Moussa ba kariya ba ce " yanzu me ka ke tunani a kai ? "
" me kuma na ke tunani , kawai ka koma Daular Saudiya , ka fada musu dama ba mutuwa ka yi ba , bayanar ka ita za ruguza duk wani makircin da su ke shirin kulawa ta hanyar auren nan "
girgiza mishi kai Zayd ya yi kafin ya ce " sai dai ka yi hakuri amma Batun komawa Daular Saudiya ka bar shi kawai "
" why ba za ka koma ba , Amir yanzu kennan ka hakura da ahalin ka , ba za su sake ganin ka ba ? "
shiru shi dai Zayd ya yi bai ce mishi komai ya na kallon gaban shi Allah kadai ya san abun da ya ke tunani
ganin yadda ya yi shiru bai ce komai ba ya sa Moussa sakin wani cool murmushi ya rage sautin Muryar shi ya ce " Ko dai ba za ka iya rabuwa da babyn ka ba "
" Ba zan iya tafiya na bar ta ba gaskiya , kuma ba zan iya raba ta da ahalin ta ba , ba zan so ta ji kewar su ba kamar yadda na ke jin kewar nawa " Zayd ya fada ba tare da ya kali Moussa ja
shi a tunanin shi cikin zuciyar shi ya yi wannan maganar kawai sai jiyo Muryar Moussa ya yi ya bushe da dariya
a hankali Zayd ya juyo kai ya kale shi cike da rudu ya ce " lafiya ka ke dariya kai kadai ? "
tsagaita dariyar shi Moussa ya yi ya na girgiza mishi kai ya ce " ba komai Mister Love "
dan karamin tsaki Zayd ya yi kafin ya ce " minene kuma Mister love ? Diya ban san dalilin da ya sa kullum sai mun fara magana da kai sai ka kawo shirme a ciki "
yar karamar dariya Moussa ya yi kafin ya ce " Sorry sorry...... "
bai kai karshen maganar shi ba ya ga Zayd ya mike ya nufi corridor
da sauri Moussa ya ce " a'a Mister love ina za ka je haka ? "
ko sannu Zayd bai ce mishi ba ya sa kafa ya shige corridor din ya nufi bedroom din shi
sai da ya shige corridor din sannan Moussa ya sake bushewa da dariya ya na fadin " wa ya ga Inaya da cikin Amir , ni dai na gani " ya na gama fadar haka ya sake bushewa da dariya shi kadai kamar zautace
▪Inaya
Bayan ta fita gidan ta fara tafiyar ta cikin konciyar hankali , kai tsaye gidan su ta nufa
Da sallama a bakin ta ta shigo cikin gidan
Mama na zaune bakin kofar dakin ta , dai'dai lokacin da Nesrine ke fitowa da ga dakin su ta na sanye da uniform ita ma
Ta na ganin Inaya ta saki wani kyawatencen murmushi da gudu ta je ta rungume ta ta na fadin " na yi kewar ki sosai "
Rungume ta ita ma Inaya ta yi ta na murmushi
Cen su ka tsinci Muryar mama ta na fadin " toh malama kin sake ta, ta zo ta gaishe ni ko ? "
A tare su ka yi dariya su na raba jikin su da na juna sannan Nesrine ta riko hannun ta su ka nufi mama
Ta na isa mama ta bude mata hanayan ta akan ta zo
Ba musu ta fada jikin ta ta na murmushi ta ce " ina kwana mama ? "
" lafya lau autar mama ya ki ke komai dai'dai ko " ta fada ta raba jikin ta da na Inaya
Kallon ta da kyau mama ta yi cike da mamaki ta ce " ban gane ba school za ki koma tun wuri haka "
Murmushi Inaya ta yi kafin ta ce " eh mama yaya Zayd da kan shi ya sayo min uniform ki na gani ? " ta kai karshen ta na juyawa
Mama na shirin magana Nesrine ta riga ta cewa " wuce mu tafi don Allah kar mu yi late"
" shikenan wuce ku tafi , sai kun dawo " mama ta fada ta na murmushi
Hannu Nesrine Inaya ta kamo su ka juya ta ce " mu tafi "
Jinjina mata kai Nesrine ta yi kafin ta juya su fara takawa su ka bar gidan
