule Kutunkari dajin Kayaba sannan ku,isa Rijiyar dake kan Dutsan kayaba kudibi ruwan kuba Shugabanku yasha sannan xaisami lafiya kawai saiyabace bat Nanfa sukai xuruxuru Sarauniya Atine tace Wanene yasan Dajin Kayaba Sai Miraa tace wani kasurgumin dajine maicike da miyagun halittu aljannu da munngan dabbobi Masucin naman dan,adam tabbas shiga wannan daji daidai yakeda fadawa tarkon mutuwa sannan koda munyi nasaran shiga Dajin tosai munkarisa Dutsen maidibi shima wani masiface maixaman kanta sannan kusani tunkaran Rijiyar dake kan Dutsennan tamkar tunkaran mutuwane domin akwai wasu bakaken aljannu dasuke bautama wannan rijiya hatsabainenakarshe Sannan shaidanune sunada mutukar Karfi sannan matsafane na innanaha tabbas gogo yakidasu takar karo da ajaline Wohoho kawai Sai Sarki Lukman yace Faduwar gaba asaran namiji lallai babu tattaunawa babu shawara kawai mutunkari Dajin kayaba ayita takareTake sukadauki hanya suna tafiya cikin matsanancin gudu tamkar masu shiri xagaye duniya ,suko su Kairuf sunnutsa cikin jeji tafiya sukeyi cikin Sauri sauri dakuma taka tsantsan watarana daga cikin Rane kunsusai suka riski wani fili maitsawo gafadi sannan akwai wasu busassun ciyayi wanda kekwace awannan guri saura kiris Kairuf ya Fada Wannan Fili Sai Kilxam yai tsawa cikKairuf yadakata Yakalli Kilxam inadalili wannan ihu Kilxam yace kusani abokai, wannan fili akwai wasumiyagun halittu aboye awannan guri mutukar mukai garajen shiga tofa xamu hallaka Yarima Lamir yace to menene abinyi yanxu xamu juya dabayane Kairuf yace aa ai indai musa gabanmu aguri tofa bamaganan komawa baya damin bakidayanmu sai Mun hallaka acikin wannan Daji, Xamir yace har yanxu aikin Kilxamne yasamar mana da mafita domin shine Maidawa Kilxam yace tokusaurareni kuma kowannemmu yanemi Gurin buya take suka koma bayan manyan itatuwasuka Rabe Kilxam yadaki kasa gamida ambaton wasu bakin kalmomi take wata Barewa tabayyana agabansa yasa hannu yadaki Barewar sai tafada cikin ciwarnan Dankari aisai wasu mahaukatan kuraye suka taso mata sunkai su arba,in suka yanyameta lokaci guda suka cinyeta hatta kashinta saida Sukai masa Kurmus sannan Sukoma sukwanta acikin duhun ciyawar sai KILXAM yaceda abokansa sufuto atsorace sukaFuto domin sunga abinda yafaru ga Barewannan Kairuf yace yakai Kixam wadannan wasu irin shaidanun kurayene Kilxam yace sune akema lakabi da yan kwanta kwanta baxasu taba Farautankaba harsaika afka musu tofa asannanne xasuimaka kofar rago sudaka maka wawa Sannan kusani yaku abokaina duk girman dajinnan hanya dayace itace muketa tacikin KurayannanMuwuce Yarima Lamair yace baxaiyuwaba Xamir yace xai yuwu idanhar xamu dage sannan kuma xamubi Shadin Kairuf yace menene Sharadin Xamir yace xan busa wani garin magani Kuraye xasu makance natsawon dakika Sittin inhar mukai nasaran futa acikinsu kafin cikar Dakika Sittin tofa muntsira inkomugaxa to Mun halaka Yara sukalli junansu sannan sukalli Xamir suce kai muke jira lallai xamui iyakokarimmu muga muntsallake wannan tsinannen guri mai hadarin tsiya Kawai sai Xamir yabude jakarsa yadauko wani jan kullallen tsumma yakwance saiga wani bakin gari aciki Xamir yadamki garin yawatsa acikin duhuwan take ilarin gurin yagauraye da wani hayaki mai tukuki yalullube Duhuwar harba,a ganinta Xamir yace abokai kushir shirin gudu lallai daxaran haske yabayyana to mufada aguje babu tsayawa