Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
8 / 10
dake ratsata, hannu biyu ta saka tana tallafo fuskarsa fashewa da wani matsanancin kuka mai ban tausayi tayi tana furta "Innnalilahi wa'inna ilaihirraji'un sun kashe man JODDi , dan Allah ka miƙe karka mutu kar ka tafi ka barni bani da kowa, wajenka nake raɓa naji sanyi JODDi bana da wanda ya Fika ka taimakeni ka tashi" ta faɗa wani kuka mai ciwo na ƙara kufce mata ganin shiru ba Alamar zai tashi ya sakata miƙewa tana ratsa wata hanya da gudu tana binta sosai take gudu har Numfashinta na shiɗewa taci uwar tafiya sosai amma babu motsin koda Mutum ɗaya ne a cikin jejin, kasancewar ta san magunguna ya sakata ƙara dosar cikin Jejin tana ƙara duba itatuwan dan ta tabbatar JODDi ba mutuwa yai ba, ganyayaykin data sani ta ɓallo tana biyo hanyar ta dawo kamar ranta zai fice haka take tafiyar kota ciwo jikinta bata bi da jirin dake ɗibarta *Pls Habibties ayi manage da wannan dan Allah love U All my lovely Habibties ina matuƙar ƙaunarku har cikin zuciyata* *Riamcool ce* [5/21, 8:18 PM] RIAMCOOL: *BAYAN WUYA* *Book 1* *By Riamcool* *MIKIYA WRITTER'S ASSOCIATION* *BISMILLAHIRRAHMANIRRAHIM* *P.35&36* A haka harta ƙaraso inda ta barshi kwance, har iyanzu koda ɗan yatsa ne baya motsawa, hawayen da take riƙewa ne suka ƙara samun damar zubowa, a hankali ta saka ɗan yatsanta tana ɗaukesu tare da duƙawa ƙasa ta ɗauko ganyen maganin tana matsa ruwansa, a hankali take buɗa masa bakin tana matsa masa ruwan a haka harta ɗan bashi ya shiga, kingin kuma ta shafe masa jiki dasu babu kamar inda yaji raunuka sun ɗauki tsawon kwanaki cikin jejin kafin ta samu jikin Joddi ya fara dawowa dai_dai Kwance take ta ɗaga kanta sama tana tunanukan dake ƙara karyar mata da zuciya, hawayen da taji ya biyo kuncinta ne ya sakata sanya hannu tana sharewa tsawon kwanakin da suka ɗauka basu ga koda gibcin wani mutum a cikin jejin ba hakan ya sakata yanke shawarar dan tafiya ko sunga mutane, miƙewa tayi tana zuwa wajen JODDi masa magana "JODDi miƙe muje" miƙewar yayi dan a ɗan zamansu yanzu yana fahimtar magana sai dai mayarwa ne baya iya yi, tafiya suke iya ƙarfinsu dan sunyi tafiya mai ɗan nisa kafin su shiga wani ɗan ƙaramin ƙyauye, hamdala Fattu tayi tana sauke wahalallen numfashi kafin ta samu wuri ta ɗan tsaya shima tsayawa yai ƙyam yana ƙarewa wurin kallo hannuwansa mai dai a baya, kallonsa tayi taga kamar wani mai cikakken hankali dan babu wanda zai kallesa yai masa kallon mahaukaci "Zauna" ta furta masa da Yaren fulatanci zama yayi bakinsa na motsi amma ya gaza furta wani abun, murmushi kawai ta saki tana kawar da kanta gefe sun juma anan zaune rasa inda zasu nufa, "Bayin Allah tun ɗazun na ganku anan zaune amma ku baƙi ne?" ɗan Dattijon ya tambaya da murmushi sosai a fuskarsa, itama Fattun Murmushin ta saki da hausarta marar fita tace "Ye mu baƙi ne bamu shan kowa anan ba dan Allah ko zaka iya taimaka mana wallahi bamu da kowa a duniyar nan bawan Allah ka taimakemu idan har kana da hali" ta faɗa wasu hawayen na sake biyo kuncinta da tausayawa mutumin yace "Ayya ku taso muje gidana" babu musu suka bisa har gidansa, iso yai masu suka shiga har cikin gidan ruwa