da zafi, daga baya kuma sai taga kamar abin koya fita daga ranshine, yanayin wannan hirar da take gani tsakanin mata, ita kuma inta siya tayi amfani dashi sai taga dai babu wani canji ta bangaren Baffa, saima ita da wasu magungunan zata ga kyansu, wasu kuma inta sha idan sun cika bauri ta wuni cikinta na murdawa. Sai kuma takeji kamar ta daina burgeshi yanzun, wannan soyayyar duk ta disashe. Amman duk da haka kai tsaye bai taba bude baki ya fada mata magana mai zafin ta yau ba. Idan ma gajiyar yayi to zai kyaleta ne ta shige jikinshi sosai ta kwanta.
Yanda gwiwoyinta sukayi mata sanyi yasa ta kasa tashi tabar masa dakin, zuciyarta ta dinga mata zafi, musmaman ma data ga ya juya kwanciyar shi yana matsawa ya bada tazara a tsakaninsu. Ta rufe idanuwanta da sukeyi mata yaji-yaji, bata kasance cikin mata masu saurin kuka ba, asalima abinda zai saka hawayenta zuba ba karami bane ba, ta dinga jero duk wata addu'a da tazo bakinta ko zata samu saukin zafin da kirjinta yakeyi, ashe bacci ne ya dauketa a haka, bata sani ba sai data fitsari ya tasheta tunda ta daddaki zobon da tayi babu laifi. Bataga alamar Baffa a kusa da ita ba, saita dauka ya shiga bayi, shisa ta nufi kofa ta bude da nufin tafiya dakinta, kuma har zata wuce saita dinga juyo karar kiran wayarshi daga falo.
Da mamaki ta nufi falon, yana kwance kan doguwar kujera yana bacci, ga wayar nan a kasa da alama subuce masa tayi bai sani ba, daman Baffa da bacci, sau nawa ko kiranshi akayi ita kiran saiya tasheta shi yana baccinshi. Ta karasa ta dauki wayar, sai dai tana dauka kiran na yankewa, zata ajiye masa a gefenshi sako ya shigo, kuma da yake ko a mukulli take zaka iya karanta sakon ta saman inka dan taba, haka kawai taji tanaso ta karanta, anyi saving din lambar da "AZ" kawai.
"Habibi bacci kayi ko? To bari in tashi inyi sallah in rokar mana Allaah Yasa next azumi kana gefena zakayi baccin nan"
Wani duhu-duhu ya nemi rufe mata ido, musamman da wani sakon ya kara shigowa
"Ina sonka sosai. Allaah Ya kulamun da kai Habibi Na, sai anjima In Shaa Allaah dan yau gara na kwana a zaune da in bari kayi dorere"
Daman haka kishin yake? Duk wanda take zato tanaji a baya karya ne, yanzun ne tasan yanda yake. To taya mata suke iya danne shi? Ya suke kallon mijinsu ya ketare ya tafi dakin wata matar batare da zuciyarsu ta kama da wuta ta kone ba? Ita gata, sako kawai tagani amman zuciyarta kamar tana gab da zama toka saboda yanda takejin tana ci da wuta. Sai gashi tanajin alamar hawaye suna neman zubo mata, ta ajiye masa wayarshi inda ta ganta a kasa, ta wuce dakinta da kudiri daya. In Shaa Allaah har a karasa azumi nan da kwanaki bakwai ko takwas ta gama tashin shi Sahur, ita AZ din saita tashe shi kafin azumi na gaba din da zasuyi tare saita dora daga inda ta tsaya a wannan din.
Yau ko dar bataji bama, dan daya shigo dakinta bankan-bankan lokacin ma da hijabinta a hannu
"Ke Jamila wai wanne irin abune ya sameki yau ma?"
Ya fadi bayan ya turo kofar
"Kasan goman karshen nan, sallah jima inayi, sai na dan kishingida sai yanzun na tashi naji anata kiraye-kirayen sallah, to alwala nayi ma yanzun nake shirin zuwa in tasheka"
Taji ranta yayi mata sanyi-sanyi ganin nashi ran a bace, a nutse tayi sallarta ta idar tana zaman Azkar. Tana idarwa ta koma tayi kwanciyarta.