Sannan babu waige har sai munfuta acikin Duhuwar yana rufe bakinsa Sai hayakin yagushe haske yabayyana take suka tsunduma aguje karce gudu inbakayi bani guri gudusuke tsulawa basuda wani buri Facesujisu awajen Rinki kayya saida tafiyarsu tainisa sunadabda futa awannan Duhuwa sai Yarima Lamir yataka wani Guri ashe akwai Rami agurin kawai Sai kafarsa taxurma cikin ramin yaikokarin cirowa amma sai yakasa sai yakwarara ihu inda Alokacin Su kairuf sun isa gefe ammasunajin Ihun Lamir Saisuka waigosai sugaNshi atsaye yana kwarara ihu kayya adaidai wannan lokacinne kuma Dakiku Sitti suka cika Kurayen suka tashi suka fara xaxxare idanu gamida kada Kunnuwa tabbdisai sukai Toxali Da lamir kaitsaye Kurayen sukai gunji sukai kansa suna yakare munanan bakunansu Kairuf yakwarma ihu yakoma dabayasuma abokansa su juya Sunufi indYarima Lamir yaKE TOFA DAMATSALA BARI INYINAN SHAYIII;;;;;;#BANGON DUNIYA PART 37 Lokacinda Yarima Lamir yakafe akasan ramin da kafarsa taxurma yawaiga baya yaga kurayennan na tunkaroshi yakalli gabansa yaga abokansa sunyi nisa suna dabda futa awannan duhuwa alhali basu san halin dashi yake cikiba Sai yakwarara ihu cik Kairuf,Xamir,Kilxam suka tsaya sannan alokaci guda suka juyo dankari aikoda Suga Yarima Lamir amakale gakuma kuraye nadabda cimmasa sai suma sukwarma ihu sannan suka runtuma aguje suma sunufi inda Lamir yake amakale suna isa Kurayen na isowa nanfaKilxa da Kairuf suka xare wasu kananan takubba suka rika kaima KurayeN Sara shikuma Xamir yakama kokarin taimakon yarima Lamir nanfa ashiga dauki badadi tsakanin kuraye dasu Kairuf caraf wata katowan kura tacafki kafar Kairu tagatsa tsananin xafi yakwarara ihu Kilxam yaikumaji yasokama kuran tsinin takobi a,ido take yafasa idonnata bashiri tasaki Kairuf yai karfin hali yamike wata kura takawomar yaga yasa takobinsa yafarke kirjinta wasu kuraye biyu suka dako tsalledaniyyar dira akan Kilxam hoho dannagada wanda yafi dan nakoya kawai sai yaxame kurayen suka dira akasa aikafin sukara yin wani yunkuri Tuni Kilxam yasa wani karfe yadaki bakin daya bakidaya yadagar gaxahakwaranta suka xube bakinta yakarkace dayan tairimi yasakafa yadaki kirjinta taigunji sannan takife akasa yadaka tsalle yahaye ruwan cikin Kurannan yashako wuyanta yasa wata karamar wuka yassyayanke kanta Yadaga kansama yanunama kurayen yakwarara ihu yanunama kurayen kurayen suka tsaye suna wani turjiya gamida gunnji alokacinne Xamir da Kairuf Suka xaro Yarima Lamir daga raminnan koda Xamir yaga sunciro YarimaLamir sai yakwalama Kilxam kira yace kai mafarauci, yarima yakubuta kaxo mutafi Kilxam yace ina kuje kawai lallaini ina tareda Kurayennan Kairuf yace meyasa kake neman halaka madadadin karayu Kilxam yace aa aboki Mutukar na sauki kan Kurannan dana yanke, kasa tofa nidaku duk xamu Hallaka bakidaya saboda haka kawai kutafi lallai ina muku fatan alkairi Ku,isa Bongon Duniya ku,ajiye Sarkan Ajali a,ida yadace yadaga murya yace kuje abokaina nina sadaukarda Rayuwata dominku koda Kairuf,Lamir,Zamir sukaji wannan kalamai na ABOKINSU sai hankalinsu yatashi idanunsu sukai Jawur tamkar xasu fasheda kuka Sai yarima Lamir yace aa lallai Sarauniya Atine Yar mama tace duk wuya duk rintsi kada murabu da juna yace lallai baxamu bar abokimmu ya hallakaba kuma baxamu mutuba Sai yadubi Xamir yace kai jinin tsafine lallai muna bukatan taimakonka Xamir yarintsa