Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
3 / 5
mummunar ak'ida. Shidai Alh Sani k'ani ne ga Mahaifin Alh Mubarak, wanda akafi sani Liti kulkul ko kuma Liti Brothers. *WAYE ALH MUBARร€K* Sunanshi na gaskiya Mubarak Muhammad Amman anfi kiransa da Dan Liti, ya taso cikin gata, gaba da baya, kasancewar sa shi kadai ne gurin iyayensa Hajiya A'isha dakuma Alh Muhammad Dan Maliki, amman duk da haka idan yayi badai-dai yana gane kurensa, wannan ne yasa yazama abin alfahari sbd nutsuwar sa dakuma hankalinsa yana da farin jini kwarai da gaske sbd kowa nashine ba ruwanshi da kyamar talaka da wasu masu kudin keyi. Wannan halayya tashice kesawa mutane suji suna son shi. Wann kenn...... Alh dan Maliki ne ya gida katon gida wanda za'a iya kiransa da Aljannar duniya duba da yanda ya kawatu matuk'a gaya, part biyu ne a gidan cikin gidan, nashi da na kaninshi Alh Sani, bayan ankammala gidanne Alh Dan Maliki ya bukaci kanin nashi daya baro wnn gidan ya dawo nasu haka kuwa akayi inda yayi biyayya kamr yanda iyayensu kamin su rasu suka bammasu wasiyya. Basu dade da dawowa ba ALLAH yabawa Hajiya A'isha haihuwa, inda ta haifi kyakywan danta namiji, Alh Dan Maliki yayi murna matuk'a da gaske, inda sbd dadin wnn haihuwa ya bawa mutane 15 kyautar kujerar hajji. *7days ago* Yaro yaci suna Mubarak, an bannatar da dukiya tamkar ba'aso, mutane koh wadanda aka gayyata da wadand ba'a gayyata bama zuwa suke kawai domin su kashe kwar-kwatar idanunsu, anci ansha anyi hani'an dan wasu muatanen ma harda spoon suka zo kai wani abun dariya harda masu zuwa da leda yadda idan sunyi ragowa saii su juye su tafi dashi gida lols. Wani abu daya tsaya wa Hjy A'isha arai shine duk da suna gida daya tare da Facalar ta wato {Hjy Hasfat} amman hakan baisa tazo mata barka ba, ta ayyana a ranta anya kuwa lpa?, a ranta tace "bari in ALLAH ya kaimu gobe naje na dubota" Bayan Mijinta Dan Maliki ya fita ne itama ta fice, ta tunkari part din Hjy Hafsat, tura kofar tayi da sallama a bakinta. Hjy Hafsat ta amsa sallamar fuskar nan a murtuke, ganin ba walwala a tare da itane yasa Hjy Aisha tace "Wai niko Hafsat ko baki da lpa ne naga kamar kina cikin damuwa?" "Eh kawai tace mata ta kauda kai" tamkar wadda taga kashi, haka Aisha tagama tsayuwar ta, tashi tayi tabar part din, ta nufi nata part din cike da tunanin cewa kishi take da ita sbd ALLAH ya bata haihuwa ita kuma babu. *5years Ago* Tun daga wannan ranar Aisha bata sake zuwa part din Hafsat ba itama Hafsat din bata kara zuwa na Aishar ba. Ana cikin wannan zaman ne irin na 'yan marina, itama Hafsat din ALLAH ya bata haihuwa inda ta haifi santaleliyar yarta mace Masha ALLAH, zokaga rawar kai wajen Hafsat domin daman akwaishi ballanta yanzu anga ansamu magajiya. Ran suna aka rada wa yarinya suna Rahila amman ana kiranta da suna "Lami" kasancewar sunn mahaifiyar Hafsat kenn. Tun ranr da aka haifi Rahila, Alh Sani yaje ya shaidawa yayan nasa, sanan ya sanar da yaya nasa cewa "Nifa yayi wa Lami miji" Alh Dan Maliki ya kalli kanin nasa yace "Ban gane inda kadosa ba?" Alh Sani yace "ina nufin