*
Wajen Azahar tana zaune tana firar dankali, Nana kuma ta gama kukan faduwar da tayi da keken Arif ta buge bakinta har saida yayi jini, shine ta samu take baccin wahala, tayi mata shimfida anan tsakar gidan. Da yake gidan inka shigo gate, akwai wata yar haraba da har mota ma za'a iya parking dinta kuma a samu waje, sai ka kara shigowa wata kofa da zata hadaka da cikin gidan, daka shigo kofar akwai dan filin tsakar gida da ba wani girma ne dashi ba, daga gefe kitchen ne wadatacce anyi masa kanta mai kyau daga ciki, da yake itama ba wani tarkace ne da ita ba sai tsarin kitchen din yayi kyau. Akwai karamin bandaki a tsakar gidan, sai kuma wata kofa da inka shiga itace zata sadaka da falon Jamila, a cikin falon akwai daki daga hannun dama, inda ta mayar dashi dakin yaran, sai kuma daga hannun haggu dan dogon corridor ne da zai sadaka da dakuna guda biyu da suke kallon juna, daya na Jamila, dayan kuma na Baffa, kowanne daki kuma da bayi a ciki.
Tsarin gidan yayi kyau, dai-dai na masu rufin asiri. Sai dai yanda Baffa yake gaya mata tsarin saman ne yasa taji son wajen ya kara kamata, tunda yace a falon har wajen dining za'a fitar, sannan kuma kitchen a ciki za'ayi shi shima, ba kamar na kasan da yake a waje ba. Irin dai tsarin gidajen 'yan gayu. Abinda kawai take so da kasan shine tsakar gida, dan ita tanaso ta fito taga sararin samaniya lokaci zuwa lokaci, bawai kullum kana cikin daki ba. Har mamakin irin gidajen da basu da tsakar gida kwata-kwata takeyi.
"Mami waken duka zan tsince? Akwai yawa fa"
Asaad ya fadi cike da kosawa, tayi 'yar dariya. Shi Arif in dai akwai kallo tofa bashi da lokacin komai tunda yarone marar hayaniya, komai nashi da sanyi-sanyi yakeyi. Asaad kuwa irin yaran nan ne masu kulafacin uwa. Baiki duk inda tasa kafarta ya mayar da tashi ba, gashi da son aiki, shisa bata rasa abinda zata bashi ya tayata ko danma ya zauna waje daya
"Duka zaka tsince dan albarka, kayi maza kagama in baka ka dakamun maggi"
Aikuwa saiya kara maida hankali, dan yanason ta bashi dakan abu a karamin turminta, kwankwasa gidan da akayi yasa ta ajiye firar dankalin taje ta bude, tun daga kofar suka fara gaisawa da Rufaida. Wata mata guda daya da tun ranar da suka dawo unguwar suka fara mutunci saboda kirkinta, itama tace basu fi shekara biyu da dawowa unguwar ba, tana da yaranta hudu
"Dan Allaah ki taimako mun da flavor in kina da milk zansa a kunun aya, ragowar Intee ta mungular mun dashi"
Cewar Rufaida bayan sun gaisa da Jamila
"Allaah Ya shirya mana yaran nan, gashi kai ba abin ka jibgi kudinka ba"
Kai Rufaida ta jinjina
"Inka biye musu ai karyasu zakayi 'yan albarkar"
Daki Jamila ta shiga tana barin Rufaida da Asaad da yake gaishe da ita, tunda dan karamin firij din nata a falo yake, data ajiye shi nan tsakar gida rana ta hanashi abin kirki, a kitchen kuma ya cike mata waje, saita mayar dashi falo tayi masa waje tunda falon wadatacce ne. Data fito ta kawo mata ne take ce mata
"Kinga wata gumba ce aka kawomun naji dadinta wallahi, kin aiko Arif ya karbar miki na manta dana fito miki da ita"
Tabe baki Jamila tayi
"Dan Allaah ki rabani da 'yan shaye-shayen nan ina azumina"
Hararta Rufaida tayi
"Wannan gumbar yanda kikasan kina shan madara da kantu haka zakijita, kefa mazan yanzun saida gyara"
Yanayin fuskar Jamila dai inka gani kasan yau zancen bai zauna mata ba sam, saima yake tuno mata da wulakancin da Baffa yayi mata jiya
"Wannan duk baya hanasu karo aurensu insun tashi"
Dariya Rufaida tayi sosai
"Allaah Ya shiryaki wallahi, to ke ina ruwanki da karo aurenshi? Daman ai bawai zaki gyara bane dan karya karo aure, a'a taki mafitar zaki duba, ki gyara dan ki samu naki matsayin a wajen shi, in kika tsaya wallahi 'yan matan nan na yanzun da suke da ido a tsakar kai sai su sa kwabarki tayi ruwa"
Dan jim Jamila tayi tana tauna maganganun Rufaida din, wata irin shakuwa ce ta shiga tsakaninsu kamar sunyi shekaru tare, dan Jamila zatace ita dai a yanzun bata da kawa kamar Rufaida, kuma sukan tattauna matsalolin da ba'a rasa duk wata mace dashi, musamman ta maza, su ba juna shawara
"Hmmm..."