idanu yakama sambatu gamida kalaman Surkulle yai yace da kilxam maxa kasaki Kankurannan kai baya Kilxam yace aa baxaka iyama wadannan tsinannun Kurayen komaiba Xamir yadakama Kilxam tsawa yace kakauce nacema take Kilxam yasaki kan kuran yai baya aguje Kurayen naganin Kilxam yasaki kan Kuran yajuya aguje Sai sukai gunji sutaho aguje daniyyar afkamusu to alokacinne Xamir yabude idanunsu gamida nuna Kurayen da Babban yatsarsa Aitake Saiwani wawukeken Rami yawanxu yashiga tsakaninsu da Kurayennan Yarima Lamir Kairuf Kilxam Xamir suka rungume juna dan farin ciki indaKurayennan sukama kaikawo abakin Raminnan Can sai Kilxam yace lallai mukara gaba domin kurayennan tsinannune xasu iya tsalleke wannan ramin anjima kadan take sukaci gabada tafiya har suka isa wani katon dutse suka rasa hanya domin Dutsen yatare ko,ina koda suka gajida xagaye Dutsennan sai suka sami tushen wata katuwar bishiya suka xauna domin suhuta kaiyada sunsan masifarda take wannan itaciya toda basui kuskuren XamabaSukuwa tawagar Sarki Kaushatu dan Kan,ana karkashin jagorancin Shaidanu biyu Sarkin yaki Kanwar dakuma Sarauniya Xa,uma gudu suke Runtumawa adokar daji saikarantse duniyar zasu kure Duniya suna cikin keta daxuxxuka da Koramugamida Duwatsu sai suka isa wani tsuburi mai Suna Sabti lokacinda suke kokarin Ketare wannan Tsuburi sai wasu jama,ar aljannu suka taso musu aljannun suka kewaye ko,ina sukai rantsuwa babu wata halitta daxata gifta tawannan tsuburi face sun turata kiyama nanfa akai cirko ciko ana hararan juna can sai Sarkin yaki Kanwar yace kai tsinannu tanbadaddu lallai inamai mukuumurni daku kauce kubamu hanyamuwuce domin bagurinku muxoba muna kan hanyarmuce taxowa Bahar Jabal mu,isa kogin San,ana domin muima Sarki Kaushatu dankan,ana magani kaiya aikoda SarkinAljanu Manjus yaji cewa Sarki Kaushatune ba lafiya sai yakwarara ihu yadaga murya yadaka Dadakarun, Sarki Kaushatu yace kai tsinannu lallai lallaikoda muna da niyyar barinku kuwuce tofa yanxu baxakurayuba domin kuna tareda babban makiyimmu wanda yajefamu acikin masifa da bala,inda baxamu taba mantawaba yadaga murya yace lallai yaune xamu sauke Fushimmu na tsawon shekara arba,in akannku Sarki Majuss yagirgixa kai yace kai maxaje mutukar kuna so kurayu to saidai ku mikomana Sarki Kaushatu mumai Danyen hukunci domin muhuce takaici afusace kuma ahassale Sarauniya Za,uma tabarka ihu tace Wane yaro kuma wane uban yaro tanuna Sarki Majuss da tsinin takobi yace lallai abisa cika bakida kurarinka sai mundanndamaka mugunyar axaba takwararaihu taitsawa tace maxaje aljannu da mutane gamida dodanni ina Umurtanku daku afkama Wadannantsinannun aljannun kuimusu Daurin huhun goro tadaga Murya tace lallai bana bukatan akashe koda aljani daya acikinsu kaiyyasa nanfa kowanin bangare yakwarma ihu Sannan suka xare makamai suka afkama juna da axabebben yaki hodijon lallai maxa suke maganin maxadumin haka dambarwa tabarke atsakanin mutun da aljan inda Jama,ar Sarkin aljannu MANJUSS ke yunkuri Hallaka Jama,ar Sarki Kaushatu Sukuma suna bigesu suna daurewa TURKASHI ABIN BAMAGANA BARI INKURBI KUNU GYADA{#BANGON DUNIYA PART #38} Lokacinda yaki yakaure tsakanin Dakarun Sarki Kaushatu da DakarunSarkin ajannu Manjus sai arinka bigi inbiga inda Arika sumar da dakarun Sarki Manjus ana Dauresu Kai koda Sarki Manjuss Yaga ana kame Jama,arsa kamar kaji Sai yabarka ihu yasabi