na bawa d'ana Mubarak yar ka Rahila" Dan Maliki yayi murmushi yace amman gaskiya naji dadi wannan magana taka, fatanmu ALLAH ya hade kanmu danasu baki daya ya nuna mana lokacin. Alh sani yace "Ameen summ Ameen" Toh duk cikin su biyun babu wanda ya sanar wa da matarshi abunda suka yanke, kawai dai sun bar abun a zuciyarsu ne. *10 years Ago* Nifa wlh Ammi na gaji kullum waccan yar iskar yarinyar saita b'ata mani lokaci, kuma wlh Ancle's dinmu basu da mutunci duka suke mani amman banda ita inaga ma shiyasa take jawa muna latti sbd ita ba'a dukanta ya karasa maganar ta k'wata. Ammi tace Son hakuri zakayi wata rana sai labari kaida saurama shekara d'aya ma ka kammala, kumama ai naga kanwar kace, bai kamata kana zagin ta ba daga yau karna karajin ka zagi wani, babu kyau kaji koh?" Yace "Eh ammi" daman ya saka uniform dinsa ya dauko school bag dinshi ya rataya yace "Ammi na tafi" tace "ALLAH ya dawo daku lpa son" yace "Ameen Ammi" ya fice daga part din nasu zuwa parkin space. Yana karasawa yace wa Musa driver "Baba wai haryanzu bata fitoba?" Cike da kulawa Mal musa yace "Wlh kuwa d'ana haryanzu" Duba agogon dake hannunsa yayi *8:05am* ya nuna masa wani dogon tsaki yaja mtswwww..... Yace "Wlh yau nasan zan daku wajen Ancle Ema aiko wlh sai na rama akanta" duk wadannan maganganun acikin zuciyarsa yake sakasu, suna nan tsaye sai gata ta fito daga part din nasu itama cikin school uniform iri daya dana jikin Mubarak din, tana tafiya a hankali kai kace tana tausayin kasa tana wani karairaya duk da kwata-kwata bata wuce sheka 12 ba, amman idan kaga yanda ta iya kissa da kisisina kace yar shekara 20 da doriya ce. Wnn abunne ya kara bak'anta wa Mubarak rai yaji ya kara tsanar ta fiye da koyaushe, tana karasowa ya bude gaban mota yashiga, itama ta kama murfin kofar tana kokarin budewa, wata uwar tsawa daya daka matane yasa tayi saurin sakin kofar, ta bude ta baya tashiga tana share yar kwallar dake bin kumatunta, sbd ta saba idan za'a kaisu school a baya suke zama shida ita amman yau ya gujeta. Shidai Musa driver baice k'ala ba ya shiga mota ya tada ya fice da matsiyacin gudu, sbd har ga ALLAH bayason yaga abinda zai b'ata ran Mubarak. Suna isa bakin kofar school din Mubarak ya fito daga cikin motar yayi gaba bai kara bi ko takanta ba, saidai Mal. Musa ne ya fito da Lami daga cikin mota sai kuka take tana fadi yaya kadawo ka daukeni....... Tana cikin kukan ne wani Malami Mai suna Ancle Musaddiq ya leko aiko ya hangota tana birgima akan floor, fitowa yayi yaymata cancak ya shiga da ita cikin makaranta. Bayan an tashi daga makaranta ne, Mal. Musa yazo daukarsu yanzummadai Mubarak gidan gaba ya bude ya shige, itama kuwa ta kama murfin kofar ala dole saita shiga gaba, ran Mubarak yay matukar b'aci ai baisan lokacin daya bude motarba ya dauketa da wani lafiyeyyen mariba, abunka da farar fata nan da nan fuskar nan ta kunbura tayi jajir, yayin da ta fashe da kuka ta runtuma a kasa sai birgima take, da kyar da sidin goshi Mal. Musa ya sakata a mota ya tayr da mota suka aisa gida, bude yayi ya fice cike da k'unar