Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
5 / 6
ba domin wani mutum ne ya kawo su gabana ya fadi nan nai ta addu a cikin zuciyata wani katon mutum shirgege yazo inda muke ya ce zan shiga dakinnan daya bayan daya ku dinga shigowa yana shiga aka dinga shigar da mu ashirin ne ni ce ta karshe ina shiga sai naga dukanninsu an musu aski nima zura kaina akayi cikin inji sai ma fafur inji yaki tashi sai dai wata kara ya dinga yi ka ka ka ka mutumin ya fusata ganin ina bata masa lokaci sai ya dinga dukana amma a banza mikewa yai ya fita bai jima ba ya shigo shi da wata mata suka nuna ni suna magana da turanci ni dai ban san abin da suke cewa ba na dai ga taja hannuna matanan ina jin ihunsu wasu na addua ni kuma zama nai nayi ta kuka ina zaune tace in yanka mata albasa ita kuma tana yankan alayahu sai kunama ta harbe ta tai ihu da sauri na kulle mata kafar da dankwalina sannan na kashe kunamar.mahida ta dinga dariya tace mom ci gaba muji ko sun yanka ki nace bbu yanka fa bada sun yankata ma ganta wai ba zaku yiwa mutane shiru ba munyi shiru mom ci gaba mahida don Allah kiyi shiru ki barta zata laftu inta ji saukar socket.BANA KAUNAR KA!!! 35 -------------------------------------------- mahida ta mike ni na gaji da jin wannan labarin ya amin yace don Allah zauna mahida mu gama ji ma na muji karshen toni yaya haushin jauro nake ji nai dariya nace ai kuwa babankine tunda mijin babarkine Allah ya sauwake talakan sai,ya faruq ya harzuka tuni muka yi shiru mom taci gaba. koda na kulle mata na kuma kashe kunamar na shafa mata ruwan sai taji dadi har tace in kwantar da hankalina zata kubutar dani nace na gode,amma don Allah ta bari a yankani domin in na fita ban san inda zani ba,ta girgiza kai tace ba zan bari ba yanzu shekarunki nawa? nace sha uku domin shadaya akai min aure gashi ina da shekara biyu ta sani a hanya har titi sai sai sam bana cikin hayyacina,saboda haka wata mota na zuwa tai gaba dani daga nan ban san me ya faru ba illa na farka na ganni a wani kayataccen guri ina bisa gado me dan karan laushi,sanyin AC da kamshin wani irin turare....wata farar mace sanye da farar kaya ta shigo tace min sannu,nace yauwa ta min aune aune sannan tace me yake damunki yanzu na nuna cikina tace wannan sai a hankali saboda barin da ki kayi cikin jikinki ya zube,ku tashi kuyi sallaha ina yaso sai in karasa muku,wayar mahida tai kara ta dauka haba kinga na kalle ta haka aka iya soyayya Allah ya shirya ku,ku ko gajiya bakwa yi,to ina ruwanki ni bana son shiga sharu ba shanu la!! ya amin ka ji tace min shanuwa ko,yi hakuri ke mahida kar ki kara ce mata shanuwa,don Allah ya faruq kaji nace mata shanuwa? ke ni kar ki dame ni ku kenan fada kamar kaji. ina kwance jikin mom suka soma shigowa mom taci gaba,matar na tambaya don Allah a ina nake tace min a kano tace wanda ya kawo ki anjima zai zo nace to.da yamma ina zaune yayi sallama saurayine kyakkyawa in kunga al'amin kun ganshi hannunsa ya zuba cikin aljihu yana kallona na sunkuyar da kai tare da gaishe shi ya amsa yana me tambayata jiki nace da sauki,yace baki sani ba ko na daga kai ya ce nine wanda na bige ki a kaduna sai dai ina sauri ban tsaya a asibitin can ba,na kawo ki nan ni sunana sulainman muhd radda,mahida tace iye iye abban mu ne fa ya faruq ne ya doketa.koda ya bukaci jin labarina ba abin dana boye masa ya tausaya min haka ya dinga ziyarata wataran yakanzo shi da kanwarsa khadija wataran kuma shi da babarsu koda aka sallame ni ma gidansu na koma kanwarsa khadija na soma sani kuma tana hidima dani haka mahaifiyarsu sam bata nuna min kyama na basu