kirarari yana cewa saini Sarki Manjuss uban maxaje inkashe mutun insha Kwanyarsa inkashe aljan inci namansa yakara Kwarma ihu yakarci wanikaton Dutse da takobinsa takedutsen yarabe biyu sannan yaikundubala ya,afka Filin yaki wohoho ai al,amarin bakyan fada domin tashi Farko yafekema sama da aljanu Dari kawuna yafarke tubin Mutane Samada Dari kamar Balbalin bala,i tamkar barnan Iska haka Sarki Manjuss kewatsida Jama,ar Sarki Kurungu duk inda yagilma saidai kaga gawawwaki na xuba tamkar annobar Mutuwa kamar wutar karmami Haka Sarkinaljannun Manjuss ke sarrafa takobiyana aika dodanni da aljannu da Mutane lahira kaiya aituni yadamakomai inda yarikabi yana datse igiyoyinda da,akadaure jama,arsa koda Sarkin yaki Kanwar yaga Mummunan barnanda Sarki Manjuss kema Jama,arsu saita kwarma ihu tafalla aguje tafuskanci Sarki Manjussnanfa Suka Sarkeda yaki maitada hankali inda Akaci gabada daure jama,ar sarki Manjuss SHiko da Sarauniya Xa,uma saisukarika kaima Juna sara dasuka cikin xafinnama sukarikita guri gamida ruda ko ina inda kura tatashi taisama tamamaye ko,ina yaki yakaxanta inda Sarauni xa,uma tashekamar Sara tamkartasari Dutse haka takobinta yai tsalle Sarki Manjuss yasa kafa yabanketa taibaya xata fadi yasa Takobi yasareta akafada jini yai tsartuwatsananin xafi Sarauniya Xa,uma takwarara ihu Sarki Manjuss yakecedadariya yadaga takwobi xaimata Fashin kwakwa saiyaji ansa kafa an bankeshi kafin yaiwani yunkuri ansureshi Sama anmakada kasa yayunkura xaitashi saiyaji kaifin takobi amako gwaransa anrutsashida,Ita tabbas yai imanincewa mutukar yamotsa xai hallaka aisai yatsaya cik gamida daga hannayansa Sama Bawanibane yaritsashida tsinin Takobinba Face Sarkin yaki Kanwar yanawani Muxurai daxaxxare idanu sannan yakwarara ihu yadaka tsawa take yaki yatsaya cik Sarkin yaki yaceda Dakarun Sarki Manjuss kai tsinannu kusani Sarkinku yakai kasa sannan yamika wuya gamida Sallamawa shin xakumika wuyane kokoinyi umurni ga Jama,ata suturaku Kiyama ai saisuka karaya gamida tsorata sukaxubarda makamansu sannan sukaxube bisa giwowinsu Sarkin yaki Kanwar yakeceda Dariya yaceDa Sarki Manjuss kaitsinanne menene Maganarka takarshe ga jama,arka maxa kafurta domin mutuwa xakayi saiyace yakai Sarkin yaki lallai idan kakasheni babu watariba da xaka Samu amma idan harka banni araye to xanmaka anfani nida Jama,ata munacikin amanarku lallai xamui mubaya,a gaSarki Kaushatu dankan ana Sarauniya Xa,uma takeceda dariya tace tabbas Dole itace uwar naki tace akyaleshi yarayu shida Jama,arsa sannan suna cikin amanammu take Sarki Manjuss da Jama,arsa sukai muba,ya,asuka hade da tawagar Sarki Kaushatu Sai Sarauniya Za,uma tace Dakaru kushirya domin xamucigaba tafiya domin mu,isa kogin Bahar Jabal mukarisa Koramar San,ana domin Samun lafiyar Shugabammu sarki Kaushatu Danka,ana Runduna tai yyammacin Duniya, Sukuwa Dakarun Xumunci Tafiyarsu tainisa daniyyarsu xuwa Dajin Bikir domin su iski Rijiyar Xurum domin sushayarda Boka Barnuhu ruwanRijiyar domin yasami waraka dagacutardake Damunsa tafiya suke cikin Sauri kamar xasu tashi Sama basuda wani buri face sugansu adajinBakir sunacikin tafiya sai sukai kicibis da wata dandaxon Jama,a maxa da mata yarada manya gasunan Fululu fiyeda fin irga sunkafa bukkoki sunata kaikawo da,alamu wannan al,Umman tanacikin tashin hankali domin mafi yawancinsu sunrame sunkanjale sun xamo