Jamila ta iya fadi, kuma yanayinta yasa Rufaida ta fahimci cewa tana da damuwar da bataso ta fito fili ta fadi
"Karki yarda ki bar mijinki a hannun wata, musamman ma yarinyar da duk wani feleqe da takeyi kokarinta ta taddoki ne, kibari inta shigo sai kiyi lokacinta, amman yanzun kam ki kara rike mijinki"
Haka Rufaida ta dinga bata shawarwari kala-kala har saida taga tana aminta da maganganunta, ta kuma kira Arif tace ya bita ya karbo mata gumbar. Rufaida na fita bata jima ba, dan dawowar Arif kenan shima ya ruga daki dan ya cigaba da kallon shi, taji wayarta na ringing, ta dauka tunda tana nan ajiye a kusa da ita. Baffa ne, ta daga tasa a kunne hadi dayin sallama
"Mamin yara"
Ya fadi daga dayan bangaren yanasa tayi murmushi, kafin kuma ta amsa ya dora da
"Daman zanji ya kuka wuni ne? Ina yaran? Kinata aiki halan?"
Sai taji wani sanyi ya ratsa zuciyarta, akace abubuwan da mata suke so daga wajen mazajensu ba masu yawa bane ba, kulawa komin kankantarta na daga cikin wannan abubuwan, ta manta rabon da haka kawai Baffa ya kirata a waya. In kuwa ya kira to sako zai bata, ayi masa wani abin, ko ita ta kirashi suna bukatar wani abu, da takan kira inya tafi dan taji ya ya isa shagon sai yace mata
"Daman shikenan abinda zaki fada? Kai kema dai kina da rigima, sai kace wanda zai bace a hanya"
Irin wannan sage gwiwar da yakeyi mata kan abubuwa da yawa yasa ta hakura ta yakicewa kanta yi masa su tunda basa burgeshi. Ko kuma ita dince ta daina burgeshi ba zata iya cewa ba
"Bama aikin da nakeyi, dankali ne nake ferewa"
Ta fadi muryarta cike da annashuwa
"Akwai saura ne har yanzun? Ko in bada a karo sai a kawo muku?"
Kai ta girgiza tanata murmushi
"Akwai fa, kasan shi saurin lalacewa yakeyi, kuma azumin ma yazo gangara"
Tunda ita dankalinma baya cikin abubuwan da suke burgeta, saita soya shi sau nawa bataci ba
"To shikenan, kinga dinkunan nan da yawa, daman ince miki karki wahalar da kanki yau ba zan dawo gida da wuri ba, mun nemi wani abin muci anan. Kiyi abinci mai sauki kawai na sahur"
Lokaci daya taji wani abu ya haska cikin kanta
"Me kake so a dafa maka?"
Dariya yayi
"Kome kika dafa ai kinsan zanci"
Saita jinjina kai
"Zan dan fita anjima to tunda ba zaka dawo da wuri ba"
Dariyar ya sakeyi
"Kafarki ce take kaikayi daman, Allaah Ya tsare, ki dauki dubu biyu a dakina inda nake ajiye kudi saikiyi kudin mota..."