labarina ta tausaya min sannan tai min alkawarin rike ni fisabillilahi sai dai me koda yayansa ya dawo ya samu labarina akai masa bayani ai sai ya dinga bala'i muddin yana numfashi sai na bar gidan hakan kuwa akayi sai da yaya yasan yadda yayi ya fitar dani,na rasa inda zani gani dai naje titi amma sam na kasa tsallakawa,sai kalle_kalle kawai nake,oh ni Allah kai min magana wata mota ce irin ta sulainman tai fakin kusa dani mai motar ne ya fito ya jima yana kallona da alama yana mamaki ganin ya juyar da kaina bani da niyyar yi masa magana sai ya karasoBANA KAUNARKA!!! 36 mahida ta mike ni na gaji da jin wannan labarin ya amin yace don Allah zauna mahida mu gama ji ma na muji karshen toni yaya haushin jauro nake ji nai dariya nace ai kuwa babankine tunda mijin babarkine Allah ya sauwake talakan sai,ya faruq ya harzuka tuni muka yi shiru mom taci gaba. koda na kulle mata na kuma kashe kunamar na shafa mata ruwan sai taji dadi har tace in kwantar da hankalina zata kubutar dani nace na gode,amma don Allah ta bari a yankani domin in na fita ban san inda zani ba,ta girgiza kai tace ba zan bari ba yanzu shekarunki nawa? nace sha uku domin shadaya akai min aure gashi ina da shekara biyu ta sani a hanya har titi sai sai sam bana cikin hayyacina,saboda haka wata mota na zuwa tai gaba dani daga nan ban san me ya faru ba illa na farka na ganni a wani kayataccen guri ina bisa gado me dan karan laushi,sanyin AC da kamshin wani irin turare....wata farar mace sanye da farar kaya ta shigo tace min sannu,nace yauwa ta min aune aune sannan tace me yake damunki yanzu na nuna cikina tace wannan sai a hankali saboda barin da ki kayi cikin jikinki ya zube,ku tashi kuyi sallaha ina yaso sai in karasa muku,wayar mahida tai kara ta dauka haba kinga na kalle ta haka aka iya soyayya Allah ya shirya ku,ku ko gajiya bakwa yi,to ina ruwanki ni bana son shiga sharu ba shanu la!! ya amin ka ji tace min shanuwa ko,yi hakuri ke mahida kar ki kara ce mata shanuwa,don Allah ya faruq kaji nace mata shanuwa? ke ni kar ki dame ni ku kenan fada kamar kaji. ina kwance jikin mom suka soma shigowa mom taci gaba,matar na tambaya don Allah a ina nake tace min a kano tace wanda ya kawo ki anjima zai zo nace to.da yamma ina zaune yayi sallama saurayine kyakkyawa in kunga al'amin kun ganshi hannunsa ya zuba cikin aljihu yana kallona na sunkuyar da kai tare da gaishe shi ya amsa yana me tambayata jiki nace da sauki,yace baki sani ba ko na daga kai ya ce nine wanda na bige ki a kaduna sai dai ina sauri ban tsaya a asibitin can ba,na kawo ki nan ni sunana sulainman muhd radda,mahida tace iye iye abban mu ne fa ya faruq ne ya doketa.koda ya bukaci jin labarina ba abin dana boye masa ya tausaya min haka ya dinga ziyarata wataran yakanzo shi da kanwarsa khadija wataran kuma shi da babarsu koda aka sallame ni ma gidansu na koma kanwarsa khadija na soma sani kuma tana hidima dani haka mahaifiyarsu sam bata nuna min kyama na basu labarina ta tausaya min sannan tai min alkawarin rike ni fisabillilahi sai dai me koda yayansa ya dawo ya samu labarina akai masa bayani ai sai ya dinga bala'i muddin yana numfashi sai na bar gidan hakan kuwa akayi sai da yaya yasan yadda yayi ya fitar dani,na rasa inda zani gani dai naje titi amma sam na kasa tsallakawa,sai kalle_kalle kawai nake,oh ni Allah kai min magana wata mota ce irin ta sulainman tai fakin kusa dani mai motar ne ya fito ya jima yana kallona da alama yana mamaki ganin ya juyar da kaina bani da niyyar yi masa magana sai ya karasoBANA KAUNAR KA!!! 37 -------------------------------------------- kamar