Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

babu mai tunawa ma da shi. Ba suba ko Jay da baisan yawan surutu yau sai yaji hakan bai gunduresa ba, wani wajen ayi kuka wani wajen ayi dariya, wani wajen ayi tausayi da al'ajabi. Haka kawai bilkisu ta tsinci kanta da yin matsanancin kuka akan labarin Aunty Mah-mah (Rahmah), haka kawai taji tana ƙwaɗayin ganinta koda kuwa a hotone. Hakama Umm-Anum ta shiga matsanancin mamaki da jin wai Bilkisu ba ɗiyar Rahmah bace ba. Yayinda shi kuma Jawaad al'amarin yay masa tsaye cak a zuciya baisan dalili ba, kawai yanaji a ransa kamar akwai wani abu dake a binne game da rayuwar bilkisun, musamman idan ya tuna da maganar baba ƙaura akan duhun dake biye da Bilkisun, da kuma furucin baba ƙauran a jiya da yaje wajensa saboda kiran da yay masa. ‘Kai anya kuwa babu wani abu........?’ ya faɗa a cikin ransa yana kafe Bilkisu da idanu harta tsargu ta ɗan ɗago suka haɗa ido.
            Barci ma da kansa yasan inda yake zuwa yay sata, dan kuwa idanun waɗanan bayin ALLAH ko gyangyaɗi basaji balle ai maganar barci, suna zaune dingangan har agogo ya nuna ƙarfe uku saura na dare. Jay ne ya katse firar tasu da roƙonsu akan suje su kwanta haka da safe idan ALLAH ya kaimu saisu ɗora. Badan sunso hakan ba suka miƙe dan suma susan Umm-Anum na buƙatar ace ta huta kodan doguwar tafiyar da tayo wadda bata saba ba. Su mamaki ma abin ya basu dan basusan lokaci yaja haka ba, jima suke tamkar daren bai wuce ƙarfe goma ba. Dole dai yau su kwana gidan ɗansu.
       Ummah babba Umm-Anum da Ummah ƙarama ɗakin bily aka kaisu su kwanta tare da ƴar uwarsu, duk da dai ba kwanciyar sukaiba wani babin sabuwar hirar suka sake buɗewa ma su. Batool da Anum da Nabeelah kuma ɗaki

n dake kusa dana Bilkisu, Anuwar yana a ɗakin baƙi. Jay ya nufi nasa ɗakin, Bilkisu na shirin shigewa wajensu Nabeelah Ummah ƙarama ta korata ɗakin Jawaad.

        Sosai kunya ta lulluɓeni har inaji kamar ƙasa ta tsage na shige, to amma yaya na iya suɗin ba abin wasana bane balle nai tunanin musu gardama ma, haka na nufi sashen nasa kamar na nutse dan kunya. Ina jiyo su Nabeelah namin dariya harda Yah Anuwar. Sam banso hakanba, dan naso ace mun samu nisa da juna ni da shi koda na kwanaki biyu ne dan ya fahimci inajin zafin abinda ke faruwa tsakaninsa da ƴan uwana, ƙila ta hakan zan samu ya faɗamin abinda ke faruwar. Badan a ciwon kan da nake ji ba da falo zanyi zamana na ƙarasa daren, haka dai na daure fuska a ciskule na nufi bedroom ɗinsa, ciki ciki nai sallama na shiga, yana kwance a saman gado da ga shi sai noxer kawai, idanunsa a rufe suke amma na tabbata ba barci yake ba, na ɗauke kaina daga garesa na nufi bayi. Ban wani jimaba na fito dan fitsari kawai nayi da abinda baza'a rasaba. Yanda na barsa haka na fito na samesa, bani da kaya a ɗakin, sai naita tunanin mizan saka na kwanta dan bazan iya barci da kayan jikina ba. Ganin lokaci na sake ja ga zazzaɓi nama neman saukarmin yasa na nufi Wadrobe ɗinsa, cikin sa'a kuwa idanuna saka sauka akan t-shirt ɗinsa mara nauyi ruwan toka, nasan indai na saka zata sakkomin dan babbace kuma girman ba ɗaya ba.
        Zagayawa nai ta ɗayan gefen na kwanta can ƙarshen gado na juya masa baya.....
       “K har kin isa mu kwanta a gado ɗaya ki juyamin baya!”. Na tsinkayi saukar muryarsa da furucinsa a fusace cikin kunnuwana. Ɗan rintse idanu nayi ina haɗiyar yawu da ƙyar, zuciyata sai harbawa take da sauri-sauri na tsoro. A hankali na juyo ina tura baki da sake ɓata fuska sosai, abin mamaki har yanzu yana a yanda yake. A ƙasan ido naɗan hararesa naja bargo na rufe har fuskata ma.
         Wani haushi ya sake kume zuciyar Jay, jiyake kamar yay mata filla-filla ɗin da saita ƙarasa daren da kuka, sai dai yanata ƙoƙarin danne fushinsa kawai.
        Ba ƙaramar razana naiba jin an fincike bargon, na waro idanuna dake cika da ƙwalla a kansa, fisgoni yay na faɗa jikinsa ya matseni tsam-tsam, wani marayan kuka na buɗe baki zan sakar masa sai dai kuma ya hana hakan ta hanyar baƙar muguntarsa da ya ƙware a iyawa, nasan bani da wani ƙarfin ƙwatar kaina daga garesa musamman ma a irin wannan lokacin da sam banajina ma garas. Ɓacin ransa baisa shi kasa bidani cikin salon natsuwa da salo mai tsayawa a zuciya ba.............

