masa albashin sa ijuwa naira dubu dari bakwai {700,000}, duk wata sannan aka bashi mota da kuma gida kasan cewar haka ka'idar take.
Zaune yake a gaban ancle din nasa yana fada masa tagomashin daya samu a wajen aiki da kuma daukakar dayake samu, ancle din nasa ya fara magana kamar haka: "to yanzu abunda ya rage maka shine kayi aure Abbas kaima naga zuri'ar ka, kaga ka girma yanzu kusan 35yrs kaga ko ai kai ba yaro bane yaka mata kaima ace ka samu wadanda zasu rinka yi maka hidima" yace toh ancle in sha Allahu zanyi kwanan nan ma, yace toh ai shikenn Allah ya nuna mana ace Ameen cike da kunya kasancewar sa daman akwai kunya. Ana cikin haka saiga momy ta fito daga daki tanemi kujera 3sitter ta xauna, tace "wai alhaji mai ke gudanane kaida dannaka" alhaji yace "maganar aure ce mana nake masa ace ya girma amman yaki aure anya rayuwa tayuwu a haka kuwa", momy tayi murmushin jindadi domin kayanta ya kwance a gindin kaba ga damanan tasamu, tace "Alhaji ai komai lokacine kila zainab yake jira ne ta kammala exam dinta, dan inba hakaba ni bantaba ganinshi da budurwa ba," Alhaji yace "aiko danafi kowa jin dadi wlh kinga ni zanyi lefe kuma ni zanyi kayan daki," ya karkato da kallonsa ga Abbas wanda duk maganganun dasuke kansa na kasa sbd tsabar kunyarsu dayake ji, ya dago da kansa yayi dan mirmushinsa wand ya saba yace "Ancle ai ba wai zainab ba koma wacece kace na aura wlh bazan tsallake umarninka ba, sbd kagama min komai a rayuwata." Alhaji yace "a'a idan kana da wadda kakeso kayi mani magana ni kuma ko 'yar gidan wanene insha Allahu zan tsaya maka," Abbas yace "ni banida kowa," tun dazu sai yanzu momy tasa baki tace "a'a Abbas wlh bawai tirsasaka zamuyi ba idan kana da wadda kakeso kawai kasanar damu ba matsala duk da harga Allah momy bataso fadin maganar ba amman bata dayanda zatayi, yace "a'a momy zabinku ai nima shine nawa," aikuwa yana fadar haka momy ta sauke wata nauyayyar aziyar zuciya. Har ga Allah tanayi wa yar tata sha'aawar samun miji kamar Abbas sbd nutsuwarsa, hankalinsa, kyawunsa, da tsabtarsa ga fara'a kamr gonar auduga amman fa ga wanda ya sani, wannan halayenne yasa momy takeyi wa diyarta fatan samun miji kamar Abbas.
2 days later da yin magana tskanin Ancle da Abbas, ancle yayi wa Abbas waya yace zasu je katsina ziyara zuwa wajen wani abokin sa inda yake sanar dashi cewa kwana biyu zasuyi su dawo, amman bazasu je da Zainab ba sbd sun fara waec shiyasa bazasu je da ita ba amman za'a tafi da kanin ta, Ancle yaci gaba da cewa "da zarar mundawo kuma za'a sanya ranar bikinku ba wani lokaci mai tsawo xamusaka ba," nan dai Abbas yayi masa godiya ya katse kiran. Sun fito zasu tafi ne Zainab ta fito tana kallon su, tace "wlh Momy ji nake tamkar idan kuka tafi kun tafi kenn bazaku dawo ba," mahaifiyarta ta kalleta tayi murmushi duk da itama jikinta yayi matukar sanyi da jin wagga batu tace "kiyi hakuri in sha Allahu zamu dawo lapia kedai kiyi mana addu'a kawai kuma ki kula da kanki kiyi karatu banda shashanci", tace "to umma Allah ya dawo daku lpa." Yayin da Momynta ta bita da wani kallo irin na bankwana. Tana kallon su dai suka ja mota suka fice daga cikin harabar gidan, ita kuma ta fashe da kuka yayin data durkushe a kasa tana kuka mai tsuma zuciya, gwanin ban tausayi.......