yadda nake yi a makaranta sam bana kula samari kai hadda dattawan na kance ammin mji,amma an kusa bikina in naga zaka takura min in ma fata-fata.salamu alaikum,sai dana dan firgita domin ban san zuwan sa ba amin wa'alaikas salam,ya tsungunno sannu bebi ni sunana umran s sulainman tunda kuka shigo gurinnnan na kasa samun sukuni ina son inyi miki wata magana sai dai ki min kwarjini maganar gaskiya naji na kamu da sonki nai murmushi nace ah maganar gaskiya sai dai kayi hakuri domin tuntuni am mana miji ya wani zabura kin san koni waye? nai masa kallon sama da kasa ba shi da wani kyau na tabe baki yace waye shi wanda aka zaba mikin kin san Allah zan iya gogawa dashi nai murmushi na rasa wa zan ce masa sai dabara ta fado min nace ka san shahid yaro dan kwalisa,wai bomboy kike nufi nace ashe ma kasan shi gani nai ya sara min yace na barki lafiya nai murmushi,ina nan zaune sai ga wani guy yace sannu hajiya nace yauwa alhaji to ni sai sunana small ismail na jima ina ganinki sannan na dade ina fama da sonki domin na fuskanci ke yarinya ce nitsattsiya nayi bincike akan gidanku mahaifinku mutumin kirkine,da fatan zaki amsa tayina to mallam small na gode ainun batun so kuwa nima ina sonka da wannan damar kuma nake baka hakuri domin maganar gaskiya am min miji na gode da kika fada min gaskiya don Allah ya sunanki "wahida sulainman muhd,to wahida na gode. wani guy yazo yana zuwa bbu wata sallama ya tsunguna gabana sannu bebi ban kalle shi ba nace bomboy ya kamata mu tafi gida what me kika ce? nace sorry na dauka shahid ne what ina kika san bomboy? nace ban gane ba ai yau saura wata biyu bikinmu kina nufin ke bomboy zai aura,ko ba mu dace da juna bane? no ba haka bane ina mamaki to ko za kai takara dashi ne? no ni da bomboy bama haka na hakura.wani guy ne ya nufo ni hadda masu take masa baya tun kan ya karaso kamshin turaransa ya cika gurin yana zuwa ya tsunguna ya kamo hannuna wata wawuyar sumba ya kai min na kuwa tofa masa yawu tare da fizge hannuna a fusace,nace kai wanne irin dabba ne a fusace shima ya mike yana shirin sharara min mari aka rike shi ta baya,yana kar ka taba musu bebi ka barni in duke ta in yaso inga uban da ya tsaya mata,ita kuwa take da mai tsaya mata kasan ko waccece kar ka yadda ka tafka abin kunya,domin wannan yarinyar kanwa ce ga abokinku bomboy,sannan ta wani bangaran mata domin an kusa bikinsu.....ido ya zuba min da alamu kunya ce ta kama shi na mike da sauri na bar gun,gun motar mu na koma abin haushi har gun motar aka dinga bina raina ya baci na kudirce a zuciyata ni da zuwa fati sai de a aljanna.yaya ni dai gaskiya zan tafi amir yace haba anti wahida ko dan kinga bomboy baya gurin nai murmushi nace ai yanzu muka gama magana ta waya da shi sai sa ma ban damu baBANA KAUNAR KA!!! 38 -------------------------------------------- na fadi haka ne don in tura masa haushin ni dai yaya ka bani key din motar in tafi kwa taho,anty mahida zo mu tafi,no ni sai ya amin zai tafi shikenan ni ku bani in tafi in yaso ku direba yazo ya dauke ku ya amin ya mike mukai sallama musu sallama har kuzo kuga zugar yan rakiya sai kace shugaban kasa zasu raka an raka mu bakin mota amir yai saurin bude min mota na shiga to anti mahida sai naxo mahida ta kalle su da fatan zaku zo bikinmu? ina gayyatar kowa da kowa insha Allahu zamu zo goode bye,suna daga mana hannu ya amin yaja mota.tun kan yayi fakin na hango abba zaune yana kallonmu toh abba ya dawo muka fito gunsa muka nufa abba sannu da zuwa kuya kamata inyi wa sannu ku da kuka iso yanzu daga ina kuke mahida tace abba daga gidan baba rabi'u muke