....
..........✍

ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏻
[2/12, 7:51 PM] Wasila: Bilyn Abdull 📚:
Page 57
          
_______________________________
SHAHUDAH
_______________

                 Saukar su Umm-Anum ƙasar haihuwarta tayi dai-dai da komawar Shahudah gida. Mom da Aamilah ne kawai a gidan, Dad ya fita tun bayan barin su Jay gidan. Waya Mom keyi da Mama Atika. A take ta saki wayar ƙasa ta tarwashe bisa tiles jikinta na tsananin tsuma.
         Shahudah da ke cikin wani yanayi kamar ba'a hayyacintaba ta ƙaraso cikin falon tana tangaɗi ta zube saman carpet. Da ga Mom har Aamilah zubewa sukai a gabanta jikinsu na rawa, sai kuma Aamilah ta miƙe da sauri taje ta leƙa waje. Babu kowa sai maigadi daya taimakama Shahudah ta shigo ya juya zai koma wajen gate. Komawa falon Aamilah tayi bayan ta rufe ƙofar ruf ta garƙama mata key. Ta koma wajen su Mom da gudu tana faɗin “Mom ita kaɗaice fa wlhy babu ɗan iskan”.
     Mom tace, “Nashiga Uku ni Aysha, Shahudah daga ina kike haka? Miyayi miki ne?”. Bata da mai amsa mata waɗanan tambayoyin dan Shahudah sai faman lumshe idanu kawai take. Mom ta ƙanƙameta a jikinta ta fashe da kuka tana jama ɗan-fir'auna mugayen addu'oi. Suna cikin haka akai knocking ƙofar, duk ɗagowa sukai suka zubama ƙofar falon ido kawai, sai dai daga Mom ɗin har Aamilah babu wanda ya iya motsawa. Shiru ba'a sake bugawar ba, hakan yasa suka share suka maida hankalinsu ga Shahudah.
        Salman dake buga ƙofa ganin ba'a buɗeba sai ya zagayo ta kitchen, shikansa ba ƙaramin mamakin ganin Shahudah yay ba, jikinsa har rawa yake wajen ƙoƙarin kiran Dad ya sanar masa Shahudah ta dawo.