zuciya. Itama bud'e motar tayi ta fice da gudu zuwa part dinsu tana kuka..... Shiga tayi cikin falon tana kara sautin kukan nata, Momy ce ta karaso da sauri ta tareta tace "Momyn waya dakarmin ke?" tace "Yaya Mubarak ne" Kutumar uba can shi mubarak din ya dakeki? Toh wlh bazan yarda ba, bari naje naji uban waye ya daure mashi gindin ya dinga dukanki sai kace ya samu jaka. Ta fice ta nufi bangaren su mubarak, ai tana shiga ta fara tijara saida tayi mai isarta sannan ta fito, itadai Ammi ko ci kanki bata ce mata ba dan idan dasabo ta saba da cin mutuncin Hafsat. A haka dai har Mubarak ya kammala Secondry school dinshi inda result dinsa yayi kyau sosai sbd haka Dadynsa ya nemar masa admission a England. Ranar da zai tafi Lami tasha kuka wai ita sai ta bishi abin ya b'ata wa Momynta Rai sbd haka ta zaneta, sbd ita ta tsani Mubarak, haka iyayensaa suka rakashi har Airport din Mal. Aminu Kano a gaban idansu jirginsu ya tashi, suka dawo cike da Alhinin rashin tilaudin dansu, Wannan kenn,,, *5years Ago* Lami ce tsaye gaban momyta sai zabga mata shagwab'a take yi tace "Momy na wlh ni bazanci wannan abicin ba ni kawai a siyo mani Shawarma tana maganar tana bubbuga k'afarta akan floor din, Momy dake kallon TV tace ta juyo cike da kulawa tace "Maza jeki cikin drower ta ki dauko mani hand bag dita" juyawa tayi da sauri don dauko jakar, bayan ta dauko jakar ne ta kawo ma Momy tata jakar, budewa Momy tayi ta dauko kudi ta bata tace "ungo jeki kikai wa Musa driver kice ya siyo maki kinji koh?" Ta karbi kudin ta manna wa momy kiss a kumatu tace "Nagode momyna ina alfahari dake momy" ta fice da gudu tamkar zata tashi sama, bata zame koh ina ba sai parking space, ind ta tarar da Musa mai gadi yana goge mota yana ganinta ya fara washe baki yana cewa "Ahh! Hjy karama barka da fitowa" Ko kallon kirki bata yimasa ba kawai watsa mata kudin dake hannunta tayi tace "kasiyo mani Shawarma" ta juya. Kallonta yayi yana mamakin hali irin na masu kudi, yace "A zuciyarsa yannzu kenn indai kai talaka ne baka da wani mutunci a wajen jama'a, kai! ALLAH Yayi mana muwafak'a da wannan batu nasa ya shiga mota ya fice don zuwa ya siyo abunda Lami ta Aikesa. A bangaren Mubarak kuwa England ta karb'eshi, ya zama saurayi hadadden gaye kalar gayun da yan mata ke so, ahalin yanzu ya kammala degree dinsa na farko a fannin Accounting yau ake saran dirarsa Kasa Nigeria sbd haka Ammi sai shige da fice take sbd son din nata yace mata bayason cin abincin yan aiki shi nata yake da muradin ci. *Abubakar Saleh Al~Quyraemey* _(young writer)_ [6:19AM, 6/7/2019] Abue Saleh Al~Quyraemey: https://m.facebook.com/Zamaniwritesassociation? ๏ปฟ *DUK GIRMAN GONA!!!* _{Akwai kunyar 'karshe}_ ยฉ2019 *A mystery story just keep on following me.* ๐Ÿ‘จ๐Ÿปโ€๐Ÿ’ป๐Ÿ‘ฉ๐Ÿปโ€๐Ÿ’ป *ZAMANI WRITERS ASSOCIATION* _____________________________________ โ€‹โ€‹Wษ› ษ‘ส€ษ› ษฆษ›ส€ษ› tัณ ษ›ษ—ucษ‘tษ›, Mัณtiัตษ‘tษ› ษ‘ษณษ— ษ›ษณtษ›ส€tษ‘iษณ ัณuส€ ส€ษ›ษ‘ษ—ษ›ส€เธฃโ€‹. _____________________________________ *๐Ÿ‘‰๐ŸผPage 13-14* *Author.......