A tare su ke tafiyar su cikin konciyar hankali su na tafe su na hira gwanin ban sha'awa
Sai da su ka kawo bakin kofar college din , Inaya ta ga masu sayarda kayan marmari
Da sauri ta saki hannun Nesrine ta nufi guda da ga cikin su
Karasowa wajen Nesrine ta yi ta kai hannu ta daura a kafadar ta ta na fadin " to sarkin ciye² me kuma za ki saya "
Kallon ta Inaya ta yi sannan ta ce " Apple mana , ina marmarin Apple sosai wlh dama ban tsaya breakfast ba "
Ta kai karshen ta na meda kallon ta kan mai sayarwar ta ce da shi ya saka mata Apple shida ta na kai hannu cikin jakar ta, ta ciro kudin da Zayd ya bata
Zaro idanu Nesrine ta yi ta na kallon kudin cike da mamaki ta ce " ke Inaya ina ki ka samu uban kudi haka ? "
Ba tare da ta kaleta ba ta na kokarin ciro dubu biyu ta bawa mai sayarwa ta ce " yaya Zayd ne ya bani " ta kai karshen ta na karbar ledar Apple din ta juyo ta kali Nesrine ta ce " mu tafi ? "
Ba musu su ka juya su ka shiga cikin college din su na tafe su na hira har sai da su ka kai bakin kofar class din su sannan su ka rabu
▪After some hours
Zaune su ke saman chair a cikin cafeteria , Inaya sai faman cin Apple ta ke ,Nesrine kuma na kallon ta ta na murmushi har ga Allah ta yi kewar Yar uwarta sosai , tun tafiyar ta har yanzu ba ta samu ta yi barcin kirki ba , ta saba kullum sai ta rungume Inaya cikin barcin ta , yanzu kuma ba ta nan ita daya saman gadon sai dai ta yi ta juyi idan ta gaji ta rungume pillow
Sai da ta kusa kamalawa ta dago kai ta kali Nesrine , murmushi kadan ta yi kafin ta mika mata Apple din hannun ta ta ce " za ki ci ne ? "
Girgiza mata kai Nesrine ta yi ta na murmushi ta ce " a'a ci kayan ki babyn Zayd "
Daga kafadun ta Inaya ta yi ta ci gaba da cin Apple din ta hankali konce , ita komai na ta irin na yara ne
Sai da Nesrine ta ga ta Kamala sannan ta ce " Inaya zan so na tambaye ki wani abu "
Jinjina mata kai Inaya ta yi ta na fadin " wane abu kuma ? "
Ajiyar zuciya Nesrine ta sauke sannan ta ce " da gaske ki na son yaya Zayd , a yadda ya ke hakan ba ya magana kuma ba ya gani ? "
Murmushi kadan Inaya ta yi kafin ta jinjina mata kai allamun e sannan ta daura da cewa " ina son shi a haka , kuma ai yanzu miji na ne , tsakanin shi da Allah ya ke tare da ni , ni ma tsakani da Allah na ke tare da shi , Ni ma ban san ya a ka yi na kamu da son shi haka , lokaci guda ya shiga cikin zuciya ta , kuma ba na fatan ya fita , ko bayan mutuwa ta , rashin ganin shi ko rashin maganar shi hakan ba zai sauya abun da ke cikin zuciya ta ba har abada "
" why Inaya ? Ki duba duk mazan da ke cikin duniya , ki rasa wanda za ki so sai kurma kuma makaho , me na sama ya ci bare ya ba na kassa , da wane idon zai kula da ke , mutumin da ko magana ba ya yi miki , wai a haka za ki bude baki ki Ce ki na son shi , me ya mallaka da su sauran mazajen duniya ba su mallaka ba , da har soyayyar shi za ta rufe miki ido ki kasa ganin minene al'heri a gare ki , ko ke ma kin zama makafniya kamar shi ? "
" wai Nesrine wa ya fada miki yaya Zayd kurma ne , ko kuma shi ya fada miki shi makaho ne " Inaya ta fada cikin bacin rai
❤⚘ EXILED PRINCE ⚘❤
(LOVE MEETS POWER ) 👑🔥
( A heart touching love story , Romance , injustice & destiny )
BY : MEERAH ❤✌