        Cikin mintuna ƙalilan sai ga Dad a hargitse kamar zai tashi sama, yanda yake buga ƙofar kawai kasan babu lafiya, Aamilah ta buɗe masa tana matsawa ta bashi hanya, da sauri ya shigo. A gaban Shahudah ya durƙushe tare da maido kanta jikinsa idanunsa na kaɗawa lokaci guda dan ɓacin rai. “Shine ya kawota?”. Yay tambayar yana kallon Mom. “Nima ban saniba Dadynsu, shigowarta kawai muka gani ita kaɗai. Leɓe Dad ya taune da ƙarfi, ya kalli Salman dake tsaye cikin damuwa shima, “Kai Salman kiramin Dr Tayyib, ke kuma Aamilah kiramin maigadi, ai bazai rasa sanin wanda ya ajiyeta ba”.
         Babu jimawa maigadi da Aamilah suka dawo falon, cikin girmamawa Maigadi ya rusina yana gaida Mom. Bata amsa masaba, sai Dad ne ya jefa masa tambaya, “Yaya akai Mamana ta dawo gidan nan?”. “Wlhy Alhaji ban saniba, kawai naji nishin mutumne a jikin gate, shine na leƙa nama zata ko yaran nanne masu addabama mutane, sai naci arba da ita kwance jikin gate ɗin, sai kuma ƙurar mota da nake zargin a ita aka ajiyeta”. Ran Dad ya ƙara digunzuma sosai, yay ma maigadi nuni da hannu alamar ya tafi kawai.
     Maigadi na fita Dr Tayyeb na isowa gidan, bai zaman ɓata lokaciba ya shiga bama Shahudah taimakon gaggawa bayan an kaita ɗakin Mom an kwantar a gado. Duk wani taimakon da ake buƙata Dr Tayyeb ya bata, ya kuma tabbatar musu da cewar babu wata matsala normal zata farka insha ALLAH, ruɗanine ya sakata shiga wannan halin kawai. Hakanne ya basu ƴar nutsuwa, har suka kira su Mama Atika suka sanar musu dawowar Shahudah ɗin.

          Normal Shahudah ta farka a safiyar yau kamar yanda Dr Tayyeb ya sanar musu, kasancewar ɗaki ɗaya, gado ɗaya ta kwana da Dad da Mom sai suka baibayeta da tambayoyi akan abinda ya faru da ita?. Tsaf ta kwashe yanda akai ta sanar musu.
         “Dad ashe shiɗin ba mijina bane, tunda ya tafi dani wani gida ya kaini kawai ya ajiye bamma sake ganinsaba sai bayan kwana huɗu, ya sanarmin a randa aka ɗaura mana aure a ranar Bb ya saka shi ya sakeni, yace dan kawai yana ganin mutuncinsa yay hakan, amma badan Bb bane wlhy ko za'a kashesa bazai sakeni ba, kuma koda ya sakeni badan na taɓa zama matar Bb ba da bazai ƙyaleniba sai ya ketamin mutunci, wai Bb yana da kimar da bazai iya mu'amulantar abu shima yayi hakanba, Mom wlhy Bb mutumin kirkine, dan ALLAH ku bashi haƙuri mu koma aurenmu kamar da, ALLAH yanzu na amince zan haihu ko nawa yake so”.
     Mom da Dad da mamaki ya cika suka kama hannayenta cikin nasu, cikin zafin rai Mom tace, “Zaki koma gidan Jawaad kuwa Shahudah, zaki koma kodan shegiyar yarinyar can tasan asirinta ai

kin banzane, namiki alƙawarin a yau ɗin nan basai gobe ba za'a maida aurenku da Jawaad”. “Mom da gaske? Dad kaima kuma ka yarda da hakan?”. “Ɗari bisa ɗarima kuwa mamana, duk abinda kikeso a duniyarnan saikin samesa ko minene shi, duk abinda Momynku ta faɗa kisa a ranki ya gama tabbata”. Rungume Dad tayi tana fashewa da kukan jin daɗi, suma suka rungumeta cike da so da ƙauna harma da tausayinta.
          Gari na ƙarasa wayewa Mom ta ɗauki Shahudah suka tafi family house ɗinsu.

______________________________
      BEEJAY
______________

           Da ƙyar muka iya tashi sallar asuba, musamman ma ni da jikina ke ciwo ta ko ina, idanuna sunmin nauyi sosai na rashin barci da kukan da na sha. To nidai bansan randa zan zama jarumar ba, duk yanda zan fasaltama mai saurarona zai ga kawai nacika rakine da ragwanta, amma ni kaɗai nasan sirrin al'amarin kawai.
     Da taimakonsa mukaje bayi badan bazan iya tafiya da kaina bane, hakan kawai shi yaso shiyyasa ya kamani muka shiga tare. Tare mukai wankan da bamu samu damar yi ba saboda tsabar barcin da yaci ƙarfin idanunmu, muna fitowa ya fice daga ɗakin.
      Tsaye nai ina tunanin ta'ina zan fara ne? Bani da wani kayan sakawa a ɗakinsa sai abinda baza'a rasaba, tunanina ne ya katse jin motsin mutum da sallama ciki-ciki, ya ajiye kayan dake hannunsa kusan kala bakwai, sai leda da alamu ya nuna kayan barci dana cikine a ciki, ajiyar zuciya naɗan sauke, bai jira cewataba ya sake ficewa.