*Abubakar saleh Al~Quyraemey*
_{Young Writer}_
[6:19AM, 6/7/2019] Abue Saleh Al~Quyraemey: https://m.facebook.com/Zamaniwritesassociation
*DUK GIRMAN GONA*
_{Akwai kunyar 'karshe}_
©2019
👨🏻💻👩🏻💻
*ZAMANI WRITERS ASSOCIATION*
_____________________________________
Wɛ ɑʀɛ ɦɛʀɛ tѳ ɛɗucɑtɛ, Mѳtiѵɑtɛ ɑɳɗ ɛɳtɛʀtɑiɳ ѳuʀ ʀɛɑɗɛʀร.
_____________________________________
*👉Page 7-8*
*Author.......🖋*
*Abubakar Saleh Quyraemey*
```@Facebook Abubakar Saleh AlQuyraemey```
*DEDICATED TO*
*Zamani Writers Association Group*
*Bismillahir rahamanir rahim*
Tana cikin kukan nanne taji gabanta yana mata dukan uku-uku tamkar zuciyarta zata fito, tarasa meke shirin faruwa da ita kawai sai ta fara fadar:
"Innalilahi Wa inna ilaihirraji'un acikin zuciyar ta"
Aiko bata jimaba bacci barawo ya dauketa. Can cikin baccin ta tajiyo ringing din wayar ta, ta bude idanunta da kyar ta mika hannunta kan table din dake gefen bed dinta, tayi duba izuwa kan screen din wayar taga Sunnan Abban tane ke yawo tayi saurin dagawa da Sallama, an amsa sallamar amman abunda ya bata mamaki shine a madadin taji muryar Abban nata sai taji muryar wani daban, jitayi ance maza-maza kizo Asibitin Aminu kano Teaching Hospital yanzu-yanzu, jitayi kamar mafarki takeyi ta murza idanunta dan farkawa amman ina sai taga da gaskene bawai mafarki take ba sbd haka tace "Mai yafarune da Abban nawa ne? Kuma ina Momy na?"
"Yace kedai kiyi maza kizo muna nemanki Emergency site"
"Tace toh gani nan zuwa"
Kiran number Momy tashiga yi amman kashh! an sanar mata da cewa wayar data kira a halin yanzu a kashe take saboda haka ta hakura. Tashi tayi daga kan gadonta tunanunnuka nata mata yawo acikin nazarinta komai ya faru da Abbana? Da Umma, tayi shiru ganin bata da wanda zai bata wannan Amsar yasata shiga bandaki ta watsa ruwa a gurguje ta fito, tasaka wata atamfa England wax dinkin yayi mata kyau masha Allah, snn ta dakko zunbuleliyar Abayar ta tasaka ta saka flat shoe, sannan ta dauki hand bag dinta har takai bakin kofar fita daga gidan sai kuma tajuyo ta dawo, ta dauki phone dinta ta fito ta saka dan mukulli ta rufe gidan, tafara tafiya da d'an sauri domin ta karasa babban titi, tana karasawa kuwa tayi sa'a ta samu mai Adaidaita Sahu
"Tace mashi Aminu Kano Teaching Hospital zaka kaini"
"Yace toh shiga muje"
••••••••••••••••••••••••••••••••••••••••••••••••••••••••
Abbas na zaune haka kawai yau yatashi jikinsa ba kwari dukda yasan lapiar sa kalau amman jiyake jikinsa ba kwari, haka dai yaci gaba da yan rubuce-rubucen sa cikin karfin hali da jarumta, yana cikin wannan rubuce-rubucen ne yaji wayarsa ta soma ruru, ya daukota dan duba wake kiransa dubawar dazaiyi yaga number Ancle ce,
"Ya daga kiran cikin girmamawa da sallamar sa"
"Daga can bangaren yaji ance duk abinda kake ka bari kazo Aminu kano Teaching Hospital muna nemanka emergency room"
"koda yaji haka nan take jikinsa ya bashi ba lpa ba, yace ina Ancle din kuma, mai ya faru da shi?"