Marubuciyar littafin
TAURIN ZUCIYA 💖💍🌺
TAP THIS LINK TO JOIN MY WHATSAPP GROUP COMMENTS SECTION
👇👇👇👇👇
https://chat.whatsapp.com/IrsjzfoHUHBJzdgRtskPcY
TAP THIS LINK TO JOIN MY WHATSAPP CHANEL
👇👇👇👇👇👇
https://whatsapp.com/channel/0029VaGhJCqKmCPUvpvIJ80i
♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡
PAGE 11 ❤🔥
Dan zaro idanu Nesrine ta yi ta na kallon ta cike da tantama ta ce " wai Inaya me ya ke damun ki ne , inda ya na magana duk shekaru hudun nan da mu ka yi tare da shi me ya sa ko kalma daya ban ji ta fito da ga bakin shi ba , kennan a haka ku ke rayuwa cikin gidan na shi , kennan rayuwa da kurma na yi miki dadi ? "
Mikewa tsaye Inaya ta yi ta dauki jakar ta ta na fadin " kin ga Nesrine ban san me ya sa ba ki son yaya Zayd ba, ni fa ina son shi a haka kuma duk abun da za ki fada bazai sa na daina son shi ba , ku duka kallon kurma da makaho ku ke yi mishi amma ai ni ina gane abun da ya ke fada kuma da makaftar tashi ya ke aiki , kin ga ya fi karfin a ce mishi makaho kin ga idan ba za ki fadi abun al'heri a kan yaya Zayd ba ki daina yi min magana "
" Inaya yanzu saboda wancen banzan za ki fada min haka , minene shi a wajen ki , da ga na fada miki abun ya ke gaskiya "
" Gaskiya guda ce , ina son shi a haka , wai shi makaho ko kurma ba shi da zuciya ne , kafin ki yi min wannan maganar ki je ki fadawa Abba , ai shi ya bawa yaya Zayd aure na , da bai yarda da shi ba , ba zai yarda ya aura mishi ni ba "
marairaice fuska Nesrine ta yi ta na fadin " yanzu Inaya kin fi son wacen mutum a kai na , ni Nesi din ki , me Zayd din nan gare shi da har idanun ki za su rufe a kan soyayyar shi , me ya ke da shi , da sauran mazan duniya ba su da shi , dama zama da makafi na meda mutum makaho ? "
a hankali Inaya ta girgiza mata kai cikin sanyin murya ta ce mata " a'a Nesrine ke ce dai makafniyar , har yanzu idanun ki sun kassa gwada miki , kyakyawar zuciyar yaya Zayd , Soyayya ta ita ce ya ke da , kuma har abada babu namijin da zai same ta , Nesi wai ya ki ka sauya lokaci guda haka ? a sani na ba haka ki ke ba , ba ki kaskantar da mutane kamar haka ko ma dai minene zan so ki sani , yaya Zayd dai miji na , kuma a hakan na ke son shi , a hakan zan zauna da shi , idan ki na jin haushin hakan ki kashe kan ki ki huta "
( TO FA YAU A TABO BABYN ZAYD 🤣🤣🤣🤣 )
Ta kai karshen ta na juyawa za ta bar wajen kawai sai ta ji ta bugi mutun
Dan bayan kadan ta ja ta dago kai ta kaleshi ta ce " sorry "
Murmushi kadan Moctar ya yi kafin ya ce " ba komai "
Da sauri ta raba ta geffen shi za ta wuce
Da sauri ya riko hannun ta ya ce " haba ina kuma za ki je , ni fa wajen ki na zo "
Cikin bacin rai Inaya ta kwace hannun ta ta juya ta fara takawa za ta bar wajen
Da sauri ya sha gaban ta ya ce " ba da ke na ke ba , za ki wuce ki kyale ni ? "
Cikin bacin rai Inaya ta ce " ka ga malam ka ba ni hanya na wuce ni matar aure ce "
Dariya Moctar ya yi har da dafe ciki
Sai da ya tsagaita dariyar shi sannan ya ce " oh sannu madam to , shi ne za a yi biki ba'a gayace mu ba ? " ya kai karshen ya na kashe mata ido guda
Dan tsaki Inaya ta ja kafin ta raba ta geffen shi ta wucewar ta
Da kallo ya bi har sai da ta kurewa ganin shi sannan ya juyo ya kali inda Nesrine ke zaune
Sai dai kuma me ?