na ce la! wallahi abba karya take abokin yaya muka je muka taya murnar bikinsu kaga abba inba ma zuwa muma bbu me zuwa namu yauwa wahida gwanda da kika fada min gaskiya,ya amin yace abba kayi hakuri abba murmushi yayi yace kunci arzikin auta amma da duk sai na muku bulala, mahida tace abba tsaya kaji.....ni ba ruwana dame karya wai tace tawa mahida tace ni kuma ta mom da ya faruq yace ai shikenan ku wuce muka shige mahida tace me yasa kika fadawa abba gaskiya? ya amin yace gwanda data fadi gaskiya ai gaskiya dokin karfe ce in kin kula sam wahida bata iya karya ba. abba zaune yace abinda yasa na tara ku shine ina son hada aure tsakanin wahidda da shahid amma ba tare da sanin wahida ba har sai ranar da shahid din ya dawo dakin yayi tsit ba wanda yace kala abba yace alamin kayi shiru gaskiya abba ina gudun rikincin wahida shi yasa nake so a fara sanar in ta amince shi kenan ya faruq yace haba alamin wai me yasa kake nuna kana tsoron wahida ne mune sama da ita ko itace sama da mu? ni shawarata anan itace in an tashi bikinsu mahida kawai a hada a daura musu aure in yaso a bar wahida a gida har sai bom boy ya dawo yanxu a sanar da smallboy shi zai yi komai,mahida tace haka shine daidai sannan ko bayan daurin auran abba kar ka hanata zuwa makaranta mun riga mun san halin wahida zata kare mutuncinta sauran dabara kuma ta mom ce sai a san yadda akai mata wayo aka boye mata. al'amin ya kastse ta wai me ku ka dauki wahidar? kuna nufin bata da hankali ko karamar yarinya ce? ni dai wallahi bbu ruwana, abba shawara ka samu wahida ka sanar nata inta amince na amince, in kuma bata amince ba ina bayan yar uwata yana kai aya ya bar dakin.zaune nake ina kallo ko da filim din ya kare sai na kashe na nufi dakin ya amin domin in samu wani kaset din nai sallama yana zaune ya hada kai da gwiwa ya dago nace ya amin lafiya yace lafiya amma ba lau ba na zauna kusa dashi meke damunka big brother yai murmushi yace ba komai bane illa ina tunanin big brother wafa bomboy tuni na tuna irin cin fuskar da bomboy yai min bbu wani namiji daya taba yi min makamancinyarta ban san sanda naja tsaki ba.BANA KAUNAR KA!!! 39 -------------------------------------------- nace bomboy n tsane shi na tsani halayansa ya amin ya kamo hannuna ya zaunar dani yace please my sister bani labari saboda Allah me ya hada ku ban fiya boyewa ya al'amin sirrina ba domin mun fi shakuwa fiye da kowa a gidan,don hakan bbu abin dana boye masa sai dai na lura na batawa yayan nawa rai mikewa yayi yana safa da marwa inalillahi wainna ilaihi rajiun kawai yake maimaitawa ya kalle ni ransa a bace,wahida kowanne hali shahid ya shiga kece sila,domin wallahi tallahi ni shaida ne shahid bai taba shan wani kayan maye ba,shahid ba dan iska bane,shahid ba manemin mata bane,shahid mutum ne shahid mutumin kirki ne wanda samun irinsa sai antona kin ban kunya wahida,a da ina ganin kin fi mahida hankali amma wallahi mahida ta fiki sanin ya kamata ta fiki iya magana,ya faruq ya shigo shi da mahida saukar mari naji ya cire belt dinsa ya shiga dukana da kyar ya amin ya kwace ni ya faruq yace naji komai kuma kamar a kunennen abba ya amin ya dafa shi yace bai dace ba wannan sirri ne tsakin shahid da wahida,nima donna matsanta mata ne naji na mike nace wato shi shahid bakuga laifinsa ba baku yi kishin yar uwaarku ba sai shi ba kuji zafin abin da yayimin ba sai ni kuka ji zafin maganganun dana fada masa cool down na gode wa Allah daya tserar dani,ya kuma tsallakar dani daga mummunar manufar shahid ta son rabani da mutuncina ya goga min bakin fantin da har abada bbu mai iya goge