Ta fara jera masa godiya
"Wai ina ma zakije matar nan?"
Saita kama dariya
"Badai kace kabarni ba?"
Shima dariyar yakeyi
"Bazan biye miki ba, bari inyi aikina koma ina ne a dawo lafiya. Ki kula da kanki dai, kar kuma ki dade"
Ta jinjina kai, saida tasa hannu tana share wata yar kwallar farin ciki, yaushe rabon data jita cikin nishadi haka? Yaushe rabon da Baffa ya biye mata suyi hira cike da kulawa irin wannan? Harta manta, waya kuwa ko history ta duba na shekara daya basuyi wayar data wuce yan sakanni ba dashi, tunda yana gama fadar abinda zai fada yake kashewa batare ma daya jira tace wani abu ba, hira kuwa tunda ya gane mayi da 'yan matanshi inya dawo ta yanke a tsakaninsu, saita kirga magana nawa take hadasu inya dawo gidan kafin su kwanta.
"Asaad ajiye tsintar waken nan haka..."
Tace tana tsame hannunta daga cikin dankalik ta tafi ta dibo cefane ta hau gyarawa, bayan ta wankesu, ta dauko wani kwali da busashen kifi yake a ciki, Yayanta Kabiru ne ya kawo musu tsarabar shi daga Jos inda yake aiki, da yawa ta diba ta zuba a wata tukunya ta yanka albasa ta zuba citta da tafarnuwa, dan Allaah Yayita da jin karni matuqa, in zatayi amfani da kifin saita fara tafasa shi haka ta zubar da ruwan, tukunna ta zauna ta gyara shi ta cire kan da kaya. Cikin wani lokaci sai gashi ta gama miyarta mai yawa. Yau kam yanda ya faranta mata rai, itama saita faranta mishi.
Zata bashi mamaki, kayan buda baki zataje ta kai masa har shago, yaran shagon nashi ma sai bakinsu ya canza yau, ba zata bari yanda baiyi sahur ba, yayi buda baki a wahale. Shinkafa da miyar kifin zatayi, ta soya dankalin da wainar kwai, sai ta hada musu lemon citta, ta sauko wasu kulolinta da bata taba amfani dasu ba, a ciki zata shirya komai, haka wasu filet dinta masu kyau ta dauraye, ta fiddo robobin da taketa boyo don irin haka, Rufaida ce ta bata su guda goma, design dinsu yayi kyau matuka, shisa ma ta adana, yau ga ranar amfani dasu tazo, shawarwarin Rufaida na dazun suka dinga mata shawagi
Haka kawai da zata biyewa zuciyarta da bakin kishi taje ta illata mijinta, a yanzun dai in wani abin ya same shi ai ita da yaranta sune da asara ba AZ din ba
Sai dai a lokacin da Jamila take aikinta cike da nishadi da son farantawa Baffa
Haka a gefe daya Baffa yake cikin nishadi da dokin ganin Magriba tayi dan yaje yaga abinda Aziza take ta fadin ta tanadar masa...!
#LubnaSufyan ✨
#WomenOfWords
#09035723778
Littafin nan na kudine akan #1k kacal, zaizo a manhajar Telegram 10/12/2024 In Shaa Allaah, bayan mun kammala shafukan dandano.
9035723778
Opay
Lubabatu Sufyan
Saika turo shaidar biya ta lambar da take sama. Nagode da addu'a'inku, nagode kuma da kwarin gwiwar da bakwa gajiya da bani
*
Duka littafin nan sadaukarwa ne ga Marubuciya Aisha Shafi'i, idan kunci karo da littafin nan, kun nishadantu, kun karu ta kowacce irin fuska, ku rokawa mijinta Isma'il Rahmar Allaah, ku roka mata sauki da juriyar rashin shi, ku rokawa yarinyarta rayuwa mai albarka. Nagode
********************** **************************
********** Ai Hausa Novels ****************
************************* **********************
DOWNLOAD More complete Hausa Novels, Education Books, Adventure, Drama, Mystery, Religion, Fiction, Non-Fiction, Romance, Meimor, True Life Stories & Others from our blog.