ya fara sakawa a kai musu na wanka dan yaga suna da buƙatar hakan,bayan sun gama aka basu Abinci da ruwa suka sukai nak,kallonsu mutumin yai yace "ko zaku iya bani ɗan takaitaccen labarinku?" "Eh Baba" Fattu ta furta nan take ta faɗa masa labarinsu tun daga farko har ƙarshe batai masa ƙarya ba, da tausaya yake binsu da ido shi kanshi yai matuƙar tausaya musu, "Sannu kunji ko, lallai Ubangiji ya kareku daga ma sharrin shaiɗan da har baku aikata wani abun ba dukda ba isasshen hankali ne dashi ba amma bai kamata kuna yawo babu aure a tsakaninku ba, abinda nake gani a karo na biyu zan sake taimakonku, zan ɗaura muku aure a goben nan in sha Allah" wani dummm gaban Fattu ya faɗi jin kalmomin mutumin taya zata iya rayuwar aure da JODDi? ita fa a matsayin Yaya ɗan uwanta ta ɗauki Joddinta da kuma soyayya ta Addini musulunci ita haka take gani, amma komai Ubangiji ya ƙaddara mata mai kyau bata da ikon jayayya akan lamarin da Ubangiji ya tsara mata, zata amshi ƙaddararta a yadda tazo mata, ita a yanzu dukkan wata rayuwa da zata zo mata hannu biyu zata saka ta karɓeta ta godewa Ubangiji, "Ƴata naji kinyi shiru" ɗago da fuskarta tayi tana faɗin "Baba duk hukuncin daka yanke mai kyau ne yadda ka taimakemu Ubangiji ya baka mafiyinshi mun gode shoshai" "babu damuwa Ƴar Nan Addinina na hidimta mawa taimako shi wani abu ne mai tsananin lada a duk lokacin da kaga ɗan uwanka na buƙatar temako kayi ƙoƙarin tai maka masa da iyakar ƙarfinka kaima Ubangiji zai taimake ka a dukkan wani hali da ka tsinci kanka, rayuwa kake amma gaba kaima baka san inda zata kaika ba" ɗaga kanta tayi tana matsa yatsun hannunta, dukkan maganganun da suke tsab JODDi ya riƙesu yana binsu da ido wani abu na daban na masa yawo a brain ɗinsa tsab kalmomin da Mutumin yai suka buɗe masa wani abu daya rufe masa ƙwalwarsa "waye Ni?" ya furta yana dubansu a mugun razane Fattu ta ɗago idanunta tana kallonsa "Joddi kana magana dama, ka tuno waye kai??" Tai masa tambayoyin a jere da ido ya bita yana faɗin "Ni dai ban san waye ni ba nima haka kawai na ganni" jijjiga kai tayi sannan tai hamdala ga Ubangiji daya buɗewa JODDi bakin yin magana "Masha Allah tun da Ubangiji ya buɗe masa baki yanzu dare yayi kije wajen mai ɗakina ki kwanta zuwa gobe da safe zan isa wajen mai gari na sanar masa da buƙatarmu" Dattijon ya furta da to ta amsa zuciyarta na bugawa dan bata san kalar matar da zata taras a gidan ba wataƙil ma ƙara Innaro da ita, bakinta ɗauke da sallama ta shiga amsa mata ƴar Dattijuwar dake zaune tayi tana furta "shigo ƴar nan kin jiko Malam ya sanar Mani da zuwanki" ta faɗa da Murmushi tana miƙewa Ajiyar zuciya Fattu ta sauke ganin Matar ba irin Innaro bace, a ladabce ta gaisar da ita tana zama, amsa mata matar tayi da fara'ar sosai, kamar ta goyata haka ta dinga nan da nan da ita harta kwanta tana tunanin halayen Mutanen nan biyu dama akwai mutane irin haka? ta tambayi kanta, a ranar dai wani bacci mai masifar daɗi ya ɗauke ta wanda zata iya rantsaewa tun da take bata taɓa yin Bacci mai daɗi irin wannan ba *Washegari* koda suka tashi daga Fattu har JODDi Mutumin ya kaisu wajen mai gari, tsab cikin hikima Dattijon ya ɗan faɗa masa wani