tamkar kashidarai yaransu sairafka Rafkankai idanu xuru xuru koda Dakarun Xumunci suka isa wannan Sansani saiWasu maxaje su tara sukataresu nanfaakafara kallon kallo can wanidaga cikin Maxaje Tarannan yaceda Dakarun xumunci Barkanku daxuwa Dakarun xumunci masu burinSamama Duniya Sauki Jama,ar Sarki Kilad suna muku barka daxuwa kuma suna mubaya a gareku Sarauni Atine tace kusuwaye kuma ya,akai kusammu kuma menene yasakuke xaune awannan guri mai mutukar hadari ga rayuwan dan,adam Sai saurayin yace ni Sunana Yarima Sauwar bn Kilad domin amsa tambayoyinku muna bukatan kushigo cikin sansanimmu musami guri muxauna domin muna bukatan taimakomku saikawa yajuya yakama tafiya Dakarun Xumunci suka rufamarbaya Saida sukadauki tsawon Sa,aguda suna tafiya acikin wannan Sansani Sannan suka isa wata katuwar tanti wanda akai mata ado tamkar masarauta sannan gadaru masutarin yawa sunkewaye ko,ina sai muxurai sukeyi kaitsaye Yarima Sauwar yashiga Tantinnan Dakaru sukai gaisuwa da jinjina agareshi sannan yakunna kaicikin tantin Dakarun xumunci suka bishi koda suka shiga cikin tantin saidakarun xumunci sukasha mamaki ganin Ankawata cikin tantin dakayan kawa na Sarauta manyan kujeru na alfarma da kilasai ga bayi nakai komo sannan sai Yarima Sauwar yaxauna awata katuwar karaga sannan samari takwas suma suka xauna akujeru Takwas Sannan aka Umurci Dakarun Xumuncidasu xauna awasu kilasai goma Shadaya da,aka taxa dansu sannan aka Shimfide Boka Barnohuawani gado shima na masamma bayan angabato dakayan abinci da ababensha Sai Ba,yan anci ansha sai Gimbiya Ela taigyaran murya taceda Yarima Sauwar ahalin yanxu kai muke jira domin kabamu labarinku Yarima yace Labarine maicikeda tausayi gamida takaici dakuma rashin imani yarima Sauwar yace Da farkodai sunan Kasammu Laharim sannan kamar yadda na fada muku Sunan mahaifina KILAD yakasace Sarkine mai adalci atsakaninjama,arsa Sannan yanada Farin jiniagun talakawansa#BANGON DUNIYA PART {#40} Anjere Mamyan akwatuna guda Shida Domin xuba kuru,u inda aka wari uku na Masoyan Yarima Sauwar Uku kuma na Magoya bayan Gimbiya Nariyya Jama,a suka hau layi domin gudanad da wannan Xabe xuci yoyinsu nacikeda Rudani gamida tarin Fargaba axahiri sunason Suxabi Yarima Sauwar domin yagaji karagar Mahaifinsa domin Halinsu dayane amma suna Fargaban abinda xaibiyo baya domin suna tuna alkawuran axaba da Gimbiya Narriyya taimusu mutukar basu xabetaba tofa saisun gwammace Mutuwada Rayuwa akai tsurutsu Sai Waxiri Dandanu yahau dandamali yadagaMurya yace yaku Jama,a lallai Kutsaya Kuxabi Shugaba adali kada tsoroda Fargaba yasa kukashe kawunanku alhali kuna Raye Sannan yadaga hannunsa Sama yace nariko Farin Dutse kuma Yarima Sauwar shine xabina tabdijam aikamar dama jiransa jama,asuke sugaxabinsa take sukarika tulama Yarima Sauwar kuri,a inda akacika akwatunansa da Kuru,u sannan akarika xubawa akasa inda Akwatun Gimbiya Nariyya babu komai aituni Garin Balwan yabarkeda ihu mata suka sa guda Makada suka Saki Ganguna Mawaka sukama Rerama Yarima Sauwar Wakokin yabo awannan Rana akanada Yarima Sauwar Sarkin Kasar Balwana saida akai mako uku ana biki sannan kowa yakama gabansa inda Sarki Sauwar yarika gudanarda muliki tamkar na Mahaifinsa inda Jama,a dadama suke cewa yafima Mahaifinsa iya mulki al,amarin Gimbiya Nariyya kuwaba,amasan ina tashigaba tsawon Watanni Uku kwatsam rannan sai wata