๐Ÿ–‹* *Abubakar Saleh Quyraemey* ```@Facebook Abubakar Saleh AlQuyraemey``` *DEDICATED TO* *Zamani Writers Association Group* _Happy sallah to all Muslim_ ุจูุณู’ู€ู€ู€ู€ู€ู€ู€ู€ู€ู€ู€ู€ู€ู€ู€ู€ู€ู€ู€ู€ู€ู€ู…ู ุงูŽู„ู„ู‘ู‡ู ุงู„ุฑูŽู‘ุญู’ู…ู†ู ุงู„ุฑูŽู‘ุญููŠู…ูู" Karfe 6:00pm agogon dake dakin ya nuna Alh Dan Maliki ne yace "Hajiya tashi mutafi na ga lokacin saukarsa yayi fa" tace "Toh" Daman tayi wanka, tashi tayi tashiga dakinta ta dauko hijabinta ta saka, ta fito tace "Alh na muna iya tafiya fa" yace "toh shikenn muje" Acan bangaren su Lami kuwa, Hjy Aisha ce tayi fir ta shafa wa idonta toka tace ai sam bazata je taro Mubarak ba, haka dai Alh Sani ya hakura badon ranshi yaso ba. Yazo zai fitane sukayi kicibus shida Rahila, yace "Lami daga ina haka cike da shagawaba tace wlh dady daga gidan k'awata nake, yai murmushi yace "Uwar yawo ke ko gajiya bakiyi da yawo koh?" Tace "Dady ina zaka yace yayanki ne ya dawo shine xamuje tarbarshi" Tace "Lah yaya Muby tana maganar tana washe baki" yace "Kwarai kuwa" (aiko wlh dady saina bika) 'acewar Lami' Yace "Daman neman yar rakiya nake uwarki taki rakani toh ke zo mutafi." Futowa sukayi yayi inda suka tarar da Dan Maliki harsun fito daman su kawai ake jira, suna karasawa ta durk'usa har kasa ta gaida Dan Maliki sannan ta juya ta gaida Ammi ciki-ciki, shidai baisan me yasa ba har ga ALLAH yana bala'in son yarinyar. Driver ne ya tada motar suka fice daga harabar gidan Sannu a hankali yake tuki, Lami ji tayi tafara kosawa da tafiyar, jitake tamkar ta rufe idonta ta bude ta ganta a filin jirgin, amman ina saida suka dau akalla kusan 40mins sannan suka iso filin jirgin, suna yin parking jirginsu Mubarak na dira a Nigeria. Fitowa sukayi gaba dayansu suka tsura wa jirgin idanu dan ganin ta ina Mubarak din zai fito, wani hadden gaye ne ya kunno kai sanye cikin riga T~shirt white in color da wando jeans Black sunyi masa masifar kyau ai Lami kasa rufe bakinta tayi sbd ganinshi tayi tamkar bature, shiko yana hango su Ammi ya jefar da trollyn dake hannunsa ya rugo da gudu ya rungume Ammi, sannan ya rungume dadi ya koma kan Small Dady shima ya rungumeshi, ai itama Lami sai ta ware hannayenta a tunaninta itama zai rungumeta, hmmm sai taji wayan jin shiru data yine yasa ta bude idonta a hankali, abinda ta gani shiya bata mamaki, bakomai tagani ba face duk sunbar wajen Suna kokarin shiga mota, sai Malam Musa kawai daya je ya dauko trolley din Mubarak yana janta dan ya karasa inda motarsu take. Wani bakin ciki taji ya turnuke ta, ji tayi duk wani farinciki na ta ya gushe ya koma bakin ciki, haka itama ta doshi motar rai bace kamar wadda aka aikowa sakon mutuwa, tana karasawa Alh Dan Maliki yace Yadai daughter na waya tab'a mani ke? Tace cike da shagwaba kamr zatayi kuka "ba ku bane kuka tafi kuka barni ba" Dan Maliki yqce "Eyyah yi hkr my daughter kinga shi bak'one ai shiyasa kekuma yar gida ce" ya kwantar da ita akan cinyarshi, yana mai lallashinta. Mubarak ya kasance irin mutanen ne da akecewa "Giant" ga tsayi ga jiki, farine sol, sannan ga kwantataciyar sumarsa kamr balarabe Masha ALLAH, duk kyan da Lami take