           Ana idar da sallar asuba ban zaunaba, ina ƙoƙarin tashi ya shigo ɗakin da sallama, da alama ko azkar bai zauna yiba balle ai maganar motsa jiki, jallabiyar jikinsa kawai ya zare ya ajiye ya haye gado, matsawa nai na gaishesa, batare da ya amsa minba ya jawo hannuna na faɗo kansa, “Ouch” ya faɗa a hankali alamar yaji zafi, ɗan kallonsa nai sai kuma na kumbura baki. Hancina yaja yana wani lullumshe idanu, ya birkiceni na koma ƙasa fuskokinmu daf da juna muna shaƙar iskar numfashin junanmu. Cikin yin mar-mar da idanu na tsoro nace, “Ina kwana?”. Shiru yay kamar bazai amsaba yanzunma, yanata ƙarema fuskata kallo, ya sumbaci goshina yana sake ɗagowa da ƙoƙarin saka idanunsa cikin nawa amma naƙi yarda da hakan. Saima ɓata fuska nai ina faɗin, “Abinci zan ɗora fa”. “Da wane ƙarfin?”. Ya faɗa a ƙasan maƙoshi, dan koni dake daf dashi badan ina kallon lips ɗinsa ba ba lallaine na fahimtaba. “Da nawa mana” na bashi amsa nima ciki-ciki. Nauyinsa ya ɗan sake sakemin yana faɗin, “Oh ni kika raina kikema raki dama kenan?”. Tuni idanuna sun fara tara ƙwalla, “ALLAH zaka kasheni”. Nai maganar a rarrabe dan na fara sauke numfashi da ƙyar. Yi yay kamar zai ƙarasa sakarmin nauyin sai kuma ya ɗagani yana dunguremin kai. Nannauyan numfashi na sauke ina lumshe ido irin na ALLAH na gode makan nan. Na yunƙura zan tashi ya maidani ya sake kwantarwa. “Barci” ya faɗa a cikin kunnena. “Idan nayi barci sukuma mi zamu basu suci?”. “Shiiii!!” ya faɗa batare da ya bani amsata ba. Shirun kuwa nayi ina masa kallon mamaki, yaja bargo ya lulluɓemu da shi tare da sakani a cikin jikinsa, a hankali ya furta, “Thanks you Miemaa”. Bansan dalilin godiyarba, dan haka na sake lafewa a jikinsa nace, “For What?”. “For Everything Zinaran” Ya bani amsa da wani irin salon da yasa tsigar jikina tashi. Sake lafe masa nai a jiki ina shaƙar mayataccen ƙamshin turarensa da akwanakin nan yakemin daɗi fiye da komai. barcin mukeji, dan haka kafin wani dogon lokaci yayi gaba da mu.

            Barcin da su Umm-Anum suka gagara yinsa a daren jiya yau suna idar da salla suka nema yinsa, koda Jay da Anuwar suka shiga gaishesu sama-sama suka amsa musu, Jawaad da yasan za'a rina yaja hannun Anuwar suka fito. Dama yasan ai wannan barcin sai sunyisa dan shi ba'a cin bashinsa daman.