abu daya saka su baro gida sannan ya kawo musu buƙatarsa, babu musu mai gari ya Amince sannan ya tara mutanen garin ya faɗa musu buƙatarsu, mai gari ya bayar da sadaki, kallon JODDi Dattijon yayi yana furta "Ya sunanka?" kamar wani mai Imagine haka JODDi ya tafi can kuma sai ya cije baki da ƙyar yana furta "Muhammad" "Sunan Mahaifinsa fa?" Mai gari ya tambaya "Ahmad" JODDi ya furta, babu ɓata lokaci aka ɗaura auren JODDi da Fattu *********************** zaune take bisa Ƴa kujera ta guragu tana kallon fuskar mijin nata da tausayawa wanda take matsa mata ƙafafuwan ta, Allah kaɗai ya san irin ƙunci da baƙin cikin Abinda take ji idan harta ga Mijin nata cikin wannan hali kullum hankalinsa ba a kwance ba ga matsanancin ciwon da yake fama dashi, itama kenan da take kallonsa ina ga A'ishatu wacce yai mata nisa a iya tsawon shekaru to ita wane baƙin ciki ma ne bata ƙunsa ba? hawaye ta share tana jana Majina, ɗago da idonsa Abbie yai yana kallonta "Mansura kukan ne baki daina ba, ita fa ƙaddara babu yadda bata zuwar wa mutum ko wane bawa kika gani da tashi jarbtar sai dai wata tafi wata kiyi haƙuri da rayuwar da kika gammu a ciki, kiyi tunani da Ƴar Uwarki Aysher mana ki hasaso dake ke cikin halin da take ciki ya zakiyi? amma tai haƙuri ta jure taci gaba da rayuwarta ba wai dan bata jin ɗaci da zafi bane a a sai ɗan wadatar zuciya da Ubangiji yai mata,nayi Imani da mahaliccina babu ranar da zata fito ta koma Aysher ba tayi tunanimmu ba ko kuma kewarmu, tabbas akwai ciwo ke kin rasa ƙafa da baƙi ita ta rasa idanuwa, kin san ma kuwa irin tsangwamar da take fuskanta a Al'umma da ita da yaranta ƙazafi babu wanda Aysher bata gani ba, kuma duk ina kallo amma babu halin taimaka mata abin na man zafi da ciwo yadda baki tunani, babu ranar da zata fito ban zubar da hawaye ba,amma a haka Mansura kullum ƙara godewa Ubangiji nake"Abbie ya ƙarashe da murmushi mai ciwo tunda yake zancen hawaye masu raɗaɗi da zafi ke biyo kuncinta tabbas ita tafi tausayin A'ishatu a kanta A'ishatu Ƴar uwa ta ɗauke ta ba a matsayin kishiya ba, tabbas tasan duk ɗaci da raɗaɗin da take ciki A'ishatu ta fita shiga cikinsa shin ita ya take ji? share hawayen tayi tana mai kawar da kanta haka shima Abbie bai ƙara magana ba kasancewar Abinda Ya tsaya masa a maƙoshi ga zuciyarsa dake wani harba masa da sauri_sauri daman ya san za'a rina domin duk lkcn da yai maganar A'ishatu haka ce take faruwa dashi, Anya zai iya wannan rayuwar tabbas zai karya Alqawarin daya ɗauka ya fito da gaskiya fili sannan ya fashe rufaffen ƙwan daya daɗe ba a ƙyanƙyasa sa ba sai dai komi zai faru ya faru koda kuwa hakan yana nufin zai rasa nasa numfashin ne ********************************* Alhamdulillahi anyi biki lafiya an ƙarashe lafiya inda Maheer ta zama matar Bobbi, ba ƙaramin farinciki Maheer ta tsinci kanta ba a lokacin da ta zama mallakin Bobbi sai dai zullumin ta ɗaya ne yadda zata sace zuciyar BOBBI ta tabbatar abu ne mai wahala sace zuciyar mutum kamar Bobbi ba ƙaramin kuka da dana sanin son maso wani Maheer tai ba a lokacin data kwana ɗaya bata ga Bobbi yazo gunta ba da niyyar raya wannan dare, ko wace Amarya na farinciki A daren farkon data kwana