min shi sanin kanku ns tun farko ban munafurci shahid ba na fito face to face na fada ba gaskiya bani da lokacin soyayya amma kun kafe kun goyi bayansa kuna shirin yi min auran dole toku tsaya kuji tunda nace bana sonsa bana sonsa soyayyar ba nayi toko zaku haka rami ku binne ni ba zan amince da shahid ba,domin ba sona yake ba sha'awata yake in kun kuskura kun bada goyon baya amin auran dole wallahi baku ba har wadda suka hada auran zan baku mamaki tai ficewarta .ina shiga dakinmu na hada kayana ina kuka ina fitowa na gansu a falo ina cikin jan akwatina ya amin ya fito lafiya ina kuma zaki? bar muku gidan zanyi tunda bakwa sona, din Allah madadin ku dawo da shahid tunda shi kuke so shi kun fi son farin cikinsa gwanda in bar gidan tun kan ku kashe ni,na shiga jan akwatina mom ta fito tace me ya hada ku? mom sun gaji dani ne basa sona farin cikina,burinsu su muzguna min,burinsu su bakantamin gwanda in bar musu gidan .mahida ta rike akwatin ina ja tana ja koda naga sun dauki abin wasa sai na sakar mata akwatin basu ankara ba sai tashin mota suka ji da gudu suka fito suma suka shiga motarsu suka bita da gudu mahida kuka ta kama. matsala gosilo shi ya taka mata birki duk da kutsa motar take yi amma ina hanyar ta tushe kasancewar motar su al'amin tana bayan to wahida,al'amin ne yai hanzarinn fitowa ya sh iga motar wahida ta mudubi ta hango shi tace cikin fushi,BANA KAUNAR KA!!! 40 -------------------------------------------- tsiwa da masifa ni ka fita min daga mota ko yanzunnan in kurma maka ihu,ya kalld ni cikin kwantar da murya yanzu wahida niki kewa wannan tsawar kar fa k manta nine al'amin naki yi hakuri kinji wahida yanzzu ina za ki nace ni katsina zani shi kenan bari in raka ki kinga sai in taho da motar inna kai ki kona ce eh to dawo nan in yaso sai ka tuka mu ji mu kayi ana mana hon ashe tuni wannan cunkoson ya baje a guje ya amin yaja motar na dinga ihu kamar wanda ya sato ni muma zuwa ya tisani gaba har cikin gida,ai kuwa a falo na dinga birgima ina kuka bbu wanda ya kula ni har nai mai tsata na bar gun ina daki a kwance ina jin san da abba ya dawo yace ina nake? aka ce masa nayi bacci yace wanne irin bacci da magariba maza ataso ni inyi alwala inyi sallah. wahegari gaba daya gidan bbu wanda na gaida asali ma ko fita ban yiba ina zaune mahida ta shigo wahida good morning nai mata banza ta kare surutunta ta fita tana fita ya al'amin ya shigo wahida ya karaso tare da dafa kafadata,wahida ina kwana nayi shiru oh wahida fushi kike dani im sorry my sister please na mike na bar masa falon haka ya faruq ya shigo yau sister tamu lafiya muka ji gidan shiru kai har mom hatta yan aikinmu sun rude autar mom ta zama kurma haduwa sukai suka dinga bani hakuri har na sauko na dawo normall. mamy muga littafinnan ta miko min "INSIYA" na kalle ta yana da dadi? gaskiya yayi min sai dai gaskiya tana shan wahala na tausaya wa yarinyar na daya dana biyu ne ko har na uku? na daya na siyo amma ina tunanin har na biyu zaiyi sai dai na dau alwashin duk matar data karkace ta shirya karya ya wuce 1-2 na daya dana biyu in tayi na uku ba zan ko kalli litrafin ba, me yasa kikace karya ne? kina nufin duk littafin da ake rubutawa karya ne? tabbas shida tatsuniya duk kusan daya na dauke su to me yasa kike bata lokacinki kina karantawa? ai a iya sanina tatsuniya bata da wani amfani ai kawai tunda kina ganin karya banza ce to kawai ki bar katantawa tunda bbu wani abu dayake amfana miki.BANA KAUNAR KA!!! 41-42 -------------------------------------------- baba rabi'u shi ya biyu musu sadaki kowannan su dubu hamsin hamsin (50,000) haidae kuma small boy shi ya hada musu lefe akwati shida shida manya masu tsanin kyau sai sabuwar mota kasaitacciya kirar zamani kai gaskiya koni na yaba haidar domin yayi bajinta sannan na jinjinawa ya al'amin domin shi ya zubawa kannansa kayatattun kayan kicin na azo a gani,ya faruq kuma yayo musu kayan daki ita kuma mai taji da gyaran jiki yaranta takanas ta tura sokoto aka samo me gyaran jiki sannan akwai wata makociyansu yar maiduguri ita tayi rawar gani wajen fito da yaran mom din ina zaune mom ta shigo na kalle ta fuskanta dauke da damuwa,nace nifa mom ban gane ba ni ba amarya ba amma komai sai a dinga yii min irin na amare,anya mom ba wani abu kuka boye min ba? mom ta gyara zamanta tace auta kenan,ai abin da yasa kika ga ana muku haka don anga ku yan biyu ne ya zama dole kome akai miki ayiwa yar uwarki domin tare aka haife ku na kalle ta au shi yasa naga komai ana mana iri daya nifa abin ya daure min kai shi yasa lokacin da yan katsina suka zo naji sunce min amarya,amaryar shahid ni fa ina jin haushin in aka hada ni da shahid to ai ko shima haka abokan wasanku zasu ce masa domin sunga ku yan biyu ne ni dai gwanda a hada ni da wani sam bana so ana hada ni da shahid.......na fafa miki abokan wasa sai hakuri in fa kika nuna musu ba kya so sun dinga ce miki kenan gwanda ma ki saki ranki ki dauki komai ba komaiba nai murmishi farin ciki nace ni kuwa har gabana ya soma faduwa,amma yanzu naji dadi sosai domin na fiso ku barni inyi karatuna mom ta rungume ni tace zakiyi alfahari damu auta.yau saura kwana biyu daurin aure yaune kuma muka shirya zuwa gambu gurin su mom kasancewae mu rubuta komai mun amfani da direban gidanmu domin shima dan gyanmbun ne sai dai wani abu da baku sani ba,ko da wasa bamu sanar dasu mom ba bbu wanda ya san da tafiyar sai nida mahida,ya amin ya faruq sam bamu sha wahala ba wajen gani gidan kasancewar mahaifin mom fitace ne sannan gidansu bac wani boyayyan gida bane in kace gidan tsamiya koda titi ne to za akai ka gidan,munyi sallama dan ma dai dakin gidan mai yar katanga wadda duk rabin gidan ya rushe sai dai an gyara shi ta hanyar jera wasu karare,kallo daya zakai wa gidan kasan mutanen gidan suna cikin kunci talauci munyi sallama turus mukai fakin a zaure domin wata tsohuwa muka gani tanawa wani tsoho fifita zaune suke a soron suna shan iska sai dai da alama wannan tsoho bashi da lafiya domin gaba daya ya koma kalar tausayi,tsohuwa tace sannunku da zuwa yan samari ciki ta koma ta dauko mana taburmar kaba ta shimfida mana muka zauna ta kawo mana ruwa mai sanyi muka sha sannan muka gaishe ta muka gaida wannan tsohon ya amsa da kyar da alamu yana jin jiki mu kai masa sannu matar ta zuba min ido kafin daga bisani tace yan mata yan samari daga ina kuke don Allah ina kuke?BANA KAUNAR KA!!! 43&44 -------------------------------------------- wallahi ina muku kallon sani sannan ina ji a jikina duk daga inda kuke ku jininmune amma meke tafe daku ya roki ya amin yace nanne gidan malam abdulkadir? tsohuwa tace nanne nanne gidan tsamiya? nanne ke kuma sunanki inna furera? ta amsa ya ce yayanku nawa ko baku taba haihuwa bane? tsohuwa tace a to mun taba haihuwa shekara talatin da biyar kenan tai shiru tana matsar hawaye,ya amin ya ce ina dan da kuka haifa koya mutu? ai ba namiji bane mace ce sunanta maryam amma kasancewar yar farice muna kiranta inna wuro,gaba dayanmu muka lalli juna tsohuwa ta bamu labari kamar yadda yadda mon ta shaida mana na sanadiyar barin gidan mahida tace inna ki bar kuka domin maryam tana nan da ranta tsohuwa ta rike kai da gaske kin san maryam