bakar Kwanama Narkekiya tabayyana atsakiyar kasuwa Girmanta yakai Rikakkensaniya tanadakari har guda goma Shabiyu nanfa tarika harbin Jama,a duk wanda Kunaman taharba take ilahirin jikinsa xaikoma Bakinkirin tamkar gauwayiyakama aman jini ahaka xaimutu alokaci Guda kunaman na harbin Mutane goma shabiyu kuma babuwanda xairayu kayya aituni Jama,a sukama gujeguje da ifeife inda wasu suka rikadanne wasu nanfa guri yadame wasu dakaru suka tunkari Kunamannan nanfa sufa jifantada Kibiyoyi da wukake da majajjawa amma saida kunaman tahallakasu bakidaya Koda labari ya isa Fada Sai Hankalin Sarki Sauwar yatashi dakansa yai damara sannan yadibi Gwaraxan jarumai kuma masujida KarfinDantse cikin Dimuwa suka isa Ga kunamannan nanfa afara kairuwa rana inda dakaru samada Dubu Hamsin suka tarumata amma Saida kunama takashe samada Maxaje dubu ashirin dakyar Suka hada karfidaKarfe sukaimata Rufdugu sannan sukasheta Kayya aisuna Kashe Wannan Kunama Sai akajiwani Sakaran Ihu take Jama,a sukamaida Kallonsu xuwa inda wannan ihun ke Futowa Dankari aisai Sukai toxalida Wata sabuwar annobahankulansu sukatashi tsoroyabaibaye xukatansu sukafara tunanin rugawa aguje bakomai yafurgita Sarki Sauwar da Jama,arsaba Face ganin Gimbiya Nariyya itada wasu Barka bakan Dakaru kimaninSu dari uku sannan kowannensu yana kan wannan katuwar kunama wanda Guda dayama tagallabi Jama,a nanfa Gimbiya Nariyya takwarara ihu sannan tabarkeda dadariya inda tarika cewa kai Karamin Sarki wanda baxai iyakare kansa daga abokan gababa lallai kasani dayanku baxaiTsiraba domin nayi rantsuwa sainakashe kowa awannan birni domin indau fansan wulakancin da kukaimin takwarara ihu tace dadakarunta taje Kufada cikin gari kukashe kowa kada kukyale koma Dakarun Kasar Balwan suka jadaga inda Sarki Sauwar yakwarara ihu yace yaku jama,ata lallai abisa,Umurnina matada maxa yaro dababba kada abar kowa bakidaya kufuta awannanbirni takofar Gabas domin baxamuiyadaukan lokaci maitsawo muna yaki da wannan annobaba xasui galaba akammu domin Shaidanune daga Duniyar Hatsabibai take jama,a sukai baya sukarika tarkata yaransu da tsofaffinsu suna ficewa abirnin inda Dakakkun jarumai yan amutu suka fuskanci Dakarun Gimbiya Nariya Sukarika dauki badadi tabbas Sai ankashe wasu domin wasu surayu domin Dayawa maxaje sunrasa rayuwansu inda akarke Jama,a suka fuce abirnin bakidaya sai yarage daka dakarun Kasar Sai Dakarun Gimbiya Nariya sunama maxaje kisan Gilla aikoda Sarki Sauwar yaga Jama,arsa sunficedaga birnin sai yaima Dakarunsa tsawa yace suma Sufice abirni take sukai baya shima yabi bayansu Ginbiya Nariyya takwarara ihu taceda Dakarunta kai tsinannu kada kubarsu sufuta inasun makara aisuna Futa sai Sarki SAUWAR yanuna kofar birnin da yatsansa yana karanto wasu sidirorin tsafi take kofar tashafe bubukofar Futa tarufeda Dakarun Nariyya, takwarara ihu tadubi duk wata hanyada tasani amma saitatarar Kofar atoshe take sannan katangar Kasar bakidaya takara tsawo fiyeda kima Gimbiya Nariyya tai umurnida arusa katangar amma abin yagagara nanfa tarika karanto tsatsuba da tsunvvurikai amma abin yagahareta adaidai nanne Sarki Sauwaryakalli Dakarun Xumunci yace tokunji bala,inda mukeciki Yar uwan mahaifina takoromu abirnimmu abincimmu dukiyarmu dabbobinmudakomai namu sunacikin birnimmu sannan abintashin hankalimma koda yaushe Sarauniya Nariyya da Dakarunta,xasu,iya