Daga can bangaren mai maganar yace "Kawai kazo koma menene kaji daga baya"
"Yace ohk toh ganinan zuwa"
Tashi yayi jiki ba kwari ji yake kamar bazai iya taka kasa ba sbd kasalar dayakeji a jikinsa, futowa yayi daga offishin sa wani offishin ya shiga wanda yake gaf danasa, ya tura kofa da sallama a bakinsa,
Aka amsa sallamar tasa hadi da cewa "come in"
Shiga yayi ya tsaya a tsaye yace "Barka da aiki Ranka ya dade"
Mutumin yace "Have a sit mana Abbas"
Abbas yace "Ba zama nazo ba wlh kiran gaggawa akayi mani daga Asibin Malam Aminu Kano wai duk abinda nake nabarshi nazo yanzu-yanzu nan shine nazo na sanar dakai"
Mutumin yace "Ohk ba matsala Allah ya tsare"
Abbas yace "Ameen thumma Ameen"
Ya juya ya fice daga offishin cike da tunanunnuka, karasawa yayi park space na kamfanin ya sa key ya bude motarshi ya fice daga harabar asibitin ya doshi Asibitin Malam Aminu Kano.
*AMINU KANO TEACHING HOSPITAL {AKTH}*
Tana can tana tunani taji mai Adaidaita yana cewa "Malam munzo fa"
Firgigit tayi tadawo daga duniyar tunanin datakeyi, ta bude jakarta ta bashi kudinsa ta fice ta shiga harabar Asibitin ta doshi Emergency site kasancewar kana shiga Asibitin zakaga indicated board ma'ana Allon dake dauke da taswirar asibitin, wani Dr ta hango ya fito daga emergency room din tayi, aiko da d'an gudu ta hada kada ya bace mata ta karasa tana dan haki
"Tace yauwa Dr nice wadda aka kira dazu akace nazo nan asibitin"
"Yace kece zainab Abdullahi?"
"Tace eh nicee"
"Yace mata toh zomuje"
Inda ya fito nan ya nufa, itama tabishi a baya suna shiga ciki ta kame saka makon abunda ta gani, ba wani abu tagani ba face Abba a kwance koh motsi bayayi ansa masa oxygen a hancinsa
Juyowa tayi a fusace ta shagi Dr tace "mai kukayi wa Abbana! Mai kukayimasa........." Ta fashe da kuka
Ana cikin haka ne shima Abbas ya shigo dakin ganin abinda yake faruwa ne yasashi saurin karasawa gurin da zainab take ita da Dr yana fadin lpa meyake faruwa zainab?
Ganin dayayi tana kuka yasa ya rikice ya juya akalar tambayrsa ga Dr yace "Mai ya farune likita?"
Likitan bai iya ce masa komai ba sbd muguwar sha'ka dayaji, duk da yake namijine amman ya gagara kwacewa daga hannun Zainab, idanunnan sunyi jajir kamr gauta, ganin da Abbas yayi likitan ya fara tarine yasa yaje ya fincikeshi daga hannun Zainab din aikuwa yayi maza ya jingina da bango yana haki sbd tsabar sha'ka dayaji, ita kuma Zainab ta karasa gurin Abba da gudu tana fadin "Mai sukayi maka Abba tana jijjigashi?"