Visit > https://www.aihausanovels.com.ng
Ka tura mana sako ta adireshinmu na email, domin tuntubarmu ko turo mana hausa novel ko kuma post.
Email > aihausabooks@gmail.com
******* FOLLOW US ******
Facebook: Ai Hausa Novels
Twitter: Ai Hausa Novels
Telegram Channel: https://t.me/Aihausanovels
WhatsApp Number: 08138873799
Haka kuma domin shiga kowanne daga cikinsu za ku iya ziyartar shafinmu ku yi search na AI HAUSA NOVELS, hatta facebook group dinmu ma za ku samu.
********************** **************************
*************** Ai Hausa Novels ****************
********************** **************************
MATAR HABIBI
3
(Free page)
Wannan shagon na yanzun, guda biyu ne ya siya, da 'yar karamar plaza ce, akace mai ita ya rasu, to cikin yaran bayan an raba gado sai wasu suka siyar da nasu kason, wajene mai kyau, kuma a bakin hanya. Bayan ya siya a hankali saiya rushe katangar data raba shagunan, aiki yayi masa sosai, kusan duk wani tari daya dingayi da nufin siyan mota a wajen gyaran shagon suka tafi. Aka fadada shi, akayi musu dan karamin bandaki a ciki, saboda yaran shagon nashi idan aiki ya kacame musu, sukan kwana, da yake Baffa mutum ne mai tsantsani, bayason amfani da bandakunan plaza din sam.
Har yar doguwar kujera aka saka a cikin shagon daga gefe. Da shigar kananun kaya ya fito daga gida, sai kawai cikin yaran shagon nashi, Isma'il da yanzun zaice ma yana neman finshi kwarewa a harkar dinkin nasu na maza, gashi shi harda na mata ma yakeyi, ya dauko masa yadin daya manta ya siye shi yana fadin
"Oga Baffa nafa gama maka dinkin nan"
Ya karba, yadine ruwan toka mai duhu, irin masu laushin nan, ba wani abu akayi a jikin dinkin ba, amman yayi kyau matuqa, hannun dogo mai links, sai maballai a jiki, yasha guga, sai kamshin turaren sa Isma'il din yake amfani dasu a jikin duk wani kaya da zai dinka sukeyi, sai yaji ai wannan kayan sune ma yakamata ace ya saka anjima in zaije wajen Aziza. Haka kuwa akayi, yana ganin shida tayi ya shiga bandakin nan, yayi amfani da soso da sabulun da suke dashi ya kara wanke kafafuwanshi da babu abinda sukayi, har fuska ya wanke, inda ace shi din ba kumama bane ba wanka zai karayi, to komin zafin da akeyi saiya sirka ruwa yake iya wanka. Haka ya dauki mai da yake ajiye a saman wata yar shelf din katako da akayi, ya murza a hannuwanshi da kuma kafafuwa, sauran ya murza fuska, ya daura alwala, tukunna ya dauki kayan ya saka a cikin bayin
Yana fitowa ana fara kiran sallar magriba, Usman ya mika masa ruwa mai sanyi da dabino, yayi Bismillah ya fara cin dabinon tukunna yasha ruwan
"Oga Allaah dai yasa ba zance zakaje ba, irin wannan shan wanka da magribar nan"
Cewar Rabi'u dayake mikewa daga kan kekenshi
"Kaga wani sa'ido ko?"
Baffa ya fadi yana murmushi
"Da gaskiyarshi fa Oga, ba zamu bari a hada baki damu ayiwa Maman Arif haka ba, kai Isma'il kaine kayi dinkin nan, kamar a kunnenta"
Dariya Isma'il yayi yana daga hannuwa sama alamar saranda
"Ku rufamun asiri, ni na dauka ma cikin kayan sallah ne wallahi"
Kai kawai Baffa ya jinjina
"Wato dai in na lura daku, kamar bayan Jamila zakubi"
A tare suka hada baki suka amsa, ciki kuwa harda Abbati da bai cika magana ba, dan shi saida ya dora da
"Nan Madam take shaqaro kuloli da abinci ana aiko mana, so kakeyi a janye mana tallafi?"