Fasa katangar suriskemu wanda idan hakan tafarumukumaSai buxummu Sai SadaukiAmirul Jaishi yace Dukda yake cewa munahanyarmuce taxuwa samoma shugabammu Magani a Kayaba yaxama dole Gobe mutunkari GINBIYA NARIYYA domin mufatattaketa itada Dakarunta,Al,amarin Sukairuf,kuwa tunda sukatsiradagaharin xakunannan sai suka sami wata tushen bishiya suka xauna domin su huta kayyada sunsan masifan dake tushen bishiyannan todabasu xaunaba domin xamansu kedawuya saisukaga ganyayyakin wannan itaciyar Sunakama xubowa kasa suna taruwa aguri gudu suna wani jujjuyawa Sukai yawa Ganyayyaki sukai dam akwalla ihu Sai Yabayyana, karr uba tsananin tsoroda furgita SAIDA KAIRUF,KILXAM YARIMA LAMIR,DA XAMIR SUKAMIKE ATARE SUKWARARA IHU TABB NAFCE NANUFI RUNFAR SHAYIII kuhuta abokai An dauko wannan littafi daga shafin https://taskarnovels.com.ng ku ziyarci shafin na https://taskarnovels.com.ng domin samun kayatattun littatafan hausa kama daga kan na yake yake dana soyayya Marubuci ko marubuciya zasu iya turo mana da littatafansu mu dora masu a shafinmu kyauta don masoyansu su rika Downloading a online, Sannan marubuta zasu iya turo mana da tarihin rahuwarsu da tarihin rubutunsu, dama sharhin littatafansu don masoyansu su gani kuma su karu da hakan Domin turo mana da littafi ko tarihin rayuwar marubuci ko marubuciya sai ayi mana magana ta whatssap da wannan nambar +2348140419490 A lura dakyau - kyauta muke saka littafi a shafinmu bama amsan ko sisin marubuci, duk wanda ya amshi kudinku da sunanmu babu ruwanmu, Alura dakyau - manazarta bama tura littafi ta private ku dena binmu private kuna neman mu tura maku littafi, duk mai bukatar littafi yaje website namu Alura da kyau - Littatfanmu suna fitowa cikin manhajoji uku ne PDF,TXT da DOC amman munfi amfani da PDF da TXT masu amfani da wayar android ko tablet ko computer zai fi kyau ku riga dauko PDF da DOC Masu amfani da kananan wayoyi java ko mara java TXT zakuna zaba don shine daidai wayarku This hausa novel was uploaded and downloaded from https://taskarnovels.com.ng You can download more hausa novels there Also you can send us your novel to upload it in our website for your fans to download it online It is free we do not charge for uploading novel Also if you are an Author be it online or Non online you can send us your biography including your book summary,commentary and others via this number +2348140419490 its free we do not charge for our services Note that - we do not charge for our services we uploaded novels and posted biography free, any person that collect your money in our name is your fault do not blame us Note that - pls readers stop calling us and be asking us to send you a novels we are not sending novels through whatssap or private our novels is public at any day, any time you can visits our site and download it Note that - our ebooks came as PDF,TXT or DOC format but the popular format are PDF or TXT, those with android or tablet or pc we suggest you to download PDF or DOC those with java phone or non-java phone we recommend you to download TXT This Novel is downloaded from https://taskarnovels.com.ng to download more hausa novels visits our site at www.taskarnovels.com.ng For feedback and support Facebook : https://facebook.com/taskarnovels Twitter : https://twitter.com/taskarnovels Telegram : https://t.me/taskarnovels

Chapter 6 of 6