        Kasancewar na kwanta da maganar abincin a raina sai barcina baiyi tsahoba na tashi, a hankali na zare jikina daga nasa na sauka a gadon, badan barcin ya isheniba na tashi, zuciyatace kawai bata aminta dana kwantaba bayan gida cike da baƙi. Ina fitowa babban falo naci karo da kulolin abinci, da mamaki na isa garesu na bubbuɗe, lafiyayyen breakfast ne a ciki wa

nda ya fito shar kamar ka zauna ka cinye kai ɗaya. Mamaki ya kamani na inda ake kawo wannan abincin? Sanin bani da mai bani amsa sai kawai na shiga kwashesu zuwa kitchen, na dawo nahau gyaran falon zuwa falonsa da nawa da duk inda dai bazan takurama masu barciba. Kafin su tashi na shirya abincin a falona na koma nayi wanka na na shirya tsaf cikin zani da riga na atanfa da sukaimin ƙyau.
      Jinai kamar ana kallona, na juyo da sauri na kalli gadon batare dana ƙarasa ɗaurin ɗan kwalin ba. Boss dake kwance idanunsa a kaina ƙyam ya ɗan lumshesu ya sake buɗewa a kaina cike da salo. “Dama ka tashi?”. Kansa ya jinjinamin kaɗan batare da yace komaiba. Ɗan kwalinma sai naji na kasa cigaba da ɗaurasa saboda idanunsa duk sun takurani, haka dai na daure na ƙarasa na miƙe har lokacin idanunsa a kaina. Toilet naje na haɗa masa ruwa na fito, yanzu kam zaune na iskesa a bakin gado da waya a hannu. “Ga ruwan wanka can”. Kansa kawai ya girgiza min, batare da yace komaiba. “ba yanzu zakayi ba?”. ajiye wayar yay ya ɗago yana kallona, “Barshi idan naci abinci zanyi, bara na duba saƙon nan da Jabeer ya turo min” yay maganar yana miƙewa ya nufi Computer ɗin dake a ɗakin inda ya gyara a can gefe tamkar wani ɗan office. Da kallo kawai na iya binsa, danni mamaki yake bani yanda sam bai gajiya da aiki. Komai banceba na gyara gadon kawai na fice daga ɗakin.
            A falo na iske Aunty Batool ta fito cikin shirin fita, na bita da kallon mamaki da alamar tambaya. Murmushi tamin kaɗan tana gyara mayafinta, “Zanje gida saboda abincin Alhaji babba, naga Ummah ganin ƴar uwarta yama mantar da ita”. Murmushi nayi, “Ah haba aunty Batool itama nasan ba mantawa tayi ba, kawai dai tana cikin yanayine mai wahalar fassara, to mizai hana ki ɗiba masa na nan? Idan kuma wani ya keso daban ai saina girka masa yanzun nan insha ALLAH”. “A haba, wahalan ai sai yayi yawa, bara kawai naje can ai zan dawo, koda yake nama san acan kuma yau za'a yini ma”. “A'a dan ALLAH, muje kiga na nan ɗin dai aunty Batool, shima idan yaji kin tafi can dan kawai dafa abincin baba ai bazaji daɗiba”. Nai maganar ina marairaice mata.
       Da ƙyar na samu ta amince mukaje kitchen ɗin, duk abinda tasan zai iya ci shi ta ɗiba masa, ta zuba a kwando ta fice riƙe da key ɗin motar da sukazo a ciki.

        Coffee na haɗa na koma kaima Boss, yanata aikinsa hankali kwance, na ajiye ɗan tray ɗin dana ɗora ƙaramar butar shayi da kofinta sai cokali a gabansa, tsiyayawa nai na miƙa masa, batare da ya kalleni ba ya amsa yana faɗin, “Waye ya fita da mota?”. “Aunty Batool ce” na bashi amsa a taƙaice. Baice komaiba yakai kofin bakinsa, ɗayan hannunsa kuma yana amfani da mouse.

★★★★★★

          Zuwa goma da rabi duk mun hallara gaban abinci, bayan gaishe-gaishe da tambayar lafiyar juna mukai zaman karyawa, kowa nacin abinci cikin salama bandani da naketa tsakurarsa, badan rashin daɗiba kuma, haka kawai dai nakeji bana sonci kuma yunwa nakeji.
       Jay ya lura bily batacin abincin sam, sai dai kunyar iyayensa ta hanashi cewa komai. Ummah babba ce ta lura da hakan, saita kira Bilkisu. Tashi nai na nufeta dan nazata wani abun zata sakani, sai dai ina zuwa ta jani ta zaunar kusa da ita, da kanta ta shiga ɗuramin abincin duk da nace mata na ƙoshine, ina kallon sanda boss ya sauke ajiyar zuciya. Daurewa kawai nake ina amsar abincin.
          Boss ne ya fara miƙewa alamar ya ƙoshi, yaɗan kalli iyayen nasa yana faɗin, “Bara naje na watsa ruwa kafin time ya ƙure, jirgin su Abbu ƙarfe sha biyu zai sauka”. Cikin kulawa Ummah babba da ƙarama suka amsa masa.
      Shigewarsa babu jimawa muma duk muka kammala, da taimakon su Anum na gyara wajen, gudun kar kwanikan su bushe sai mukai zaman wankesu, muna wanke-wanken ina tunanin abinda ya kamata na dafa mana da rana, dan koma daga ina ake kawo wannan abincin bana buƙatar a cigaba da kawosa, ya kamata nima in-lows ɗina suci girkina ai....