Maganar taba Baffa dariya sosai
"Ni sallah zanje, ku kuka sani"
Suma sallar suka wuce bayan sun rufe shagon, da yake akwai masallaci a nan gefensu. Ana idarwa Baffa ya fadawa Usman akwai inda zashi, in dai wani abin ya taso sai su kirashi a waya, ya dauki mashin dinshi bayan ya turawa Aziza sakon cewa yana hanya, sai lokacin ma ya kula da cajin wayarshi saura 2%. Tunda yaje shago da safe bai sakata a caji ba, daman kuma jiyama haka bacci ya dauke shi da dare suna chatting da Aziza bayan wayar da suka sha, wayar da itace ma tasa shi ya barowa Jamila dakin nashi ya dawo falo. Addu'a yakeyi kar wani ya kirashi wayar ta mutu kafin ya karasa, dan bayason saiya nemi wanda zai aika a kira masa Aziza, gara dai ya kirata a waya.
A ranshi ya dinga zabga tsaki, shifa abinda ya tsana da unguwar nan ta Rijiyar Lemo kenan, musamman wannan layin 'yan chanan, kamar babu layin daya kaishi yawan kwatoci, jiyan nan ya bada aka wanke masa mashin dinshi tas, wani lokacin har mamakin yanda za'ace yarinya kamar Aziza tana irin wannan unguwar yakeyi. Ko a cikin layin nasu ma gidansu ne kadai mai katoton gate. Sai dai bayan ya karasa, ya samu waje a gefe yayi parking din mashin dinshi yana kara kallon unguwar tasu, cike da mutane anata hada-hada, ga masu awara nan da dankali waje-waje, an zagaye su layi danqam. Baiyi mintina uku ba Aziza ta fito, kamshin da take zabgawa ya wanke masa duk wani takaicin bata mashin dinshi da yayi.
Daya kalleta kuwa saida ya tsinci kanshi da rokon Allaah daya hore masa halin karasa gininshi ko zai samu ya mallaki Aziza kafin wani yazo yayi masa shigar sauri, bakinta daya sha jambaki ja ya kara fito masa da hasken fatarta tar da kwan lantarki ya haske masa kamar don shi aka bar wuta
"Kinyi kyau"
Ya fadi yana mata murmushi, ta danyi far da ido kafin ta saukesu cikin kunya
"Zaka fara ko Habibi?"
Yanayin yanda tayi maganar yaji duk ya susuce, shifa wannan abubuwan, yanayin yanda take lankwasa murya in zatayi magana, 'yar shagwabar da takeyi masa, kwarkwasar nan, sai yaita kallon Jamila yana tunanin yanda akayi tun farko bai taba kula bata da wannan abubuwan ba, ya dinga zurfafa tunani, daman ko lokacin kafin suyi aure haka take? Ko kuma daga bayane ta canza tunda tanajin aita same shi bata bukatar ta dinga yi masa irin wannan abubuwan
"Kazo mu karasa ciki"
Cewar Aziza, bai kuma yi mata musu ba, yau ma kamar duk zuwan da zaiyi, ya shiga tunanin yanda za'ayi a shiga da mota gidan nasu Aziza. Inka shiga karamar kofar jikin gate din, baifi kayi taku hudu ba zaka samu katanga data raba gate din da cikin gidan nasu, sai kuma wata kofa da ba'a sakawa kyaure bama, nan zaka shiga, wani dan surkukin soro ne da su biyu ma in suka tsaya shi da Aziza a ciki tsaf yan hisba zasu samu sabon case, sai dai suji ana tambayar lambar wayar iyayensu, don da wahala jikinsu ba zai gogi na juna ba saboda kankantar shi, a gefe kofa ce da take a rufe, bai taba ganinta a bude ba, sai kuma dayar kofar da zata sadaka da wadataccen falon da suke zama suna zance a ciki.
Aziza ce a gaba yana biye da ita, tun daga bakin kofar kamshin turaren wuta yayi masa sallama kamar ya shiga Maiduguri. Yaji wani sanyi na ratsa shi, kasala da gajiya duk suka rufar masa, suna kara tuna masa da ya kamata shima yasa AC a gidanshi, ko da iya dakinshi ne kuwa. Ya zauna a daya daga cikin kujerun dakin da sallama a bakinshi yana ba Aziza dariya duk da ta amsa, ta dora da
"Ina wuni, an sha ruwa lafiya? Ya aiki?"