Sai a sannan hankalin Abbas yakai ga inda Abba yake a kwance shima ya karasa cikin mutuwar jiki, koda yaga irin halin da Abba yake ciki, shima sai zuciyarshi ta karaya ya fara zubar da hawaye, suna cikin wannan halinne wani likitan ya shigo ya karaso wurn dasuke yace masu kuzo muje office nayi maku bayani.
Haka suka bi bayan wannan likitan badan ransu yasoba amman babu yanda suka iya, suna shiga office din ya nuna masu wasu kujeru guda biyu masu facing din juna "Yace have a sit" suka zauna suna mai zura masa idanu danji abinda zai fada masu dukda har a snn basu daina zubar da hawaye ba.
Dr ya nisa yace "Dazu aka bugo mana waya cewa mukawo agajin gaggawa, wata mota mai kirar fijo 406 tayi taho mugama da wta tirelar daukar kaya kafin akai Bichi, inda bamu bata lokaciba muka tada ma'aikatan mu sukaje wurin saidai koda sukaje masu tirelar sun gudu sun bar motarsu ita kuma 406 din mutum biyune suka mutu wani karamin yaro da kuma babba mace...." Ai kafin Dr ya karasa maganrshi saiji sukayi Zainab tayi wata kara ta kife a kasa ko motsi bata yi.
Nan fa hankalin Abbas yayi kololuwar tashi ya mike tsaye shima yaji kafafunsa sun kasa daukar gangar jikinsa sai ya fara fadar:
"Ina lillahi Wa innah Ilaihirraji'un"
Bashiri ya zauna kan kujerar yayin da likitan ya tashi daga kan kujersa ya kira wasu nurses su biyu suka dauki zainab suka fice da ita izuwa emergency room, domin cetoh rayuwar ta.
Ya dan samu nutsuwa saboda hailalar daya dinga yi sbd haka yace da Dr "Shifa Ancle"
Likitan yace "Shi ya bugune a kansa inda kansa ya tabuwa amman banda nan babu wani rauni a kansa, gobe xamu yimasa aiki insha Allahu"
Abbas yace "toh Allah ya kaimu" likitan yace "Ameen dai"
Zanci gaba Insha Allahu.
A mystery story just keep on following me.
*Abubakar Saleh Al~Quyraemey*
_(young writer)_
[6:19AM, 6/7/2019] Abue Saleh Al~Quyraemey: https://m.facebook.com/Zamaniwritesassociation?
*DUK GIRMAN GONA!!!*
_{Akwai kunyar 'karshe}_
©2019
👨🏻💻👩🏻💻
*ZAMANI WRITERS ASSOCIATION*
_____________________________________
Wɛ ɑʀɛ ɦɛʀɛ tѳ ɛɗucɑtɛ, Mѳtiѵɑtɛ ɑɳɗ ɛɳtɛʀtɑiɳ ѳuʀ ʀɛɑɗɛʀร.
_____________________________________
*Page 9-10*
*Author.......🖋*
*Abubakar Saleh Quyraemey*
```@Facebook Abubakar Saleh AlQuyraemey```
*DEDICATED TO*
*Zamani Writers Association Group*
*Bismillahir Rahamanir Rahim*
: بِسْــــــــــــــــــــــمِ اَللّهِ الرَّحْمنِ الرَّحِيمِِ"
يَا أَيُّهَا الَّذِينَ آمَنُوا إِذَا نُودِيَ لِلصَّلَاةِ مِن يَوْمِ الْجُمُعَةِ فَاسْعَوْا إِلَىٰ ذِكْرِ اللَّهِ وَذَرُوا الْبَيْعَ ۚ ذَٰلِكُمْ خَيْرٌ لَّكُمْ إِن كُنتُمْ تَعْلَمُون
Alhamdulilah today is another beautiful day. Haza yaumul akbar; yaumul shukur, yaumul salama! Alhamdulillahi ala ni'matil Islam. May Allah shower His endless blessings upon U my fan's & Ur family.