kin san inna wuro? nan ya amin ya bata labarin ita da dan tsoho kuka suka dinga yi gaskiya mun ga gata gun wadannan bayin Allah washe garri tun safe muka tarkato tsofaffinnan zuwa kano ta dabo. a gida kuwa hankalinsu abba in yai dubu ya tashi har katsina anje bama nan wannan ya kara daga hankalin iyayenmu har gidan rediyo talabijin kafafan yada labarai ansa cigiyarmu misalin karfe biyar muka iso tun kan muyi fakin aka baibaye mu kowa ka gani fuskarsa akwai alamar tambaya,kai tsaye dakin mom muka nufa Allah sarki mominmu hankalinta a tashe ta mike ta nufo mu Allah mom har ta rame daga ina kuke na nuna mata tsohuwa mom ta zubawa matar ido sai kuma ta fada jikinta kukan farin ciki suka dinga yi ni kuma dakin abba na shiga duk da ya samu labarin dawowarmu nan na shaida masa gaskiya su abba sun taya mom farin ciki ganin iyayenta,mom farin ciki kamar ta goya mu tayi ta sa mana albarka.zaune nake anmin kunshi su ya amin anci uwar kwalliya shida abokansu sai faman shige da fice suke yi kasancewar yau ne daurin aure,ya shiga ya tsugunnna gabana yana kallona nai dariya yaya kamar kaine angon? yace wahida kamar kece amaryar na taba baki kawai na yi shiru yace wai me dame dame kuka shirya nace ai komai ma yaya mun shirya,yanzu so nake a gama samin rani inje in anso mana dinkinmu,munyi da telan zai aiko min amma shiru yace ki bari zan anso miki amma kiyi zamanki.dan kar wahida ta san me ake ciki yasa aka daura auran a babban masallacin juma'a sai dai ita ko a jikinta,fati sun sha shi kalala sun rakashe sun case duk inda zaka ga mahida tana manne da mijinta yayinda wahida ta manne wa yayanta gwauro al'amin mamy ma tana jikin angonta faruq a ranar aka kai amare wahida sunyi kukan rabuwa ita da mahida an kai amare dakunansu sai dai ban da wahida domin baba rabiu yace a barta sai bomboy ya dawo.yau watan mahida uku a gidan miji yaune kuma na kai mata ziyara muka rungume juna hadda kukan farin ciki tare muka shiga kicin muka shirya komai bayan mun gama cin abinci muna zaune muna hira muka ji takun takalmi kwas kwas alamar za,a shigo aka turo kofar wata budurwace tai sallama ta shigo muka amsa ya shigo daga yanayin shigarsa dressing dinsa ko ba a fada ba kasan ko waye sanye yake da kayan sojoji ya turo kofar muka zubawa juna ido wani annuri ke fita a fuskarsa yayi kyau ainun,inalillahi ji nai sam bazan iya daina kallon kyakkyawar fuskar ba.BANA KAUNAR KA!!! 45 -------------------------------------------- wani irin azababban son sa naji ya mamaye duk ilahirin jikina rankwafowa yai ya hura min iska na lumshe ido ina budewa naga yasha mur wamman matar ko ince wannan yarinyar ta riko hannunsa tace my king wacece wannan? yace wannan itace kanwata wahida,wahida ga antinki matar yayanki sunanta zee baby,na kalleta wani irin azababban kishinta ya taso min na maida kallona ga mahida ita kuma ni take kallo na mike ina shirin barin falon ,haidar ya fito wani tsalle ya daka ya rungumi shahid bom boy wannan wacece? inji small boy matatace sunanta zainab yanzu da gaske bom boy kayi aure? wallahi nayi aure na kuma aure ta a legas. ya jawo ta jikinsa beby zo muje muyi wanka wahida kawo mana abinci na dauki makullin motata na ce me zai hana ku ku dauka ko kuma ku tsaya kuci na fice wata a mota na kifa kaina innalillahi wa inna ilaihi rajiun me yasa na cuci kaina na zalinci kaina na munafurci kaina me yasa haka ta faru shahid me yasa kai min haka tabbas zuciyata na kaunarka halin kane bana so me yasa kayi aure alhalin kasan muna son juna wayyo ni wahida ya zanyi in nunawa bom boy ina sonsa da wanne baki zan

Chapter 5 of 6