★★★

         Jay na fitowa daga wanka ya samu wayarsa na haske kasancewar a silent take, matsawa yay gaban mirror ya shiga shafa mai batare da ya duba mai kiranba ma, bayan ya kammala yana gaban Wadrobe zai ɗauka kayan d

a zai saka ya kuma hangar wayar tana haske, guntun tsaki yaja, ya ɗauka kayan da yake bukata ya fara sakawa, sai da ya shirya tsaf sannan ya nufi wayar yana idasa saka maɓallan rigarsa. Gabansa ne ya ɗan faɗi ganin Batool ce ta jera masa har missed calls kusan talatin, sai kuma number sojan da sukanyi magana da baba ƙaura idan hakan ta taso. tabbas wannan kiran bana lafiya bane, dan kaf cikin ƴan uwansa babu wanda ya kai Batool iya zama da shi da halinsa, inhar tai masa kira ɗaya tai na biyu taga bai ɗaukaba bazata sake kiransaba sai idan shine ya kirata. Yana ƙoƙarin kiranta sai gashi ta sake kira, ɗagawa yay da sauri....
         Daga can Batool ta sake fashewa da kuka jin an ɗaga, a cikin tsananin ruɗani tace, “Yayanmu akwai matsala, wasu mutane sunzo har gida sun tafi da Alhaji Babba da baƙon mutumin nan”.
         Wani irin yankewa ƙirjin Jawaad yay ya faɗi, furicin Batool ya jisane cikin kunnensa tamkar saukar guduma, cikin rawar baki yace, “Su su.. Su wanene?”. “Ban sansuba Yayanmu, ina ɗakin Alhaji babba ina gyarawa suka shigo. fuskokinsu duk a rufe suke da facemask, nima nasan da sun ganni bazasu barniba, tun shigowarsu nake kiran wayarka amma baka ɗaukaba, ina tsoron na kira su Ummah su ruɗar da kansu shiyyasa ban kiraba.....” Bai bata amsaba ya katse kiran, ƙirjinsa na wani irin lugude tamkar ana gasar dakan fura a kansa. Da sauri ya fice daga ɗakin, harya nufi sashen Bilkisu sai kuma ya jiyo dariyarsu a kitchen ita dasu Nabeelah, can ya juya ya nufa......
          Muna tsaka da yima Anum dariya boss ya faɗo kitchen ɗin, yanayinsa kawai ya sakani faɗuwar gaba, Anum da Nabeelah kam duk ɗauke numfashi sukai dan tsoro, baice komaiba yaja hannuna muka fice, har munje ƙofa ya juna yana watsama Nabeelah kallon gargaɗi, “Kucigaba da aikinku, idan kuma ƙafar wani ta fita a kitchen ɗin nan saina ɓallata”. Kai kawai suka jinjina masa, ya ja hannuna muka ƙarasa ficewa zuwa bedroom ɗinsa.
       “Boss lafiya kuwa?”. “Babu lafiya Miemaa, yanzu Batool ta kirani........ Akwai matsala ace su Ummuna susan wannan maganar, musamman ma ita da nasan yanzu babu wanda ta ƙagu ta gani kamarsa, dan haka kiyi shiru da bakinki yanzu zan tafi can, kosun tambaya kice nafita amma zan dawo yanzun k.......”. Da sauri na katsesa da faɗin, “Boss tare zamu tafi, nima bazan zaunaba”. “Bazai yuwuba Miemaa, idan muka fita mu duka zasu iya tunanin wani abu”. “Dan ALLAH kayi haƙuri mutafi tare, koba komai nima zanyi wani amfanin ai, zamana anan zaisa na kasa jurewa na tona asirin komai”. “Miemaa!....” “Please boss”. Nai azamar katsesa. Bakinsa ya cika da isaka ya furzar da ƙarfi yana ɗaga wayarsa dake haske. Ban saurari amsarsa ba nashiga ƙoƙarin canja kayana.