ɗakin mijinta amma ita sai tarin baƙin ciki da takaici ta ƙunsa tabbas ta shiryawa wannan rana domin fayyacewa Bobbi soyayyar da tayi mata mugun kamu tayi niyyar fayyace masa dukkan wani sirri na zuciyarta a daren farkon ta amma sai dai kash bata samu wanna ikon da damar ba kwance dake jikinta lulluɓe da blancked idanunwanta sunyi luhu_luhu saboda kukan data sha Nocking ɗin da taji anyi ne ya sakata miƙewa da ƙyar tana gyara gashinta "come in" ta furta a hankali, kanta a sunkuye ta ɗago tana duban Maheer tace "Am Hajiya tace ki sabko kici Abinci" fuskarta da ɗan murmushi tace "ok you can go" harta tafi kuma sai taji Yarinyar ta birgeta cikin ɗan ɗaga murya tace "Nace ba" ɗan juyowa tayi tana haɗiye abinda ya tsaya mata a maƙoshi tace "na'am" tana kallon Maheer wacce ke murmushi "Ya sunanki?" Maheer ta tambaya tana kallonta "Muneebba" ta furta ba tare data kalleta ba "wow nice Name you can to be my friend?" "Yes Mah" ta furta tana ƴar dariya, itama dariyar tayi "ok you can go pretty" ok ta furta tana fita tana mamakin halayen Maheer a farko ta saka zata yi girman kai da wulaƙanci amma sai taga saɓanin hakan, a yau da ta samu wacce ta ɗan sake mata fuska sai taji ta wata ta daban,duk damuwar da take ciki sai taji ta ɗan rage, amma sai dai idan tasan da cewar ita ɗin ko wacece ta tabbatar sai ta sauya mata ta musguna mata may be tama fi su Mom ƙuntata mata Dan ganin Mijinta take aure da wannan tunanin harta safka ƙasa ba tare dama tasan ta safka ba "ke!!!" taji daka tsawar Mom A hanzarce ta ɗago tana dubanta "na'am Mah" ta furta bakinta na kyarma, a wulaƙance Mom ta bita da kallo "gidan Uban wa zaki tafi? baki isar man da saƙon dana aikeki dashi ba" baki na rawa ta furta "Sorry Mah, tace gata nan sabkowa" taɓe baki tayi tana furta "da tsiya sai kinyi turanci kina ƴar matsiyata faƙiriya, maza zo yi Saving namu" dariya su Aunty Meera suka fashe da ita, sosai Muneebba taji ta muzanta da kalar cin mutuncin da sukai mata ga Mazan dake zaune waɗan da suke Binta da kallo hakan ya saka taji ta ƙara muzanta jiki ba ƙwari ta iso wajensu kamar ta fasa ihu, kallonsu ABEED yai yana ɓata rai "haba Mom miye laifinta za kuyi mata wannan cin mutuncin, shin shi talaka dan ya zama Silifas abin takawa? zakuna dinga mata cin mutuncin laifi ne dan tazo nema a karkashinku zaku wulaƙantata kunsan gaba yadda Ubangiji zaiyi daku ne, shin kun san kalar baiwa da ni'imar da Ubangiji zai mata nan gaba ne?" harara Mom ta zabga masa tana furta "to sannu Malam, wace baiwa Ubangiji yaiwa talaka idan banda baiwar faƙiranci kaga riƙe wa'azinka" shiru kawai yai yana danna wayarsa dan yasan ba zasu gane ba "Mom a kira Indo tai man Peppersoup" Zameer dake ida safkowa daga Step ɗin benen ya furta, hakan ya saka Muneebba ɗagowa tana dubansa "wow bala'in can Mom Ina kuka samu House maid balarabiya?" Zameer ya furta yana kafeta da ido, kawar da kanta ƙasa tayi taci gaba da yin Saving nasu, wata uwar harara Mom ta zabga masa "to na Mamajo sarki mata kai dai mace indai fara ce koda Mayya ce tana burgeka, ina ruwanka dama ko wace kala ce inda ƴar aiki ce" "To ita ƴar aikin ba mace bace?" ARYAN ya furta , Zameer ne yace "a to gane