Jumu'at Mubarak
.........Fita sukayi daga office din, koda suka fice basu zame koh ina ba sai emergency room inda Zainab take kwance bata koh motsi tamkar gawa, kusan a k'alla likitoci biyar ne a kanta, amman ankasa shawo kanta, sundau lokaci mai tsawo Allah cikin ikonsa, taja wani gauron numfashi aiko ba karamin dadi Abbas yajiba, kasancewar duk abunda yake gudana yana kallonsu ta mirror din dake dakin, ya samu wuri ya zauna yayi "Hamdala Ga Allah Subhanahu Wata'ala" ya samu wuri ya xauna.
Koda ya dan jima a zaune sai kuma ya wani xabura yayi dakin da Ancle yake jinya, shigarsa keda wuya kuwa yayi dai-dai da farkawar da Ancle yayi daman allurar bacci sukayi masa, kuma yanxu ta sakesa, saboda haka Abbas ya karasa gurin Ancle da sauri yana mai cewa "Ancle ya jikin naka?" da k'yar ya bude bakinsa yace "Abbas ina kanwarka?" Abbas yace "Ancle tana can itama ba lpa sakamakon ganinka da tayi a wannan hali" Ancle yace "Toh ka saurareni kaji abinda zan fada maka ga kanwarka nan ka riketa amana ina ji a jikina cewa bazan tashi daga wannan kwanciyar ba shiyasa nakeso tun kafin lokacina ya kure nakeso na baka wasiyyata, ko bayan babu raina karkuyi jinkiri wajen aurenku, kaje can Funtua wajen Kanin mahaifinku Alh Lawal ya zama maka waliyyi, ita kuma Zainab k'anina Shehu ya zama mata waliyi dan Allah ka bata hakuri ka lallasheta, ka tarairayeta kaga har yanxu ba wata babba bace...... yana zuwa nn a zance sa tari ya sarkafeshi ya fara aman jini da sauri Abbas ya tashi yana kiran Doctor! Doctor!.......... Amman ina kafin su dawo ai tuni rai yayi halinsa.
Abbas ne ya shiga office din likitan bako sallama yace "Dr yafa farka kuma yanata aman jini"
Dr yace "Subhanallahi" ya dauko stethoscope yace "Muje na gani"
Karasawa dakin sukayi inda Dr yayi 'yan gwaje-gwajensa, ya juyo dubansa izuwa Abbas yace Malam Abbas saidai hakuri amman abbanku shima ALLAH yayi mashi cikawa.
Ai Abbas jin maganr yayi kamar a mafarki, ya juyo a fusace ya shaki kwalar Dr yace cikin k'araji "Ya akayi kuka barshi ya mutu, meyasa! Meyasa!!"......... Sai kuma ya fashe da kuka ya durkushe a kasa bisa gwiywoyinsa ya fashe wani marayan kuka mai tsuma zuciyar mai saurarenshi.
Tasowa Dr yayi ya karaso inda Abbas yake yace "Hakuri zakayi sbd Wanda ya fimu sansa shine ya karbeshi mu yanzu abunda yafi dacewa mu shine muyi masa Addu'a amman ba kuka ba"
Wannan magana da Dr yayi wa Abbas ce tasahi ya tsagaita da kukan dayake amman har yanzu hawaye suna shatata bisa kan kyakykyawan kuncinsa, ya mike tsaye yama rasa ina zai sa kansa yaji dadi, sbd da haka ya bar dakin ya fito ya samu wata bishiya ya zauna a karkashi ta, yana mai tunano rayuwar dasukayi shida Ancle dinsa da iyalansa, rayuwa ce mai cike da so da k'auna gwanin bansha'awa, dan idan ba fada maka akayiba zaba kace ba dan gidan bane sbd yanda Ancle din nasa yake matukar ji dashi, amman duk da haka bai bashi damar ya sangarce ba, haka abun yake a 'bangaren Momy itama tana iya kokarinta na ganin ta ba Abbas tarbiyya tamkar 'ya'yan data haifa a cikinta, Abbas yana cikin wnn tunani ne yaji an dafa kafadarshi ya dago a razane!