Babu ita babu mai kama da ita, tun lokacin da ya bata baya ta tatare kayan ta a hankali ta tsere dan ta sani tabass Moctar ya na tare da Hafiz , idan kuma Hafiz ya zo wajen ta san tabass ba zai kyale ta ba shi ya sa ta tsere
Abun da ba ta sani ba Moctar shi kadai ya ke tafe , Hafiz bai san da cewa college din zai zo kawai ya ce mishi zai fita ne
Tsaki kadan ya ja kafin ya fara takawa ya fice cafeteria din shi ma
▪Inaya
Ta na barin wajen ta koma kai tsaye class din su ta koma dai'dai lokacin da prof din su zai shiga class din
After some hours
Bayan sun sauka da ga school ko wace ta wuce gida , Inaya kuma gidan mijin ta kai tsaye ta wuce dan yau fa Nesrine da Moctar sun tado mata na bacin ran
▪Zayd
Su na zaune cikin falo shi da Moussa ko wane sai faman latsa wayar shi ya ke
Su na zaune a haka Inaya ta shigo falon ta na sallama kassa kassa
Dago kan shi Moussa ya yi ya na amsa mata sallamar ta da murmushi
Ya na shirin yi mata magana ya ga ta wuce corridor kai tsaye ko gaida su ba ta yi ba
Da kallo ya rakata har sai da ta shiga bedroom din Zayd sannan ya dawo da kallon shi kan Zayd ya ce " Amir ina ga yau wani ya tabo ran baby na "
Slowly Zayd ya dago kan shi ya zubawa Moussa wadanan hazel eyes din shi ta cikin glass kafin ya ce " wai wanene babyn ka cikin gidan nan ? "
Hararrar wassa Moussa ya yi mishi sannan ya ce " bayan wadda ka ke kira da matar ka wa ke cikin gidan nan, ita ce baby na mana, ka ga na ma tafi na rarrashi abu na " ya kai karshen ya na mikewa tsaye zai shiga corridor
Da sauri Zayd ya riko hannun shi ya ce " kai Diya ban san rainin sens matar tawa ka ke kira da baby ? "
Kwace hannun shi Moussa ya yi kafin ya ce " tun da kai ba ka so ni ina so wlh , ni wlh ka ci gaba da kyale ta ma , hakan ya yi min dadi , ko na samu son da ta ke yi maka ya dawo kai na , i really love her, i don't know how ko yaushe hakan ta faru i'm falling in love for her , ni da za ka min Alfarma ka sake ta na je na roki malam ya aura min ita tun da kai ba ka son ta "
" Diya wai ka na jin abun da ka ke fada ne "
" ka ga malam ni don Allah kyale ni , wai ba ka ga yadda baby na ta dawo ne gidan ko gaisuwar arziki ba ta yi min ba , ka ga ni na tafi rarrashin ta " ya kai karshen ya na juyawa ya shiga corridor ya nufi bedroom din Zayd
Sumar zaune Zayd ya yi ya na jin abun da Moussa ya ke fada mishi nan take ya ji wani uban kishi ya taso mishi yanzu shi Moussa zai yanka a baya ya zagayo ya ce matar shi ya ke so kuma
Da sauri ya girgiza kan shi ya ce " no ! No ! Impossible bazai yi yu ba "
Ya na gama fadar haka ya mike tsaye da sauri ya shiga corridor kai tsaye ya wuce bedroom din shi cikin zafin nama ya bude kofar dakin ya shiga
Cak ya tsaya bakin kofar ya na bin dakin da kallo , duk wajen a tirje ya ke , ga pillow duk an zubar da su kassa , an zare bedsheet an tila shi gefe guda
Cen ya hango Inaya zaune a kassa ta saka kan ta tsakanin cinyoyin ta, ga jakar school din ta cen gefe ta tila ta
Tsaya wa ya yi ya na bin dakin da kallo ya na son ya ga Moussa amma ita kadai ya gani
Abun da bai sani ba shi dama Moussa wassa ne ya ke yi mishi dan ya san abokin shi da mugun kishi nan take zai fara bibiyar Inaya duk wane abu da za ta yi sai ya Ankara da shi , dalilin da ya sa ya ke yi mishi wannan abun amma shi gaskia ba son Inaya ya ke ba ko yanzu da ya shiga corridor din bedroom din shi ya shiga ba na Zayd ba
A hankali ya fara takowa cikin dakin har ya karaso inda ta ke zaune shi ma ya zauna gaban ta ya yi irin zaman cin tuwo ya zuba mata idanu, da allamun ba kuka ta ke ba
Sai da ya gaji da kallon ta sannan ya kai hannu shi ya kyasta mata dan yatsun shi biyu saitin kunnen ta
Da sauri ta dago kan ta ta na kallon shi dan ita ba ta ji shigowar shi ba cikin dakin har lokacin da ya zauna gaban ta , duk ta yi nisa cikin tunanin ta
Dan murmushi ta saki kafin ta gyara zaman ta, ta yi irin zaman da ya yi ta sunkuyar da kai ta riko tafin kafarta guda da hannayan ta duka biyu
Ganin ba ta da niyar yi mishi magana ya sa ya kai hannu ya dago habar ta ya na kallon face din ta , sam babu digon hawaye a cikin idanun ta , to me ya faru kennan ?