Mani hanya, ke Ƴar nan ban son naga farar mace balarabiya kamarki tana wahala ajiye na ida Saving nasu ni dai indai akan farar mace ne na zama bawa daga yanzu" "Alqur'an ban ga laifinka ba, dama baƙaƙen Ƴan aiki sunyi wa gidan nan yawa babu ƴan Farare" Afif ya furta yana dariya, dariya dukkansu saka saki harda shewa kamar wasu mata, Mom kuwa bata ƙara cewa ƙala ba, Maheer ce ta safko fuskarta wasai babu wanda zai kalleta yace ta sha kuka, a ladabce ta gaida Mom sannan taja kujera tana zama,dasu Aunty Meera suka gaisa a mutunce sannan su Zameer, Muneebba dake tsaye ta jawo Warmer tai saving ɗin Maheer "tnx pretty" Maheer ta furta da murmushi itama murmushin tayi tana ja baya ta tsaya, Tunda Zaidu ke sabkowa yake kallon Muneebba da kuma Mamakin abinda ya sakata sanya kayan House maid ya dai tabbatar wannan ɗin ita ce Matar Bobbi ba wata ba, Murmushin gefen baki ya saki yana kallon Muneebba, babu wan da yaiwa Magana,ya kalli Mom yana furta "Mom ki aika wannan House maid ɗin takai man Abinci a ɗakina" ya furta fuskarsa ɗaure tamau tsam Zameer ya miƙe yana jawo Warmer ɗin Abincin yace "Yah Zaidu bari na kai maka Alharam abinda za'a aikata kasan muna kare martabar Musulunci babu yadda za'ayi zuƙeƙiyar budurwa fara tas jinin larabawa taje kai maka Abinci a Bedroom".................. *Riamcool ce* [5/21, 8:18 PM] RIAMCOOL: *BAYAN WUYA* *Book 1* *By: RIAMCOOL* *MIKIYA WRITTER'S ASSOCIATION* *BISMILLAHIRRAHMANIRRAHIM* *P.37&38* Da wani kalar kallo Zaidu yabi Zameer yana tauna leɓe,basarwa yai yana ɗaga kafaɗa "ok kai man a ɗaki" Wata wahalalliyar Ajiyar zuciya Muneebba ta saki tana hamdala ga Ubangiji, "Mah an gama zan iya tafiya" ta tambaya bakinta na kyarma, wani banzan kallo Mom ta watsa mata tana faɗin "daman na riƙe maki ƙafafu ne na hanaki tafiya?" jiki a sanyaye ta fita tana matso hawayen da suka tarar mata a fuska, da wani kalar sheɗanin kallo Zaidu ya bita yana sakin murmushin gefen baki Koda ta fita kai tsaye Part ɗin da zai sada ta da ɗakin Bobbi ta nufa key ta zaro tana buɗe ɗakin, a hankali ta furzar da iskar bakinta tana sauke ajiyar zuciya kamar wacce tai gudun tseral, bisa ɗaya daga kujerun Falon ta samu tana zama tare da dafe kanta dake mata Azababben ciwo,ɗan kwanciya ta samu tayi ko taji sawaba nan take bacci mai masifar nauyi ya ɗauke ta ba ita ta samu ta farka ba sai wajen 1:30pm sannan ta fara buɗe lumsassun idanunta,a hankali ta ida ware su tana miƙa tare da furta Addu'a, wata irin zabura tayi tana miƙewa jikinta na kyarma ganin wanda ke cikin Falon yana dannan Laptop ɗin sa hankali kwance, "ina....wuni" ta furta a rarrabe cikin tsoro, ba tare da Bobbi ya ɗago ba ya furta "miye ya shigo dake ɗakina?" "gyara zanyi" ta furta tana matsa yatsun hannunta wanda wannan ya zame mata Al'ada cikin kallon tarin tsanar mace ya ɗago da fuskar sa yana dubanta fuska a haɗe tamau babu alamar sassauci ko rahama ya furta "daga yau bana buƙatar sake ganinki a koda sashen nan, kar ki ƙara shigo man ɗaki da niyyar gyara idan ba haka ba ranki zaiyi mummunan ɓaci" murya a can ƙasa ta furta "ok sir" tana jifanshi da kallon tsana wanda lokaci guda wata kalar muguwar tsanar Bobbi ta dirar mata