Dr yagani tsaye kyam a gabanshi, Dr "Yace da Abbas angama saka gawarwakin acikin mota kawai kai ake jira"
Abbas bai tanka mashiba, shima Dr bai damuba yana gama fada mashi ya kara gaba izuwa inda ake ajiye motoci ya shiga cikin wata Ambulance yana jiran karasowar Abbas.
Abbas dai yaga ba wani sarki sai Allah haka ya tashi jiki ba karfi ya karasa inda wnn ambulance din take ya jagaya gaban motar yace wa da Dr "ina zainab koh a nan zamu barta"
Dr yace "Eh zatafi samun kulawa a nan kawai shiyasa bamu sallameta ba amman jikin nata" "Alhamdll".
Abbas yace "Toh shikenn" ya bude gaban motarshi ya zauna mazaunin driver, koda Dr Hashim yaga abunda Abbas yake shirinyi, sai yayi sauri ya fito daga ambulance dinn yace da driver "Ka biyo mu a baya" kawai abinda ya fada masa kenn ya fice ya karasa inda Abbas ke kokarin tada motarshi.
"Yace Mal. Abbas dan bude mani motar mana"
Abbas ya bude masa ba tare yace uffan ba, Dr Hashim ya zauna, Abbas kuma ya tada mota yana tuki snnu a hankali har Allah ya kawosu kurna masallaci wnda annan gidan Ancle yake.
Lokacin da suka kaso layin Abbas yasha mamaki sbd cikar da layin yayi ba masaka tsinke da kyar suka iya karasawa kofar gidan mutane suka taimaka aka fito da gawarwakin aka shiga dasu cikin gidan domin yi masu wanka.
Abbas bai kara cika da mamaki ba saida ya shiga gidan yaga mahaifiyarsa da 'yan uwanta, da kuma 'yann uwan momy anata koke-koke wasu kuma wadanda suka san abinda suke suna ta yi masu addu'a wanda dama haka Annabinmu, Annabi Muhammad S.A.W ya koyar damu.
Abbas dai shigowa yayi cikin gidan sbd kidimewa da rudewa da yayi baya ganin ko gabansa, Ummanshi tana tayi mashi magana amman ina baimasan tanayi ba, ya wuce izuwa dakinsa ya fada kan gadonsa ya limshe idanu jiyayi wasu hawaye masu zafi suna zubo masa akan kumatunsa bai damu daya sharesu ba, yana cikin wannan haline yaji Ummansa tana cewa "Abbas ance kafito kayi masu sallama za'a wuce dasu"
Tashi yayi da kyar yaje inda akayi wasu Momy da Ancle sutura yayi masu Addu'a sannan aka fita d gawarwakin nasu waje domin a sallacesu.
Babban limamin masallacin juma'a ne ya sallaci Mamatan, inda bayan angama sallar ne, dangin mamatan suka rushe da kuka harda masu na shiga uku na Lalace.
Wani dattijone datun d'azu suke shigi da fici daga wani d'aki zuwa tsakar gidan yace, "ya salam! Habadai Dan ALLAH, wannan kuka bashine zaidawo mana dasu duniyaba, amatsayinku Na musulmai wannan kururuwar da ihun bai kamacekuba, addu'ar ku suke buk'ata agareku amatsayinku Na 'yan uwansu, kukanmu bazai dawo mana dasuba, amma hak'urinmu da nutsuwarmu zaisa murok'a masu gafarar UBANGIJIN Al'arshi.
Dan ALLAH muyi hak'uri hakanan, ALLAH ya gafarta masu, yabamu hak'urin rashinsu.
Tunda dattijon yafara magana gidan yayi tsit, wannan nasiha tashi tayi tasirin saka kowa yin shiru, saidai shashshekar kukan wasu da ajiyar zuciya.