Ya sauke numfashi yana amsawa, hankalin shi yana kan kwanonin da aka shirya a tsakar dakin, bawai abinda ke ciki yake hasashe ba, kwanonin ne sukayi masa kyau matuka, dan bai taba ganin irinsu ba. Aziza ta sauko ta fara budewa, kamshi ya cika hancin shi, saida ta mike ta dauko wata darduma mai kyau, tukunna ta shimfida masa tana fadin
"Ka sauko Habibi, nasan bakaci komai ba"
Saukowar yayi ya zauna, yana kallon fararen yatsunta da jan lalle a jikin faratan, yayi saurin maida idanuwanshi kan farantin yana jan Istigfari saboda tunanin da yake neman kutso masa cikin kai
"Kice mun ba wahalar da kanki kikayi ba kika sake shirya wani abin, ai nace jiya ki sakamun a firij"
Saboda shifa wannan tortilla din data kirane a ranshi har yanzun, so yake kawai yaga daga inda zata bullo
"Ya zanyi dakai tunda baka zo ba? Kuma kasan Mummy ma zatayi mun fada tace ya za'ayi in baka abincin jiya"
Ta fara mika masa wani dan karamin kwano da wani abu a cikin narkakke da dan barbadin wani ganye-ganye a ciki. Ya karba yana kura masa ido na dan sakanni kafin ya duba sauran tarkacen da take ta kiciniyar dibar masa, shi dai baiga biredi ba, abinda yake hannun shi kuma yayi masa kama da butter
"Nasanka da son dankali, gashi anci maiko tunda azumi ne shine nace gara inyi maka mashed..."
Yaji kalmar, kuma yasan turanci ne, a dan abinda yakeji dai ya kasa fassara shi balle hadinshi da abinda yake hannunshi, ya dai karbi cokalin da ta mika masa ya dibo yana kaiwa bakinshi da Bismillah, ba don korar shaidan ba, don neman sa'a kar bakinshi ya kunyata shi yaki karbar wannan abin. Hakan kuwa ya faru, shi dai yaji galmi-galmi, amman baiyi masa yanayi da abinda zai iya ci ba. A yunwar da yakeji ai gara ma ta bashi kunu akan wannan mashed abin. Gudun karya bada kanshi ya dinga turawa yana hadiyewa yana rokon Allaah Ya kiyaye shi da bacin ciki, saboda cikinshi bai cika son bakon abu ba. Har wani numfashi ya sauke lokacin daya ajiye dan kwanon ta bashi filet
"Bari inzo Habibi, dan Allaah ka cinye komai"
Cewar Aziza tana tashi, yaji dadin bashi wajen da tayi, tana ficewa kan tsiren da yake ciki ya fara, yayi masa dadi sosai, yaso ace shine yafi komai yawa, sai kuma yaci samosa da spring rolls, shima sunyi masa fiye ma da tsiren, kamar ya bude sauran kwanonin ya kara haka yakeji, ya dauki lemon data tsiyaya masa ya kurba, akwai sanyi, amman dai bai gane ma dandanon lemon ba, yayi masa wani daci-daci saiya ajiye
"Sufa 'yan gayu harshensu ma kamar daban yake dana sauran mutane"
Ya raya ma ranshi, yanata barin abinda yake tunanin yamballs ne daga karshe saboda soyayyar da take tsakaninsu, idan Jamila tayi wuni yake yana ci, ya kudurce a ranshi zai siyi doya gobe tunda ta fada masa sauranta ne ta soya musu jiya, ya dan ajiye filet din yana, daya dauka dai sai yaji shi sakat a hannunshi, gashi da girma, amman baiyi masa nauyi kamar yanda ya sani ba. Sannan daya kalla da kyau ma, bayan abin kamar ba kwai bane ba, yadai yi kyan suya, sai kawai ya jefa shi a baki duka yana taunawa. Sai yaji kamar kubewa ce a tsakiyar, gabaki daya komai