a zuciya, cikin daka tsawa ya furta "miye na tsaya man a kai kina kallona maza fice man a Falo" ya faɗa kamar yai mata dan banzan duka A hanzarce ta fice ta fita daga side ɗin ma baki ɗaya, waje ta samu tana fashewa da kuka, ita shi kenan duniyar nan kowa ya tsaneta kowa ta raɓa sai ya nuna mata tsana, duniyar nan wane laifi ta aikatawa Mutane da har suke nuna mata tsana har haka? kuka taci sosai dan sai da taji kanta na neman tsagewa sannan tai shiru tana nufar famfan dake gefe ta wanke fuskarta, *Maheer* tun shigowar Bobbi Maheer ta gani hakan ya sakata shiga bathroom ta wanka sannan tazo ta cancanɗa uwar kwalliya kamar zata tafi gasar kyau, ƙara kallon kanta take jikinta sanye da rigar dakakkiyar Shadda Arsh color ɗinkin Straight gown wacce taji aiki da Ado sai walwali take gashi ba ƙaramin fito da ainahin hasken fatarta tayi ba da kuma surarta, wuyanta sanye da sarƙar Gold wacce keta walwali da sheƙi, jikinta tabi da manyan turaruka ta feshe shi, Agogon Diamond ta ɗauka tana ɗaurawa a haɗaɗɗen tsintsiyar hannunta, ba ƙaramin kyau tayi ba dan babu namijin da zai ganta bai ji wani abu a kanta ba, ƙayataccen murmushi ta saki, tana ficewa daga ɗakin nata, kai tsaye Part ɗin sa ta nufa gabanta na tsananta faɗuwa koda tazo kan ƙofar shiga ja tayi ta tsaya tana furta sunan Allah shahada tayi tai Nocking,ta ɗan jima tana yi kafin taji an furta "come in" A hankali ta tura ƙofar Falon kanta a sunkuye tana tafiya cikin nutsuwa da kuma birgewa, cikin ɗaya daga cikin kujerun Falon ta samu ta zauna tana kallon Bobbi kamar ta cinyesa, sun ɗauki tsawon lokaci babu wanda ya cewa wani ci kanka, ɗan ɗagowa yayi yana furta "mi ke tafe dake?" hawayen da take riƙewa ne suka samu damar zubo mata a kunci zuciyarta na mata zafi da ƙuna "Au haka ma zaka ce Yah BObbi? shin laifi ne dan kaso wanda zuciyarka ta Aminta dashi, dacewa ne Abin da ka aikata ace A daren farkommu baka ziyarceni ba,ina ga ko auren ƙiyayya mukai da kai bai kamata kai man haka ba akwai ciwo abinda ka aikata man" ta furta wani sabon kukan na sake kubce mata tun da take kukan Bobbi ke jifanta da wani kalar mugun kallo mai rikita wanda ake mawa, "yaushe mace ta samu damar da zata furta masa haka, yaushe mace ta samu zarran kallon ƙwayar idonsa harta furta masa haka, mace ita ce wacce yafi tsana a rayuwarsa, Abinda ya ɗauki Mace maƙaryaciya maci Amana muguwa kuma Azzaluma, makira, mace ce mafarin tarwatsa masa dukkan wani farin ciki, shi yasa bama zai taɓa bawa mace damar da zata furta masa koda kalma ɗaya bace" ya furta a zuciyarsa yana sake bin Maheer da kallon tsana tun da yake bin ta da kallon jikinta yai sanyi wani kalar tsoronsa da shakkarsa ta shigeta,ba tare daya tanka Mata ba ya miƙe yana tattara Laptop ɗinsa ya shige bedroom,da kallo ta bisa tana miƙewa itama fuskarta tayi jawur ɗan sai ta nutsuwarta tayi tana fita,kai tsaye wajen Mom ta nufa tana shiga Falon ta faɗa cinyar Mom tana fashewa da wani kalar sabon kukan, "Maheer mi ya faru" Mom ta tambaya hankalinta a tashe "Mom wallahi ba zan iya jurewa ba,Yah BObbi har yanzu bai damu dani ba,yanzu haka da naje wulaƙanci yai man" Maheer ta faɗa kamar zuciyarta zata faɗo ƙasa dan