dashi indai suka hadu sai kaga tazama wata mummuna da ita. Wannan kenan,,,,,,,,,,,,,, Bayan sun isa gidane kowa yayi part dinsa, Mubarak bai zame koh inaba sai daning table, ita kuma Ammi ta wuce kitchen don dauko masu abincin. Mubarak ne ya fara magana "Ammi wlh yunwa nakeji kamar ta kasheni fa, kuma naga kinki kawo abincin da wuri" Ammi tace "Matsalata dakai wlh dan wutar cikine, ganinan zuwa" shidai Dady ba abinda yake sai dariya, Ammi ce dauke da tray bata zame ko ina ba sai gaban Mubarakn wanda a halin yanzu ko gabansa baya gani sbd yunwar dayake ji, bude cooler din tayi wani kamshi ne ya doki ancinsa yayi saurin kallon inda Ammin take yana murmushin farin ciki yau shekarar sa biyar kenn rabon dayaci daddan girkin Ammin sa, Tuwon shinka fane miyar egusi da bushashshen kifi, ai Ammi ta cika da mamaki sbd irin abincin da mubarak yaci, dan saida ya share mal-mala uku, sannan yayi hamdala ya jawo ruwa ya wanke hannunsa, Ammi ta zuba masa ruwa mai sanyi ya sha, Tace "toh yanzu tunda kaci abinci ka koshi sai kaje dakinka ka kwanta ka huta kaji son?" Yace "ohk Ammi" Tashi yayi ya bar falon inda Dan maliki da Hjy hafsat suka ci gaba da firarsu abunsu cike da murna, inda anan ne Dan maliki yake sanarwa da hajiya maganr auren Mubarak da Lami nan da 1month, Ammi ta nuna rashin amincewarta amman bata da yanda ta iya sbd sani halin Mijin nata wajen kafiya da taurin kai, indai yace sai yayi abu toh babu shakka sai yayi shi sanin haka ne yasa ta hakura, Tace "Toh ALLAH ya saka hakan shine mafi alheri ALLAH kuma ya basu zaman lpa" Yace "Ameen Summa Ameen daman haka nakeson ji daga gareki fa ALLAH yayi maki Albarka" Acan bangaren Alh Sani kuwa rigima ce ake sha shida Hjy Aisha inda tace wlh baza sab'uba bindiga a ruwa ba, ita sam 'yarta baza auri Muby ba, Alh ne ya fara magana kamr haka: "Ita lami dince ta fada maki batason shi?" Ta kada kai alamr a'a yace "toh kiramani ita lamin inji daga bakinta" tace "Toh" ta fice ta doshi dakin Lami Tana shiga ta isketa a kance ta lumshe idanunta tana kallon sama tace "Ke Alh yana son ganinki akan maganar Yaronnan Mubarak ko yace kina sonshi kice bakison shi kinji koh" Ba kunya ba tsoro lami tace "Nidai wlh momy inasonshi hasalima ban taba jin son wani d'a namiji ba face shi pls momy kiyi hakuri kinyarda na auteshi dan idan ban aureshiba mutuwa zanyi" Momy cikin Bacin rai tace "To ki mutu ma mana ai wlh akan wannan yaron koh zamu bata dake" tayi gaba ta barta ana zaune kan bed din, Koh da taje kiran da dadi yake mata taji abunda ya fada mata, ba karamin dadi taji, nan take ta amince. A bangaren Mubarak dai sam abun baiyi masa dadi ba Amman sbd yasan ilar bijire wa umarnin iyaye shiyasa ya amince Amman har ga ALLAH bawai dan ranshi yaso ba. Dan maliki yaji dadin hakan duk da ya fuskanci Mubarak bayason Lami amman ya hkr. Rana bata k'arya saidai uwar d'iya taji kunya "Inji hausawa" a yaune 30/4/2019 dubban mutane suka shaida daurin auren Mubarak (Muby) da Amaryarsa Rahila (Lami). Dan Maliki da Ammi sunyi masu nasiha, inda shima Alh sani ya dora amman momy ko tari bata