Ankai mamatan gidansu na gaskiya, inda kowa ya dawo yana alhinin mutuwar su, kasancewar Ancle mutum ne mai hakuri da kyauta, haka zalika matar shi Momy anata yabonta sbd ko leke ma baruwanta dashi balle Aliyu Haidar wanda kwata-kwata bazai wuce 5yrs ba, wnn dalilai yasa mutane suke kyautata masu zaton rahama. Bayan an dawone Abbas ya zauna kofar gidan yana kar'bar gaisuwa.
To saimuce ALLAH ya gafarta masu, da dukkan 'yan uwa musulmai dasuka rigamu gidan gsky.
*7days ago*
Ayau akayi addu'ar bakwai d'in Su Momy, Ancle Da kuma Aliyu Haidar, bayan lafawar komai kuma shak'ik'ansu Abbas suka had'a taro Na family.
Wanda a lokaci zainab ta dan warware sosai dan har an sallamota daga asibiti, Mal. Shehu ne Kanin Ancle shiya fara gabatar da sallama agaresu, yayi doguwar addu'a ga mamatqn, harmada sauran al'ummar musulmi dasuka rigamu gidan gaskiya.
Daga nan yaja dogon bayani akan gado da kuma biyama mamatan bashi da kar6o abinda sukebi, yaymusu nasiha da nusar dasu muhimmancin rik'e zuminci, da kuma addu'oi ga mahaifansu, yanda zasu rik'e maraicinsu harya amfanesu.
Daga nan kuma sai yayi magana akan wasiyyar daya bari na Auren Abbas da Zainab, duk mutanen dasuke wajen sunji dadin haka, amman duk cikinsu basu kai Umma farin ciki ba sbd bakinta kin rufuwa yayi don murna, haka dai taro ya wace cewa ranar 40 din su Ancle za'a daura auren Abbas da zainab. Sunso umma ta zauna, amman umma fur taki a cewarta "Mijinta yana can yana kewarta sbdn haka bazata xauna ba".
Rana bata k'arya yaune ranar 40 su Ancle kuma shine Ranar daurin auren Abbas da Zainab. Abbas yayi kokari dan har dubai sukaje shida Zainab din yayo mata lefe sannan ya shiyo mata furnitures, Mal. Shehu yaso shiyayi furnitures din amman Abbas ya hanashi yace "Shi zai yi mata komai" aiko nan Mal. Shehu ya fara samasa Albarka........
Bayan an kammala Addu'ar 40 dinne, dubban jama'a suka shaida daurin auren Abbas Mas'ud da Amaryarsa Zainab Abdullahi wanda ya samu halartar manyan yan kasuwa ciki kuwa harda Alh Liti Kulkul Mamallakin campanonuwa da gidajen mai masu inkiya da Liti Brothers.
An biya sadaki akan naira dubu dari 500 lakadan ba ajalan ba, inda abokan ango da yan uwansa suka rika tayashi murna, har dare yayi inda Umma ta tarasu tayi masu nasiha, bayan ta gama ne Mal. Shehu da Alh Lawl suka dora tasu nasihar.
*5 year ago*
Tafiya tayi tafi, lokaci yaja, shekaru sun fara lulawa, amman haryanzu Zainab ko bari batayiba hankalinta yayi matukar tashi, dan gani take kamr matsalar daga gareta ne, tq fara damun Abbas kan cewa suje asibiti, da yayi mata taurin kai amman daga baya ta shawo kansa ya yarda.
*Emirate hospital* Dake a Nasarawa G.R.A sukaje domin check up, likitan yayi dube-duben da zaiyi ya sanar dasu cewa "Babu mai matsala a cikinsu" duk da haka hankalin Zainab bai kwanta ba gani take kamar Abbas zai karo mata kishiya ita kuma har ga ALLAH ta tsani kishiya acikin gidan ta, Abbas ya fuskanci yanayin damuwar ta.