takaici da baƙin ciki "duk magana da nasihar da nayi Wa Bobbi bai ji ba, kiyi haƙuri Ƴata kiyi shiru Ni da kaina zan jawo hankalin Mijinki" Mom ta faɗa shiru tayi tana share hawaye "Amma Mom ai nasan ita waccan ba haka yake mata ba nice kawai baya ƙauna" kallonta Mom tayi tana furta "haba ita ɗin banza ita da ƴan aikin gidan nan ma sun fita gata da ƴanci kisha kuruminki ke ɗaya tal a wajen Bobbi babu kamarki Ni da kaina zan jawo maki hankalin mijinki sannan ita waccan na mayar da ita kwandon shara a gidan can dan har Abada bazan taɓa barin Bobbi saninta ba, Dan na mayar da ita cikin Ƴan Aiki ba zaki taɓa gane cewar Matar Bobbi bace" girgiza kanta Maheer tayi "Amma Mom kina ganin kin kyauta abinda kuka aikata itama fa Ƴa ce kamar ni" kallonta Mom tayi tana faɗin "Maheer ba zaki gane ba, nasan kin ga wacce na aika maki a ɗazun kizo kici Abinci, kinga kalarta kinga surarta wane Namiji ne zai ga wannan bai sota ba? bana son BObbi ya ganta ne ballantana harya faɗa tarkon sonta,gashi kin san ɗiyan talakawa da iya Asirce _Asirce" gaban Maheer ne ya faɗi jin cewar Muneebba ce Matar Bobbi, "Duk da haka Mom baki kyauta ba dan Allah ki cire ta a jerin ƴan aiki ni wallahi tun a ganina da ita na farko naji ta kwanta min a rai sannan zubinta da yanayinta ya bani tausai" kamar Mom ta rufe Maheer da duka haka take ji dan takaici "wallahi Maheer baki da hankali har yanzu baki hankali ba aka gaya miki ita kishiya abar tausayi ce to wallahi janza hali tun wuri" girgiza kai kawai Maheer tayi ta san da cewar tabbas Mom sunyi nisa ba zasu gane ba, hakan ya sakata miƙewa ta haura Up stairs, da kallo Mom ta bita kawai A haka rayuwar taci gaba da tafiya ba wani sauyi sannan a hankali Maheer ta din ga jawo Muneebba a jikinta, haka ɓangaren Zaidu kullum da baƙin ƙudiri akan Muneebba ya shiryawa Muneebba tarko kala_kala amma Allah na tseratad da ita, Tsaye take ɗakin Zaidu hankalinta duk ba'a kwance, ba dan babu yadda ta iya tun da Mom ce ta sakata gyaran ɗakin Zaidu, a hanzarce ta fara gudun karya zo ya sameta, tana kammalawa ta fito daga bedroom ɗin sai dai turus tai ta tsaya gabanta na tsananta faɗuwa ganin yadda Zaidu ya rufe ƙofar Falon key ɗin a hannunsa yana wasa dashi, wani yawu ta haɗiye tana tunkaro ƙofar da nufin buɗewa, hannu ta saka ta buɗe amma taji ƙofar ƙyam da ita a rufe, juyowa tayi tana faɗin "dan Allah ka taimaka ka buɗe" Murmushin gefen baki ya saki yana dubanta sama da kasa kafin ya taso yazo daf da ita har numfashnsu na haɗuwa ,Hijab ɗin dake jikinta ya cire "wow" ya furta lokacin da idanuwansa sukai arangama da manyan Boobs ɗin ta wanda suke cike tab a riga, ƙanƙame jikinta tayi tana rufewa, hawaye na biyo kuncinta,tana girgiza masa kai bakinta na rawa saboda tashin hankali " Kada ka keta man haddi ka dubi girman Allah ka ƙyaleni" shafa gefen bakinsa yai yana cire ƴar singlet din dake jikinsa ya rage daga shi sai Boxer, rufe idonta tayi tana kiran sunan Allah,jawota jikinsa yai yana ƙara ƙare mata, kallo yadda ko ina na jikinta ke cike ,wani yawu ya haɗiye yana kai hannunsa kan Manyan mazaunanta ya fara shafawa yana lumshe idanu,so take ta kufce amma ta kasa saboda riƙon da

Chapter 8 of 10