yi ba kasancewar batayi maraba ba da auren ba. Zo kaga rawar kai wajen amarya, anyi duk wani abunda ya dace ayiwa amarya da ango Dan maliki shi yayi komai baiyarda Alh sani yayi ko tsinke ba. Suma a cikin gidan aka yanka akayi masu tafkeken gini naji da gani coz duk yafi nasu k'awatuwa. Hakadai suka share *2weeks* ammi tana kawo masu abinci, daganan Mubarak yace ta daina haka, Tun daga kan girki suka fara fad'a kasancewarta kwata-kwata bata iyaba sun sha rigima inda har takaisu ga garzayawa wajen Dan maliki, inda ya yanke shawarar cewa za'a d'auko yar aiki kafin ta koya itama, a hakane maganr ta mutu. Bayan wani dan lokaci Dan maliki ya kwanta rashin lpa mai tsanani, anje kasashe da dama amman ina an rasa gane abunda yake damunsa, sbd haka yace da iyalansa su dawo dashi gida Nigeria, ba bata lokaci kuwa aka dawo dashi Nigeria, ALLAHU AKBAR ai a wnn dare yace ga garinku nan ya amsa kiran Mahalincinsa ya koma gidansa na gaskiya, Koda ammi ta ga mijin ta ya rasu abun alfaharin ta, ya rasu itama nan take zuciyar ta ta buga aiko nan take ta fadi kasa a matukar galabaice numfashinta yana sassarkewa, kasan cewar babu kowa a dakin ne ya yasa duk ihun datake babu mai yinta, haka ta kari ihunta mara sauti itama tace ga gartinkunn. Daya ke mubarak yana bangaren shi bai san abunda yake wakana ba, sai can daya ji shirun yayi yawa. Bude k'ofar dakin nasa yayi a hankali ya fito, ya doso dakin mahaifin nasa, zuciyarsa na dukan uku-uku ahaka dai ya tura kofar dakin ganin dakin babu haske ne yasa shi ya zura hannunsa ya dauko wayarsa inda ya kunna light din wayar, haskawar da zaiyi sai akan mahaifiyar sa wadda ke kwanshe shab'e-shabe a kasa tamkar mara numfashi, karasawa yayi da sauri gurinta ya fara jijjigata amman ina rai yayi halinsa, amman shi kwata-kwata bai fahimci hakan ba, ya koma kan Abba shima dai Haka baya ko motsi, Sbd haka ya yanke shawara yaje ya tada small dad, karasawa yayi part din nasu ya fara bubbuga kofar da karfin tsiya tamkar wanda zai balla kofar dakin, Jin bugun kofar yayi yawa ne yasa small dad farkawa ya kalli agogon dake manne a dakin yaga *02:00am* tashi yayi ya jura jallabiyarsa ya fito don gani waye wnn cikin tsohon daren nn yake buga masu kofar gida haka, Kafin ya bude motar tasa saida ya fara tambaya yace "waye ne?" Daga can bangaren akace "Mubarak ne dady" Yace "mai ya faru ne lapia dau koh?" Yace "small dad dan Allah zo kagani wlh ammi da dady ne sunki tashi fa" Bai gama rufe bakinsa ba Small dada ya bude kofar part din nasu ya biyo bayansa, koda ya shiga dakin yan dube dube yayi sannan ya daga wayarsa ya kira family Dr, dinsu fada masa yayi cewa yanzu zai zo. Shidai Mubarak kasa zama yayi sai safa da marwa yakeyi yakasa zaune ya kasa tsaye............ *Abubakar Saleh Al~Quyraemey* _(young writer)_ https://m.facebook.com/Zamaniwritesassociation? ๏ปฟ *DUK GIRMAN GONA!!!* _{Akwai kunyar 'karshe}_ ยฉ2019 *A mystery story just keep on following me.