Ita kuma murmushi kadan ta saki kafin ta ce " yaya Zayd me ya faru ? "
Janye hannun shi ya yi kafin ya girgiza mata kai sannan ya kai hannu ya nuna nata sannan ya mata allamu da hannu " me ya ke damun ki ? "
Sunkuyar da kan ta yi kafin ta ce " yaya Zayd wlh Nesrine ta na yawwan takura min wai na auri kurma kuma makaho duk cikin mazan da ke cikin duniyar nan wai shi na zaba, ban San minene matsalar ta ba , ni na fada mata ina son ka a hakan amma ta ki jin magana har wasu classmate din ta ta fadawa yanzu duk sun bi sun takura min a school , ni wlh in ba ta bani lafya sai na fadawa Abba , shin minene matsalar in baka gani ko baka magana na ga kai ma mutun ne ka na da tsoron Allah , ka na sallat ka na azumi ka yarda da Allah da manzon sa , kuma ka na da zuciya mai kyau , amma ita duk ba ta ganin wannan , wlh ina jiye mata duniya ba ta san abun da zai faru da ita ba nan gaba , sam ba ta ganin darajar mutane , duk abin da na ke son na gwada mata ta ki gani amma a haka wai ta ke ce maka makaho al'halin ita a bata gani "
Tun da ta fara magana ya tsare ta da idanu ya na kallon ta cikin ranshi kuma cewa ya ke " Moussa ya yi gaskia she is so innocente , her heart is so pure , ba ta jin tsoron fadin abun da ke cikin zuciyar ta , duk zaman da na yi a Nigeria ke ce mace ta farko da ta ce min ta na so na a matsayin makaho kuma kurma al'halin ba haka ba ne , ina ga zan yarda da maganar Moussa na amshi soyayyar ta , muyi sabuwar rayuwa nassan bazan samu wadda za ta zauna da ni tsakanin ta da Allah kamar ke ba "
Ya na gama fadar haka ya mike tsaye ya juya ya fara takawa ya fice dakin
tun da ya mike ta dago kai ta na kallon yadda ya ke tafiya cike da nitsuwa , ita ta rasa dalilin da ya sa komai na shi burge ta ya ke yi , haka kawai ta ci gaba da kallon shi har sai da ya fice sannan ta saki wani cool murmushi ta ce
" ina son ka yaya Zayd , kai ma na san wata rana za ka bude baki ka ce ka na so na "
ta na gama fadar haka ta tashi ta shiga gyaran dakin
Zayd kuma Ya na fitowa falon ya isko Moussa ya na konce saman sofa ya na latsa wayar shi
Ya na ganin Zayd ya fito ya mike zaune ya na murmushi ya ce " har ka ida rarrashin baby na "
Ko kallon shi Zayd bai yi ba ya sa kai ya fice falon, ya bar gidan baki daya
Tafiya ya ke cikin konciyar hankali ya na taku cike da izza har ya karaso bakin kofar gidan su Inaya, ko me ya zo yi oho !
Ya na shirin shiga gidan Malam ya fito da cikin gidan ya yi shirin tafiya massalaci dan lokacin sallat ya yi
Ya na ganin Zayd ya saki wani kyawatencen murmushi ya mika mishi hannu su ka yi musbaha sannan ya ce " a'a malam Zayd yau kai ne a gidan na mu haka , ina fatan ba dai laifi autar tawa ta yi maka ba "
Girgiza mishi kai Zayd ya yi kafin ya ce " no ba maganar ta ba ya kawo ni gidan nan uncle ! "
" toh , lafya kuma ? Maganar mi ta kawo ka in haka ne ? " malam ya fada ya na tsare shi da ido
Sai da ya dauki lokaci kafin ya ce " uncle ina so in san dalilin ka na aura min Yarinyar nan al'halin ba ka san ko ni wanene ba ka san kowa nawa ba za ka dauki d'iyar ka ka bani ita haka kawai , Uncle na gaji wlh , na kassa gano komai , na tambaye ka , ka ki fada min ya ka ke so na yi ? "
Dan murmushi malam ya yi kafin ya ce " Ni daman na sani ba za ka gano komai ba , kawai na kyale ka ne ka kai matar ka dakin ka , Zayd na fada maka in lokacin ya yi za ka sani amma tun da ka matsa bara na