Sbd haka wata ranar week end suna zaune yana kallon TV, itama tayi kuri tana kallon TV amman a zahiri ba kallon take ba tana can ta luluk'a duniyar tunani, Abbas yace "Wai ni Zainab yaushe zamuje Funtua ne domin muyi ziyara?" Ji yayi tayi shiru batace komai ba, ya sake maimaitawa a karo na biyu kai har saida yayi maganar sau uku amman batasanma yanayi ba.
Takowa yayi har wajen datake zaune ya rungumeta tsam a jikinsa yace "Wai ni meke damunki ne sweetyn fada mani damuwarki naga two days dinnan kin rikice feye da da, bata boye masa komai ba tace wlh akan haihuwarnan ce, banason ka kawo mani kishiya wlh, yayi murmushi yace da gaske yace toh ai shikenn nikuma nayi maki wannan alkarin cewa "Da yardr ALLAH da Izininsa Bazan sake aure ba keda kishiya sai dai amakwafta fa sweety" Ba karamin dadi taji ba sbd wnn kalamai dadi mata sbd hak tace "Ina Alfahari dakai Habiby"
Tun daga wannan lokaci ta saki jikinta, yayin data ci gaba da harkokinta kamr da amman lokaci zuwa lokaci idan ta tuna cewa bata da d'a ballentana jika tana shiga damuwa kwarai da gaske.
Ana cikin hakane Abbas ya dawo da Albishirin cewa ya biya masu Aikin hajji shida ita dakuma umman sa, haka kuwa akayi inda ALLAH cikin ikonsa ranar tafiyarsu tayi Zainab tafi kowa murnar zuwan wannan rana, sbd haka sukaje Aminu kano Airport suka shiga jirgi ya garzaya dasu sai birnin jidda.
Bayan sunje ne Zainab ta jage damtse dare da rana Addu'ar Allah ya basu haihuwa suke, har lokacin dawowa gida yayi badan sunso ba suka dawo gida Nigeria ba.
*10 years ago*
Tun Hajiya Zainab tanasa ran cewa zata haihu hartafara fidda rai, toh shine fa ta bijiro da maganar cewa aje gidan marayu. Wannan shine asalin tarihin su.....
A mystery story just keep on following me.
*Abubakar Saleh Al~Quyraemey*
_(young writer)_
[6:19AM, 6/7/2019] Abue Saleh Al~Quyraemey: https://m.facebook.com/Zamaniwritesassociation?
*DUK GIRMAN GONA!!!*
_{Akwai kunyar 'karshe}_
©2019
*A mystery story just keep on following me.*
👨🏻💻👩🏻💻
*ZAMANI WRITERS ASSOCIATION*
_____________________________________
Wɛ ɑʀɛ ɦɛʀɛ tѳ ɛɗucɑtɛ, Mѳtiѵɑtɛ ɑɳɗ ɛɳtɛʀtɑiɳ ѳuʀ ʀɛɑɗɛʀร.
_____________________________________
*👉🏼Page 11-12*
*Author.......🖋*
*Abubakar Saleh Quyraemey*
```@Facebook Abubakar Saleh AlQuyraemey```
*DEDICATED TO*
*Zamani Writers Association Group*
: بِسْــــــــــــــــــــــمِ اَللّهِ الرَّحْمنِ الرَّحِيمِِ"
أَعُوذُ بِاللَّهِ مِنَ الشَّيْطَانِ الرَّجيـمِ
I seek refuge in Allah from Satan the outcast.
*WACE CE HAJIYA LAMI*
Lami dai shine sunanta na Gaskiya, ita kadai Allah yabawa Mahaifanta Alh Sani da Hajiya Hafsat, sbd haka ne suka d'auki son duniya suka dora mata, komai tayi daidai ne acewarsu basu da kamrta a wannan duniyar, wanda a sanadiyyar hakane ta taso da