        Ta kitchen muka fita, bayan boss ya jama Nabeelah dogon gargaɗi akan ta kama bakinta wlhy, idan har sukace mun fita sai yay gutsi-gutsi da ƙasusuwanta yanda babu mai iya shaida itace harma Anum ɗin kanta. Daga haka muka fice, Sadiq baizoba, saboda weekend ce, dan haka boss da kansa zaiyi driving ɗin.
         Mahaukacin gudu ya ke zubawa tamkar shi kaɗaine da titin, to dama yaya lafiyar giwa balle....., dama can shi ɗin ɗan babu sauƙine wajen gudu da mota, balle yanzu data zamto na ƙare numfashi. Ko gezau banyi da gudun nasaba yau, gani nakema tamkar baya gudun, sai faman kaɗa yatsun hannuna nake jikinna na wani irin tsuma. Yayinda boss kuma yana tuƙi yana waya da su Oga Hafiz.
    Cikin mintuna ƙalilan muka iso gidan, mun iske tawagar su Jabeer a gidan harma da ƴan sandan zahiri, sai wasu daga cikin ƴan anguwa da abin ya faru akan idanunsu su Hafiz nata musu tambayoyi.
      Aunty Batool ta iso garemu da gudu tana kuka, riƙo hannunta boss yayi idanunsa na sake kaɗawa suna sake komawa jajur fiye da yanda muka fito gida. Bayanin duk yanda yanda al'amarin ya faru ta shiga yimasa kamar yanda tayima su Sir Ahmad ma. Kasa cewa komai yay, sai jikinsa dake wani irin rawar bala'i, ƙwanjinsa da jijiyoyin kansa na sake buɗewa, yanda ƙirjinsa ke sama da ƙasa kawai zai tabbatar maka zuciyarsa na gudu maiban tsoro dake neman fin ƙarfin gangangar jikin nasa. ya saki hannunta ya nufi inda su oga A

liyu suke. Matsawa nai na rungumeta muna hawayen tare, sai dai ni saɓanin ita ina ƙarfafa zuciyata yau ina lallashinta, sai da naga ta tsagaita da kukan sannan na ɗagota na share mata hawayen. “Ki kwantar da hankalinki aunty Batool, insha ALLAHU zasu dawo, kosu wanene ALLAH bazai basu dama akan ƙudirinsu ba”. “ALLAH yasa haka mami” ta faɗa wasu hawayen na sake jiraro mata. kiran da oga Jabeer yaymin ne yasa na taimaka mata ta zauna a cikin motar.

        Tun a yanda Jawaad ɗin ya taka birki sanda suka iso gidan su Sir Ahmad sukasan ransa a matuƙar ɓace yake fiyema da yanda sukai hasashen ganinsa. ganin Batool ta nufesa sai duk suka dakata daga yunƙurin zuwa inda yaken, bayan yabar wajen ya nufesu ne, Sir Ahmad yay saurin tararsa cikin zafin nama yana riƙe hannunsa “Jay! Ka kwantar da hankalinka, insha ALLAHU zamu gano inda suke, koma su wanene suka aikata hakan basuyi nisa damuba a halin yanzu tabbas, yanzu haka har su Jabeer sun fara ƙoƙarin gano inda suke. Ka nutsu banason ka fusata kanka da yawa, domin nutsuwarka ce abar buƙatarmu fiye da komai a yanzu. shin akwai wani da kake zargi ne?”.
          Jawaad dake tsaye kawai yana kallon yanda su Aliyu da sauran ƴan sandan keta kai kawo akan al'amarin ya lumshe idanunsa yana busar da zazzafan numfashi, “Sir! Kowama

1 Comments On KWAI CIKIN KAYA
avatar
zainab-nasir

1 year ago

Reply

Muna jin ddin yanda kuke ilimantar damu

Please Login or Register in order to submit comment