* ๐Ÿ‘จ๐Ÿปโ€๐Ÿ’ป๐Ÿ‘ฉ๐Ÿปโ€๐Ÿ’ป *ZAMANI WRITERS ASSOCIATION* _____________________________________ โ€‹โ€‹Wษ› ษ‘ส€ษ› ษฆษ›ส€ษ› tัณ ษ›ษ—ucษ‘tษ›, Mัณtiัตษ‘tษ› ษ‘ษณษ— ษ›ษณtษ›ส€tษ‘iษณ ัณuส€ ส€ษ›ษ‘ษ—ษ›ส€เธฃโ€‹. _____________________________________ *๐Ÿ‘‰๐ŸผPage 15-16* *Author.......๐Ÿ–‹* *Abubakar Saleh Quyraemey* ```@Facebook Abubakar Saleh AlQuyraemey``` *DEDICATED TO* *MUTAN KATSINA STATE HADI DA XAMFARA* *YA ALLAH INA ROKONKA DA SUNAYEN KYAWAWA DA SUFFOFIN TSARKAKA DUK MASU HANNU AKAN ABUBUWAN DAKE FARUWA A KATSINA DA ZAMFARA ALLAH KA SHIRYASU IDAN KUMA BAZASU SHIRYU BA TO ALLAH KA KAWAR MANA DASU ALLAH KA JIKAN 'YAN UWA MUSULMAI DA SUKA RASU A WANNAN RIKE-RIKE ALLAH KA KAWO MANA KARSHEN WANNAN BALA'IN DAYA TUN KAROMU AMEEN YA HAYYU YA QAYYUMU* ุจูุณู’ู€ู€ู€ู€ู€ู€ู€ู€ู€ู€ู€ู€ู€ู€ู€ู€ู€ู€ู€ู€ู€ู€ู…ู ุงูŽู„ู„ู‘ู‡ู ุงู„ุฑูŽู‘ุญู’ู…ู†ู ุงู„ุฑูŽู‘ุญููŠู…ูู" ............Can kuma bangaren Dr Muhsin futowa yayi hankalinsa a tashe sbd Dan maliki tamkar uba yake a gareshi, bayan ya dauko key din motarsa ya fito yana cikin tafiya sai kawai yaga police a gabansa, ba shiri ya nemi birki sa ya take ya tsaya, karasowa sukayi gab da motar tasa suka shiga yi masa tambayoyi, shi kuma yana amsawa, bayan sun gama mashi yan tambayoyi sai daya daga cikin yan sandan yace kai nifa wlh banma yarda dakai ba kilama kai dan fashine, Ya fahimci inda suka dosa cin hqnci ne kawai suke nema ya basu ganin zasu bata mashi lokaci yasa ya zaro dubu biyar daga aljihun sa ya ware dubu biyu zai basu sauran kuma zai maidasu aljihunsa, amman caraf yaji an rike masa hannu dubawar da zaiyi sai yaga wnanna dan sandan ne, Dr muhsin yace "yallabai ya haka? Yayi masa tambayar yana kokarin kwace hannunsa amman ya kasa kadancewar dan sandan akwai energy, sbd haka ba yanda ya iya haka ya hakura ya bar masu kudin gaba daya ya shige motarsa domin karasawa gidan dan maliki. *ANGUWAR G.R.A KANO* Kasan cewar anguwar manya mutanece kai kace da rana ne sbd security light da suka haskaka kafatanin anguwar wani tankamemen gida ya dosa inda ya fara jera horn ba kakkautawa, karar horn dince ta tada mai gadi a firgice yana dube-dube tamkar wanda yayi wni mugun mafarki jin horn din ba kakautawa ne yasashi fitowa rike da kokara (sanda) rike a hannunsa, karasowa bakin kofar yayi amman ya kasa bude kofar sbd fargabar wanda zai gani koh mugajene, inbude koh kar in bude 'haka zucviyarsa take ta fada masa' kawai sai ya dora hannunsa a bisa kofar da niyyar budewa wani wawan tsalle yayi ya fadi kasa saka makon wani horn din dayaji an yi wannan horn din ba dan ladi ba har su Alh sani saida saida suka jiyoshi sbd hakane ya fito da sauri don yasan mai wannan horn din fitowar da zaiyi me zai gani ai dan ladi mai gadi ya gani kwance yanata rawar sanyi abun ban dariya, yaso ya dara Amman ina ba dama kasancewar shi dimauceyake karasawa yayi bakin kofar zai bude dan ladi ya runtumo da mugun gudu yace "Alh wlh karka bude yan fashi ne suka kawo mana ziyara" Alh sani ya dubeshi yace "kai Dr ne fa kuma nina kirashi shi ya karasa maganar yana kokarin bude kofar, yana budewa kuwa yayi arba da motar Dr muhsin, Dr muhsin ya fito da sauri yace "Alh yamai jiki" Shigo da sauri dan ALLAH acewar Alh

Chapter 3 of 5